Advertisements
Chapter 2 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   2 / 48

3K to 6K   out of 143.7K words

zuwa sai na Tashi bana jin Dadi,ga Amir nata Zazzabi Da Amai Shiyasa kika ga Baki ganni ba Ammh Insha Allahu Cikin Satinan ina Tafe karki Damu kawata.."

Subai"atu tace"Haka dai kikace Don ki Kare kanki da Mijinki bakomai..Sai na ganki.."Hafsah tace"Lah..Baki yarda ba...? Share zencen Subai"atu Tayi kafin tace"Jiya Ammi tazomin Barka Harda Abun arziki ki Tayani Godiya Qawata Allah ya saka da Alheri ya kara Tsawon Rai.."

Hafsah tace"Kajiki da wata mgana..?Don Uwa tama yarta wani abu sai ya zama Abun Godiya.."Subai"atu tace"Hakane kuma..ammh ai Godiya Abu ne mai kyau ko..? Ni ba wannan ba Ina Jiranki Allah kuwa Har Danki yayi Fushi Dake ya kwana Goma Aduniya baki zo kin ganshi ba ballatana Shi Yaya Abdullahin...." Hafsah tace"Kiyi Hakuri Insha Allahu Zamu zo.."

Subai"atu Tace"Toh Allah yasa."Daganan sukayi Sallama kowa ya Ijiye wayarsa Hafsah ta Gyara zama tana Sauke Numfashi Abun yazomata Cikin Ranta na Rashin kyautawarta ga Kawartata Subai"atu wanda kuma Ba Laifin Kowa bane sai na Abdullahi Domin Tunda akayi Haihuwar take mai nacin Tambayar ya barta Taje tama Subai"atu Barka ammh ya ki Kula Mganarta Har Suna yazo,Ranar sunan kuma Har yace ta Shirya ya kaita Ita da yara sai kuma yan Masifarsa suka Tashi Daga kawai Ta bata Lokaci wajen Shiryawa Shikenan yace ya Fasa kaita kuma Bai lamunta ta Fita ba Takaichi kamar ya kasheta,Tana ji Tana gani ya kwashi su Amira Zuwa Gidan Mama suka barta agida saboda Takachi Sai da tasha kuka,Ranta ya baci yasaa bata karamai mganar Zuwa Gidan Subai"an ba ta barshi ai Shima kanwarsa ne In Ya barta Taje Domin kanshi in ya Hanata Shima kanshi yayi mawa Ita miye nata aciki.

Gashi Abunda ke bata mamaki da Abdullahi yana da kyakyawan Mu"amala da kowa banda ita Shiyasa ko zata Shekara Fadin Aibun Abdullahi babu mai yarda,Ko Wajen iyayenta bata Isa ta Kushe Abdullahi ba,baya kwana Biyu baije Tudun wada ya Gaishesu ba,weekend kuwa Shi da yara a Cikin Zaria suke yinshi da Tudun Wada,Shiyasa komai zai mata Take Shanyewa sanin ko Zata Shekara Fada bamai yarda da Ita Saboda in ka Ganshi Bazaka Taba Zaton yana iya Doguwar Mgana ba ballatana Har ya iya wannan Hayagaggar,Abunda ke Daurema Hafsah game da Abdullahi Shine,Komai tayi mai Bata Burgeshi kuma komai tayi ba Daidai bane Duk ko iya Kokarinta na ganin ta zama mai Daidai acikin Idanuwansa ammh Abu ya Gagara Shekara Biyar da Auransu ammh ba wani Abunda ya Chanza Suna nan Jiya yau.

Ajiyar Zuciya ta Sauke jin Sallaman almajirinta yunusa,mikewa tayi ta Fito suka Gaisa,Rijiya ya Nufa ya Fara Zuba mata Ruwa Cikin Babban Roban Dake wajen,Ganin haka yasa ta Bude Kitchen ta Shiga ta Dauko kayan Miya ta Fara gyarawa Ta Tagama sai ta Saka Cikin Wata Robarta mai murfi tana cema Yunusa in ya Gama Zuba Ruwan ya mata Wanke wanke ya Dauki Nikan nan ya mika mata Gidan Nene mai nika yace mata Toh Daganan Ta koma Daki,Tana nan kwance Bayan Fitan Yunusa Zuwa Nika sai ga Nepa sun kawo Wuta ta Mike tana Fadin"Kash Nepa baku kyauta ba sai da yunusa ya tafi kai min nika kana kuka maido Wuta..?

Sai Lokacin kuma Abun yayi mata Shar cikin Ranta Da Sauri ta Mike tana Salati Cikin Ranta Tuna Abdullahi baya som Miyar Nika yafison kuma na Jajjage,ita kuma Abunda yaasa bata Jajjaga ba Taga kayan Miyan yana da yawa ne Bata iya zaman Jajjagasa Shiyasa takai Nika ajiyar rai ta Sauke afili ta Furta.."Fada ne da korafi yau zan Shashi Acikin Gidan nan Har sai na Godema Allah.."

Yunusa na Dawowa Daga kai mata Nika ya karbo mata ta Bashi Abun karyawansa Bayan ya gama ta Bashi Sakon Danmagaji tace ya Siyo mata kayan Lambu,Kabeji,da caras,sai Cocumber,Tana so tayi Cowslow ne kuma Ta Duba Cikin Fridge dinta Duka sun kare,Bama kadai Gareta sai kwai kudin Mota ta bashi Tace yayi Sauri ya Dawo yana Fita ta Dauki Tsintsiya ta Share Tsakar Gidan Tas ta kwashe Dattin Takai Bola aranta Tana Fadin kafin yunusa ya Tafi zai Zubda da Sharan Domin Ta Taru da yawa.

Yunusa bai Dade ba ya Dawo koda ya Komo har ta Gama Miyarta,Already dama Tana da Sauran Naman Jiya da Abdullahi ya Zo Dashi batayi amfani Dashi Duka ba sai tayi amfani da Sauran yau,Ruwan Farar Shinkafa ta Dora,Sauran gawayin Safe ne bai kare ba,Ta bama yunusa Hamsin ya karo mata kada ya yanke mata kuma Babu kowa Sallaman yunusa tayi ya Tafi makaranta yace mata yana da Rubutu sai Zuwa anjuma zai zo ya karbi abincinsa Dayake makarantar Allon nasu kusa ne babu Nisa Sosai.

Kokafin 12pm na Rana Hafsah ta Gama Komai Ta kwashe Cikin Kula,Cowslow ne din ne Bata Hada ba sai Zuwa anjuma Gudun karya ya Lalace,sai da ta gama yanka komai ta wanke ta Adanashi acikin Kitchen dinta,Dama ta saka Ruwan zafi Cikin Kittle ta juye tayi wanka Dashi ta Sauya kaya Zuwa Atamfar wata Doguwar Riga,Falo ta Dawo tazo ta kunna kallo Tashar africa Tv ta saka Tana kallon Wa"azi Domin Hafsah kallo bai Dameta ba har gwara ma India tana kallonsu akan Hausa Film.

Sallar azahar ne ya Tada ita ta Tashi ta Shiga Cikin Bedroom dinta ta Dauro alwala tazo Tayi Sallah,Ta idar da sallar kenan tana Addu"o'inta Taji wayarta na neman Dauki Daga Falo da Sauri ta Shafa Addu"arta ta Fito Falo ta Dauki Wayarta Ganin Sunan mai Kiran yasa sai da Gabanta ya Fadi Abdullahi ne.

Tana Gabda Katsewa Ta Daga Kiran Tana mai sallama Dagachan Bangaren Abdullahi yace"Yau kuma wani Salon Wulakancin kika sake samu Hafsah...?

Ido ta Runtse kafin tace"Wulakanci fa kace Abban Amira..? Kai tsaye yace"Eh mana Banda Wulakanci kinaji ina Kiran Wayarki ammh Saboda ki Kaini Bango sai da kika Ga Dama zaki Daga Kiran nawa."Batace komai ba kawai tamai Shurun jin Shurunta yasa yace kara Fadin"Au kina Jina ina mgana Shine kika min Banza.."Hafsah tace"Ba banza na maka ba Jira nake kagama Fadan naka sai na Baka Hakuri na kuma gayamaka Cewa Lokacin daka Kira ina Sallah ne.."Jin Haka kuma sai Jikinsa yayi sanyi Sai kawai yayi kwafa yana Fadin"Dama kiran  Saboda Nace miki in Lokacin Tashinsu Amira yayi Daga makaranta ki Kulle Gida kije da kanki ki Daukosu mai Mashin dinsu yau bai Fita aiki ba yana Gida Baya Jin Dadi ni kuma aiki yayi min yawa Bazan samu Lokacin Zuwa na Daukosu ba.."Yafada Cikin Sanyin Murya Cikin Sanyinta tace"Shikenan...Allah ya kaimu zan je na Daukosu in Lokacin Tashinsu yayi.."

Daga Haka bai kara mgana ba Tana Shirin yanke wayar Taji yana Fadin"Akwai kudi a hannunki ne..?kai Tsaye tace mai"Eh akwai.."Bai Tsaya jin wani mgana ba ya katse Kiran Ajiyar Numfashi ta Sauke kafin ta Ijiye wayar nan saman kujera Ta koma ta Zauna tana kada kai,gefe Daya kuma Jifa Jifa Takan maida Hankalinta Wajen Tibi.

2pm na Rana Daidai ta Saka Babban Hijabinta ta Dauki Wayarta da Kudi Cikin yar karamar pos dinta ta Fito Bayan ta Kulle Gidan,Adaidaita ta samu ya Dauketa har makarantansu Amira wato Alhazawa Acadamey Zaria,Amira tana primary 1 ne Shi kuma Amir yana Nursery 2 ne,Shi karfe 1pm na Rana ake Tashinsu su Amira kuma 2:10pm ake Tashinsu,In Abdullahi yakaisu da Safe in an tashesu wani mai mashin nan yake makotansu Abdullahi ya Dauka yana Biya Duk wata yana zuwa yana Dawowa Dasu Amir zai Jira Har atashi su Amira a Daukosu Tare,Sai da ma ta jira aka tashesu kana ta Shiga cikin makarantar har ajinsu Amir suka gaisa da malamansu ta Daukoshi Dayake tana zuwa Daukosu Wani Lokacin in Wata mtsala ta Faru haka Amira kuma aharaban makarantar da Ganta Tashinsu kenan Ta Riko mata Hannu suka Tafi Mai adaidaitan nan nan dama tace ya Jirata ya maidasu sai ta Bashi kudinshi Gabadaya.

Suna Dawowa Amira ta Cire Uniform Dinta ita kuma Hafsah ta Cire ma, Amir suka sauya zuwa kayan Gida Sai Lokacin ta Hada Cowslow din ta Zuba musu Farar Shinkafar da miya sai Cowslow din suka Hadu Sukaci Gabadayansu suka Sha Ruwa,Bayan sun gama ta tattara komai Zuwa Kitchen,Ta Zubama Abdullahi nashi Cikin Kololinsa Coslow dinshi kuma Bata Hadamai ba sai indan ya Dawo kada ya lalace iya wanda zasuci ta Hada musu sai na Wanda ta Zubama Yunusa Wajen la"asar sai gashi ya Dawo ya sake Zuba mata Ruwa ya mata wanke wanke ta Bashi abincinsa ya Tafi Bayan ya mata Sallaman sai da Safe.

Su Amira ta Shirya suka Tafi Islamiya nan kusa dasu suka Barta Ita kadai acikin Gida,ganin haka kawai sai ta Tsiri wankinsu Amira daya Taru na Abdullahi da nata Dama wanki yakan kai musu in sun Taru,Suma nasu Amiran yace tabar wankewa zai Dinga Hadawa dasu yana kai wanki tace ya bari ta Dinga wanke musu kayan yara ne kada su Dinga bacewa wajen Wanki Shiyasa ya Bar mata na yaran Tana wankewa da kanta,Mganar Gaskiya Banda Fadan Abdullahi da Korafinsa bai da wani illah Daidai gwargwardo yana iya Bakin Kokarinta akanta da ya"yanta,ga lalurori akansa nashi dana kannensa Da kuma na Mama Don ma Allah na Rufa Asiri ammh bazaka Taba kallon Hafsah kace tana Cikin Wahala ba Abdullahi gwarzo ne kuma Tsayayye ga Lamarin Gidansa.

*******

Karfe 7:30pm Abdullahi ya Shigo Gidan kan Mashin Dinsa,Lokacin Hafsah Sun idar da Sallar mangariba  Ita dasu Amira tana Biya musu karatun Qur"ani Amir najin Karan Mashin din Abbansu ya Ruga da Gudu Zuwa Waje yana Kiransa Aran Hafsah kuwa tace kila ya Biya Gidan mama ne Domin Ta Duba agogo taga Bakwai ta wuce ta kuma Tattabata 6pm yake tasowa Daga Office.

Tana Kokarin mikewa Bayan tace ma Amira ta Nade Darduman Taji yana Kiranta da Sauri ta Fito Tsakar Gidan tana amsawa yana Zaune Bisa Mashinsa Dinsa bai ma kai ga Shiga da mashin Din ba Ciki ya Dauki Amir ya Dora agaban Mashin Dinshi nashi Hannanunsa Guda Daya kuma Dauke da Ledoji Guda 2,Da Sauri Hafsah ta karisa tana mai Sannu da Zuwa kamar Abun arziki ya Dago ya amsa yana Tambayanta ya Gida tace lafiya ne Ta mika Hannu zata karbi Ledan Hannunsa ya Kalleta yana Fadin"ai na zata bazaki karba bane.Ni kike jira na kai miki Shi inda ya Dace.."Bata tankamai ba sanin Halinsa ta karbi Ledan Zuwa Kitchen ganin Kalanzir ne Aduka Ledojin Guda biyu din.

Galan din kalanzir din ta Dauka ta Juye su Duka aciki kafin ta,wanke Hannunta lokacin har Abdullahi ya Shiga da Mashinsa dinsa Ciki,Ya Shiga Daki itama sai Tabi bayansu ta iskeshi Zaune kan kujera yana ma Amir wasa Amira na gefensa Itama tana Ma Amir din wasa,da Sallama ta Shigo Abdullahi ya Dago ya amsa mata ta wuce Bedroom dinsu ta Sake mai Ruwan wankansa ta Surkamai Har Lokacin suna da Wutar Nepa,tana Cikin Tailet din ya Shigo yana Nade hannun Rigansa Ta Dago tana Fadin"Bakai Sallah bane Bisa Hanya..?

Tafada Tana Zubamai Ruwa Cikin Botar dake Tailet din bai kalleta ba yace"Gidan Mama na Biya ta Tsaidani da mgana Ban samu nayi sallar ba.."Daga haka Bai kara mgana ba ta mikamai Butar tana Fadin"Ga Ruwa wanka nan fa.."Da kai ya amsa mata ita kuma ta Fice Daga Toilet din ta koma Falo taDauke mai karamar Jakarsa ta Shigo Dashi Cikin Bedroom din Gudun Fitinarsa yasa ta ijiye mai nan saman Gado ta Fita Zuwa Kitchen Ta Hadamai Coslow dinsa ta kwaso Abincin nashi Zuwa Falo ta Jera atsakiyar Falon,saman Center Carpent din Dake Tsakiyar Dakin.

Bayan yayi Sallar mangariba ne yayi wanka ya Dauro alwala,ya Fita Zuwa masallaci Shida Amir Sai bayan daya Dawo ne ya Zauna Hafsah ta Zubamai abinci,Hafsah taji mamaki da Har Abdullahi ya kusa Gama Cin Abinci baiyi korafinsa Daya saba ba,Bata gama mamaki ba Taji mganarsa.."Miyar nan Tayi Dadi Hafsah.."

Ya Fada yana kara Zuba Miyar saman Farar Shinkafar Dake gabansa Kallonsa tayi Kafin tace"Ko..? Inaga ka Fara santi ne ko a saka maka waigi ne..? Wani kallo ya watsa mata kafin yace"ai ke za"a sakama waigi Hafsah Saboda Taurin kanki Bansan meyasa kika Rainani ba..Sai na Shekara ce miki ga Abunda nake so ammh ke kullum sai dai na Hakura Nabi Ra"ayin ki ko..?

Cikin Mamaki Hafsah ta kalleshi kafin tace"Me kuma ya Faru Abban Amira..? Kai tsaye yace mata"Bansani ba...nace bansani ba.."Cikim zafin Rai ganin haka yasa ta Kauda kanta Tana Fadin"Allah baka Hakuri.."Daga haka Taja Bakinta tayi Shuru Ta maida kanta wajensu Amira inda Amiran ta Dage sai ta ma Amir Homework shi kuma yana ta Rigiman bazai bata ba tabar mai kayansa Har ya gama Cin Abincin bai kara mgana ba,sai dayasha Ruwa kana yace"Miyar tayi Dadi Sosai..Ammh da miyar Jajjagece sai tafi Haka Dadi ammh Dayake Allah ya Hadani da marajin Mga Irinki Hafsah ai irin Ra"ayinki kikayi kin kyauta.."Kanta na kasa batayi mgana ba sai ma Mirmishi Data saki yana kallonta ammh Girman kai ya Hanashi ya kara mata Mgana ya Tsalleke ya koma Bisa Kujera yana Fadin"Kinga malama Bani Remot Don Allah.."Jin haka yasa tatashi ta Dauko ta mikamai ya karba yana Kokarin Chanza Tasha ita kuma Tatattara komai Zuwa Kitchen,ta saka komai Cikim Muhallinsa,ta kulle Kitchen din Takoma Daki yana Falon ta Wuceshi Zuwa Ciki Ta Shiga Tailet ta Sake Ruwan Data saka a kittle tayi wanka Dashi Har ta Fito bai Shiga ba ta Shirya Cikin Wasu Riga da wando wadanda suka kamata Sosai suka kuma Fitar mata da Suran Jiki bata saka Kallabi ba illah ta saka Band ta kama Gashinta takulle Baya Tana Cikin Shafa Humra Taji Muryan Abdullahi na Kiranta Daga Falo.

Da Sauri ta karisa Falon Gudun kada tayi Laifi Har ya Dago da Niyar Fara mata Korafin nashi sai kuma ya kasa Ganin Irin Shigar Daukan Hankalin Datayi Daman kuma Abdullahi na son ganin Hafsah Cikin English Wears,Fasa mata Fada yayi sai ma yace Cikin Sanyin Murya.."Kizo ki kaisu wajem kwanciyarsu Sunyi Barci.."Ya fada yana Nuna mata Amira Datayi Barci nan kasa sai Amir Dake kan Jikinsa,To tace ta Sunkuya ta Fara Daukan Amira ta kaita Cikin Tailet ta saka tayi Fitsari Tazo takaita Dakinsu kana tazo ta Dauki Amir,Tunda ta kusantoshi kamshin Humaranta Suka Taimaka wajen Sakashi Cikin kasala da Sha"awa Sai Binta yake da kallo har takai Amir Ya kwanta Shima tayi musu addu"an Barci ta kashe musu Wutar Dakin ta Fito.

Ta gaban Abdullahi tazo Zata wuce Cikin wata Kasalalliyar Murya ya saka Baki ya Kirata.."Hafsah...! Cak ta Tsaya kana ta waigo tana Kallonsa dakai yayi mata mgana kafin yace"Zo mana.."Jin haka yasa tasan kwanan zencen Cikin yanga ta karisa Gabansa Tana Shirin zama gefensa yasa ka Hannun ya Jawota ta Fada Bisa Kirjinsa Dukkansu atare suka Saki Numfashi mai karfi Hannuwansa Duka Biyu ya saka ya Rumgumota yana Shinshinar Wuyanta Nokewa Tayi ta na kara Shigewa Jikinsa Cikin Shauki da Soyayyah.

Cikin Wuyanta ya saka Kanshi yana Shinshinar kamshin Turaranta kafin ya Dago yana Fadin"A gayamin sunan wannan Turaran mai bala"in kamshi wanda yasa Take naji Sha"awar Matata ya Kamani.."?

Hafsat tayi Mirmishi Batace komai ba kara matseta yayi yana mata Rada Cikin kunni Zillewa Tayi Tana yar Dariya Cikin kunya Shima kuma ya Sake Rikota yana Fadin"Hafsatuna ta sanni Fiye da kowa aduniyar nan...Tasan in ta Batamin Rai ta lallasheni ta Hanyoyi Dadama,kamar irin ta wannan Hanyar.."Yafada yana Sakarmata Kiss Saman Goshinta,itadai sai Mirmishi Take ta lafe Bisa Kirjinsa Ganin haka yasa ya yunkura yamike da ita kam Jikinsa kafin Taji ya Dagata Cak yana Fadin"muje kan gadonmu kila achan zaki fi Min Bayanin Wani irin Turare ne wannan."

Daman Tunda Taga ya Sauke kai Tana son yana Bukatarta,kanta kawai ta maida kan kirjinsa Lokaci Daya tana Zagayo da Hannuwanta ta Wuyansa Tana Jinsa Ya sauketa kan Gadon ya kuma Bita suka kwanta Rike da juna yana Shafa wasu sassan Jikinta itama bata bashi kunya ba ta Juyo itama Ta Hade Bakinsu Waje Daya Lokaci Daya itama tana Sarrafashi kamar yadda yake Sarrafamata ta ko"ina.

*Hmm yanzu Salon ya Fara..Kudai kucike wajen da Kayattacen Sharhi Hade da Votings da Comments da Kuma Likes Ni kuma zan Faranta muku wajen baku update koda yaushe...*

*Shakira...*
4/9/21, 1:52 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*


*Dedicated To:My Habibaty💞Aisha Idris Abdulllahi..!*



*003*



      *TUSHE...*

"Abdullahi Usman Direba Shine Babban d'a Namiji na Farko agidan Marigayi Alhaji Usman Direba wanda asalinsa Haifaffan Garin Zaria ne,kuma Tashin Zaria a anguwar Babban Dodo Dake Cikin Birnin Zaria.

Alhaji Usman Direba kafin Rasuwarsa ya kasance Mutum ne mai Dabi"ar Aure Saki ya saki mata Sunfi Biyar Ciki harda mahaifiyar Abdullahi,Wato Hajara wacce ta kasance Haifaffiyar garin Zamfara ce Dake Babba birnin Jahar Gusau,A birnin Tarayyan Nageria,Wanda suka Hadu da ita wajen Wani bikin wani abokinsa Da yajema Biki nan garin Zamfara Shikenan Soyayyar ta Kullu Har takai su ga Aure,Hajara itace Matar Usman ta Farko,Auren Saurayi da Budurwa Sukayi.

Alhaji Usman Direba ne,wanda yake jan Babban Mota ta Kamfanin Dangote,Kuma Alhamdulillah ko acikin Direbobin Alhaji Usman na Dabam ne,Domin kowa Sana"ar ta karbeshi Cikin Lokaci kadan ya Tara Abun Duniya kuma yaje Ya Sauke Farali ne kafin yayi Auran Fari,kuma sai da ya Gina Babban Muhallinsa anan Babban Dodo Dake garin Zaria Lokacin Duka iyayansa Sun kare,Dama su Biyu Mahaifiyarsa ta Haifa Shida kanwarsa Habiba toh Tayi Aure a  Danja Dake Jahar katsina.

Ya samu Lakanin Alhaji Usman Direba ne saboda kwazonsa ga aikinsa kuma yafi Jin Dadi in ka Danganta Sunansa da Usman Direba Fiye da ka Kirasa Usman dinsa kai Tsaye Shiyasa Usman Direba yabisa Duk wanda ya sanshi da wannan lakanin nashi ya sanshi har yabar Gidan Duniya.

Ya auro Hajara Cikin Soyayya da kauna,Aka kuma kawomai Ita Zaria,agidan Daya gida Yan"uwan Hajara da Dangin Hajara Suka Tafi suna ta son barka Suna Fadin Hajara ta Dace,Hajara batayi Zurfi a karatun Bokonta ba iyakarta Jss3 ta Dakata da karatun sai dai Tana da Ilimin Addini Daidai Gwargwardo.

Zamansu ya Fara ne Cikin kwanciyar Hankali da kuma Soyayyah,Har na Tsawon wata Daya da wani abu Komai tace tana so Cikin Rawan jiki yake mata da Tattali sai dai Lamarin ya Sauya ne Lokacin da Hajara Ta Fara Laulayin Ciki kuma sukaje asibiti aka Tabbatar musu Da Tana da Shigar Ciki na Tsawon Sati Uku da wani abu wannan Dalilin Shine Sanadiyar Tabarbarewar zamansu wanda har yakaisu ga Rabuwa da Juna na Har Abada.

Hajara tayi mamakin Sanda Usman Direba ya nuna bayason Cikin Jikinta atakaice dai bai Shirya Haihuwa yanzu ba,ya Tada Bala"in sai an Zubar da Cikin nan ita kuma Hajara tace bai isa ba

2 / 48