Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
Wayar da Zuciyar Abdullahi yake Bugawa
Hafsah kuwa Lokacin da Kiran Umman Sadiq ya Shigo Tana kwance ne kan Doguwar kujerar Falonta ta kasa komai Tun Bayan Fitan Abdullahi Wayarma an Ci sa'a tana kusa da ita ta jawota ganin Umma ke kira yasa ta yunkura ta Mike Lokaci Daya tana Daga Kiran da sallama Umma ta amsa Hafsah ta gaisheta ita kuma ta amsa Tana Tambayanta Jikinta da kuma yata tace Jiki da Sauki kuma yara na makaranta.
Umma ta gyara zama Tana Fadin"Hafsah..Tambayarki Zanyi kuma ina so ki Fadamin gaskiya.."Hafsah tace"Insha Allahu Umma.."Ta gefen ido ta kalli Abdullahi Da Nazifi wadanda suka Sadda kai kasa Sun gama Sadakarwa yau sun gama Jin kunya da Girmansu suna karya.
Umman Sadiq tace"Wata mgana Mijinki Abdullahi Suka zo min Da ita Dashi da abokinsa Nazifi gasu Zaune agabana.."Gaban Hafsah ya Fadi acikin Ranta tace Shikena mgana ta Tabbata ammh Cikin yake da nuna bata san komai ba tace"Mganar me fa Umma..? Umma tace"yazo min da Zencen yana so ya kara Aure..kuma cikin gaggawa nan da Wata Daya ko Biyu Toh na Nuna Ban amince ba Saboda ke sai kuma ya Tabbatarmin da Saninki zai kara Auran kuma da yardanki Shin Hakane..?
Hafsah Taji mamaki ya kamata Wani Abu na Zuwa Daga karkashin Ranta tayi Shuru kawai Tana Jin Ruwan Hawaye na Taruwa acikin Idanuwanta Jin Shurunta yasa Umma ta kalli Abdullahi Cikin bacin Rai tana bamkamai Harara Cikin mamaki Sukaji Hafsah na Fadin"Eh Umma gaskiya ya Fada miki..Sai da ya gayamin na kuma amince Daman Don Allah karki Hanasa Tunda dai yana so Umma kuma Daman bazai Zauna Dani ni kadai ba Yana Da Damar da zai karo uku ma ba Daya ba Umma Tunda Allah ya bashi Dama.."Hafsah ta Karishe Fada Hawaye na Wanke mata Fuska ba Umma Sadiq kadai ba Hatta su Abdullahi jikinsu yayi Sanyi barin ma Abdullahi Daya ji Wata kunyar Hafsah ya kamashi Da kuma Wani karin Tsausayinta da Sonta.
Umman Sadiq tace"Shikenan Tunda kince Haka Daman gani nayi Hidima zatamai yawa.."Hafsah Tayi Mirmishin Dayafi kuka Ciwo tace"Bakomai Umma..Allah zai Rufa Asiri.."Umma tace"Shikenan Allah Shigemana gaba ke kuma Allah ya baki Juriya ki kwantar da Hankali kinga bake kadai bace..Allah ya Saukeki lafiya..Hafsah na Kokarin Sakin kukanta Take Fadin"Ameen Umma nagode...agaida su Zahra.."Ganin kukan nata na neman kwacewa yasa ta yanke Wayar da Sauri sai kuma Dukkansu Sunji alamun a kalaman Hafsah na karshe kuka take.
Ajiye wayar Umma tayi ta mike ko kara kallonsu batayi ba ta Fita Daga Dakin Tana Fita Nazifi ya Numfasa yana Fadin"Na Dade ina baka Shawara kan yadda zaka Tafiyar da gidanka ammh wannan karon ina Bayan Hafsah..wlh samun mata irinta sai ka Tona kuma ka Rubuta Wlh Wannan Barkat Din Daka kema Rawan Jiki bazata taba maka Hakuri da Biyayyah Hafsah gareka ba ballatana ta iya da Halinka na Saurin Fushi da Korafi ba.m."Wani kallo Abdullahi ya Sakarmai kawai kafin ya Dauke kai Shima Nazifin kai ya Dauke kawai yana kunkuni wai Abdullahi ya sakashi karya yana jinsa yayi mishi Banza.
Abinci Umman Sadiq ta kawo musu Sukaci suka Koshi kana suka Fita Sukaje sukayi Sallah bayan Sun Dawo suka gaisa da Mijin Umman Da abokiyar zamanta ko Su Zahra basu Jira Sun Dawo Daga makaranta ba Sukayi musu Sallama suka Dau Hanya Bayan sun Zube musu Tsaraban su Minti da Biskit,Umma kuma ta Bada Zuma mai kyau tace akaima Hafsah Garin alkama da Garin Konu kuma tace akaima Mama suka karba suna Godiya.
Koda suka Dawo Nazifi ya kawo Abdullahi gida bai Shiga ba.Ya wuce Abunsa Domin in garin Allah ya waye gobe yake son su koma Kaduna Abdullahi kuwa da kunya ya Shiga Gidan sai dai me Hafsah ta tarbeshi Sosai ta kokarta Tayi Girki Tayi Wanka taci kwalliya Ganinta Haka sai ya kaasa mgana Daya bata Tsaraban Umma Haka take Murna tana Tambayanshi ya suka Baro Su Umman Shidai kawai yake yake mata Duk Abun kuma sai ya Dameshi sai alokacin yake ganin Rashin kyautawarsa bai iya ce mata komai ba Har Washegari da Safe kalma Daya ya gayamata Lokacin Data Rakosu Shi da su Amira zai kai su makaranta Dagachan ya wuce Wajen aiki.
Ya kalleta yana Karban Karamar Jakarsa Dake Hannunta yace"Don Allah Hafsatuna kiyi Hakuri kinji..? Banso haka ba bani da wani ZABI NE don Allah ki yafemin kar Allah ya kamani Da Fushinki.."Mirmiahi Dayafi kuka Ciwo ta Sakarmai kafin tace"Waya gayamaka kayi laifin a wajen Hafsah..? Karka Damu...Ko ka gayamin ko baka gayamin ban isa in ja da Hukuncin Allah ba Abban Amira.."Kallonta yayi gani Hawaye sun Cikamata ido kai Tsaye yace"Ban gaya miki bane Saboda Bana so Hankalinki ya Tashi..Ga kuma Ciki Tare Dake ina Tsoron ki Shiga wani Hali.."
Dariya kawai Hafsah tayi kafin tace"Haba dai..Kamar ban yarda da Allah da kaddara ba..Kuma wacece ni da zan Hanaka Kara Abunda Allah ya Hallatarmaka..?Ban isa ba..Ina Fatan Allah ya kaimu Lokacin ya kuma Sanya alheri.."Tana Gama Fadar haka ta juya ta koma Daki Tana Share Hawayen Idanuwanta da kallon Tsausayi Abdullahi ya Bita yana Jin Hafsah ta gama Samun wani Wawakeken Fili acikin Zuciyarsa Jiki a Sanyaye ya Gungura mashin Din zuwa Waje ya Tada ya Hau,Amira ta Hau baya Amira kuma ya sakashi gaba suka Dau Hanya.
Kwana Biyu Tsakani Su Baba wada da Mijin goggo Habiba da Nazifi sukaje gidan Wan Babansu Salisu Dake Sabon gari chan suka iske Salisu Dayake yasan da Zuwansu sun Samu Tarba Sosai Sunci sunsha kafin su gabatar da Abunda ya kawosu ganin sunce suna Shiryeni basu son Jeka ka Dawo yasa nan da nan aka Fadi Sadaki da Dukiyar Aure baba wada ya zaro ya Bada Duka 150k Sdaki da Dukiyar Aure suka kama sun Gabatar da kayan sa Ranarsu suka kuma Bukaci Saka Ranar kar ya Dau Lokaci kamar yadda Abdullahi yace toh anyi dai komai Cikin Girma an saka Ranar Kwana 50 cif masu zuwa da Wannan albishir din suka koma ma Abdullahi Duk da bai so Haka ba bai da yarda zai yi Hakanan ya Hakura Shi ya ma Kira Barkat din ya gayamata sai ta mai na yan Duniya zuwan bata sani ba Nan kuwa Daganan Sabon garin Salisu gida ya wuce ya gayama Hajiya Amina komai ya kuma kai mata Sadakin a Hannunta Shine Bahiya da Bahijjat suka Kirata suna Ihun Murna Suka gayamata Bahiya tana Makaranta ammh Tunda Taji Labari ta Gudo ta bar Barkat din achan tace gida zata koma ta kwana.
Bangaren Su Zannira da Subai"atu kuwa Abakin Mariya sukaji labari Subai Zannira kuma Bakin Jidda Data je Gidanta Take gayamata Sunyi mamaki kwarai ainin Barin ma Subai washegari sai gata Gidan Mama Tana Tambayaa Mama tace kwarai an saka Rana Daganan Subai bata Tsaya ba sai gidan Hafsah ta Isketa Sai karfin Hali Domin Duk Ta Rame ganin Subai sai Rauninta ya Bayyana ta Fada Jikinta tana kuka Subai tana lallashinta Sai da tayi ya isheta kana tayi Shuru.
Subai ta kalleta tana Fadin"Kinga yadda kika Rame kuwa... ?;badai mganar Auran ya Abdullahi ne zai saka Kije ki kashe kanki ba..Kinga yadda kafafuwanki suka kumbura kuwa.."?Hafsah ta Kada kai Tana fadin"Haba ko Daya..Kawai Tausa ne kadai na yau da basu samu ba..Ammh gobezan je awo zan musu Complain naji..Mganar Auran Abdullahi kuma bai gabana Subai'atu Abu Dayane agaba na Sauka Lafiya.."
Subai tace"In bai gabanki..Meyasa naga kin Rame kuma nazo kin ganni kin kama kuka.."Hafsah tace"Kukam Dacin Rai ne Subai...Abu Daya ne ya batamin Rai game da wannan Auran Subai ko da bani da wani matsayi wajen Abban Amira bai kamata na Fara ji wannan mganar Daga bakinsa ba..? Kana kuma bai kyautamana ba Da bai bari ya kamallah Gidanshi ba kuma bai bari na Sauka lafiya ba ammh yaja jibo Aure."Tafada Hawaye na Kawo mata.
Hannunta Subai ta Rike kawai Tana lallashinta Domin bata da ta cewa nan ta Dade sai yammah ta koma Gida kowa yaji labarin Auran Abdullahi sai yayi mamaki ya kuma Kira Hafsah yace kar ta Tada Hankalinta Su Ammi kuwa da kanshi yaje ya gayamusu sai ganin Kiran Ammi Tayi Hafsah tana Gayamata kar ta Tada Hankalinta Sai kawai ta sakama Ammin kuka ita tayi ta lallashinta da ban baki da Nasiha Musamman Daddy yace taje yana son ganinta Abdullahin yakai ta Shima yayi mata Nasiha Sosai wanda yasa Taji Zuciyarta ya yi sanyi ...
Ita ko Anty Hadiza Dataji Fada ta kamayi da Abdullahin tana Fadama Ammi ya cika zalama ina yaga karfin Rike mata Biyu,ga gininsa bai gamaba ya Dauko Aure Ammi ta Takamata Burki ta kuma Haneta da kiran Hafsah ta Raunana mata Rai Fadan Ammi yasa Data Kira Hafsah batayi Korafin baa ammh tace karta Damu Duk Abunda Take Bukata ta Kirata ta gayamata Fatanta karta Damu ta Cigaba da addu"an Allah ya Sauketa lafiya.
*Domin Biyan Kudin Karatu akan Littafin Ra"ayi ne ko Buri..? Zaku iya Tura kudin karatunku ₦200 Kachal akan wannan asusun bankin 0552179550...JAMILA UMAR GTB,Sai a turo Shedar Biya ta wannan layin wayar 09069067488,In kuma Katin Waya ne zaku iya Turowa ta wannan Layin 09027767783 kai Tsaye Bayan Mutum ya Dauki Hoton katin...Ga masu Bukatar VIP zasu Biya ₦500 ne ta Lambar asusun Dana bada a sama....! Mutanenmu na Niger kuma Zaku iya Tuntumbar My Jika aglan Nissa ta wannan Layin +22794131747....Sai kunzo Masoyana*
*Janafty...*
4/9/21, 1:59 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*
*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!
_Domin ku Masoyana na Nesa dana kusa..Hakika Daga Jiya Zuwa yau naga Salon Kaunarku da Soyayyarku Zuwa gareni Dalilin Wannan Littafin..Nagani kuma na Shaida Nagode kwarai Allah bar zumunci Masoyana masu Bina ta Wattpad kuma ina Ganin Sharhinku kuma ina Yabawa Sosai Nagode Allah ya bar Zumunci Ameen Ga Tukwaicin Wannan Page din zuwa Gareku Da Fatan zaku Taya *ABDULLAHI* Da *BARKAT* Happy Marriage Life..._
*033*
"Kamar yadda Abdullahi ya gayama Nazifi Zai Dauki Loan ma'ana Bashi a wajen aikinsa Allah barshi sai adinga Cirewa Da kadan da kadan Cikin albashinsa har ya gama Biya Toh yayi hakan ammh bayan Nazifi ko Hafsah bai yarda yayi Zencen da ita ba azuwan sai dai kawai Taga ya Bata kudi a Hannunta Tayi Siyayyah kayan Haihuwa Dashi Sauran kuma yayi Gyaran Dakin da Barkat zata Zauna Da Akwatuna da kuma na Hidiman Biki kafin kuma Aga Abunda Allah zai yi.
Sai dai Abunda bai sani ba Tuni Hafsah Taga Takardan Bashin bata Dai mai mgana bane kuma Bata Nuna mai Ta gani ba Tunda bai mata mganar ba Sai kawai ta Kyaleshi ammh batayi wani mamaki ba Sanin Daman Dole sai Abban Amira ya kare da Cin Bashi Abunda batamai Sha"awa Toh ammh Tunda zai Dauko yar Mutane ai zama bai ganshi ba.
Bayan Saka Ranar Abdullahi Sun Hadu da Barkat ammh acikin Makaranta yaje ya sameta Suka Sha Hiransu Tun Wajen La"asar yaje Domin Daga Wajen aiki ya Dauki Exvuse ya koma Gida yayi Wanka ya Sauya kaya ya Hau Mashin Yatafi Chan Barkat ta Rikeshi da kalamanta na kwantar da kai da Nuna ma Namiji kamar Sarki yake Tun Abdullahi na Duba agogo har ya Daina ya Share kafa ya Biye Barkat Tana ta mai Hira Cikin kwarewa da kuma Salon Sace Zuciyar Da Namiji Dama ita Barkat Irin Matanan ne masu Wayau ga ta da iya Kalamai da iya Sarrafa Harshe Wajen yadda zata Dawo Da Namiji Gabadaya Hankalinsa akanta Toh da Irin Haka ta Jawo Hankalin Abdullahi Gareta Har ya Fada Tarkon Sonta bai sani kuma Ita Haka Salonta yake in Har kayi Zama da ita na wani lokacin Koda bata Sonka Zakaji Duk Duniya ta maka kunci Indai ba Barkat ka mallaka Gabadaya ta zama Matarka ba Sau Taru maza SunSha Wahala a kanta matuka ammh bata Basu Fuska sai akan Abdullahi Da Tundaman Chan Tace Shi take Jira Domin ya Gama Cika Duka Sharadinta na Irin Namijin Datake Buri.
Da irin Salon Soyayyarta da Shagwabarta Tana wani Kiransa My Man,shi kuma ya Biye mata ya Share kafa Har Wajen 11:20pm na Dare kana ya Farga Shima Kiran Hafsah ne ya Shigo Wayarsa Sai Lokacin Hankalinsa ya koma Gida ya mike yana Cema Barkat din zai Tafi nan ma Kukan Shagwaba ta Fara wai bataso ya Tafi Wani bata lokacin ya kara Wajen Lallashinta kafin ta yarda ya Dauketa a Mashin Dinsa Zuwa Kofar Hostel dinsu kana sukayi Sallama ya Fito Daga Cikin makaranta Gudu ya sakarma Mashin Din Ganin Dare yayi Sosai Abunda bai tabayi ba.
Koda ya iso Gida 12pm na Buga Na Dare,Mashin Dinsa yakai Dakin Dayake ijiye Kafin ya Shigo Falon Hafsah ya gani Zaune ga Tsohon Ciki Tana Jiran Dawowarsa Tana ganin Shigowarsa Ta Mike Dakyar tana Fadin"Na Tsorata Abban Amira ina ka Tsaya ne..?naga baka Taba kaiwa Pass 10 awaje ba ammh yau har 12 na Dare kana Waje gashi ina ta Kiran layinka yaki Tafiya sanda kuma na Sameka Baka Daga Ba Hankalina ya Tashi yanzu Haka Auwal nake Shirin kira naji ko kana Gidan Mama ne.."
Ta karishe Fada Cikin Tashin Hankali kamar tayi kuka ajiyar zuciya ya Sauke yana jin bai kyautaba akallah dai ya gayama Hafsah ga inda zashi,Gabanta ya Karisa ya Riko Hannunta yana Fadin"Afuwan Matar Abdullahi..Laifina ne kafin na Fita ban gayamiki inda zani ba Sam...Cikin Abu Samaru na Shiga Wajen Barkat Muna ta Hira Wlh bansan Lokaci ya Tafi haka ba.."Tunda Taji ya ambaci Barkat tayi Saurin Zare Hannunta Wani Abu na Sukan Ranta Tace"Ka Tadamin Hankali..ammh Ko ina kaje..Abban Amira Sai ka Tuna ka barni ni kadai agida ga Halin Danake Ciki Dagani sai yara.."Tafada Tana Kallonsa Ido Cikin Ido kansa ya Shafa yana Fadin"Naji Ban kyauta ba Kiyi Hakuri Don Allah..Haka bazata Sake Faruwa ba.. !
Kada kai kawai tayi tana Fadin "Ya wuce ga Abincinka fa..? Tafada Tana kallonsa Fuska yadan yamutsa kafin yace"Wlh na Koshi Hafsatuna sai dai da Safe.."Kallonsa Tayi a kaikace kafin kawai ta kada kai ta Shige Cikin Bedroom Bayanta yabi yana Tambayanta Su Amira tace Sun Dade da yinBarci Sun gaji Da Jiran Dawowarsa Bai Tanka ba ya Sabule Rigar Jikinsa ya Tura Kofar Tailet ya Shiga Hafsah ta Bishi Da kallo Lokaci Daya Tana Kada kai Ta koma ta kwanta Tana kokarin maida Hawayen da Suka Cikamata kwarmin Ido.
Washegari kuma kafin ya Fita aiki ya Bata Kudi 50k yace Tayi Siyayyah kayan Haihuwa da komai da komai Harda kayan da zatayi Fitar suna Tayi Hakuri ba Haka yaso ba Da Farko Taso taki karba ne Ganin Anty Hadizan ma ta aiko mata da Sakon Kayan Jarirai Kala kala Sabbi da overroll Kala kala suma kadan ma Zata Kara,Kuma Daddy ya sakamata 50k cikin Bankinta Duk Domin kar ta Tada Hankalinta bata gayama Abdullahin ba ganin bai da Lokacinta yanzu yana Shirye Shiryen Dauko Sabuwar Amarya,In ya Fita Tun Safe Sai yammah yake Dawowa inya Dawo Bai da Lokacin kowa sai Chart da Barkat,ko kuma ka ganshi Dai da waya yana ta latswa Shiyasa ta kama kanta Fatanta Allah ya Sauwaketa lafiya.
Godiya Tamai ta amshi Kudin Ta Ijiye,sai da yaje gidan Mama Sukayi Mgana kana ya Kira Zannira yamata mganar Hada akwatuna Saffa Saffa Guda Biyar zai Tura mata Dubu Dari biyu Da Hamsin Tace sai Dari Uku da hamsin Harda na Hafsah yace Shikenan kafin ya bar Gidan Mama sai da suka gama Mgana yace mata Ma"aikata Zasu Fara gyaran Dakin Dayake ijiye mashin Dinsa Zai saka a Fasa Wani Waje ta Baya ayi mata Tailet a Dakin Tunda Dakin Ciki da Falo ne kuma masu Girma Kicthen kuma Suyi Maneji Ita da Hafsah kafin Su koma Sabon Gidansu Mama tace Hakan yayi tayi mai Fatan alheri.
Ana Gobe ma"aikatan zasu zo Abdullahi ya gayama Hafsah,ya kuma Gayamata Zasu yi Sharing kichen da Barkat Din Kafin su koma Sabon Gida aranta Tace Daman ban Mamaye Kitchen din ba,Yawancin kayan Kitchen Dina Suna Dakina Cikin kwali ban Fito Dashi ba,Afili kuma tace Allah kawo su Lafiya Washegari suka zo Dama Ranar ta kama Lahadi ne,Yana Gida Dama ita bata saka kaya adakin Shine Daman kan Saka Mashin Dinsa da Sauran Abubuwan da ba"a Raasa ba,ya kwashe Silin Suka Farayi,Dama Dagashi ne sai Floor sai Filista sa Fenti Sai kuma Bayin Dayace Za"a Fitar ammh Taga an Siyo Kwalayen Tayes su Zai saka mata afalo kila Daga ciki kuma ayi Siminti.
Aranar Da yammah Tana Jinsa Suna Mgana da Barkat din Tana gayamai ta Dawo Gida Sun Gama Test,Inaga tace mai yazo yace bazai Yuyuba Yana wani Uzuri ne Ammh Daga baya kuma sai Taga ya Shiga yayi Wanka ya Shirya Cikin Dakakkiyar Shadda Fara yaci Hula ya Fesa Turare Tana Falo yazo ya Sameta Yana gayamata Zai je Gidansu Barkat ya Gaida Mamarta Tunda Mganar ta Bullo bai leka Gidan Ba,Ta Gefen ido Ta kallesa Acikin Ranta kuma Tana ta maimaita Suna Allah ganin Shedan na Shiga Zuciyarta yana Saka mata Wani Irin Kishin Abdullahi.
Jiki na Rawa ya Fita Chan Yaje ya iske Barkat tayimai kwalliya da Girke Girke kala yaci yasha kana Tamai Jagora Har Falonsu na Cikin Gida ya gaida Hajiya Amina Tayi ta saka albarka Tana Fadin Abun Allah kenan Gashi Nazifin Dayazo Neman Auran Allah bai yi ba Shi da yayi Rakon Dashi Allah yace,3k ya bata ta karba Tana Godiya,ya iske Duka yaran Hatta Aina ta Dawo Daga makaranta kuma Sunzo Sun gaisa Dukkansu Yana Gidan ma sai ga Salisu nanma suka gaisa Duka suka Dan Taba Hira yana Tambayan yanzu Nazifi ya Daina Shigowa Garin Abdullahi yace gaskiya Sai da wani kwakwaran Dalili Salisu yace Amarya ta iya Rike angonta Shida Abdullahi dariya kawai yayi bai ce komai ba nan Salisu ya barshi ya Shiga Cikin Gida bai Dade ba ya Fito Sukayi Sallama ya Tafi,Abdullahi bai Dade ba Karfe 9am Yayi musu Sallama suka Rabu da Barkat kan Gobe zai zo Ta kaishi Sabon Garin Gidan Wan Babansu ya gaisheshi Har Kofar gida Ta Rakashi Da Leda Shake dasu Sweet tace yakai ma Su Amira sai Turare Datace ya kaima Antynta Hafsah Abdullahi Sai Godiya yake Hakika yaji Dadin kyautar Bangirma Irin na Barkat.
Koda ya Dawo Har Auwal ya Maido Su Amira Gida Ya kuma Baje musu Tsarabansu yana Fadin Sabuwar Antynsu da zasuyi kwananan ne ta kawo musu Suka Karba suna Ihu Suna Tsalle Hafsah na gefe Tana kallon Ikon Allah itama ta waigo ya mikamata nata Turaran ta karba Tayi godiya Ko a Fuska bata nuna