Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
ta Dora tafashen Naman gas kuma ta Dora Shinkafa su Abdullahi ya Siya musu ganin Gidan ba yara sai dai in sunzo.
Nazifi kuwa Koda 10am tayi tamai agidansu,Booth dinsa Shake da kwalayen Minti da Cingam,Yara suka Dinga kwasa suna Shiga Dashi Cikin gidan Baba waada,Auwal na kofar gidansu Ya Hangi Zuwa Nazifin wanda yaci wani Danyan Shadda Mai kalan Sararin samaniya Dinkin zamani ya saka wata Hula zanna Bukar kafarsa sanye da wani Takalmin sawu Ciki na Fata,Haka Tsiyayan Hannunsa Dauke da Agogon Fata na Kamfanin Rado iya Haduwa ya Hadu Domin in kamai kallo Daya sai ka kara Auwal har Kofar gidan Baba wada yazo suka gaisa kana ya wuce Shago.
Nazifi ya Shiga Sun gaisa da Baba wada da Inna Abu kana ya Fito da Kudi Dubu dari da Hamsin yace Dubu Dari Sadakin Jidda Dubu Hamsin kudin nagani ina so da kuma Gaisuwan iyaye Baba wada ya karba yana ta Sakamai albarka,Saboda zumudi ko Tsayawa karyawa bai yi agida ba Koda yake ina yaga Abun karyawan har ya hutu yar mulkin tana kwance,Dama Jiya ta Dawo Daga Abuja Ta kwanta sai barci take nan Da yayi mgana sai tace Barcin gajiya ne Shiyasa ma Tuni ya Fita Batunta,tana kwance yazo yace mata zashi Zaria adawo lafiyan ma Ciki Ciki ta Furtamai bai Damu ba Ya Fice Domin yana ji acikin Ransa komai ya kusa zama Tarihi.
Dumaman Tuwon Masara Miyar kukan da Inna Abu tayi yaci yasha Ruwa,Kana ya Kira Abdullahi yace gashi nan ya iso Abdullahi yace shima gashi nan zuwa Domin Yanzu suka gama Mgana da mijin Goggi Habiba ya kariso yana gidan mama,Da haka suka yanke Kiran Minti Talatin Yayi yawa sai ga Abdullahi ya iso Shida Alhaji mamuda sai da ya Shiga Gidan Mama suka gaisa ya iske Har Mariya ta kusa gama Girki Jidda kuma na Ciki kwance Aikuwa mariya tana gayamai ya Shiga ya Fattakota Dole ta Fito ta Shiga wanka tana Sharan kwallah Mama kuwa na Tsakar gida tana Bude sakon da Goggo Habiba ta aiko mata dashi ita da Inna Abu sako ne irin na kauye irinsu kuka,kubewa,Garin alabo,Zogala da Sauransu.
Atsakar gidan Baba wada suka yada zango Bayan Inna Abu ta Shimfida musu Babbar Tabarma,bayan gaishe gaishe sai kuma mganar Hadin Aure ya Biyo baya,Baba wada yace Shine Waliyin Amarya sai dai in Alhaji mamuda ya zama waliyin ango,ana ta Dariya Alhaji mamuda yace"Yaji Bakomai ai daman Abdullahi da Nazifi sune ya"yansa.."Nan Baba wada ya gabatar da Sakon da Nazifi yazo Dashi da kudin daya bashi da kuma Su Tabarmu da goro,Shi kuma Alhaji mamudan ya maidama Baba wada amatsayin suna neman yardasu agame da Auran Jidda da Nazifi Baba wada yace an basu nan aka sanya Lokaci nan da wata uku masu Zuwa abun yayi ma kowa Farinciki da Burgewa,Baba wada kamar bakinsa ya yage saboda Farinciki Basu bar gidan ba sai da suka ci Danwaken da Inna Abu tayi musu Lokacin ana Kiran Sallah suka Dunguma zuwa Masallaci Bayan sun Fito Abdullahi ya kalli Nazifi yana Fadin"To kai Mutumina sai munyi waya kenan zan karisa Gra wajen masu ginin nan na gani na kwana Biyu ban je ba..
Nazifi yana Shafa Kansa yace"Ok..Ammh ba Rakiya abokina..'?Hararan wasa Abdullahi yayi mai yana Fadin"A"a kai ai dan gida ne...kuma zaka Neman Yakin aure ne Adawo lafiya.."Ba yadda Nazifi bai yi kan Abdullahi ya Rakashi ammh yaki,Nan ya bar Alhaji mamuda wajen Baba wada Kofar gida suna Hira sai anjuma zai wuce 5k Abdullahi ya bashi yace yayi na Mota ya Hau mashin Dinsa Zuwa Gra.
Nazifi kuwa Kunya kuma Duk sai ta kamashi gashi kofar gidan ammh ya kasa Shiga,Sai da yaga ba Sarki sai Allah kana yayi Kundubala yashiga Cikin Gidan nasu Abdullahi Lokaci Daya yana Sallama Cikin Muryansa mai Amo da Sauti..
*Domin Biyan Kudin Karatu akan Littafin Ra"ayi ne ko Buri..? Zaku iya Tura kudin karatunku ₦200 Kachal akan wannan asusun bankin 0552179550...JAMILA UMAR GTB,Sai a turo Shedar Biya ta wannan layin wayar 09069067488,In kuma Katin Waya ne zaku iya Turowa ta wannan Layin 09027767783 kai Tsaye Bayan Mutum ya Dauki Hoton katin...Ga masu Bukatar VIP zasu Biya ₦500 ne ta Lambar asusun Dana bada a sama....! Mutanenmu na Niger kuma Zaku iya Tuntumbar My Jika aglan Nissa ta wannan Layin +22794131747....Sai kunzo Masoyana*
*Anitha...*
4/9/21, 1:58 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*
*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!
*025*
"Lokacin Da yayi Sallama babu Kowa a Tsakar gidan Dukkansu Suna Cikin Daki,Shiyasa basu Ji ba,Jin ba"a amsa ba yasa ya kara Wata Sallamar Daidai lokacin da mariya ta Fito Daga Dakin Mama sai Tajiyo Sallama ta amsa Lokaci Daya tana Bada izinin Shigowa Duk da Dama Ranta ya bata Yaya Nazifin ne.
Cikin Takun natsuwa irin na masu Ilimi ya Shigo Gidan,Mariya na ganinshi ta gaisheshi Cike da girmamawa Cikin Fara"a kadan ya amsa yana Tambayanta karatu tace Alhamdulillah,kai tsaye ya kalleta Yana Fadin"Mama na Ciki..?
Kafin ma Mariyan ta bashi Amsa Mama Dake Cikin Tace"Eh ina Ciki Nazifi naji Shigowarka Lokacin Ina Sallah ne Shigo Daga Ciki mana ka Tsaya anan kamar bako.."Ta Fada Tana Daga Cikin Daki Jin Haka yasa ya Sabule Takalmi sawu Cikinsa yayi Sallama Mama ta amsa ya Shiga Nesa da ita ya Durkusa yana Gaisheta ta amsa Tana Fadin"Haba Dai Nazifi karmuyi Haka Dakai mana..? Don Allah ka Tashi ka koma Bisa kujera Don Allah.."
Jin ta Saka Roko da Allah yasa ya Tashi ya Dofana Kan kujeran ammh kansa na kasa haka kurun yake ji wata kunyar mama Wacce bai Taba ji ba,Tambayansa Iyali Mama tayi yace suna Lafiya Daganan kuma sai Falon ya Dau Shuru Mariya Mama ta kwalama Kira ta amsa sai gashi ta Shigo Kallonta Tayi Tana Fadin"Kai shi Dakin Auwal Mariya kizo ki kimai Ruwa da Abunsha Tunda ita yar mulki Tana Ciki kuma Taji Shigowarsa ammh bata Fito ba.."
Da To Mariya,Mama ta kalli Nazifi Tana Fadin"Nazifi kuje Dakin Auwal kafin Jiddan tazo..Sai fa kayi Hakuri da Halinta kasan ta yarinya ce akwai kuruciya akanta Da kuma Rawar kai kamar Uba kake gareta in tayi wani abu ba Daidai kai mai sakata a Hanya ne har zuwa ta gane Watarana.."Kansa na Kasa ya Murmusa yana Fadin"Insha Allahu Mama..Nagode Allah saka da alheri ya Jikan magabata Ameen.."
Mama tace"Ameen..Bakomai Daga kai da Jidda da Abdullahi Duka Dayane awajena...Tun da naji Abun alherinan nake Murna Allah yasa ace gwara da akayi Allah sa kuma muna da Rabon ganin Lokacin.."Kunya Duk sai ta kamasa ya Sunkuyar da kansa yana amsawa mama da Ameen kafin ya mike ya mata Sallama ya Fito Tsakar gidan ya Saka Takalminsa ya wuce Dakin Auwal Tunda ai gidan ba bakonsa bane.
Ya Iske Mariya aciki Tana ta Jeramai kololin abinci,Saman Karamar katifar Auwal ya yada Zango Lokaci Daya yana Bin karamin Dakin da kallo Duk da ba wasu kaya Daga katifa sai Kayansa sai Cafet sai Littafan karatu da akwatin kayansa Dakin Dai Tsaf dashi Sai kamshi Turare yake Tashi,Mariya ya kallah yana Fadin"Sannu da aiki Mariya..yau ba Zuwa asibitin ne..?
Tana Shirin Fita tace"Laa..Ba komai Ya Nazifi..Eh yau bazani ba sai gobe.."Kai ya gyada yana Fadin"Olrigt Allah ya kaimu..."Yafada Lokaci Daya yana Fito Da wayarsa Daga aljihu,Mariya kuma ta Fice ta barshi Tana Shiga Dakin Mama ta isketa tana ta Fama da Jidda kan ta Fita Taje ta samu Nazifin ammh Taki ta tsaya sai wani Bata rai Take,Duk da Daman wajen kwalliyama Tsiya suka Tafka da mariya ita kuma ta nace sai ta mata kwalliyar ta sakata ta Shirya Cikin wani Ubansu Leshi mai kyau da yarari da Tsada Cikin Wanda Hajiya Sa"a tayi Mata ne,Dinkin Riga da Sikat ne kayan sun kamata sun Fitar mata da Duka Suran Jikinta Kanta kuma wani Irin Dauri ne mai kyau Mariya tayi mata,ta mata Feshin Turare.
Wani Takalmi mai Tsini Mariya ta Dauko mata tace ta saka Sai Mayafi Yana da girma ammh ba Sosai ba sai dai kuma Shara Shara ne ana iya ganin Komai na Kayan Jikinta,Ganin haka yasa Mariya ta karisa ga Jiddan Ta Riko Duka Hannayenta Tana Fadin"Haba yar kanwata..Miye haka kinga yadda kikayi kyau Shine xaki bata kwalliyanki..! Ko bakomai ki Je kinga dai abokin Ya Abdullahi ne kuma bazai Taba Jin Dadi ba in aka wulakantashi Plz kije ku gaisa sai ki Dawo.."Tafada Cikin karya Wuya Kallonta Jidda Tayi Tana Tura baki kafin tace"Naji zan je..Ammh muna gaisawa zan dawo Abuna.."
Mariya na Danne Dariyanta Tace"Eh naji..Da kun gama gaisawa ki Fito abunki ammh Don Allah ki Zubamai abinci kinji ko Jidda..? Kai ta gyada Cikin Cinmgani kafin tace,"Shikenan..Ammh Da ban yi Niyya ba.."Mariya tace"Yauwa..Nagode ko kefa..Muje na Rakaki har Kofar Dakin ma..."Daga haka ta Rike Hannunta Suka Fice Daga Falon Mama tarakasu da kallo Tana Mirmishi acikin Ranta Kuma Tana Fatan Allah ya Tabbatar da wannan Abun..Da sai Tafi kowa Jin Dadi.
Har kofar dakin Auwal Mariya ta Rakata kana ta Saki Hannunta Tana Fadin"Oya..Sai kin Fito ko..?Kai Jidda ta Daga mata,Mariya ta Juya Tatafi Tana kashe mata Ido Daya,Bayan Tafiyar Mariya sai Jidda ta kasa Shiga Domin Tana Jin Muryan Nazifi yana mgana ta Waya Gyara ma Tsayuwarta Tayi Tana Tunanin yadda za"ayi ta Shiga Ba zato ba tsammani Taga kawai an yaye labulen Dakin Dago Idanuwanta tayi Karaf suka Hada 4eyes dashi yana Tsaye yana kare mata kallo Tunda Ga sama Har kasa kafin ya Dire kallonsa nashi kan Fuskarta Cikin wani Yanayi na Bugun Zuciya wanda baisan Dalili ba.
Ita kanta Jiddan Zuciyarta ne ke Bugawa Fat..!Fat..! Kamar wacce Tayi Gudun Tsere,Ga Jikinta ya Fara rawa Domin idanuwan Nazifi akanta suna sakata taji kamar Tana Jin sanyi kanta ta maida kasa ta Fara waasa da adon gyalenta Taki Cemai komai Shi kuma sai kawai Daya gama Morema kallonta ya Kada kai yana Fadin"Ki koma Tunda bazaki Shigo ba..Bazan matsama miki ba Jidda sam.."Yafada Lokaci Daya yana Sakin Labulen Dakin ya koma Ciki ya barta nan Tsaye.
Sai kuma Taji bata kyauta ba ko bakomai Ya Nazifi bai Chanchanci wannan Tozarcin Daga gareta ba, Sai kawai tayi Kudunbala Ta yaye Laluben ta Shiga da Siririyar sallamarta Yana zaune gefen katifa ya Tankwashe kafafunsa yana ta Danne Danne acikin Wayarsa ya amsa mata Sallaman batare Daya Dago ma ya kalleta ba,Ganin haka sai ta Duka ta Cire Takalminta Cikin Sanda ta kariso Cikin Dakin Nesa Dashi ta Zauna Kanta na kasa Tana Fadin"Ina yini Ya Nazifi..!!"
Kamar bai jita ba yayi mata sai kuma Taji bata ji Dadi ba Idanuwanta suka Ciko da kwallah ta Tura baki ita kadai Ta kauda kai bata kara mgana ba, Shi ma kuma yana nunamata yana gaba da ita sai yayi kamar Babu Mutum mai arai awajen Cigaba kawai yayi da Taba wayarsa,da Farko taso Tatashi Tayi Ficewarta ne sai wata Zuciya tace Kin Tanadi amsan da zaki bama ya Abdullahi in ya Ritsaki..?
Tuna Haka yasa Ta kauda wannan Tunanin Fushinta ya Sauka Ta Dago Gefen idonta Tana Satar kallonsa Tagama Hankalinsa na kan wayarsa bai ma Kallon Barayinta,Waro ido Tayi kai Tsaye Tana karemai kallo Acikim Ranta tace"He is Cute,and Simple ba kamar ya Abdullahi ba."Ta fada Lokaci Daya Tana sakin Mirmishi.
"Kingama kallon nawa..? Me kuma ya baki Dariya atare dani.? Kawai Taji ya jefomata Tambaya kai Tsaye Idanuwanta suka Fito waje Cikin mamakin Dama yana kallonta ne,Sai ta daburbuce ta Sunne kai Tana Tunanin amsan da zata Bashi ba abun tace karya bane ya riga kamata ganin Tayi Shuru yasa ya Dago yana kallonta kai Tsaye yace"Umh..Dake fa nake mgana Hauwa"u.."
Yafada Cikin Muryan kamar ta Bawa da Uban gidansa,Jin haka yasa tace"..Ni...Ni ba kai nake ma Dariya ba.."Kai tsaye yake kallonta yace"Bani kike ma Dariya ba wa kike mawa..? Naga Dagani sai ke acikin Dakin nan ko.? Uhm...Zo ki zauna nan Sai ki Fadamin Abunda ya baki Dariya ajikina.."Ya Fada yana nuna Mata gefensa..
Ido ta Zaro Tana kallonsa Shi kuma sai ya Hade Rai yana Fadin'Eh...Ki zo nan nace.."Ya Fada irin so Commondely haka Marairaicemai Tayi Tana Fadin"Don Allah kayi Hakuri ya Nazifi...Nifa ba kai nake ma Dariya ba.."
Tafada tana wani karya wuya wanda Ita kanta Batama san Tayi ba Wani iri yaji Kawai Shima sai ya Biye mata ya karya Wuya yana Fadin"Naki na Hakura sai kinzo nan ki zaunan kin gayamin Abunda kike ma Dariya..?ko kinga kaina da Furfura ne Shine kike Dariya za"a Hadaki da Tsoho ko..?.
Yafada Cikin Sigar Zolaya Jin haka yasa ta Bude baki Tana Fadin"Laaa..Kai ne Tsoho..? Kai ya Gyada mata yana Fadin"Eh mana..Naga kamar nayi miki Tsufa Shiyasa kike min Dariya ."Baki ta kama Kafin tace"Nifa ba kai nake ma Dariya ba Kuma injiwa yace kai Tsoho ne..?
Kai Tsaye yace mata'"Inji Amaryata Jidda mana.."Yafada yana Kafeta da ito Kunya ya kamata ta Sadda kai Tana Mirmishi Gefensa ya Nuna yana Fadin"Nace ki Dawo nan ko..? Ko ni kike son na ijiye Girman na Biyoki..?Da sauri ta girgiza kai Mirmishi yayi yana Fadin"Ahto..Tunda naga kamar haka kike so..
Cikin kunya tace"Ni fa bance ba.."Tafada Lokaci Tana zama Nesa Dashi,Kallonta yayi kai tsaye Shima yana gyara zama Yana Fuskanta yace"Uhm ina jinki Fadamin me kike ma Dariya..'? Kanta na kasa tace"Allah ni ba kai nake ma Dariya ba.."Rausayar Dakai yayi yana Fadin"Toh naji bani kike ma Dariya ba..? Dariyar tame cece..? kamar bazatayi mgana ba Sai chan kuma tace"Kawai nace ne U are so Simple ba kamar ya Abdullahi ba.."
Dariya ta kamasa sai da ya Dara kafin yace"Who tell u ina da Sauki akan Abdullahi..? Baki Tunanin sai Hali yazo Daya ake abota.."?Dagowa tayi tana kallonsa karaf suka Hado Ido Kallon Juna sukayi na wani Lokaci kafin Jidda Ta Dauke kanta,Shi kuma sai da ya kara Moran ma kallonta kana yace"Umh kinyi Shuru.."Kai tsaye tace"Haka kurum..Nake ganin kuna da Bambamci.."Mirmishi ya saki Lokaci Daya yana ijiye wayarsa a gefenta kana yace"Hmm..Ana ki ganin kenan.Eh bazan ce miki bamu da bambamci ba yes muna Dashi..Wasu Hallayar tamu Tasha Bambam kamar wani Lokacin Yayanku yafini Zuciya da Saurin Fushi.."Yafada yana kallonta Kai ta gyada batace komai ba kafin kai tsaye yacigaba da Fadin"Jidda as u know bari mu tafi kai Tsaye Nasan dai zuwa yanzu kinsan Abunda ke Tsakanina Dake ko..?
Haka kurum Taji ta Natsu tana Sauraransa ganin haka yasa ya Cigaba da Fadin"To Da farko dai Kisanni kinsan Gidanmu da iyayena da kannina Sunana Kamar yadda kika Nazifi Wada nibamai kudi bane ammh ina da Rufin Asiri Ina aiki a hukumar nepa Dake kaduna Da Albashina wanda Bazan Raina ba kana kuma Ina Da matar Aure Daya,haihuwarce Allah bai kawo ba Ina da gidana a kaduna sai kuma wani Danake ginawa anan zaria,Kana kuma ayanzu haka na koma Kasu ina so na Hada Masters dina,Kinji kadan Daga Cikin Wanene Nazifi Wada..".
Kanta Na kasa tace"Allah ya taimaka.."Yace Ameen kana ya Zarce da Fadin"Kinsan meyasa nake miki wannan bayanin..? Bai bata Zarafin mgana ba yacigaba da Fadin"Saboda muna Kokarin zama karkashin Ihuwa Daya Jidda amatsayin mata da Miji..Kinga ya kamata all Ni kisanni nima na san komai naki Saboda muna Fatan zama ne tsakaninmu na Muddin Rai Duk da bansani ba ko kin karbeni na zama abokin Rayuwarki ko nayi miki Tsufa ko kuma saboda ina da da Mata ba ki sona.."!
Baki ta Bude Kafin ta Rufe Tana Fadin"Ni ban ce haka bafa.."Mirmshi yayi yarintar ta na Burgeshi yace"Naji baki ce ba..Ammh ki Dago kanki ki kalleni shin zaki iya maneji dani a matsayin Mijinki? Shin zaki yarda Na zama abokin Sirrinki na Har Abada..?Zaki yarda ki ZAMA mace mafi Daraja da kima acikin Idanuwana.."!
Yafada yana kafeta da mayen kallonsa Duk sai Jikinta yayi sanyi Tana jin wani yanayi atare da ita,Kanta ta Sunkuyar tana ji har acikin Ranta Ya Nazifi bai da makusa,Ita din wacece da zataje bai mata ba amatsayin miji?,Kafin Shigowarta Dakin Bata taba Zaton Haka ba sai gashi bayan Shigowarta komai ya Chanza Ji take in yana mgana kamar Muryansa tana Tsulamata Bulala agadon bayanta ganin Tayi Shuru yasa ya Sauke ajiyar zuciya yana Fadin"Baki karbeni ba ko jidda..?
Yafada kamar zai yi kuka da Sauri ta Dago Tana Fadin"A..a...Na amince ammh.."Da sauri ya tari Numfashinta yana Fadin"Ammh me Jidda..?look ki Fadamin Duk Abunda ke Ranki Ni dake mun zama Daya In ma baki sani ba bari na gayamiki Tuni Waliyanki Sun bani ke Har sadakinki na Biya so ina nace ina da iko Dake kamar banyi karya ba ko..?
Ido Ta zaro ta kallonsa Mirmishi yayi yana Fadin"Yes..Duk da nasan baki sani ba..Ammh Dalilin Shigowata garin yau Dalili biyu ne na Farko gabatar da saka Ranarmu na Biyu na ganki na kuma Baki Hakkinki Agame da Zabin mijin da kike so.."Jikinta ya kara yin sanyi An Biya Sadakinta... ? Toh Tunda an Biya ai bata da ta cewa Ganin Tayi Shuru ne yasa yace"Uhm ina jinki..? Ko kunyana ake ji..?
Rufe Fuskarta Tayi da Tafukan Hannayenta tana Fadin"Eh..Ka bari na gayamaka ta waya.."Wayarsa ya Tura mata yana Fadin"To sakamin Lambarki in na koma gida sai na Kira ki muyi mgana Duk da Zuwa Sati mai zuwa gaskiya wata wayar zan kawo miki.."Cike Da mamaki tace"Saboda mene..?
Wuya ya karya yana Fadin"Cos Jidda is Belong to me..Only me.."Yadda ya Fadi mganar ne sai da Taji Tsigan Jikinta ya Tashi Ta Shagwabe Fuska tana Fadin"Mommy fa ta Siyamin wayar..Shine zaka ce zaka kwace.."Ta fada Tana Tura baki,Shima Bakin ya Rike yana Fadin"Au bansani ba...Kinga am Sorry..Bazan karba ba sai kawai na Sauya miki Layi hakan yayi..?
Hararansa Tayi Tana Tura Dariyan Nishadi yayi yana Fadin"Kaina Bisa wuya nidai a sakamin Lambar..Sai abani Ruwa nasha Madam duk da sai da na Roka.."Kunya ya kamata ta Sadda kai kawai kasa tana yarDariya Shi kuma yana kallonta Wayar ta Dauka Taga da Password ta gayamai kai Tsaye ya gayamata ta Bude ta sakamai lambar Data bashi sai yaki karba yace mata"Kiyi Saving mana."Kallonsa Tayi tana Fadin"Kai..ni kuma..?Wani Suna zan saka maka.."
Sai da ya lulubi kwanyan idanuwanta kana yace"Habibty...."Wani iri Taji kai Tsaye ta narkar da Idanuwansa Cikin Nashi Shima kawai sai ya wani Lumshe ido kamar zai kwanto mata sai yayi baya da kanshi Hannunta na Rawa tayi Saving bayan ta saka Suna ta mikamai wayarsa ya karba yana Binta da wani mayen kallo Abinci ta Fara zubamai kana ta Zubamai Ruwa da Kunun ayan Ta Dago Tana Fadin"Don Allah Ya Nazifi kayi Hakuri.."
Yana Kishingide yace"Hakurin me... ? Abincin Ta nuna mai tana wani Shagwabe Fuska Mirmishi yayi kafin yace"Karki