Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
yayi har ya ishesa Kafin yace" Shi Daman bai ce bazata koma ba Daman ya bari ne ta zauna agidan sai ta gaji ta Nemo Taimako Don kanta Tunda yanzu Ta gane kuskuranta Shikenan ammh da Sharadi sai ta Kira Hafsah ta Roki gafaranta kan Ce mata Datayi munafuka Nazifi yayi kokarin Abdullahi yabar mganar kiran Hafsah Ammh ya Rantse sai ta Kira Dole ya kira Barkat din ya gayamata yadda Sukayi da Abdullahi ba Gaddama tace Taji Zata Kirata ta bata Hakuri.
Ranar Hafsah na Kitchen Tana Girki Taga Kiran Barkat din Taji mamaki Bayan ta Daga Sun gaisa Tatambayi yara Cikin Sanyin Murya ta Fara bata Hakuri kan Abubuwan da suka Faru Dagajin muryanta Kasan Tagama yin Laushi Cikin Tsausayawa Hafsah tace mata karta Damu bakomai Ita Daman Bata Taba Rikonta Ba ta yafe mata Har gaban Abada Barkat din Ta Dinga mata godiya gwanin Ban Tsausauyi Sai da Hafsah tayi mata kwallah Tana Tsausayinta ga Ciki ga Damuwa.
Bayan ta Kira Hafsah sai ta Kira Abdullahi Tagayamai ta Kira Hafsah din,sai yaki Daga Kiran ,sai kawai ta Turamai Dogon Sakon Ban Hakuri da kuma Tabbatar mai data Kira Hafsah ta bata Hakuri Daya gani bai Damu Daya Kira ba sai da ya Dawo Gida ya Tambayi Hafsah ta Tabbatarmai Data Kirata ta bata Hakuri kana ya yarda sai da safe kana ya Tura mata Sakom ta Shirya zai zo ya Tafi da ita yau da Daddare.
Da Barkat Taga sakon Abdullahi kamar an Gafartamata Zunubinta Tana ta Murna da Farinciki Data gayama Hajiya Amina Itama sai da tace Alhamdulillah Jin Haka yasa ta Kira Salisu ta gayamai yace Ta isa Barka sai yace ta Tura su Bahiya su Gyara Dakin Barkat din Tunda ya Dade akulle Yayi kura gashinan zuwa Haka kuwa akayi Bahiya da Bahijjat suka je Gidan Dama Barkat ta basu makullin Dakin Suka gaisa da Hafsah suka ce mata sunzo gyarama Barkat Daki ne Hafsah Taji Dadi Sosai Burinta ya Cika Tunda Allah ya Daidaita komai,Sun Gyara komai sun Share Dakin sun goge sun wanke mata Toilent da Sauran kayan Kitchen dinta da sukayi Kura Dama Hafsah bata amfani da kayanta Da nata take amfani Tunda Itama Babu Abunda ta Rasa na Bangaran kayan kitchen wasu suna Daki Cikin kwali Bata Fara amfani Dasu ba Sai Sun Koma Sabon Gida.
Sai Wajen yammah suka bar Gidan Bayan sun ma Hafsah Sallama Suna Tafiya Abdullahi ya Kirata yana Gayamata Dawowar Barkat din tace Eh yanzu kannenta suka Fita sun Zo sun gyara mata Daki karamin Tsski kawai yaja ya kashe Wayar,Ita kuma Barkat koda su Bahiya suka Koma Ta Kira mai Kitso ta Rangada mata Kitso Har kunshi Tayi yayi kyau bakinta yaki Rufuwa Sai Murna Take ko kafin Bayan mangariba Barkat ta gama Shiryawa Cikin Wani Less Dinki Buba Tayi mata kyau ainun Taci kwalliyarta Sai dai Cikin yayi mata Cikas,Su Bahiya suna ta Daukanta Hoto sai ga Yayansu Salisu yazo Ya katsesu yakira Barkat Dakin Hajiya Amina suka Tasata atsakiya Suna Mata Nasiha Salisu yaja kunnanta Sosai ya kuma Gargadeta in ta kuskura ta karayin wani Rashin Hankali sai dai ta nemi wani Gidan ba dai nam ba Bazata kashe musu Uwa ba Barkat na kuka tamai alkawarin Insha Allahu Bazasu kara Kuka da ita ba,sun Ji Dadin haka Hajiya Amina nata sakamata albarka.
Abdullahi kuwa Sai da ya Tashi Daga aiki ya Dawo Gida yayi wanka ya Chanza kaya kana yaci Abinci,Bada mashin Dinsa yaje ba Keken napep ya Hau ya Tafi Gidansu barkat din wanda wannan Shine karo na Farko Daya Taka kafarsa bayan Komawar Barkat din Har Ciki ya Shiga suka gaisa da Hajiya Amina Tana ta godiya da kuma Rokon Hakuri Yace mata bakomai,Bai jima ba yace Barkat ta Fito su Tafi,su Bahiya suka Fito mata da kayanta,Sai ita ta Fito Daga Baya yana Bakin Adaidaitanta yana Kallonta Tana Tafiya da katon Cikinta su Bahiya sun rakota kare mata kallo kawai yake ganin Duk Ta Rame itama sai kallonsa Take Idanuwanta na Cika da Hawaye na kewa da Nadama mai karfi Bai Tankata ba ya Shige Adaidaitan itama ta kama ta Shiga Su Bahiya na Daga musu Hannu suka bar Kofar gidan.
Har suka kai gida Abdullahi bai Tanka ma Barkat ba Ita kuma kunyan mai mgana take ji kanta na kasa ne,Sai da suka kawo bayan ta Fito Daga Adaidaitan Shima ya Fito ya Fito mata da akwatunanta,ya Biya mai adaidaitanta ya wuce Shikuma ya saka Hannu zai Dauki akwatunanta Guda Biyu tayi Saurin Rikomai Hannu Tana Wani marairaicewa Waigowa yayi yana kallonta Cikin Muryan Tsausayi da Nadama Tace"Afuwan My Man....Plz..!
Ta Fada Lokaci Daya Tana kallonsa,Bai ce mata komai ba ganin Haka yasa ta saki Hannunsa ta kama kunnuwanta Duka Biyun Tana Fadin"Ka yafemin Don Allah...Nagane kuskurena..! Tafada hawaye suna Zubomata Da sauri ya Riko Hannayen nata yana Girgizamata kai Lokaci Daya yana Fadin"No..Is ok..Ai kin gane kinyi kuskure ko..? Kuma kin Fahimci inda kike kuskure kin Dawo da niyyar gyara ko..? Kai ta gyadamai tana Zubar kwallah Hawayenta ya Share mata yana Fadin"Karki Damu..Komai ya wuce Yanzu mu Fuskanci sabuwar Rayuwa kawai.."Saurin Rumgumesa tayi tana mai Godiya shi kuma ya Riketa yana Bubbuga Bayanta alaman Lallashi.
Shi ya Dauki Akwatunan da Hannayensa Guda Biyu,Suka Shiga gidan Tana Binshi abaya,Sai Dai Hafsah Taji sallamansu Ta Fito Daman su take jira ita da Su Amira ganin Barkat din suka Nufeta suka Rumgume suna Oyoyo Ga Anty Hafsah baki yaki Rufuwa tana Rike da Noor ta karisa ga Barkat din Tana mata sannu da zuwa ta amsa Cikin kulawa ita ta Riko Hannunta Har Dakinta,Shi kuma Abdullahi ya Bude Dakin Barkat din ya Shigar mata da kayanta kafin ya Dawo Dakin Hafsah din ya iskesu suna gaisawa da Hafsah din,Nan Barkat din Taci Abinci kana Hafsah dasu Amira suka Rakata Dakinta,Basu Dade ba ta mata sai da safe ta Taro su Amira suka Dawo Dakinta Suka Iske Abdullshi yayo wanka ya Sauya kaya zuwa Jallabiya,Bai zauna ba yama Hafsah sallama ya Tafi Dakin Barkat din Chan ma Dayaje Duk Rokon Bam Hakurin ne yace mata bakomai komai ya wuce Shi ya Taimakamata tayi wanka ta gasa Jikinta Suka kwanta Barkat din Ita ta taja Abdullahi da Salonta har ya Biyemata ammh da Farko yana jin Tsausayinta Shiyasa bai nemeta ba ammh ganin ita tana Bukata sai ya saki Jiki suka Raya wannan Daram.
Babu Wanda yasan Dawowar Barkat sai Data kwana Biyu Da Dawowa kana Mariya tazo Gidan Ta ganta ta koma ta gayama Mama,Mama ta nuna jin Dadinta sosai da Subai taji labari tace bata so Haka ba Hafsah tace Wlh ko Daya ai yanzu Tayi Hankali Zuwanta Gida yasa ta kara sanin Waye Mijinta kowama Dayaji ta Dawo sai yace kila yanzu za"a zauna Lafiya Tunda an Gogi jigidan Juna Illai kuwa Domin Barkat kamar ba ita ba Tayi bala"in Sanyi Tsakaninta da Hafsah kuwa sai dai girmamawa Kishinta kuma ta kaishi karkashin Ranta ta Boye ta sadda kai tana Bin yadda Hafsah din ke tafiyar da Abdullahi.
*ASSALAMU ALAIKUM BUDADDIYAR WASIKA ZUWA GA MASOYANA MASU KARATUN LITTAFIN MASIFAFFAN NAMIJI...NAJI WASU MGANGANU NA YAWO WAI NI NACE BAZAN KARISA MASIFAFFAN NAMIJI BA YA KOMA NA KUDI..? WASU HAR SUNA FADIN MAGANGANU MARASA DADI AKAN HAKA TOH BARI KUJI NA GAYA MUKU TUN KAFIN NA FARA TSARA LITTAFI ZAN FIDDA NA KUDI ZANYI SHI KO FREE KUMA IN NA FARASHI BANA SAUYAMAI ALAQA,MASIFAFFAN NAMIJI TUNDAGA FARKONSA HAR KARSHENSA FREE DAMA NAYI NIYYAR YINSA KUMA RA"AYINA BAI SAUYA BA,AM JUZ JOKKING DANACE ZAN HADESHI DA RA"AYI NE KO BURI MU HADE A PAID GROUP,AMMH WASU SUN MIN MUMMUNAR FAHIMTA SUNA TA FADAN ABUNDA YAZO MUSU ACIKIN RANSU WASU KUMA SUNA TA BULAYIN CIGIYA NE,TOH ABU DAYA ZAN CE KO 10K KU KA SAKA KUKA SIYA LITTAFIN RA'AYI NE KO BURI..? BA KU BIYANI ADADIN WAHALATA BA WLH BALLATANA WATA #200 WANDA BAZATA KARA MIN ARZIKIN DA NAKE DASHI BA MASIFAFFAN NAMIJI LABARINA NE KUMA NI NAKE RUBUTASHI BAN TABA FARA LITTAFI BAN KARISA SHI BA WANNAN MA SAI NA SAUKESHI DA YARDAN ALLAH,IN MUTUM NA RA"AYI YA SIYA PAID BUK DINA IN BAYA RA'AYI YA BARSHI BA"A DOLE NIDAI ABUNDA NA SANI NAUYIN DAKE KAINA ZAN SAUKESHI KUMA HANNUN DAYA RUBUTA MASIFAFFAN NAMIJI SHI YAKE RUBUTU RA'AYI NE KO BURI SO DUK DAYANE AWAJENA INA GODIYA MASOYANA WADANDA SUKAYI TA PAYMENT DOMIN NUNA MIN KAUNARSU WADANDA KEDA NIYAR BIYA ALLAH YA BASU IKON BIYA WADANDA BASU DA NIYYAR BIYA SUMA ALLAH YA BASU IKON KARANTA FREE DIN IN MUNYI RAYUWA BA TILAS KUMA BA DOLE SAI DAI BAN JI DADIN YADDA WASU SUKA KASA FAHIMTA TA BA..*
*Janafty...*
4/9/21, 2:00 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*
*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!
~Alhamdulillah...Dukkan Godiyata Ta Tabbata ga ALLAH shugaban Halittun Duniya...Salati Tare da Rahma Gafara Aminci Su Tabbata ga Annabin Rahma Annabi Muhammad Sallalahu alaihi wasallam Shida Iyalansa da Sahabansa gabadaya..~
*041*
Tunda Barkat ta Dawo Gidan bata kara yarda Tayi zaman Dakin data saba abaya ba,Tun Safe Zata Fito Bayan ta Gyara Dakunanta,Tafito tace Tana so Ta karbi Wani aikin ta Taya Hafsah ita kuma Hafsah sai taki Bata Daman Tun Dawowarta Tace mata Sai ta Haihu ta gama Jegonta kana zata bata Girki ammh Kwanan Miji yana nan ayadda yake in ya kwana Biyu Dakin Hafsah,Sai ya koma Dakin Barkat din ya kwana Biyu,Bai saka musu baki ba sai da Hafsah Ta nemi Daya koma kwana Dakin Barkat da kwana Gabadaya Saboda Tsohon Cikinta gashi kuma Haihuwan Fari kada wani Abu ya taso ba kowa a kusa Da ita.
Lokacin da Hafsah ke Fadamai Haka yana Zaune a kasan Cafet Dinta ne ya Tankwashe kafa yana Cin Tuwon Semo miyar kubewa Bushashiya wacce Hafsah Ta Dafamai Da Daddare,Ita kuma Tana Gefensa Zaune Rike da Noor tana bata Nono Amir da Amira kuma Suna Dakin Barkat tun Dazu Chan ma Sukayi Sallar mangariba Yanzu Chan suke zama Tunda Taja yaran ajiki Sosai.
Yana kai Lomar Tuwo bakinsa yana kallon Hafsah a karkace Gefe Daya na Cikin Zuciyarta Najin Haushin Shisshigin Hafsah na Wani Lokacin..Ina Ruwanta..? Waya aiketa Shiga Hurumin da ba nata ba bai gama mamaki ba ta katseshi da Fadin"Har ma Dazu nake ma Barkat din Zencen tadai Nuna min ba komai ammh ai nima Mace ne nasan Yanayin,kaga kuma Haihuwar Fari ce Gwara asamu wani kusa da ita Tunda bamu san Wani Yanayi Haihuwan zata zo Dashi ba Gashi kuma kai ba barinta Zakayi ta koma Gidan Gaban Hajiyarsu ta Haihu ba ko Zaka barta ne..?
Ta fada Tana kallonsa Mamaki ya kara kamashi bai samu Zarafin mgana ba sai da ya Koshi da Tuwon kana ya Ture Kololin gabansa yaja Roban Wanke Hannun Dake gabansa ya Wanke Tas ya saka Tissue ya Goge Bakinsa Tsaf kana yayi Gyatsa Lokaci Daya da Hamdala yana Fadin"Alhamdulillah..."
Yafada Lokaci Daya yana Mike kafa,Kansa ya jinginar kan Hannun Kujera Lokaci Daya yana Balle Botorin Rigan Shaddan Dake Jikinsa Dama Yana Shigowa da yunwa ya Dawo Abincin ya Fara ci kafin Wanka, Hafsah Ta Karkace kai Tana Fadin"Baka ce komai ba Abban Amira..Ina ta mgana..?
Waigowa yayi yana kallonta kafin yace"Na"am kika ce me..? Ban ji bane..! Ya fada yana Zabga Hamma Galala Hafsah Tayi Tana kallonsa Kafin tace"Kai Abban Amira yanzu Duk mganganun da nagama yi baka Jini ba..? Kai ya gyada mata yana Fadin"Ban ji ba sake maimaitawa.."Baki Hafsah kawai Ta Gimtse Ta Cigaba da Noor Nono ammh ta bata Ranta Sai Abun ya bamaa Abdullahi Dariya,Ganin yadda Hafsah Tasha kunu sai ya Matso Kusa da ita yana Fadin"Meye kuma na Fushi Hafsatun Abdullahi..? Uhmm gayamin yanzu ina Sauraranki kisan Dazu Ina cin Abinci Kuma kinga ba kyau ma kana Cin Abinci kana mgana..! Yafada yana Sosa Sajensa Cikin Dariyan Dayake ta Dannewa
Jin Haka yasa ta waigo ta kalleshi Tana Koramai Jawabin Da tayi mai Tun Farko,sai da takai aya kana ya Dage mata Gira yana Fadin"Duk wannan aikin waya saka ki ko waya aike ki..? Hafsah tace"Bangane waya aike ni ba Abban Amira gani nayi Hakan ne ya Dace kada ace mun kyaleta ita kadai.."Karamin Tsaki Yaja yana Fadin"Ace mana..Waya Damu..? wanda yaga an kyaleta yazo ya Taimaketa mana..ke banda ma Tsabar Saka ma kai Wahala da kuma aikata abu ba"a saka ka ba Ni kin yi mgana Dani nace Miki Eh na yarda..? Bafa ki min mgana ba ammh Har kinje kin ma Barkat mgana,ai Tunda kinyi gaban Kanki kin kyauta ammh Nidai bada yawuna ba ban kuma amince ba..Raban kwana ne da kukayi zan Dinga kwana Bibbiyu dakin kowaccenku kamar yadda kuka Tsara Mganar kuma Wani Abu ya Faru Allah ke Tsarewa kuma ga waya Cikinmu Duk wanda ta Kira zai kai mata agaji,Bana son Mganar da bazata yuyu ba..!
Yafada yana Daure Fuska Kwabe Fuska Hafsah Tayi Tana Fadin"Haba Abban Amira...b..."Bana son Wani mgana Don Allah ina Ruwanki wai da ita..? Malama kiji da kanki kawai Mganar kuma ko zata koma Gida ne,ta Haihu ki Tambayeta indai tana son komawa Fine ni bani da Matsala...'Yafada yana Mikewa Cikin Mika Hafsah ta Bishi da kallo Ta kasa mgana kafin ta kada kai tace"Shikenan Tunda Haka kace...Ammh Ban ji Dadin yadda kamin Wannan Fahimtar ba.."
Shima kai Tsaye yace"Nima ban jin Dadin yadda kike yanke min Hukuncin batare da Sanina ba..Ki Tsaya iya matsayinki kawai malama mganar kuma Taya kwana nidai ga Abunda nace in kinga Zaki iya Taimakawa malama Hafsah sai Duk Ranar girkin ki ki Rika Tafiya Dakin Barkat kina Tayata kwana Fakat.."Da mamaki Hafsah Tace"Kai kuma fa..?
Yana Mirmishin Mugunta yace"Ina Inda ya Dace mana...Domin ba inda zani ki Tafi Dakin Wata Taya kishiya kwana Ki kwana Cikin Tsinuwan mala'iku Domin nidai bada yawuna aka Tafi ba Atoh.."Daga haka ya Shige Cikin Bedroom din yana ta Fada da kallo Hafsah ta Bishi kafin ta kadai kai ta Mike Tana Rike da Noor wacce tayi Barci Ciki ta Shiga Itama ta Shimfidar da Noor Daidai Lokacin da Abdullahi ya Leko Daga Ban Daki yana Fadin"Ina Ruwan zafin... ?ko baki saka bane naga Kittle din bakomai..!
Ko kallonsa Hafsah batayi ba Cikin Kufuluwa tace"Zan saka kenan suka Dauke Wuta...Sai dai in na Dafa maka a Gas.."Tafada tana kokarin Ficewa Daga Dakin,baki ya Rike yana Fadin"me yayi zafi..? Barshi zan yi da Ruwan sanyi ni ba bakon zafi bane..Ammh fa Dole akamin ba Daidai ba Zan Fada.."Yafada yana Komawa Cikin Toilet Din Lokaci Daya da Rufo Kofa Hafsah najinsa ta Fice tamai Banza Sanin Halinsa Tunda ya kuma Turtse Shikenan kuma.
Dakin Barkat ta Shiga ta iske Amir yayi Barci Amira ce Kadai Batayi ba Suna ta Hira da Barkat wacce Take zaune ga Katon Cikinta wanda yayi kasa alamun Haihuwa ko yau ko gobe,Sannu Hafsah Tayi mata kana ta kama Amir takai shi yayi Fitsari takai Daki ta kwanta kana ta Dawo tace Amira taje ta kwanta sai da Amiran ta Fita kana Hafsah tayi ma Barkat Zencen yadda sukayi da Abdullahi Mirmishi kawai Tayi kafin tace"Dama fa naji ki ne kawai Anty Hafsah..Bakomai kamar yadda yace ga waya In naji wani Abu zan Kira Insha Allahu.."
Hafsah dai Duk Taji kunya Ta Dade Dakin Barkat din Har wajen karfe goma kana ta mata sai da safe ta Fice zuwa Dakinta,Sai da ta kulle kofarta ta kashe Duka Wutan Dakunan ta leka Dakin Su Amira ta gyara musu kwanciya tayi musu addu"a kana ta Shiga Bedroom dinsu ta iske Abdullahi har yayi Barcinsa bai Jira ta ba Bata damu ba Tunda Itama Taji Haushin yadda ya Nuna mata iyakarta Ta Fada Tiolet tana Jin Takaichin Abun Har Cikin Ranta.
Shi kuwa Bangaran Abdullahi ya Yi ma Hafsah Hakane Domin ta Kiyayeshi,In yana kyaleta gaba Sai Ta Rika bashi ma Umarni yana Bi,wani Lokacin Wajen Tsausayinta Cutar dashi Take bata sani ba,Shiyasa ya Taka mata Burki Tun yanzu kafin abun yayi gaba kuma ya kasa Controlling din Abun.
Washegari Haka Hafsah tatashi Tana wannan Fushin Abdullahi kuwa bai bi ma ta kanta ba ya nuna mata ma bai san Tanayi ba Dole ta Tattara Fushinta ta watsar ta saki ammh Duk da Haka bata Dandara ba Ranar da Daddare bayan ya Daawo ta kara Zuwar mai da mganar Yayi ma Hajiyarsu Barkat mgana Ko Kanwarta Data Dawo Gida Aina Aba Barkat din ta zauna mata kafin ta Haihu Tunda ta Dawo Gida Ta gama Candy,Abun sai ya koma Bashi Dariya da Tsausayi da wani kaunar Hafsah Acikin Ranshi Yana Tunanin samun Mata masu irin Zuciyanta ba, sai an Tona bai mata gardama ba,Yace zuwa gobe zai je gidan yayi mgana da Hajiyan Amina Hafsah Taji Dadi Sosai Tayi tamai Godiya Shi kuma ya Fanshe da cewa Sai ta Bashi Tukwaici,hakanan ta Saki Jiki ta bashi Abunda yafi so aduk Duniya ya kwana yana Moran Abunsa.
Washegari bayan ya tashi Daga Wajen aiki ya Nufi Gidansu Barkat ya samu Hajiya Amina ya Roketa alfarman da basu aron Aina Saboda ta Rika Taimaka ma Barkat din,Hajiya Batayi Gardama ba ta amince Daman Barkat din na Ranta Bai baro Gidan ba sai da Aina ta Hada kayanta ya Daukota suka Taho Tare sai dai Barkat ta gansu kwatsam Tayi ta Murna tana ma Abdullahi Godiya yace ta Godema Hafsah Domin ita ta kawo Shawaran ya Dauko mata Aina Din Lokacin Daya Fada mata Haka taji wani iri Ammh sai ta Danne Bata nuna ba tabi Hafsah Har Daki Tayi mata Godiya ita kuma Sai ta nuna bata ji Dadin yadda Abdullahi ya Fadama Barkat din komai ba,Har sai da ta gayamai Cikin Gatse yace"Toh karya zan yi..? Ke fa kika Kawo Shawaran kuma nayi aiki da ita Banga wani Abun mgana ba Mata dai bakwa Raina Abun Tsegumi..! Jin yace Haka yasa ta kama bakinta ammh ta sani Har ga Allah ba macen da zata ji Dadin Irin Abunda Abdullahi yayi ace Mijinka bai da Tunanin Dauko wacce zata taimaka maka sai Kishiya ta Bada Shawara hakan bai Dace ba ammh Dayake Abdullahi Audu ne Dole ta kama Bakinta ita kanta Barkat bata isa ba Domin Yanzu lallabashi Take bata Fatan Abunda ya Faru da ita ya kara Faruwa akan wata ma bama ita ba.
****
Zuwan Aina da kwana Hudu Barkat ta Haihu,Wanda Haihuwar ta Rana ce,Ranar laraba Abdullahi baya Gidan yana Wajen aikinsa Hafsah ne kadai agidan sai Mariya Datazo sai Aina sai ita Barkat din Tun Safe