Advertisements
Chapter 14 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   14 / 48

39K to 42K   out of 143.7K words

takeyi bama lalle bane ku sameta.."

Subai tace"wai tama taba zuwa Gidanki kuwa..? Zannira tace"Tazo Sau Daya Haihuwan Gidado Tamin barka Shi ya Nazifin yaso mu Dinga Zumunci ammh Taki baki ganta ba akwai shan kamshi da Daukan kai naje sau Daya Lokacin gaskiya suna Gidan Babanta ne nan Ndc,Tundaga Lokacin ban koma ba Wannam Haihuwan dai Basu zo ba ammh Shi ya Kirani ta waya yayimin barka.."Hafsah tace"Ai bata son Shiga Mutane Nima ko Gidana sau Biyu taje..Ni kuma Sau Daya sanda muka zo nan Nida Abban Amira da zamu Tafi muka Biya muka gaishesu.."

Subai tace"Lalle yaga Rayuwa..Don Allah me lambarsa ya bani nidai ban barin garin nan sai naje naga komai."Zannira tace"Gulma zai kai ki kenan.."?

Kai Tsaye tace"Kusan Haka.."Tafada Tana Dariya Mariya ce tayi karab tace"Bafa mai lambarsa anan inaga.."Hafsah tace"Nima wlh banda ita ammh gata Sakinar nan inada ita.."Subai tace"Yauwa Kirata kice mata kina kaduna muji ko tana Gida.."Nan da nan kuwa Hafsah ta Daga waya ta kira Sakina Sai da ta yanke bata Daga ba kira na Biyu ne ta Daga muryanta chan Ciki kamar mai Barci Hafsah tace"Hajiya sakina kin Tashi lafiya...?

Dagachan Bangaren Sakina Dake Nannade Cikin bargo tace"Lafiya kalau..Matar Abdullahi Usman.."Dama haka take Kiranta Hafsah tace"Ashe zaki gane ni..? Sakina tace"Saboda..? Ina da Layinki aie..kawai dai Abubuwa ne sai a hankali ya gida..? Ina oga da Yara..?

Hafsah tace"Duk suna lafiya suna Zaria ni gani kaduna Tun Shekaran Jiya.."Sakina tace"Kai Don Allah..? Me kika zo yi kaduna kuma..? Hafsah tace"Suna muka zo kanwar Abban Amira ta Haihuwa wacce ke nan Kaduna.."Sakina tace"Oh..Allah sarki zannira kenan Kamar naji Nazifi na mganarta ba C.s akayi mata ba..? Hafsah tace"Eh wlh...Jiya akayi suna Shine yau zamu koma nace bari na Taboki naji ko kina kaduna ko kila kin koma wajen aiki..?

Sakina tace"Ayyah Wlh ban koma ba Kingani Tun Ranar monday na saka ran komawa ammh na tashi da Fever da Ciwon kai Sai Da naje asibiti Jiya kawai sai na Dauki Excuse sai Ranar Friday in naji Sauki zan koma.."Hafsah tace"Shikenan zamu zo kafim mu tafi..Ina Ya Nazifin yana gida ko an Fita..? Sakina tace"Yana office Wlh Tun safe ya fice sai kunzo kiyima mai jego sannu in na samu Lokacin zan Shigo insha Allahu"Hafsah tace"Zataji sai mun iso.."

Daga haka suka yanke Kiran Dama Handfree ne, Hafsah ta Saka da Sauri Subai ta mike tana Fadin"Wlh sai munje ku Shirya da Habu Direba ya iso muyima Zannira sallama Dagachan sai mu wuce.."Haka ko akayi Ba Dadewa sai gashi ya iso nan sukayi mata sallama Harda kwallarta Ta basu sakon Turaman Atamfa Biyu na Mama Dana Inna Abu Inna Talatu ma ta bata nata Sai sakon Nama Da yawa Datace akai ma Mama ta Diban nata dana Ya auwal sai ta aika gidan Inna Abu na Ya Abdullahi kuma tabama Hafsah tace takai mai Sun Rabu Cikin kewa Don ma ga mariya sai Sati mai zuwa zata dawo,ammh harda ita za"aje gidan Nazifi Domin tace wlh Sai taje itama allah barshi in sun Fito sai su sauketa Boss Stop ta Hau Adaidaita ta dawo.


Daga Gidan Zannira sai anguwar Rimi Gidan Nazifi Hafsah ita ta gane Gidan Tunda suka Shigo Layin da Farko sun so su bace Ammh Daga baya sai ta gane Gidan Hon suka zuba abakin katon bakin get din megadi ya leka ya Bude musu get suka Sulala Jiki ga Bakar Motar Sakinan nan Anaconde tana Fake,Suka Firfito Daga Motan suna kallon Farfajiyar Gidan Subai sai kalle kalle take kafin tace"Shima dai Ya Nazifin da kwadayi da Buri dame wannan Gidan yafi ma wanda Ubanta ya basu duk da Banta ba zuwa ba.."

Hafsah na Dariya tace"Babu sai Abunda ba"a rasa ba.."Subai tace"Gashi yanzu ya Dawo Gidansa don Dole Domin ko yaya Guntun Gatarinka yake yafi sari ka bani.."Kafa hafsah ta Take mata Daidai Lokacin da Jidda ke Tura Kofar Falon gidan ganin haka yaasa tayi Shuru suka saka kansu Ciki Lokaci Daya da sallama.






*Janafty...*
4/9/21, 1:54 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*DEDICATED TO:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!


_Shafin yau Gabadayansa Sadaukarwa ne zuwa Gareki *MY BEST❤️HALIMA..* ALHERIN ALLAH YA KAI MIKI ADUK INDA KIKE AMEEN..._


*014*




"Falon babu Kowa sai karan Talabijin Daya ketayi Shi kadai...Kwata kwata Babu motsin kowa Cikin mamaki Dukkansu suke Bin Falon da kallo ganinsa kaca kaca da alama dai matar Gidan bata Dubashi ba.

Saman Center Table din Dake Tsakiyar Falon Ga Filet nan da kofuna da kuma Goran ruwa da lemo Wanda da alamu Harda wanda akayi amfani Dashi Jiya da Daddare dana yau da Safe, kila da megidan zai Fita ne,ya Taimaki kanshi.

Suna Ta Raba ido Cikin Falon,Subai Ta kalli Hafsah tana Fadin"Ke wai matar gidan kuwa tana nan..? Hafsah tace"Tana nan mana..Da bata nan da batace tana nan ba kinsan tace batajin Dadi kila Tana ciki ne.."Mariya ce Ta kara bude baki ta kwarara Sallama sai ga Sakina ta Bude wata Kofa dake yammah haka ta Fito Dagani Daga barci tatashi Domin Rigar barci ce ajikinta mai igiyoyi,Sai wata Hula Dake saman kanta Fuskarta Duk ta yamutse Alamun dai Tun barcin Jiya bata iya Tashi ba sai yanzu.

Da Mirmishi ta Tarbesu Lokaci Daya tana karisowa kusa dasu Cikin Fara"a tace"Sannun ku da zuwa..ku zauna Ashe Kun kariso...?Hafsah tace"Eh wlh..Muna Ta sallama muka ji Shuru..? Ta fada tana zama kan Daya Daga Cikin kujerun da sukayi ma Falon kwanya,Suma su Subai"atu da mariya da Jidda Hade da Inna Talatu suka nemi waje suka Zauna,Lokaci Daya suna gaisheta ta amsa Tana kallon Inna Talatu ganinta Babba yaasa ta gaisheta ita kuma ta amsa Tana Tambayanta gida da yara.

Mirmishi Sakina tayi batayi mgana ba Hafsah ce tace"Wasu yaran Inna..? Wadanan yan Boko ne yara ba yanzu ba.."Inna Talatu tace"Ikon Allah daman Haihuwan Tsarata ake sai sonda Mutum yaga dama..? Kai yaran zamani.."Tafada tana kyabe baki Dariya suka sakamata Harda Sakinan Subai ce tace"Inna baki gane ba..Ba yanzu suke Bukatar ya'yan ba sai zuwa Gaba.."Inna Talatu ta tabe baki Tana Fadin"Aikin Banza ai Duk wannan Shirme ne da Biyema ka"idan Yahudawa Annabi da kansa yace kuyi Aure ku Haiyayyafa sai nayi alfahari Daku Ranar lahira ammh ku kuma kuna ma Tsara Lokacin da zaku samu ya"yan ne Allah ya kyauta To.."suka kara sakamata Dariya saboda sanin Halin Inna Talatu na barkwanci da kuma Ban Dariya.

Sakina dai batayi mgana ba, sai Mirmishi sai chan ne,Hafsah ta kalleta tace"Kanwar Mama ce muna ce mata Inna Talatu.."Yake tayi Tana Fadin Allah sarki Kafin Hafsah ta Nuna Subai tana Fadin"Nasan baki santa ba Ita ke bima Zannira sunanta Subai"atu azaria take aure..su Mariya kuma nasan kila kin ganesu..? Sakina ta kallesu Daya bayan Daya kafin tace"Allah Sarki..Sannunku da zuwa.."Suka amsa da yauwa Subai"atu dai nata yan kalle kalle Tana Tabe baki Sakinar na Lura da ita,sai itama ta Dauke kanta ta Mike tana Fadin"Bari na kawo muku Ruwa...kunzo ban lahiya banyi komai Cikin Gidan ba.."

Hafsah tace"Ayyah bakomai da kin barsa ma munsha Ruwa saman Hanya muke.."Bata saurareta ba tawuce zuwa Kitchen suka Bita da kallo ganin yadda take wani taku ta kowani Kira na Jikinta yana amsawa Baki Subai ta Rike tana Fadin"Ji wai macen Aure..? Ji gidanta..?gaskiya Ya Nazifi kyan jiki kawai yabi da Dukiyar mahaifinta ammh banda haka wlh banga Abun so anan ba.."Hafsah ta Take mata kafa tana kyafta mata ido Mariya nata Dariya Inna Talatu dai bata saka musu baki ba Domin Itama Sakinar bata bata Sha"awa ba sam..

Ruwa da Lemo ta kawomusu da Kofuna kana ta koma ta Cikin Bedroom dinta ta Dauko wayarta tazo ta zauna ta Dora kafa daya Kan Daya tana latsawa Subai kuwa sai Binta da kallo take awulakance,ganin basu sha Ruwan ba yasa Sakinar ta kallesu Tana Fadin"Kun ki shan Ruwa..? Hafsah tace"Zamu sha..Dayake kinga Daga gidan zannira muke bamu tare da kishi.."Itace tasha Ruwan sai Inna Talatu Subai da Mariya da Jidda ba wanda yasha,Sunanan zaune sau Daya Sakinar ta Dago tana Tambayan Hafsah yasu Amira..? Tace suna Lafiya suna Gidan Ammi.

Sunyi zaman mintuna Talatin kana Subai ta kalli Hafsah tana Fadin"Muyi Harama ko..?12 ta wuce kada muyi Dare Bisa Hanya.."Tafada tana mikewa Lokaci Daya tana Gyara zaman Saleem Dake Hannunta,suma Duk sai suka mike suna Fadin"Ai kuwa Toh sakina mu zamu wuce.."Cewar Hafsah sai Lokacin Sakina ta ijiye wayarta tana Fadin"Tun yanzu..?

Hafsah tace"Muna Bisa Hanya ne..Zaria zamu koma.."Sakina tace'Ai nagode..Ku gaida gida Allah kiyaye Hanya mungode.."Subai ce tace"Toh in yaya Nazifin ya dawo sai agayamai mun zo..Allah kara lafiya.."Sakinar ta karba da Ameen Fuskarta ba Fara"a Sosai iyakarta Rakiyarsu bakin kofar Falonta ta koma Subai bata Samu Bakin mgana ba sai da suka Dauki Hanya kana ta kalli Hafsah Tana Fadin"Gaskiya matar nan ta Ya Nazifi bata da Kirki..Duk Fadin Rashin kirkinta dasu Zakiyyah ke Fadi ban yarda ba sai yau Dana ganta.."

Hafsah tayi Dariya tana Fadin"Wai ina Ruwanki da Rashin Kirkinta..? Matar nan kin Cika gulma.."Subai tace'"Allah ba Zencen gulma ba sai gaskiya Shiyasa ba"a son Dogon Buri,kinga da Lokacin da zai yi Aure yabi yadda Sunna ta koyar mai addini da Tarbiya Shi kuma sai yabi Mai kyan Diri da kuma Tarin Dukiya Shiysa Tunda yayi Aure yake ta kwarewa kamar kudin Guzuri.."Dariya ta kama Mariya da Hafsah suka kyakyalce da Dariya Jidda dai Tabe kawai Tayi Dayake ita ke gidan Gaba.

Mariya ce tace"Haka ake ta Gulma a anguwa ana Fadin Auran kudi yayi Gashi kuma ya Auro ma kansa wacce tafi karfinsa kwanaki Mama naji suna mganar da Ya Abdullahi Da suka samu matsala ya Taba marinta ta koma Gida Babanta ya Kira Baba wada yace wlh sai yamaka ya Nazifi a kotu Baba wada yace Abun bai kai nan ba,Ya Kira ya Abdullahi yace maza ya Raka Shi Ya Nazifin suje suyi ban Hakuri wanda ya jawo Ruwa ya Dakesa Shi kadai da Mutumcinsa bazai bari Nazifi ya maidashi Mutumin banza ba.."

Salati Subai ta saka ta na mamaki kafin tayi mgana Hafsah tace"kwarai kuwa Kwanaki sunje kano..Shida Abban Amira ammh kusan Halin yayanku Wlh ko Tadin bai taba yi Dani ba.."Mariya tace"Tabdijam Wake jin Zence abakin Ya Abdullahi in banda Mama..? Ko nima Ranar bai san ina Ciki bane Ina ma Mama gyaran Daki Dana Fito muka Hada ido kinga Ruwan Harara..?Dariya suka sakamata Lokaci Daya Subai tace"Da farko Haushinsa nakeji ina mai Allah kara ammh yanzu ya koma Bani Tsausayi Wlh inda ina da Diya Budurwa sai na wanketa na bashu Naga yarda Shegiya zata kare sai taje ta Rungumi aikinta Ubanta kuma sai ya maye mata Gurbin Nazifin..'

Hafsah ta Rike baki Tana Fadin"Lalle lamarin Babba ne..Ai bata baci ba ga Muhsina sai ya Jirata in ta kara Girma muyi Tuwona maina.."Duka Subai ta Daka mata abaya Tana Dariya Mariya na Tayasu Jidda kuma daman bata Cika saka musu baki ba in suna mgana Inna Talatu kuma taji sanyin A.C mota Tuni Barci ya saceta,Mariya ce ke Tayasu Da Dariya Dayake ita akwai manyance,Bus stop suka ijiye Mariya ta Hau adaidaita ta koma Bayan sunyi Sallama nan suka Barta tana neman Abun hawa.

Suna Tafe suna Hira gwanin Sha"awa Suna gabda Shigowa Zaria Subai tace"Jidda wai yaushe ne,Bikin autar Goggo Habiba ne..? Jidda tace"Wlh na manta ammh fa an kusa kamar naji Mama suna mgana da ita datazo mata Barkan Anty Zannira Tace watan Gobe ne.."Hafsah tace"Kai Abun har yazo..kamar fa Shekara aka saka ko..?

Subai tace"Eh mana nima nayi mamaki..Komai aka sakama Lokaci sai yazo lalle kice Danja zatayi Diban baki.."Hafsah tace"Aifa..Allah dai ya kaimu.."Jiddaa tace"Kafin na Madina din wannan Asabar din Diyar mijinta na Aure fa Shiyasa ma Tace ma Mama bazata samu zuwa Kaduna ba Tadai Kira Anty Zanniran ta mata barka.."Hafsah tace"Allah sarki..yakamata kuma ama Goggo kara kowani Sha"ani Da ita da ya"yanta akeyi.."

Subai tace"Sai Ya Abdullahi ya wakilataki kije Qawata.."Hafsah tace"Wa..? Rufamin Asiri ina Lallaba yan kayana yanzu ma Baku san Abunda zan Tarar ba na Tsiya.."Ta fada tana Dariya Dayake ta basu labarin yadda ya Barta ta Taho Tunda Ranar da sukazo da Daddare Umman Sadiq ta Kirata tana Tambayanta ko ya Kirata yace tatafi sai tace gatama akaduna.

Basu iso Zaria ba sai Wajen Biyu na Rana Dayake basu yi Gudu ba Gidan Mama Tawagar Sunan ta yada Zango suka bama Mama sakonta ita kuma tayi ta Hamdalan Sun dawo lafiya daya suka baro masu wanka sukace Lafiyarsu kalau suna gaisheta Dama koda suka iso Mama tayi Danwakenta da yajinta da manja nan suka baje sukaci suka Koshi suka Dora da Ruwa kana aka Zauna zaman Hira Bayan sunyi Sallar azahar.

Cikin Hiran ne Subai ke Fadin"Mama Ashe haka Matar Ya Nazifin nan take mara Mutumci..?Mama tace"Ho ke Subai"atu ina kika ganta kuma..? Nan mariya ke gayama Mama Yadda akayi Mama tayi Dariya Tana Fadin"Hoho..Subai kina nan da Halinki..Ina Ruwanki da Rashin Kirkinta Tunda Mijinta yaji kuma yagani.."Subai tace"Mama bawan Allah ya koma Abun Tsausayi.."Hafsah tace"Don Allah mu ki kyalemu da wannan mganar in baza ki iya gani ki kyale ba ki barshi.."Hararanta Subai tayi Daganan bata kara Mgana ba ammh haka Kurum take jin Haushin Sakina acikin Ranta.

Sai Da sukayi La"asar kana Kowa tayi Shirin komawa Gida kafin su Tafi sai Da Mama ta saka Suka Shiga Gidan Inna Abu ita da Subai suka kaimata Sakon Naman Sunanta da Turmin zanin Sakon Zannira ta karba tana ta Godiya ta sakamusu albarka suna gidan ma sai ga Baba ya Shigo nan Inna Abu ke gwadamai  Shima yayi ta Godiya yana saka musu albarka kana suka musu Sallama suka Fito Direban Mijin Subai Shi ya Fara kai Hafsah Gida kana ya wuce da ita Dama ta karbi key hannun Mama Tunda nan Abdullahi ke Barin key din Guda Daya Dayan kuma Dama yana Hannunshi ne.

Tana Komawa Gida ta Zage ta Fara Gyaran Gidan ganin Duk yayi Kura ta Share Tsakar Gida da Kitchen ta Share ganin yadda Abdullahi ya Birkita mata shi kawai Wajen Dafa Ruwan lipton,Ruwan zafi ma cikin Kittle yake sakawa,Dakin barcinsu kuwa Taga Abu kaya duk ya watsar Sai da ta gyara haka Tailet Ya watsar da Soso nan Sabulu chan komai dai ya Batashi Bayan ta Share ko"ina ta gyara sai ta koma Zaman gyara kayan Abdullahi na Cikin Wardrope wadanda kila wajen Daukan kayan da zai sakane Duk ya Birkita goggun Ciki ga kuma Kayanta da nashi wanda aka Dawo Dasu Daga wanki da Guga nan ya Turasu waje Daya Tana Gyarawa Tana mita acikin Ranta sai Gabda da mangariba ta gama gyaran kayan kana ta Fito Zuwa Kitchen ta Duba Fridge dinta taga Tana da Sauran Nama da Nikakken kayan Miya kawai sai ta Dora Musu Jallop din Shinkafa,Acikin ranta kuma tana Addu'an Allah yasa wannan karon Abdullahi ya siya mata gas Tuni Take nacin ya siya mata yaki wai saboda yara bata da Hankali wata Rana Sanda zasu je kusa ma bata sani ba Tunda Taji haka ta Hakura damai magiya.

Ta idar da Sallar mangariba kenan ta Kira Ammi ta Shaidamata Ta dawo Ammi tace"An dawo lafiya..Su Amira dai Kila sai Friday zasu dawo..Taji Dadin kiwon Tsohon Mijina ta nace taki Tafiya.."Hafsah na Dariya tace"Kai Ammi kodai ke kikaga Sabon Miji kika makalemai kina ma Daddy jan Aji Shi kuma ya kama Sabuwar amaryansa..?

Ammi tace"Wa..? Wannan ai ba megida bane Tunda baya Cefene.."Hafsah ta saka Dariya Ammi na Tayata tana jin Hayaniyarsu Amira Hafsah tace"Ammi kina ganin ba Matsala..? Kada fa Hayaniyarsu Amira ta Saka jinin Daddy ya kara Hawa..?Ammi tace"Ko daya karki damu ai shi Hayaniyar yaran yake so Tunda yanzu duk baku kusa dashi..Baki ga yadda yake sakewa dasu ba suma Sunfi son zama Dakinsa indai yana Gidan.."Hafsah tace"Shikenan Ammi..Ki gaida Daddyn zan kirasa.."Ammi tace"Shikenan.."Daga haka suka yanke Kiran Juna Hafsah na Mirmishi Sanin Diramar Ammi da Daddy kan Son Yaran da suka Haifa ita da Anty Hadiza,Koda Ammi tace sai Ranar Friday su Amira zasu dawo bata damu ba sanin Direba ke kaisu makaranta kuma Suna da kayansu chan Gidan Ammi kamar yadda suke dashi Agidan Mama Tunda suna yawan zuwa wasu kayan adawo dasu wasu kuma abarsu chan.

Koda Abdullahi ya Dawo ya Iske Hafsah ta gama Komai Har wanka Tayi ta Saka kaya Cikin Wasu Ubansu Riga da wando yan kanti wadanda suka kamata Sosai suka Fitar mata da Surar Jiki gefe daya kuma Tama kanta Barin Turare Duk inda ta gifta sai Tashin kamshi kawai take,kanta kuma wani Karamin Vail din gyale ta Daura,koda ya Shigo Gidan yaga Hafsah ta Dawo bai yi Mamaki ba Tunda ya Biya Gidan Mama ya ga Sakon Zanniran kuma Maman ta gayamai Sun Dawo Tun dazu Subain ma da Hafsah tare suka Fita.

Koda ya Shigo Hafsah Tana Sallar Isha"i Saboda haka kawai sai ya wuce Cikin Bedroom Karamar Jakarsa ya ijiye da key din Mashin Dinsa,kana ya Shiga Toilet ya iske ta sakamai Ruwan zafi a kittlle kawai sai ya juye yayi wanka Dashi ya Fito Kenan Daga wanka yana Sanye da Bakin Wando sai karamin Towel yana Goge Jikinsa Dashi sai ga Hafsah ta Shigo kallo Daya yayi mata ya kauda kansa kawai ya karisa gaban madubi ya Dauki mai ya Fara Shafawa.

Da kallo Hafsah ta Bisa sanin Hali yasa kawai ta karisa garesa ta Rumgumesa ta Baya Lokaci Daya ta Zuro Hannuwanta saman Cikinsa wanda Dukkansu sai da Jikinsu ya amsa Cikin kissa ta kwantar da kanta saman Bayansa Sanin tayi Laifi sai ta ke kokarin amfani da Hanyar da tasan Zata sauko da Fushinsa Da wuri.

Yana Jinta ya mata Banza sai ma Kokarin Rabata da Jikinsa yake yi Jin Haka yasa ta kara makaleshi Lokaci Daya ta Shagwabe Murya tana Fadin"Abdullahina Kana ganina na Dawo Shi ko mgana ko..? Tafada Lokaci Daya tana amfani da Hannunta Duka Biyu Tana Shafa kwantattacen gashin Daya kwanta saman Kirjinsa,Wanda sanadiyar haka Tsikar Jikan Abdullahi ta Fara tashi Ganin tana neman Birkitamai lissafi yasa yayi Sauri  Juyowa Lokaci Daya yana saka Hannu ya Raba Hafsah da Jikinsa Kallonsa take Cikin manyan Idanuwanta Shima sai ya sakarmata ido kawai yana kallonta ammh Fuskarsa ba Fara"a ko kadan

Ganin Haka yasa Jikin Hafsah sai yayi sanyi Duk Confident din Datazo dashi sai ta nemeshi ta Rasa,Sai kawai ta sadda kanta kasa tana wasa da Zoben Hannunta Cikin sanyin Murya tace"Sannu da zuwa ka Shigo ina Sallah.."

Yana kokarin Rabata ya wuce yake Fadin"Uhm...Na Shigo kina Sallah.."Daga haka bai kara komai ba ya Bude wardrope yana neman Jallabiyan da zai saka bata

14 / 48