Advertisements
Chapter 17 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   17 / 48

48K to 51K   out of 143.7K words

da Nazifi ba yadai ce mata sun Biya wani waje ne,Bata damu da Tambayarsa ba sanin ko zata mutu bazai gayamata ba sanin Halinsa na Zurfin Ciki da Rike sirri koda banashi bane balle na Amininsa Nazifi.

Washegari kuma Su Abdullahi suka Tafi Danja Daurin Auran Diyar Mijin Goggo Habiba amotar Nazifi dashi da Abdullahin da Nazifin da Mama sai Inna Abu da Baba wada sai Auwal sukaje sukayi samu Daurin Auren, wajen uku na Rana suka kamo Hanya suka Dawo Suna Dawowa Nazifi ya wuce Kaduna Bayan ya Kira Salisun ya mai Bayanin ba wacce tayimai Salisu bai nuna damuwarsa ba ammh acikin Ransa baiji Dadi ba sam Haka ya Kira Hajiya Amina ya gayamata Cewa Nazifin yace ba wacce tayi mai Hajiya ita kanta Bataji Dadi ba ammh sai ta nuna Allah yasa Hakan ya zama alheri,Da su Bahiya sukaji labari basu ji Dadi ba Musamman Bahiya,Bahijjat kuma ko ajikinta Ballatana ma Aina Da bata damu ba Barkat kuwa Bata bari kowa ya gane yanayinta ba ammh a zahirin gaskiya Jiya ta kwana da mafarkin Abdullahi wanda ya Shiga Cikin Zuciyarta Lokaci Daya batare data sani ba.


*******

Bayan Sati Biyu Tsakani Sai ga Waya Daga kano Cewa Anty Hadiza ta Haihu yan Biyu Duka Maza,ammh C.s akayi mata tana asibitin Murtala Aminu specialist Hop,Dake kano,Ammi ta Kira Hafsah Tana Fadamata Ihun Murna Hafsah ta saki Cikin Farinciki Dadi kamar ya kasheta Abdullahi na Office sai ga Kiran Hafsah tana gayamai Haihuwan Shima yayi murna Sosai Cikin Zolaya yace"Hafsatuna nima ko yau na Bada Himma na baki ajiya kwan Haihuwa guda Biyu ne..? Ina son Twice Sosai fa..".

Kunya ya kamata ta saki Dariya Tana Fadin"Allah ya bamu Masu albarka Yace Amin..Cikin Shagwaba tace"Abban Amira gobe zan Tafi ko..? Tunda ma su Amira na wajen su Ammi haryanzu.."Cikin mamaki Abdullahi yace"Ina zaki gobe..? Cikin Sauri Hafsah tace"Kano mana Abban Amira Kaga fa C.s akama Anty Hadizan yau Ammi tace Zata Tura Inna Asibi tatafi Chan wajenta Ni kuma ba sai gobe na tafi ba.."

Cikin Mamaki yace"Ki dawo yaushe kenan..? Hafsah tace"Wai da Bayan suna kaga nesa ne kada ayi Tafiya Rarrabe.."Baki kawai Abdullahi ya Rike yana Fadin"Hakane..Sannu Uwar Suna ko nace na Sha"ani..Allah kaimu.."Daga haka kawai ya yanke Kiran Ita kuma Hafsah jin Haka yasa ta Shiga Murna nan da nan Ta Hau Shirin kayanta bayan ta gama ta Kira Subai ta Fadamata itama tayi murna Tace insha Allahu zata je suna Nan Hafsah ke gayamata gobe zata tafi sai bayan suna zata dawo Subai ta rike baki Tana Fadin"Ke don Allah shi ya Abdullahin ya barki..?

Hafsah tace'Nima nayi mamaki kila Don suna Shiri da Anty Hadizan ne..'Subai tace"Sai dai haka..Allah sarki Allah ya bata Yayanta nawa yanzu..? Hafsah tace"Uku ne,da wadanan Yan Biyu making 5 kenan..."Subai tace'Masha Allah Allah ya rayasu"Daganan suka yanke Kiran Daga ita Mama ta Kira ta gayamawa Mama tace Ammi ta kirata yanzu Umman Sadiq ta kira itama tace Ammi ta Kirata yanzu ta gayamata,Tace insha Allahu zata yi kokari tazo Zaria Allah barshi sai ta karisa kanon.

Duk wanda ya kamata yaji Haihuwan yaji Hafsah kuwa har Daddy ta Kira tana mai Barka,Ya Dinga Tsokananta yana Fadin Yana Jiranta wata Shekara Duk kunya sai ya kamata,Abdullahi ma Daya dawo ya Kira Daddy da Ammi yayi musu barka Harda Anty Hadizan wacce har ta Farfado Tun da Rana Tunda tun Cikin Daran Jiya ne akayi aikin,Inna Asibi har ta isa Tun safe,Abdullahi yana jin Hafsah na Fadama Anty Hadizan gobe tana Kan Hanya Har Anty Hadizan tana Cemata sai suzo tare da Matar Baba Mustapha Hajiya gaje Domin yanzu suka gama waya tace suna tafe gobe Marwan zai kawota Babban Danta.


Har jinta yayi tana Fadin sai ta Bisu suzo Tare,Abdullahi bai nuna mata komai ba adaran Ranar Haka suka Raya wannan Daran cikin Farinciki da Soyayyah Tun Safe,kuma Hafsah tatashi da Gyaran Gida tayi Breakfast da wuri Ta Shirya tayi wanka Babban akwatinta ta Cika da kaya Tun safe ta Kira Mama gaje ta gayamata zata Bisu tace tayi kokari ta Biyo su Tafi tare,Abdullahi bai ce mata komai ba sai da ya Shirya zai tafi Office kana Hafsah tace"Abban Amira baka ce min komai ba.."?


Yana Daura Tek tie dinsa yace"kamar name..? Cikin mamaki tace"Baka ce min komai kan Tafiyata kano yau ba kuma baka bani kudi a hannuna ba Haka zan tafi..?.
Kai tsaya yace"Haka zaki Tafi mana Tunda ke kika Tsara Tafiyar naki.."Tsuru Hafsah tayi mai da ido cikin Rawan Murya tace"Ban...ga..ne mganar ka...ba Abban Amira.."?

Bai bama Mganarta muhimmanci ba yace"Ni nace ki Shirya ki tafi kano kije ki tare sai bayan Suna..? Ke kika Tsarama ma kanki Tafiyar bazan hanaki ba Saboda yar"uwanki ce ta Jini in na Hanaki bazaki ji Dadi ba ammh in ni zan Tsara miki Tafiya sai nace ki bari sai ana gobe suna ki tafi In akayi suna ki Dawo yau kuma sai kibisu kije ki Dubata ki Biyosu ki Dawo duk wanda kika zaba bazan Hanaki ba."

Hafsah taji ta Raina kanta Cikin Wani Irin murya tace"Ammh ai Kaasan Anty Hadiza bata da wata Kanwa sai ni ko..? Bai kamata na Tafi ba tun yau..?

Yana Daukan key din Mashin dinsa da jakar Brief case dinsa yace"Wa kika ji yace bai kamata ba.? Ya kamata mana Sosai.."

Hafsah takada kai kafin tace"Toh kagani..."Yana yar dariya yace"Shikenan Allah ya kaiku lafiya kima Mai jego barka.."Daga haka yasaka kai zai Fice Cikim mamaki tace"Abban Amira.."

Cak ya tsaya Lokaci Daya ya waigo yana Fadin"Uhmm..Menene..?

Kanta na kasa tace"Baka bani komai ba...Kasan kuma bana yi Tafiya bani da kudi a Hannuna ba.."

Kai Tsaye Abdullahi yace"Bani da kudi yanzu a Hannuna...Tunda ke kika Shirya tafiyanki na zata kina da kudinki ne Shiyasa kikaga ban hanaki ba."Yafada yana Kafeta da idanuwansa Dago kanta tayi Cikin Rau rau tace"Abban Amira waya bani kudin.? Kai tsaye yace"Ina zan sani..Nifa nazata kina da kudi ne Tunda kika Shirya tafiya yau.."..


Idanuwanta suna kawo kwallah tace"Yanzu dai bazaka bani ba kake Nufi ko Abban Amira..?

Kai Tsaye yace"Gaskiyan mgana ayanzu dai bani dashi..Shiyasa nace ki bari Zuwa ana gobe suna Lokacin na samu albashina sai na baki Ishashen kudi ammh yanzu kam ko sisi bazan baki ba keda kika Shirya tafiyan Dama baki Tanadi kudin da zaki rike bane..? Yafada Cikin nuna mamaki yana yar dariya hawaye ya kawo idanuwan Hafsah tayi maza ta Share Lokaci Daya ta kada kai tana Fadin"Bakomai nagode..Bakomai yajamin ba sai Rashin sana"a


Dariya ta kaama Abdullahi sai ya kanne yana Fadin"Allah Madam..? To ko zaki Jira in kin Kafa sana"ar taki kin samu Riba sai ki Tattara ki tafi... ? Ya fada yana mata Dariyan mugunta Takaichi ya kama Hafsah ta kadai kawai ta juya zuwa Ciki Tana Fadin"Zan tafi..Insha Allahu Tunda dai ka amince bazan Rasa yadda zan yi ba..

Shima kai Tsayen yace"Shikenan Allah kiyaye Hanya ni ba bakon zafi bane na amince ki Tafi..Ammh kuma ban yarje miki kije kina Roko ko baran kudi ba Tunda ban ce ki Tafi Dole ba Fitinarki ce atoh.."Daga haka kawai ya saka kai ya fice yana mamakin Taurin kai da Rashin Hankalin Hafsah na wani Lokacin..












*Janafty.....*
4/9/21, 1:55 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!





*017*




"Da kallon Mamaki Ta Bishi Lokaci Daya tana Dauke Kwallar Idanuwanta kada kai tayi ta koma Cikin Bedroom dinta ta Dauko Hijabinta ta saka Hade da Takalmi sai Karamar Jakarta Data Dauka da wayarta,Key din Gidan ta Dauko da Akwatinta Inda ta saka Kayanta bata da ko Sisi sai Naira Dubu Daya ita kawai ta Dauka ta Tura Cikin Jaka tana jin wani karfin gwiwan Tafiya da kuma Takchin Abunda Abdullahi yayi mata yau.

Fitowa Falo tayi  Bayan ta kashe Wutar Cikin Dakin.

Sai da ta kashe komai na Wuta kana Ta kulle Dakin nata Tana Cikin Kulle kitchen sai ga Yunusa almajiranta yazo sallamansa kawai Tayi saboda Tayi Duka ayyukanta,Tana da wata Naira Dari,ta mikamai tace bazata dawo yanzu ba sai bayan Sati Daya,amsa yayi yayi Godiya Kusan Tare suka Fita ta Kulle Gidan Yunusa ya Daukan mata akwatin Zuwa Bakin Titi ta samu Adaidaita zuwa Gidan Ammi.

Tana Cikin adaidaitan ne ta Kira Wayar Mama Bayan sun gaisa take gayama Mama tafiyarta Kano Ita kanta Mama tayimamaki Sosai ammh bata Furta ba ta mata Fatan Kaiwa lafiya da kuma alkawarin suna nan zuwa Ita da Inna Abu gobe ko Jibi,Ahaka suka yanke Kiran Hafsah sai da Ammi ta ganta da akwati Riki Riki Nan ta Shiga Fadan wani Rashin Hankali ne Jiya Daga yin Haihuwa,yau kuma zata bar Mijinta taje chan ta Tare,Tura baki Hafsah ta kama yi sai Hawaye Dama ga Takaichin Abdullahi ga ita kuma na Ammi.

Cikin Tura baki da Hawaye Hafsah ke Fadin"Shifa ya barni Ammi.."Ammi tace"Ke kika matsamai wlh..Haba Hafsah baki da Hankali wlh Tsiyata Dake Wauta..Jiya fa akayi Haihuwan nan,Kuma Hadizar bata gida Tana asibiti fa,kuma Asibi tana chan Tun Jiya banda Rashin Hankali basai ki bari zuwa Jibi ko Gata sai ki Tafi ba.."Kuka Wurjan kawai Hafsah ta saka Alhaji Hamza ya Fito Daga Dakinsa yana Fadin"Zinaru kin Cika Fada wani Lokaci ba tace shi Abdullahin ya yarjemata ba..?

Ammi ta waiga Tana kallonsa Lokaci Daya tana Fadin"Ammh Daddy Kasan dai matsamai Tayi ko..? Jiya ne fa Hadizan ta Haihu...? Yanzu kwana nawa zatayi a kano kafin ta Dawo.. ? Cewa zatayi sai bayan suna zata dawo fa.?Hafsah tatashi da Gudu ta karisa Jikinsa ta Rumgumesa tana Kuka Riketa yayi yana Dafa Kanta alamun Lallashi.

Kan Daya Daga Cikin Kujerun Falon ya Zaunar da ita,Shima ya Zauna yana Fadin"Sai me..? Ina Ruwanki ba mijinta bane ya barta..? Don Allah ki Dinga Saussauta ma Ranki Shi kanshi ya sani Itace kanwarta Duk Duniya guda Daya domin ya Barta Taje na wasu kwanaki ai ba Laifi bane Don taje..? Inda bata Kamata ba kinsan bazata je ba ...."Ammi ta Kada kai Tana Fadin"Ai Shikenan...Allah ya bada sa"a Dama baka san Laifin yarinyar nan sam.."

Daddy yace"Ba haka bane Zinaru..Mijinta ya barta baki da ikon Hanata..Gashi a banza kin sakamin Mamana kuka.."Yafada yana Share mata Hawaye Saboda Takaichi Ciki Ammi ta Shige tana Korafi Hafsah ta Kalli Daddy tana Gaisheshi ya amsa Yana Shafa kanta Cikin Farinciki Hira suka Fara sama Sama sai ga Sallaman Hajiya gaje da Marwan nan Ammi ta Fito suka gaisa tayi musu Barka basu wani Jima ba, suka Tashi,Ammi ta bama Hajiya gaje sakon Kayan wanka da maganin Jego tace ta kaima Hadiza ita kuma Hafsah 10k Daddy ya bata kamar yasan bata da kudi Ta karba Cikin Godiya acikin Ranta Tana Fadin Babu Uba Tamkar Mahaifinta.

Wajen Azahar suka isa Cikin Asibitin Murtala Aminu Specialist Hop,kano,Sun iske Anty Hadizan ma Taji Sauki Sosai Anty Asibi ke zaune da ita da Kishiyar Uwar Mijinta sai bayan zuwansu ne ma Tatafi Gida ta Dawo,Nan suka wuni a asibitin sai bayan La"asar Su Hajiya gaje suka koma Suka Bar Hafsah anan wanda Hadizan Taji Dadin ganinta Domin Duk Duniya Tana Bala'in ji da kanwarta Hafsah.

Sai Dare kana Mijin Anty Hadizan yazo ya Dauki Hafsah zuwa Gida,Gidan Hadiza aljannar Duniya kenan wajen Tsaruwa da Haduwa,Ita ta kwana da Yara Duk da Suna da mai Kula dasu harda mai Girki da Safe wanka kawai tayi ta Dauki Abun karyawan su wanda dama Tuni an Hada,sai da Taci kana Direba ya Dauketa Zuwa Asibiti,Dayake yaran sun Tafi Makaranta Tun safe.

Hafsah chan take wuni Asibitin,Da Rana kuma Asibi ta koma Gida ta Huta Da Daddare kuma Hafsah ta koma Gida ita kuma Tazo ta kwana da Hadizan,Kwananta Hudu a Asibitin aka sallameta ta koma Gida Har kuma Tsawon wannan kwanakin Hafsah ko Sau Daya bata Kira Abdullahi ba Shima bai Kirata ba,Saboda ta Dau Fushi Dashi Sosai,Shima sai ya Kyaleta kawai Yana ganin taso ta bata ma kanta ne rai ne kawai.

Washegari Sai ga su Mama da Inna Abu,sun zo wuni sukayi sai Bayan La'asar suka Tafi Bayan Mama tayo mata Yaji Inna Abu kuma tazo mata da Kubewa da Kuka,Sai Zogale Bushasshiya,Sai Sakon Abdullahi Turamen Atamfa Biyu da Rigunan yara Biyu sai Sabulan wanka da klin wanda Kudin ya bama Mama ita kuma tayi Siyayyah ta kawoma Hadizan Anty Hadiza nata Godiya Matuka da alherinsu Da zasu Tafi ta Hadasu da Direba Tace ya kaisu har Zaria.

Hafsah tasha Mamakin ganin Sakon Abdullahi,wato Shima Fushi yake da ita kenan, Kuma da gasken yake Baiyi Niyyar bata komai ba Aranar sai Ranar da yayi Niyya kenan Tana jin Anty Hadizan na Fadama Mijinta Sakon Mijin Hafsah ne,bata nuna mata ba Tana Tunanin kila ta san da Sakon alhalin ita bata san komai ba kuma bata Fadama kowa Abunda ya Faru Tsakaninsu ba sai kawai tayi Fuska Ta Nuna ma Anty Hadizan tasan komai saboda karta gane akwai matsala Ita Hadizan ma Bata da Lura ne ammh yaci ace ta Fahimci ko Waya basu yi.

Ana Gobe suna Iyalin Gidan Baba Mustapha ne,suka zo Ranar suna kuma sai ga Subai"atu da Jidda,Mariya kuma bata samu Zuwa ba sun Fara pratical a Asibiti,sai Umman Saddiq Datazo kwananta Daya a zaria suka Wuto Tare,Kwana sukayi sai washegari suka Koma,Anyi suna Lafiya an tashi lafiya an ci an sha mai kyau Raguna Uku aka yanka da katon Sa Yara sunci Sunan Abdulwaseen da Abdulaseem,Hakika Dangin Mijin Hafsah sun ma Hafsah kara Sosai sunzo kuma sun aiko da Abun arziiki,Umman Sadiq da Turamanta Biyu harda kudi 5k Shiyasa da zasu tafi,Itama ta Hada musu komai na Suna,Ta aika ma Mama Turmin zani da Inna Abu sai Umman Sadiq wacce Ta karba Dakyar,Ita kuma Hafsah sai bayan Suna da kwana Biyu ta Dawo chan ta bar Inna Asibi Sai Anty Hadiza tayi Sati Biyu kana Zata Dawo.

Koda La"asar tayi Tana Cikin Gidanta,Agajiye ta Dawo Shiyasa bata Fara ma wani aiki ba,Ammi ta Kira tace mata ta Dawo daman Ammi ke ta matsa mata ya kamata ta Dawo Gidan Mijinta,Dayake Abdullahi jiya yaje Shida Nazifi suka mata Barka ita da Daddy sun Dade sai da sukaci abinci kana suka musu sallama suka tafi,Bata iya Tsinana komai ba sai Bayan da Ta iddar da sallar Mangariba Kana ta Shiga Kitchen ta Sulala Taliya Dama Tazo da miya Daga kano,Tana gamawa ta Shiga wanka Bayan ta Fito ta saka Wasu Riga da sikat yan kanti ta yane kanta da Vail din gyale,Tana gama Shiryawa Ana Kiran Sallar Isha"i sai kawai ta Shinfida sallaya ta Tada salla Tana idarwa Ta Dauko wayarta ta Fito Falo ta Zauna ta Kira Auwal tace In ya tashi Daga Shago ya biyo ta Gidanta zata bashi sako yace mata yau ma bai je shago ba Yana Hanya ne zai Dawo daga makaranta ya tsaya yin wani abu ne yasa yakai Dare.

Kafin Auwal yazo tatashi ta Zuba Abincin Cikin wasu kololinta masu kyau Umman Sadiq ta sama Abinci Tunda tana nan bata Tafi ba tana Jiran Bikin Autan Goggo Habiba da za"ayi nan da kwana goma,Dayake batazo da yara ba,Ko Zahra gida ta barta saboda makaranta,tazo da Nama da yawa Shima ta Diban ma Umman Sadiq din da Mama sai Atamfofi Guda Biyu Cikin wanda Anty Hadiza ta bata Bayan kuma Dinkunan da tayi musu Na Fitar suna Kala uku Dataso ta hada harda wanda Zata karama Umman Sadiq sai kuma Tabari sai Umman tazo ta bata.

Ba Dadewa sai ga Auwal yazo nan yaci abincin Shima Suna Hira sai wajen goma Saura yamata Sallama ta bashi Sakon Turaman kuma tace ya bama Mariya Daya Jidda Daya,Sauran kuma tace yakaima Mama,Ta hadamai da 1k tace yayi kudin Mota ya Rike Sauran Dayake ko Kudin da Daddy ya bata bata taba baGashi kuma Anty Hadizan ta kara mata 10k da zata Dawo.

Auwal yana Zuwa Gidan Mama yaga Ya Abdullahi achan ganinsa da kaya Niki Niki yasa Mama ke Tambayansa Daga Ina yace Daga Gidan Ya Abdullahi,nan ya mikama Mama da Umman Sadiq sakon Anty Hafsah,sai Sakon su Mariya Tsalle suka kama da Murna,Ya Abdullahi na gefe yayi kamar bai ji su ba,Mama ta karba Tana gani tana ta Godiya Umman Sadiq ma Tana ta Tayasu Godiya Mama ta Bude baki tace"Kai Wlh Hafsah da iyayenta Mutanen kwarai ne...Kinga da zamu Taho Abunda ta bamu Nama Dayawa kuma gawani Hafsah ta karo mana Bayan Danyen da Ammi ta aiko mana Jiya.."

Umman Sadiq tace"Ba shakka wlh..Haba ai Hajiya Zinaru kam sai Fatan gamawa da Duniya Lafiya Macece da tasan Dattako da Mutumtata da kuma Zumunci"Mama tace"Sosai...Na Dora Turamanta ba adadi acikin Gidanan.."Nan suka yi ta yaba kyawawan Halin Hafsah dana iyayenta Jidda da dai da Mariya sai Murna suke Abdullahi kuwa na gefe kanzil bai ce ba sai da yagama Danne dannen wayarsa kana ya mike yayi musu sallama ya wuce gida Su Amira dai na gidan Ammi wajen sati Hudu kenan Suna ta shan na gidan Ammi.


Sha Daya saura Ya Shigo Gidan Tana zaune afalo tana kallon Tashar Bw,Dayake akwai Wuta Lokaci,Tana kallon maimaicin Seris Flims din da suke Haskawa Mai Suna Ameelatus Sirriya,tana son Shiri Sosai take kallonsa Bai cin ma an wuceta Lokacin datafi kano bata samu kallo Sosai ba,Tana jinsa ya saka Mashin Dinsa Cikin Dakin nan ya Rufe ya yi sallama Lokaci Daya yana Sawo kansa Falo Hannunsa Rike da key din gidan dana Mashin sai kafadansa Sagale da Briecafe dinsa.

Ciki Ciki Hafsah ta amsa Sallaman nashi Shima kai Tsayen ya kalleta,Ido Cikin Ido yace"Yan Suna andawo lafiya..? Ya fada yana Sabule sawu Cikin Takalmin Dake kafarsa Cikin wani yanga Hafsah tace"Lafiya lau Alhamdulillah.."Lokaci Daya ta wani maida Hankalinta kan Kallon Datake yi Dariya ta kamashi Sai da ya Murmusa bai kara mata mgana ba ya Taka ya Shige Ciki Hafsah ta Bishi da Harara kafin ta kwafa acikin Ranta ta Riga ta Guduri Niyyar yan kudadenta Sana"a zata Fara dashi Insha Allahu bazata kara Juran Gorin Abdullahi ba.

Sha Biyu Saura ta gama kallonta ta kashe komai ta koma Ciki ta iske har ya Fito wanka yana sanye da Dogon wando,Jikinsa ba Riga yana aiki Bisa System dinsa,
Tana Shigowa ya Dago ya kalleta itama ta kalleshi sau Daya ta Tura Kofar Tailet ta Shige kai kawai ya Girgiza Lamarin Hafsah ya koma Bashi Dariya ma Miye Abun Fushi ke da akabama zabi kika zaba sai kuma ki Dawo kina Fushin Rashin Dalili,Killer Smile yayi acikin Ransa ya Furta nasan Abunda kike so Shiyasa kike wannan Rigiman.

Yana Zaunen ta Fito wanka Daure da

17 / 48