Advertisements
Chapter 42 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   42 / 48

123K to 126K   out of 143.7K words

Barkat ya Raina Fata ta Cigaba da gyada kai kafin tace"Haka yake ma ita kanta Anty Hafsah..? Mariya tace"Kwarai ma kuwa haka ma yake ma kowa Duk wanda yake kokarin Tsallake iyakar daya ijiyeshi.."Barkat tayi Tagumi kawai Ta kasa mgana Mariya na Shirin kara mgana Taji Kiran Abdullahi Daga Dakin Hafsah ta Mike da Sauri Tana Fadin"Na bani gashi chan yana Kirana.."Daga Haka ta Fice da Sauri Barkat ta Bita da kallo Tana Ayyana Zencen mariyan acikin Ranta ashe tayi kuskure bata sani ba..? Tayi kuskuran yima Man dinta gaddama yanzu gobe in ya Hanata komawa makaranta ya zatayi..?

Ashe Kiran Da Abdullahi yake ma Mariya Noor zata Dauka tana kuka Hafsah kuma ta samu Barci Shi kuma ya Tashi zai Shiga Wanka Bayan ya Mika mata ita ya Shiga yayi wanka ya Shirya Cikin Saukakkan yadi ya Fito Falo ya karya Har Lokacin Hafsah bata tashi ba Har Noor tayi Barci Fita yayi zuwa Dakin Barkat din ya sameta kwance tana karatun Handout dinta tana Jin Shigowarsa ta Mike tana gaisheshi ya amsa Fuskarsa ba Walwala mikewa tayi Tana Fadin bari ta kawomai Ruwa yasha Dakatar da ita yayi yana Fadin"No..Ki barshi kawai nasha Ruwa..Kinsan Abunda ya Shigo Dani..?
Ta girgiza min kai Kafin ta samu Zarafin mgana ya Cigaba da Fadin"Kinga dai Hafsah ta Haihu kuma Tana Bukatar Hutu Mariya ce kadai ga yara aiki yayi mata yawa ki Taimaka mata da wani aikin..."Cikin Girmamawa tace"Ok..Insha Allahu my man.."

Kai ya gyada yajuya zai Fice tayi Saurin Riko Hannunsa Ya waigo sai ta marairaice tana Fadin"Don Allah My Man...Kayi Hakuri na Tuba bazan kara ba.."Tafada Lokaci Daya Hawaye na Cika mata ido Kallonta yayi sai ta bashi Tsausayi yasaka Hannu ya Dagota ya Dafa kafadunta yana Fadin"Is ok..Komai ya wuce karki Damu.."Yafada yana Shafa kumatunta,Fadawa Jikinsa Tayi Tana mai Godiya Rumgumeta Shima yayi,Sun Dade ahaka kafin ya saketa yana Fadin"Bari na fita...Zan leka gidan Mama muyi sallama da goggo Habiba da Zannira.."Da adawo lafiya ta Rakashi ya Fice Har sai da taji Tashin Mashin Dinsa kana ta koma Daki.

Saboda Gudun karta kara wani Laifi,yasa ta Fita sukayi Girkin Rana Tare da Mariya ta kuma Yi ma su Amiran wanka ta Share Tsakar gida,Sukayi wanke wanke ita da mariya Saboda yunusa almajiran Hafsah Babansa ya rasu ya tafi Garinsu,Abdullahi kuma Gidan Mama yaje suka yi sallama da Goggo Habiba Shi yakai ta Tasha ya sakata a Mota,Zannira kuma Mijinta yazo ya Dauketa suka Tafi Daga nan gidan Mama makaranta ya Shiga Sai gabda mangariba ya Dawo Shago ya Biya yaga Abubuwan Da suka kare bai Jima ba chan ya bar Auwal ya Nufi gida ya Iske Barkat da Mariya sun yi Tuwon Shinkafa da Miyar Agushi,Sosai yaci ya koshi Bai Jima a Dakin Hafsah yamata sallama ya koma Dakin Barkat,Chan ta kara Bashi Hakuri shi kuma yace ya Hakura Ranar dai an kwana ana Soyewa kamar baaza"a rabu ba.

Washegari Abdullahi bai Fita aiki ba,Tun Safe Barkat kemai mganar komawa makaranta ammh yaki ce mata komai sai da 1pm na Rana tayi bayan sun Gama Girki ita da mariya tayi wanka ta Shirya tace mai Zata Tafi yace ba inda zata Sai ido ya Raina Fata ta Fara kuka yayi mata Banza karshenta ma Fita yayi yabar,Gidan ya barta Tana kuka Ganin Wankin Hula zai kaita ga Dare yasa ta Shiga Dakin Hafsah Tana kuka tana Komai ta gayamata,Hafsah batayi mamaki ba Sanin Halin Abdullahi tace bari ta Jaraba ta gani ta Kirashi awaya tace yana ina ne..? Yace mata yayi Nisa,Sai ta Fara Kokarin Shigarmai da mganar Barkat tana Rokonshi kan ya bar Barkat din ta koma makaranta ta Idasa Jarabawarta.

Abdullahi yayi gyaran Murya yana Fadin"Au zuwa Tayi takai Miki karana..? Tayi abanza kinsan Allah nayi Rantsuwa bazata koma Cikin makaranta ba..Ban ce bazata Karisa Jarabawarta ba ammh mganar ta koma Cikin makaranta ne Bazata koma ba in ta Yarda sai dai ta zauna Dakin Mijinta,Ta Rika zuwa tana Dawowa Fakat na gama mganata.."Daga Haka ya yanke Kiran ko Tsayawa Sauraran Hafsah ma bai yi ba..

Barkat bata Bukatar wani karin Bayani Tunda a Speaker aka saka Taji Komai,toh ya zatayi Dole tabi yarda yace ta koma Daki Tana Kunci Bahiya ta Kirata ta gayamata bazata samu Damar Dawowa ba ga yadda Sukayi da Abdullahi Bahiya nata Bata Hakuri,sun Dade suna mgana kana suka Katse Hajiya Amina ta Kira itama tana kaimata Korafin ita Fada ta Rufe ta dashi ta kuma ce Abdullahi yayi mata Daidai Jin Haka yasa Barkat din ta Kama bakinta ganin ba wata mafita sai na Bin Umarnin Abdullahi miji ga Hafsatu angon Barkat.

Koda ya Dawo Kara Jadaddamata yayi ya kuma ce in Taki Bin Umarninsa Wlh sai dai ta Hakura da Karisa Jarabawar,Ina Barkat zata Biyema Abdullahi tayi asaran Shekarunta na Baya,Duk Girman kanta sai da isarta Abdullahi ya Damata in ma wani Iskanci take ji ya Damata ya Shanye Da Daddare ma tana ta wani Fushi da Tura baki bai Biyemata ba sai ma Zoyalanta da yafara yana Mata Cakulkuli Dole ta saki Ranta kuma ya Karbi Hakkinsa ya Mori Abunsa Son Ransa.

Washegari Tun 7am ta Fita Taje p.Z Ta Hau Motan Samaru,Domin karfe 11am suke da Paper bata ma Tsaya Jiran Abdullahin Dayace in zai Fita aiki zai kaita ba Su Amira kuma mai mashin dinsu ya kaisu Tace kawai ya bari taje ta Hau Mashin din Haya yace Wlh bata isa ba da Auransa akanta bazata Hau Bayan wani kato ba sai dai taje ta Hau Mota komai adaidaita,Dole ta Hakura ta Nemi mai adaidaitan bata samu ba yasa ta karisa P.Z ta hau Motan Samaru Har takai makaranta tana Tsaki Ita kadai,Araina nace kyayi ki gama Indai Abdullahi ne baisan kinayi ba.

*****

Kwanci Tashi ba Wuya awajen Allah gashi Har Barkat ta kamallah Jarabawarta sun samu Hutu,tana Gida Umarnin Abdullahi kuma Shi aka Cigaba da bi na zuwa arika Dawowa Har ta kamallah Jarabawarta.

Sai Lokacin suka Raba Girkinsu ita da Hafsah Tunda Hafsah nada kwana Ashirin da Haihuwa Mariya ta koma Gida,Su Amira kuma sun samu Hutun makaranta Suna Gidan Ammi Daga Hafsah sai Noor Shiyasa Abun yazo mata da Sauki.

Zama Tsakanin Barkat da Hafsah zama ne dai na zaman Lafiya Tunda basu Fada ko wani Hayaniya Barkat na Girmama Hafsah daidai Gwargwardo Tunda Abdullahi bai sakar mata ba ya Nuna mata Darajan Hafsah Sosai,ammh Ta Ciki na Ciki Domin Barkat bata iya Boye Kishinta kan Hafsah tana ganin kamar tamallake Abdullahi ne Wani Lokacin ko Abu ne ya Faru ita ke shan Wahalansa Saboda Gaddamanta da kuma Taurin kai ita kuwa Hafsah ta san Halin yan kayanta tana Bi Dashi yadda ta Fahimceshi,Shiyasa Kafin kaji kansu sai andade kuma ko Fadansa yake Shuru take mai sai ya gama dai ta Rika bashi Hakuri ba kamar Barkat ba Da komai sai tace tamai Bayani Shi kuma Abdullahi bayason Doguwar mgana Shiyasa suke yawan samun mtsala.

Ya barta Taje gida ta Wuni,Ta kuma Je gidan Mama da Inna Abu,sai gidan Subai"atu Har Gidan Goggo Habiba ya kaita Kaduna ne da Gusai yace in Hafsah tayi Arba"in zasu Tafi Gabadaya Tunda Daman Hafsah ta Neme Izinin Zuwa kuma ya lamunce mata.

*****

Bayan Hafsah Tayi Arba"in Abdullahi bai Tsara musu Tafiyar ba sai da Hafsah tayi Yawon Arba"in Dinta nan Zaria Shima Daga Gidan Mama sai Gidan Inna Abu,sai Kuma Gidan Subai"tu wanda duka arana Daya Taje gidan Mama da Inna Abu,Gidan Subai ne taje ta wuni,sai gidan Ammi Tayi Arba"in da kwana Hudu Ranar Asabar Abdullahi yayi musu Tashan Mota suka je kaduna Har Dashi Gidan Zannira suka Fara Sauka Tayi ta ina ta saka Dasu,Tunda tayi aure Sau Daya Abdullahi ya Taba Zuwa gidanta sai Yau na Biyu Hatta Mijinta Shima sai Rawan Jiki yake,nan sukayi sallar azahar sukaci Abinci kana suka yi musu sallama suka Tafi Gidan Jidda Harda Zanniran sun kuma yi Sa"a sun iske har da Sakina Dama Sun san da Zuwansu,Jidda tayi musu Girke girke Kala kala Nazifi ya Tayata Lokacin da suka zo Haka take Murna Tana tsalle kan Jikinsu Zannira sai da Abdullahin ya Dakamata Tsawa Bakin Hafsah yaki Rufuwa ganin Jidda Har Ciki ya Fito Dama kuma Dataje Gidan Subai ta kyankyasa mata Cikin na Jidda,cikin ya karbeta tayi kiba ta Sauya kamar ba Ita ba Sakina kuwa sai Dan Wuya da Kwarmim Idanuwa Dakyar ta Fito Falo suka gaisa ta koma Ciki kamar mujiya nan Zannira da Hafsah da Barkat suka Shiga Ciki Suka bar Abdullahi da Nazifi Suna Hira bayan sun gabatar musu da Abinci sunce sai Zuwa anjuma.

Da suka Shiga Ciki ne Jiddan ke Fada musu Ta samu Addmission a Kasu zata karanta Polical Science,Suka Tayata Murna Barkat dai Tana gefe ba wanda yabi ta kanta sai ma Zannira ce ke Sakota Cikin Zencen suna Gidan Har Bayan La"asar sai da suka Ci Abinci sukayi sallar la"asar kana Suka Shirin Tafiya,Zannira da Nazifi sunyi sunyi su kwana Abdullahi yace ba kwana suka zo yi ba Wlh bazasu kwana Ba Tunda sukaji ya Rantse suka ma kama Bakinsu sanin Hali,Nan suka bar Zanniran Gidan Jidda su kuma suka Dauki Hanya Daman Tashar Motar da Abdullahi yayi musu Shi zai kaisu kuma shi ya maida su Sai Dare uka iso Zaria.

Basu samu Tafiya Gusai ba sai da Sati ya Zagayo Ranar Jumma"a suka Tafi Abdullahi ya Dauki Excuse awajen aiki,Su Amira ma Ranar basu je makaranta ba,Tafiyar safe sukayi Motar Haya suka Shiga wannan karon ba Shata yayi musu ba Saboda Rashin kudi,Wajen 12pm na Rana suna Dakin Ummam Sadiq tana ta Hidima dasu su Zahra da Sadiq nata Murna sun ga Anty Hafsah da Ya Abdullahi.

Azuwansu Gusai Barkat ta kara Tabbatar ma kanta Hafsah ta mata Zarrah ko acikin Dangin Abdullahi Motsi kadan Umman Sadiq Taga Hafsah tayi sai tace lafiya Haka Abokiyar zamanta sai nan nan suke da ita da Noor,Mijinsu Umman Sadiq ma Daya Dawo Shima dai Hafsah Barkat sai dai su gaisa da ita kawai Hafsah ce yar gida,ko Wajen kwana ma ita Hafsah Dakin Umman Sadiq ta kwana Barkat kuma Dakin Abokiyar zaman Umma,Abdullahi kuma Dakin Kofar gida nasu Sadiq ya kwana Da gari ya waye kuwa bayan sun karya sunyi wanka Suka je gidan kakanin Abdullahi nan Taga yadda Suke kamar su Goya Hafsah Har Wata Abokiyar Wasan Abdullahi tana Fadin Rigima ce yasashi kara Aure ammh ita tana Ganin Duk Duniya ba macen da zai samu kamar Hafsah Abun ya batama Barkat rai Har sai da ta Nuna ta Hade Rai Hafsah nema ke kare mata,Hafsah nan gidan ta kwana Barkat kuma takaichi yasa Tabi Abdullahi ta koma Gida Wajen Umman Gwara nan din da Sauki akan chan Gidansu Umman Sadiq din da Kiri kiri wasu suka Nuna basu Ji Dadin Auran da Abdullahi ya kara ba,Ranar lahadi da zasu Tafi sun ga kara kuwa da Tsaraba,Mota guda Mijin Umman Sadiq yayi musu Shata ya Biya aka Loda musu kayansu da Tsarabansu Har gida suka Suka bar su Umman Sadiq da kewa.

Bayan sun koma Hafsah ta Raba Tsaraba ta bama Barkat tace ta aika gida,nata itama ta Kai ma su Ammi Sauran kuma ta kaima Mama da Inna Abu,sauran kuma suka ije agida,suna amfani Dashi koda suka Dawon Hafsah sukayi ta Kira Suna ma Bangaji da Tambayan Noor Datasha Iskar Mota mura ya kamata sai da suka je Asibiti ita da Abdullahi Likita ya ganta ya Rubuta mata mgani.

Bayan Dawowarsu da kwana Uku Barkat ta Shirya zata Gidansu Abdullahi ya Hanata Da ta Fara Korafi sai ya Dakatar da ita yana Fadin"Ke meyasa kin Cika kawo matsala ne .? Ya kamata ki Rika Fahimtar wani Abu..Bana son yawan Fitan Rashin Dalili me zaki je gida kuma kiyi..?me kika Rasa Fisabillahi..? Inace ba kafin mu Tafi kinje ba.. kawai sai kuma Saboda ban da Hankali sai kuma na barki ki koma ko.?Ba Haka nake ba ni ba Sakarai bane da zan bar matata ta Dinga Fita Duk inda taga Dama Ina da Tsari Kuma Tsarina nake Bi malama ki koma ki zauna ba inda Zaki.."

Baki Tahau Turawa tana Fadin"Allah nafi sati Uku Rabona da zuwa gida..Ina son ganin Hajiya da Sauran yan"uwana.."

Mamaki ya kama Abdullahi ya Rike Baki yana Fadin"lalle me kin samu Wuri..? Ke sati uku kikace Ita Hafsah tace me..? Wlh tana Fin Wata Biyu bata je gida wajensu Ammi ba kuma bata min Korafi kin fi ta son iyayenta ne..? Ina mai Tabbarmiki ko gatan banza ta Fiki ammh Bata kin Bin Umarnina inda na ijiyeta nan take tsayawa bata iya Tsallakeshi Gaskiyan Nazifi ne Bazan Taba samun Macen da Zatamin Biyayyan da Hafsatuna takemin ba abaya ban yarba ba Ammh Zuwa yanzu na gama yarda da Hakan.."

Ya Fada Lokaci Daya yana Hade Rai,Kallon Takaichi da Kishin Hafsah ta bishi Dashi kafin kawai Ta Bude baki Tana Fadin"Nidai na Shiga uku Ni barkat..? Komai Hafsah...Kai ka Kira Hafsah kannenka su Kira Hafsah Mama Hafsah Inna Abu Hafsah..! Umman Gusai Hafsah,Kowa Hafsah kowa Hafsah komai zakayi Hafsah kwatancenka Hafsah ne Shin Ita kadai ce matarka..? Ko ni bani da wani amfani a wajenka da wajen Dangina ne har Kuma Da kake min Gorin gata... ? Ni wlh na gaji Na gaji..Wannan Hafsah Tana Tsayamin a kahon Zuciyata Sunanta na Fadarmin da gaba Tana Shigemin Hanci da yawa nagaji Nagaji..!

Tafada Lokaci Daya tana Sakin Kuka Galala kawai yayi da baki yana kallonta Bai samu Zarafin mgana ba,ta kwasa Zuwa Cikin Bedroom dinta tana kuka Da kallo ya bita Har ta Shige Ciki wani Munafikin Mirmishi ya saki Lokaci Daya yana Daga Murya yana Fadin"Hafsah..! Hafsatu Matar Abdullahi bawan Allah..Wai ita kike cewa ta Tsayamiki arai..? Kin gaji da jin kowa na Kiran Hafsah ko..? Lalle kuwa Halin mutum Jarinsa,in Ko Hakane ashe zaki Mutu da bakinciki Domin Sunan Hafsah a Rayuwar Abdullahi kamar wani Zanen kaddara neda"a ka Riga aka Rubutu kinga kuwa kina da katoton aiki kenan.."Daga Haka ya saka kai ya Fice Daga Dakin nata Yana ta mamakin yadda ta iya gayamai Mgana kan Hafsah.




*Domin Biyan Kudin Karatu akan Littafin Ra"ayi ne ko Buri..? Zaku iya Tura kudin karatunku ₦200 Kachal akan wannan asusun bankin 0552179550...JAMILA UMAR GTB,Sai a turo Shedar Biya ta wannan layin wayar 09069067488,In kuma Katin Waya ne zaku iya Turowa ta wannan Layin 09027767783 kai Tsaye Bayan Mutum ya Dauki Hoton katin...Ga masu Bukatar VIP zasu Biya ₦500 ne ta Lambar asusun Dana bada a sama....! Mutanenmu na Niger kuma Zaku iya Tuntumbar My Jika aglan Nissa ta wannan Layin +22794131747....Sai kunzo Masoyana*





*Janafty Shakira..*
4/9/21, 2:00 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!


*038*

"Har Abdullahi yakai Office yana Tunanin maganganun Barkat Abun ya Dauremai kai matuka kuma Kaso mafi yawa Daga Cikin kimarta sai yaji Ta Ragu ba saboda komai ba sai Saboda Ta Nuna Kishinta karara akan Hafsah har kuma Hakan ya saka mata Tsanarta acikin Ranta Batare da ta mata komai ba..Miye laifin Hafsah..? Itafa tazo ta isketa da Mijinta Suna Rayuwansu Ta Shigo Cikinsu Ashe kuwa indai Ita bata Bude baki Tace tana Shigar mata Hanci bai kamata ita Barkat din Tace Haka ba,Domin Shi yana da yakini kan Hafsah 100%Bata da Tunani ko Zuciyar Cutar da Barkat Tana Zaune da ita ne Tsakaninta da Allah.

Tagumi kawai ya Zuba Lokaci Daya yana Cigaba da Auna Abubuwa masu Girma Ta Bangaran Hafsah da Barkat,Ko kankani basu ma Daidai ba Domin Akowani Mizani in ya Auna sai yaga Hafsah Tayi ma Barkat Fintinkau Bata iya ma Tsara da ita,Ta Bangaran Hakuri,ta mata Zarra ta Bangaran Ladabi da Biyayyah Wlh zai bada Rantsuwa kan cewa Duk Matan Duniya Ba Mace mai Ladabi da Biyayyah Uwa Uba Hakuri Bayan Hafsah,Sai kuma Bangaran iya Mu"amala da kuma Yadda zata Tafiyar da zamantakewarta Yafi kowa sanin Wacece Hafsah bai Taba Jin wanda ya Fadi aibunta ba Kama Daga Danginta Zuwa Danginsa ba,Hakika Tayi Gadon Dattako da kuma kyawawan Halin Iyayenta,Ya sani Mama Tamkar uwa take gareshi Ammh Ita kanta tana Girmama Hafsah,Umman Sadiq ita ta Haifeshi ammh Tafi Girmama Bukatun Hafsah Fiye da nashi Bukatun Kuma Tana Fadamai koda yaushe sukayi mgana kan ya Rike Hafsah da gaskiya da Amana Domin In ya bari ya Rasata ko kuma Giyar Rudin Duniya ta Sameshi ya Wulakantata Toh Tabbas Watarana zai yi Nadama,Kuma zai yi Kuka da idanuwansa Domin bazai Taba sanun mace kamarta ba bai kara gasgasata mganar Umma ba sai yanzu Daya Auro Barkat yaga Bambamce Bambamce Halayyah Da yawa ta Bangaran Hafsah sai kuma yanzu yake Tunanin kodai mganar Nazifi gaskiya Bayan Hafsah ba Macen da zata iya Hakuri ta zauna Dashi..?

Gabadaya Ransa yana Jagule ne Dakyar ya iya yakice komai ya maida kai ga aikinsa ammh Kuma Gefe Daya na Zuciyarsa na karfafamai Gwiwan Takama Barkat din Burki Domin Bazai Lamunci ta Raina mai Mata ba gaskiya Indai Hafsah batace ta Tsare mata komai ba itama bata da Wannan Damar da zata Fadi Wata mgana kan Hafsah Domin akomai Da take ganin Hafsah Ta mata Fintikau Halayyanta ne suka Siya mata Duk Wannan Kimar Datake gani tana Kishi akanshi.

******

Baiwar Allah Hafsah bata son Wainar da Aka Toya da safe Tsakanin Abdullahi da Barkat ba Dama Jiya ita ta Fita Girki Barkat din ta karba,Da Safe kuma Abdullahi ya Shigo mata Sallama ya isketa tana Wanka Su Amira Kuma Daman Mai mashin Dinsu ya kira yakaisu so basu Hadu ba Balle Taga Cikin yanayin Daya Fita Noor kadai Dake kwance kan gado yayi ma Wasa ya Fice.

Har Wajen 12pm na Rana bata ji Motsin Barkat ta Fito ta Daura Girki ba sai Abun ya bata mamaki Ta sani da Wuri take Gama Girkinta,Sai Tayi Tunanin kila Girki Daya Zatayi ammh sai me Har Pass2 shuru bata ji Motsinta ba Duk da haka dai bata Fito ba,Tana Daki Ita da Noor Dataji yunwa Sai Ta Hada Tea tasha,Har Amira suka Dawo Makaranta Barkat bata Fito ba Suna Ta Tambayan Abinci sai ta Hada musu Complex suka Sha Suka kwanta kafin Lokacin Islamiya sai Lokacin ta Fito Tsakar gidan Abun mamaki Dakin Barkat din ma na Bude ammh Kwata kwata ba Motsinta sai Hafsah ta Fara Tunanin kodai Bata da lafiya ne..? Kamar zata Shiga sai kuma ta Fasa Tunda Daman bata Shiga Dakinta sai ta kama Kuma Daman yau din Barkat din bata Leko Ta mata gaisuwan Safe

42 / 48