Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
Cikin maza masu Duka Da Tuni Barkat tana Chika Emergency Domim sai na sauya mata kammani da Duka kaji ma na Rantse.."
Yafada Cikin Tabbatar da Abunda ya Fada,Dariya ta kusa kama Nazifi ya kanne yana Fadin"Lalle kuwa bata kyauta ba..Ammh Kasani Abunda nake gayamaka abayane yau zan maimata maka..Wlh Tallahi mutumina Ko mata 100 zaka Aura matukar basu tafiyar da kai yadda Baiwar Allah nan Hafsah ke Tafiyar dakaiba, bazaku Taba Shiryawa ba..Fada ne kawai zaku yi Tayi Domin komai suka maka zaka ga ba Daidai bane,Saboda samun mace irin Hafsah sai An Tona Hakurinta Daga Allah ne,wanda Ba kowa Allah ke bamawa ba,Su kuma matan zasu ga suna iya bakin kokarinsu baka gani kullum sai kace Hafsah tafisu Don Allah ko kai ne ya zakaji in Kana Abu ba"a gani kuma ana cewa abokim Hamayarka yafi ka iya komai..? Ka auna Abunda da Mizanin Kishi... ? Don Allah za"a zauna lafiya..? Baza"a zauna ba lafiya ba Fada ce kullum zaku Dinga yi Daga karshe ku kasa Fahintar juna ku Rabu ina amfaninshi..? Sai da na Hanaka wannan Auran kaki jin mganata..? Yanzu ina amfaninshi Aure Wata uku bai ma kai ba,an fara Jin kanku..? Wlh Duk Abun bai Yi Dadi ba Mutumina sam.."
Ya Karishe Fada Cikin Damuwa,Ajiyar Zuciya Abdullahi ya saki Yana zama Gefen Gado Lokaci Daya yake Fadin"Wlh Duka mganganunka gaskiya ne Abokina..Abaya ban Fahimci haka ba sai da nayi kuma na gani..Hakika Ba mace kamar Hafsah abokina..Zan Tauye mata Hakki maimakon Tayi Fushi sai ma Tamin Godiya zan Mata masifan kan laifin da bada gangan ta aikata ba ammh Ta bani Hakuri zan Kaurace mata Bisa karamin Abu ammh Tabini tabani Hakuri zan Hukunta ta kan laifin da ba nata ba ammh Tabini tabani Hakuri Akullum Hafsah bata Fushi mai Tsawo Dani koda kuwa me zan mata..? Arayuwarta na Hana ta Cikar Burikanta Dadama Abokina ammh Bata Taba Nuna mim wani Abu na Rashin Jin Dadinta ba ita dai Abu Daya ta sani Abdullahi Mijinta ne kuma Bautar Aure take zatayi Hakuri Dashi a Duk yadda yazo mata bakomai take Fata ba sai Aljannah Hakurinta ba irin na Mutanen Duniya bane Mutumina Hakurin Hafsah na Irin Matan aljannah ne Wlh Ina Ji ajikina Tabbas Banga mace wacce zata Iya yima Mijinta Biyayyah kamar yadda Hafsah kemin ba ta Jura Zama da Masifffan Namiji ta kuma koyo Zama dani ahaka Hakika ta Chanchanci kowani yabo na kuma na Fahimci Abunda ya kamata Tuntuni na Fahimta Nagode Mutumina..Insha Allahu zan kira Salisun miyi mgana.."Abdullahi ya karishe Fada Cikin Sanyi Jiki,Shi kanshi Nazifin Jikinsa yayi sanyi Cikin Wani yanayi yace"Duka kalamanka gaskiya ne..Nima sai bayan dana Auri Jidda na Fahimci bai kamata mu Rika ma Abu Dubar duka Daya bane..Wake Daya baya bata Buhu Duka koya aka Tsince za"a samu na kwarai Ina Nadamar Shawarwari da na Rika baka kana Muzguna ma matarka ina jin kunyar kaina ayanzu na saka ka kana Hukunta matar da bai Dace ta samu komai a wajenka ba Face Soyayyah.."Mirmishi Abdullahi yayi kafin yace"Karka Damu Mutumina..Koda Shawaranka nima da nawa Halin na Saurin Fushi da Zuciya..Ammh Insha Allahi Fushina bazai kara Tashi kan Hafsatuna ba sai dai in Cikin Rashin Sani ne.."
Nazifi yace"Dakyau Mutumina naji Dadin Haka..Sai da safe sai mun kara mgana.."Daga haka suka yanke Kiran Tagumi Abdullahi ya Zabga yana Tuna Irin Abubuwan Dayasha yima Hafsah da alherinta garesa Nadama na kara Shigansa Da kuma wani Sonta da Tsausayinta,Yana nan zaune ta Shigo ta Shimfidar da Noor,bayan Ta kada su Amira sunje sun kwanta tazo Kusa Dashi ta Dafashi ya Dago Jajayen Idanuwanta yana kallonta Cikin Mamaki tace"Abban Amira lafiyanka kuwa..? Kaga yadda idanuwanka Sukayi ja kuwa..?ko Ciwo suke maka ne..?
Ta fada Cikin Tashin Hankali Girgiza mata kai yayi Lokaci Daya ya Mike tsaya ya Rike Duka Hannayenta yana Fadin"Karki Daga Hankali ba komai..Wannan Jan ido bafa komai bane acikinsu illah Tsananin Son Matata HAFSATU da Tsausayinta Uwa uba kuma Sha"awarta Nagaji da wannan Horan naki fa Rabona dake Tun Da Cikin ki ya Tsufa bayan Kin Haihu na Daga kafa kikazo kika gama wanka kikace sai kin gama wayon arba"in kin gama kuma kika Fara jamin aji da nayi mgana sai kice kin barma Amaryani Tagama Morewa kana anya kin min Adalci kuwa..? Kinbar bawan Allah Cikin wani hali.."
Yafada yana kureta da Ido Mirmishi ta saki kawai Tana kallonsa kafin tace"Eh mana...Na bar ma Amarya kai Na wani Lokaci Tunda ai ni Tsohuwar Hannuce ko..? Ya"ya na uku fa Abban Amira..?kallonta yayi ido Cikin ido kafin yace"Zaki iya yafemin Laifikan dana aikata Miki Tun Farkon Auranmu zuwa kawo yau Hafsatuna...?
Mamaki ya Cikata ta Tsuramai Ido Tana kallonsa yadda ya marairaice mata kamar zai mata kuka bata gama mamaki ba Taga yayi kasa ya Duka kan gwiwowinsa Lokaci Daya yana Rike da Hannayenta ido ta kwalalo Cikin mamaki Take Fadin"La'ila..Meye haka Abban Amira.."Ta fada tana kokarin Dagowa yaki sai ma Fadi Daya ke.."Zaki iya yafe ma Abdullahinki Duk da yasan Shi mai Tarin laifi ne gareki..?
Yafada yana sakarmata idanuwansa masu Cike da wani Sirri wanda Hafsah ne kadai ta sani,Tuni Jikinta ya Fara rawa ganin Abdullahi Durkushe agabanta kamar zai mata kuka itama Binsa tayi ta Durkushe Lokaci Daya tana Damke Hannunsa Cikin Sanyin murya tace"A"a Abban Amira bai dace ka Dukamin ba..Ni matarkace kuma ina karkashinka..Kuma aljannata tana Wajenka Abban Amira taya zan ce kamin laifi har na iya Rikeka acikin Raina..? Ko Daya Wlh bakamin komai ba koma kamin Tun Alokacin nake yafe maka Abban Amira Nine ma zan Rokeka ka yafemin Abunda na maka Abban Amira ni yafi Chanchanta na Rokeka gafara kila Ina Kuskure maka ban..."Shiiii! Bai bari ta karisa ba yasaka Dan Yatsansa ya Dakatar da ita Tsurama Juna ido Sukayi na wani Lokaci Kafin ya Bude Baki Cikin wata Murya yana Fadin"Baki Tabamin laifi ba Hafsatuna...Nine dai mai laifin a wajenki..Kuma Daga yau nayi Miki alkawarin Duk wani laifi da zakimin da gangan ko Cikin Rashin sani ni Abdullahi na yafe miki Duniya da lahira..Kuma nayi miki alkawarin Masifaffan Mijinki zai Rikide ya koma Miki Cikakken Masoyi kuma Miji na Hakika aljannah kuma Hafsah Wlh Kin Riga da kin samu Domin Tuni na Daga Miki kika Shiga ke zaki zama Jagoran Matana na gidan al"jannah Nagode Hafsatuna Nagode kwarai Allah yayi miki albarka.."Yafada yana kara Damke Hannuwanta Jikinsa kawai ta Fada tana sakin kukanta Shima ya kamata ya kamkame yana Sakin Numfashi kamar ya saki kukan Lokaci Daya yana Bubbuga bayanta alaman lallashi.
Ganin Taki Tsagaita kukan yasa ya Dagota yana Share mata Hawaye Cikin Shagwaba yake Fadin"Wannan kukan naki nasan mganinsa... " Yafada yana Lakace mata Hanci,Saurin Zillowa tayi ta koma Kirjinsa ta lafe Shi kuma ya mike ya Dagata Cak yana Fadin"Yau ko ana so ko ba"a so sai na More Abuna.."Cikin Dariyan Farinciki tace"Balle ma ana so.."
Tafada tana Zagayo da Hannayenta saman Wuyansa ta makadesa Lokaci Daya tana sakarmai Kiss Bangare mata yayi yana mata Kukan Shagwaba Ahaka suka Shiga Tiolet ya Sauketa ya samusu Ruwan sanyi Cikin Wani Babban Bawan Hafsah da takan Tara Ruwan sama,Dayake garin ana zafi ya Tube itama Hafsah ta Tube ya Dauketa ya Tura Cikin Ruwan Shima ya Shiga Dayake Babban Baho me mai Girma,Watsa watsan Ruwa suka Fara suna Dariya kafin kuma wasan ya Chanza Salo Abdullahi yakamkame Bakin Hafsah yana Tsota gefe Daya kuma yana ta Wasa da Nonuwanta da suka Cika Sakin mata Numfashi kawai yake itama Wasa take da Nipple dinsa Lokaci kuma tana wasa da reaction dinsa wanda ta saka ya Birkice mata yana neman Shigarta acikim Bahon Dakyar ta lallashe shi ya bari suka Fito Daga bayin bayan sun yi wanka Daga Tiolet din Sai kan Gado bama wanda ya nemi kaya suka kama juna Cikin Fitan Hayyaci baka jin komai sai Tashin Numfashi Kamar zasu Cinye juna bamai Saurarama Dan"uwansa kowa kokarin Nunama Dan"uwansa yake yadda yayi kewarsa.
Kusan kwana sukayi suna Abu Daya Stayels kuwa Kala kala ba Wanda basu yi ba sun Jiyar da Juna Dadi Sosai wanda baya misaltuwa sun kuma kara yardan ma juna sun Riga sun zama Hanta da Jini,Sai Wajen 3pm na Dare suka Sararama Juna Suka je sukayi wankan Tsarki Suka Dawo suka kwanta Inda Allah ya Taimakesu Noor bata tashi ba sai gabanin Asuba Ta Fara kuka Barci ya ci Idanuwan Hafsah Dole Abdullahi ya mike ya Dauketa yana Lallashi Acikin Ranshi kuma yana Gode mata Domin ta bashi Dama ya More Dakyau.
Gabadayansu sun makara Sallar Asuba,Makaranta ma su Amira Sai wajen 8am na Safe Abdullahi ya Tafi ya kaisu yabada Hakuri Daganan ya Dawo Gida yayi wanka ya karya Sukayi Sallama da Hafsah ya Fita Zuwa Cikin makaranta Domin Allah ya Taimakeshi ya kusa gama Project dinsa,Dagachan ya wuce Wajen aiki,Wajen 2pm na Rana bayan sun Fita Sallah ya Kira Salisu yace in ba Damuwa su Hadu yace Mai bakomai gashi nan zuwa ba"a Dau lokaci ba kuwa sai gashi Suka samu wani Waje sukayi mgana sosai Salisu ya bama Abdullahi Hakuri Yace mai bakomai Dayayi mai mganar Komawan Barkat Sai Abdullahi yace ta Dakata ba yanzu ba Yana son ta ZAUNA agida Tayi koda wata Biyu ko uku in ta kara Hankali sai ta koma Ammh mganar gaskiya yanzu Baya Bukatarta Duk da bazai Saketa ba Saboda baya son ya zama Namiji mai sakin Aure ammh Tabbas ta zauna agida ta kara sanin Rayuwa da kuma yadda ake ma Miji Biyayyah.
Ba yadda Salisu zai yi ya bashi Goyon Baya suka Rabu akan Haka,awaya ya Kira Hajiya ya gayamata komai da yadda suka kare mgana da Abdullahi Hajiya tace ai yayi mata Daidai gwara ta Zauna agida Sai ta kara Hankali da Barkat Taji labari bata Damu ba tana ganin Dole ya Sauko yazo ya bata Hakuri ya maidata,Ita kanta Bahiya Da tadawo Gida Taji Labari bata Ji Dadi ba kuma itama Barkat din ta Dorama laifi tare da ankaran da ita kuskuranta ammh alokacin Tayi Nisa batajin kira.
****
*Bayan Wata Biyu..*
Zuwa Lokacin Tuni Kowa yasan Labarin Barkat bata Gidan Abdullahi,Labari har gusai Umman Sadiq dataji labari tace ai Daman ta Fada Ba kowa zata iya ZAMA da Abdullahi ba sai Hafsah.
Haka kowa yake fada in yaji Labari Subai kuwa tafi kowa Murna Hafsah kuwa bata ji Dadi ba Duk da Tama Abdullahi mganar Barkat din ya Roketa da Allah da Annabi karta karamai wannan mganar,Dole ta kama bakinta Hakika Abdullahi ya Chanza kamar yadda ya Fada,Domin Yanzu Lallaba Hafsah yake kamar Tsoka daya Amiya sai Dai Abunda ba'a Rasa ba,Fushinsa kuma yanayi Lokaci Bayan Lokaci ammh yana Controlling dinshi ba kamar baya ba Bangaran Kulle kowa Babu Abunda ya Sauya in yayi Ra"ayi Taje in bai yi Ra"ayi ba yace ya Hanata Dole ta Hanu,Bata da yarda zata yi kaifi Daya ne Dama Kuma yana nan bai Sauya ba.
Bangaran Barkat kuwa Bayan Dawowarta Gida Da Sati Uku Suka koma makaranta Tattara ta Tafi Tare da Jiran Tsammanin Abdullahi zai nemeta ya bata Hakuri,Wanda bai taba Kiranta awaya ba Itama Girman kanta ya Hanata ta kirashi ta koma makaranta da kwana Goma Jiri ya Dibeta Ranar sun Fito daga Lecture ta Fadi aka kwasheta Zuwa Clinic Din makaranta gwajin Farko sai ga Ciki ya bayyana a Gareta dan Wata uku,Yayanta Salisu tace kawayenta su kira mata ta karbi Wayar tamai Bayani Shi yazo ya Tafi da ita Tare da Takardan gwajin Cikin Barkat tafi kowa Murnan da Cikin Domim tana ganin ta samu Hanyar da Abdullahi zai zo gabanta ya bata Hakuri ta koma Dakinta Ko Domin Cikib Jikinta sai dai kuma Kash Batasan waye Abdullahi ba Koda Salisu ya Kirashi ya gayamai bai zo ba Fatan samun lafiya kadai yayi mata sai kuma 20k Daya Turama Barkat din Ta Bankinta yace na Hidimar asibiti kira ko awaya bai yi ba kuma bai je ba,Da Hajiya ma Taga Samuwar cikin Sai Take Fatan komai ya Daidaita ammh kuma Ba Tabbas Domim Tunda Barkat ta Dawo gida bai Tako Kafarsa ba sai da Hafsah ta gayama Su Mama bayan yazo ya gayamata Barkat Nada Ciki tayi kokarin Nuna mai yaje Zuwansa nada Muhimmanci ammh yayi mata Rantsuwan kafarsa bazai Taka ba Tukunnah dai Har yanzu Barkat Batayi Hankali ba in Lokacin yayi zata nemeshi da kanta Wannan Dalilin yasa ta Kira Mama ta gayamata ita kuma ta gayama Inna Abu suka Tafi Gidansu Barkat din suka Dubata,Sun iske ma Taji Sauki Hajiya Aminan tace musu ma Zata koma makaranta sati mai zuwa Karatu nata wuceta,Sauran kayan Sawanta Bahijjat tazo ta Diban mata Wajen Duka Kadan Ta Rage Hafsah na Gida sun gaisa Dai sama sama Tunda Ita Bahijjat din tana Bin Bayan yar"uwantane.
Tun Barkat na saka Ran ganin Abdullahi har ta sare Tana ji Tana gani ta Tattara ta koma makaranta Lokaci Daya tana Cigaba Da Renon cikinta,Don ma Suna Tare da Bahiya tana Taimakamata Sosai Tunda Har yanzu a wajenta Take Sukwatin.
*Wa ina Masoyan nawa ne..? Nifa ban gansu ba..? Kuna ina ku Fito mana Ina yan Gidan Janafty Shakira,Janaf Novellah 1&3,Zauren Janafty,Taskar Janafty,Ina yan Gidan Masifaffan Namiji suke..? Nasan ina da Masoya na nesa Dana kusa,Ina Masoyana masu Dogon Sharhi na Wattpad Dina..? Kuna ina Har yanzu RA'AYI NE KO BURI..? BAND 1 bai cika ba Don Allah wannan ba Abun kunyarku bane..? Na tabbata wadanda suka karanta Labarin Masifaffan Mijin Hafsatu suna da yawa sunfi Dubu da Milayan fa..? Ammh kuma ace har yanzu Janafty bata cika ko Group Daya ba... ? Anya ba Kuna son amin Dariya bane...? A"a Wlh Dariya kuke so Sauran marubuta yan"uwana suyimin kuma baku san Bayan Sallah Wani Salon labarin yazo muku a barka da Sallah ko..? Indan har ba kunya kuke so ku bani ba ina son kafin nam da zuwa gobe ko Jibi Paid Group 3 su cika na RA'AYI NE KO BURI..? ammh fa in har baku son Mutane su mana Dariya ace Tarin Masoyan Janafty bama su Son Cigabanta bane kawai masu son karuwa da ita ne..! Na Tabbata akwai wadanda ko 1k na saka Buk dina zasu Siyeshi Domin ba iya Labarina Suke kauna Suna Son Cigaba na Sosai,Ina Bukatar naga zallar kauna Ta Hanyar Siyan Littafina na RA"AYI NE KO BURI..?Kan Farashi mai Sauki ₦200 Vip ₦500 ne Don Allah in kina da kudin Siyan Guda Biyu ke Siya Daya Ki siya ma wata na kusa Dake Daya Sai Allah ya baki lada in ta karanta wannan labarin kuma ta karu Dashi,Daku nake yan Gidajena na Amana,Gidan Janaf Novellah Duka ban Cire kowa ba Ku za"a Fara ma Dariya Matukar ku kabani kunya Ina Rokon Allah ya baku ikon Siya Ya kuma sa mu Dace Duniya da lahira..Ina matukar Godiya masoyana...*
*Domin Biyan Kudin Karatu akan Littafin Ra"ayi ne ko Buri..? Zaku iya Tura kudin karatunku ₦200 Kachal akan wannan asusun bankin 0552179550...JAMILA UMAR GTB,Sai a turo Shedar Biya ta wannan layin wayar 09069067488,In kuma Katin Waya ne zaku iya Turowa ta wannan Layin 09027767783 kai Tsaye Bayan Mutum ya Dauki Hoton katin...Ga masu Bukatar VIP zasu Biya ₦500 ne ta Lambar asusun Dana bada a sama....! Mutanenmu na Niger kuma Zaku iya Tuntumbar My Jika aglan Nissa ta wannan Layin +22794131747....Sai kunzo Masoyana*
*Shakira..*
4/9/21, 2:00 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*
*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!
_*Hakika Naso nayi Tuya na manta da Albasa Ina neman Dauke alkalamina kan Masifaffan Namiji Batare da na Mika Godiyata Gareta ba..Ba wata Bace Face TAKWARATA MAMAN UMMI...nagode sosai da Irin Kulawarki Gareni Allahu Ya bar zumunci Ameen..*_
*040*
"Barkat dai ta koma makaranta Tare da Jiran Tsammani Domin Ita Har yanzu har kuma acikin Ranta bata Fidda rai Da Abdullahi zai nemeta yazo ya bata Hakuri yace ta koma Dakinta ba,balle kuma Data samu Ciki sai kanta ya kara Girma Tana ganin kodomin Cikin Jikinta zai nemeta su Daidaita Ba zencen Nadama acikin Al"amarinta Balle har ta Zauna Ta gane kuskuranta nan kusa Har tayi kokarin gyarawa.
Abunda bata sani ba Shine batasan Waye Abdullahi ba yafita Taurin Zuciya ya yarda Komin Son da yake ma Mace in ta Batamai ya nuna mata kwanjinsa na D'a Namiji,Tunda Barkat ta koma Gida bata nemeshi ba sai dai Yayanta Salisu ya nemeshi da wan Babansu na Sabon gari ammh ita bata kirashi ta bashi Hakuri ba ko Wata mgana Kenan Ta na nan Har yanzu kan bakanta Girman kanta da isarta bazasu barta ta Kirashi ba Tana Jiran Shi ya Kirata ya bata Hakuri ya kuma ce ta koma,Toh yana so ya Nuna mata Tayi kuakure Babba Matukar Bata gyara Halinta ta Fahimci Gaskiyaba, zata Shekara Dubu agidansu kuma bazai Saketa ba sai yaga Karshen Iskancinta da Girman kanta.
Babu wanda bai mai mgana kan Barkat ba ammh ya nuna abarta Tukunnah Baba wada ma yamai mgana sai yace mai zata Dawo ammh ba yanzu ba Haka Daddy ma Har gida yace yazo ya Sameshi,bai ma sani ba sai Daga baya Ammi ke Fadamai Daya Nemi Abdullahin ya Dawo da Barkat din Tunda Ammi ta Fadamai Hafsah tace yayi Rantsuwa bazata Dawo yanzu ba,Toh Shima uzurin daya bashi kenan kan cewa zata Dawo ammh ba yanzu ba sai Zuwa gaba in Tagaji da zaman Gidan Rayuwa ta Horata ta kuma Fahimci Gidan Mijinta Shine Rufin Asirinta.
Dole suka kyaleshi Yayi yadda yaga Dama Tunda Matarsa ne yafi kowa iko Da ita Umman Sadiq kuwa da Inna Habiba basu Topha bakinsu ba sunce Daman sanda ya Rarumo Auransa bai Yi Shawara da kowa ba Yanzu ma Yaje chan ya karata ba Ruwansu Gwara ma Mama da Inna Abu sun saka baki ammh Abdullahi yace su Cire Bakinsu acikin mganar Barkat zata Dawo Lokacin da ita ta Bukaci Hakan,kuma Har yau bai iya Bude Baki Bayan Nazifi ya Tattauna Abunda ya Faru da wani ba gani yake kamar Za"a mai Dariya Shiyasa yayi Gum da Bakinsa kawai.. Bangaran su Subai kuwa Mariya Taje gidanta ta Tsegunta mata ita kuma ta Kira Hafsah Ta Tambayeta Shine take gayamata Abunda ya Faru wani Shewa Subai ta saki Ta Daki Cinyarta Tana Fadin"Waya gayamata Barno gabas Take don Ubanta..Ai Yaya Abdullahi sai ke Hafsah ko Ni Danake kanwarsa bana iya ZAMA dashi nayi Hakurin da ke keyi Dashi..Dama na sani wannan Auran bazai je ko"ina ba Domin bazata iya ba Karya Take Yaya Abdullahi