Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
ammh Me ya Nazifi zai ci Dake..? Kyan banza da ilimi matarsa bata Fiki ba Don ma kin samu zai Taimaka miki har wani Cewa kike baki sonsa..? A kyaleki sai ki kawo wanda ya Fishi Tunda kin zama wawiya.."Jin haka yasa ta kara saka kuka Sai Da mama ta tsawatar ma Auwal din kana Mariya kuwa Baki ta Rike tana Fadin"Lallema yarinyar nan..Kin samu Dami a akala har kina wani iskanci..? Wlh dama nice ke Danace nafi kowacce mace sa'ar samun Miji na nuna Sa"a yarda Maza ke tsada a wannan zamanin"
Wannan mganar tasa Jidda tace ma Mariya ta Bar mata taje ta Aureshi Mganar har ta kaisu ga Sa"in sa sai da mama ta Shiga mganar Jidda saboda kuka da Damuwa wayartama kasheta tayi Gabadaya Hajiya Sa"a tayi kiran Duniyan taji a kashe,gashi tana kaduna wajen kokarin Bude Shagunanta ,balle tazo gidan Taji lafiya ammh takira Lariya tace tazo Tagani ko Jiddan Tana lafiya.
*Domin Biyan Kudin Karatu akan Littafin Ra"ayi ne ko Buri..? Zaku iya Tura kudin karatunku ₦200 Kachal akan wannan asusun bankin 0552179550...JAMILA UMAR GTB,Sai a turo Shedar Biya ta wannan layin wayar 09069067488,In kuma Katin Waya ne zaku iya Turowa ta wannan Layin 09027767783 kai Tsaye Bayan Mutum ya Dauki Hoton katin...Ga masu Bukatar VIP zasu Biya ₦500 ne ta Lambar asusun Dana bada a sama....! Mutanenmu na Niger kuma Zaku iya Tuntumbar My Jika aglan Nissa ta wannan Layin +22794131747....Sai kunzo Masoyana*
*Shakira...*
4/9/21, 1:57 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*
*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!
*024*
"Washegari ta kama Ranar Jumma'a ne Tun Safe sai ga Hajiya Lariya ta Dira Gidan Mama Lokacin Jidda na Cikin Dakinsu tana Kukanta data Farashi Tunda mganar Auranta da Nazifi ya Bullo Mama tayi Lallashin Duniyan nan taki Shuru da kukan Sai ta kyaleta, Mariya ma Tunda Sukayi wannan Tsiyar haka suka kwana ko Mgana basu yi ma juna ba, Ballatana Auwal Da Dama basu Shiri kamar Itace Sakonsa koda mariya basu Cika Fadan da suke da Jidda ba kodon Mariya ita bata da Rawan kai ne kamar Jidda...?
Tun Safe ko Tsakar gida bata Fito Ba Dama Tana Fashin Sallah,Mariya kuma Tun wajen 7am na Safe ta Fita Zuwa Asibiti Auwal kuma sai da 8am ta Buga kana ya Fita yana ma ta Sauri Suna da Test a makaranta Mama ce kadai acikin Gidan Duk da kukan Jiddan ya Dameta ammh bata da yarda Zatayi ko da Safen nan da sukayi mgana da Abdullahi ta Waya ya kara Jadaddamata mgana ba Fashi So in ma zata Daina kuka gwara ta Daina.
Bayan sun gaisa da Mama Hajiya lariya Ta Tambayi Jidda Mama Ta nuna mata Dakinsu tace ta Shiga Tana Ciki tana Tashi ta Shiga Jidda na ganinta tatashi ta Fada Jikinta ta saki kukanta Cikin Tashin Hankali Hajiya Lariya ta Riketa Tana Tambayanta lafiya..? Sai da suka zauna gefen gadonsu Ita Da mariya kana Cikin kuka Take labarta mata Abunda ke Faruwa Ido Hajiya lariya ta zaro Tana Fadin"Aure wani irin aure kuma..?
Jidda na Matsan Hawaye tace"Haka yace...Kuma wai ko zan yi kuka Jini Sai anyi..Ni fa bana Sonshi karatu nake so nayi Anty Lariya...."Kai Hajiya Lariya ta girgiza kafin tace"Ko ba karatu zaki yi ba wannan ai ba adalci bane Duka Duka nawa kike da za"a Hadaki da Wani Namiji namijin ma mai mata..? Yaushe zaki iya Zama da Kishiya kina yarinyarki Dake..?Toh ita karimar me tace..?
Jidda tace"Me kuwa..?Me Mama ta Isa tace in Ya Abdullahi ya yanke Hukunci ko Baba Wada Baya iya ketare mganarsa.."Mikewa Hajiya Lariya tayi Tana Fadin"Toh wlh bai isa ba wannan karon Mu zamu ketare..Wato Saboda Yaji Yaya tace zata karbeki ya Hana Shine ya Bullo da wannan mganar ko..?Wannan ai Rashin Adalci ne Taya zasu yanke wannan mganar mai muhimmanci batare da Tuntubar Ita yayan ba..? Gaskiya karima Ta bani mamaki.."
Da Sauri Jidda Ta mike Tana Fadin"A"a Anty bafa laifin Mama Bane..Yaya Abdullahi keda ikon Zartan da kowani Hukunci na Mama Bi ne kawai.."ko Sauraranta Hajiya Lariya batayi ba Ta Fice Daga Dakin Jidda Ta Rufa mata Baya Mama na Tsarkar Gida Taji Hajiya lariya a saman kanta Tana Fadin"Yanzu ke karima kinga Abunda kuka yanke yayi Daidai..?in ma Kuna Son ku nuna kunfimu iko da Jidda ne sai kuyi Adalci wajen Tuntubar ita mahaifiyar yarinyar ko bakomai Taci Darajan ta Tsugunna ta Haifeta...".
Mama Taji Hankalinta ya Tashi Daman Abunda Take Gudu kenan,Tasan karshenta ita za"a Dora ma Laifin komai Bataso Daga Bakin Jidda zasu Fara Jin mganar ba Taso ne Daga bakin Baba wada ko na Abdullahin Dama Tunda Taga zuwanta Tasan komai ya Lalace.
Cikin Sanyin Murya tace"Haba lariya taya zaki ce haka..? Kinga auran yazo ne ba"a gaya muku ba..? Dama ina da Niyyar kiran Ita Sa"an da kaina in gayamata komai sai gaki.."Wani Harara Hajiya Lariya ta mata kafin tace"Bawani Kina da Niyyar kiranta Haba karima in Jidda yarki ce zaki yarda Ya yanke mata wannan Hukuncin..? Wato Saboda ba yarki bace Shiysa baki da Tacewa ko..?
Idanuwan Mama suka kawo kwallah Cikin Rauni tace"Yanzu Lariya Dama kina Daukata a ba wacce ta Haifi Jidda ba..? Tafada kamar tayi Kuka Hajya Lariya Tataso mata Tana Fadin"Eh haka nace Domin na Tabbata in ke kika Haifi Jidda da Cikin ki Wlh bazaki yarda a batamata Rayuwa ba karamar yarinya da ita ku Rasa wanda zaku aura mata sai abokin yayanta kuma ma mai mata.."Ran Mama ya baci Kamar zatayi mgana sai ta Fasa Jidda Ranta bai mata Dadi ba ta kalli Mama kamar zatayi kuka Tana Fadin"Don Allah Mama kiyi Hakuri.."Ko kallonta Mama batayi ba Ta wuce Daki Tana Share kwallah.
Jidda Ta kalli Hajiya Lariya Tana Fadin"Haba Anty taya zaki ce ma Mama Haka..? Na taba Fadamuku Tun zama na da mama tataba nuna min wani Abun da zai saka naji ba ita ta Haifeni ba..? Wlh ya Abdullahi bani kadai ba,Dukkanmu yana nuna iko akanmu...hatta dasu Anty Zannira Dake gidajen Auransu.."Ko Sauraranta Hajiya Lariya batayi ba Ta Dauko Wayarta Dake Cikin Jaka tana Luluban layin Hajiya Sa"a Lokaci Daya Tana Fadin'"baki da wayau ne Jidda Shiyasa bazaki gane komai ba..Muda muka san zafinki Wlh bazamu bari hakan ta Faru ba Haka kurum a kashe miki Rayuwarki kina yarinyar ki Dake .."Ta Fada lokaci Daya tana Wucewa Fuu Cikin Fushi ta Fita ta bar Gidan Sai Duk Jidda bata ji Dadi ba Data koma Daki sai ta iske Mama na kuka Rumgumeta tayi Tana Fadin"Mama Don Allah ki Daina kuka..Har Abada kema kamar uwa kike gareni.."
Mama ta Share Hawayenta Tana kallon Jidda tace"Allah na gani..Tunda Mahaifinku ya karbo ku ya Damkamin ku Banta jin bani na Haifeku ba na Rike ku tsakani na ga Allah ina Jin kamar Dukkanku ni na Haifeku..ammh kalli Abunda Lariya tazo Tami...bakomai akwai Allah.."Ta Fada Tana kara goge kwallar Idanuwanta Itama Jidda sai kwallah da kuka Sai Mama ta Buge da Lallashinta Har sai da Taga ta saki Ranta kana.
Bangaran Hajiya lariya tana Fita ta Shiga Motarta ta bar anguwan Tun a Hanya tayi ta kiran Hajiya Sa"a bata samu ba sai da ta kai Gida kana ta sameta,Batayi kasa a gwiwa ba ta labarta mata Komai Hajiya Sa"a na Zaune ne sai Gata Tsaye Cikin wani yanayi Take Fadin'Lalle nema...Aikuwa wannan karon kowaye ya Tsaya mai karya yake ba wanda ya isa yayi ma y'ata aure yanzu Karatu zatayi.."
Hajiya Lariya ta karbe da cewa"Kema kya gani Yaya..Abunda yafi bani mamaki Karima ta kasa wani mgana sai cewa take ba Daga ita bane Laifin yayansu ne..'Hajiya Sa"a tace"Koma na waye su suka sani..Wannan karon ba wanda ya isa ya Hanani nuna ma Duniya Mahaifiyar jidda ce ni..Ina Tafe yau in nagama Abunda nake yi in kuma Ban gama ba sai Gobe...Zan zo ayi wacce za"ayi Lariya...Daga haka ta yanke Kiran Hajiya lariya na Fadin"Ina Bayanki Yaya.."
*****
Tsakanin Jidda da Mama ba wanda ya iya bada labarin zuwan Hajiya lariya da Abunda ya wa Kwana,Shuru sukayi da bakinsu,Ranar Bayan Abdullahi ya Taso Daga makaranta ya Shigo Gidan ammh bai Dade ba ya Fita Zuwa Wajen Baba wada suka Tattauna kan mganar Auran da Farko Abdullahi yace Sadakin Nazifi kadai yake Bukata Baba wada kuma yace Shine Waliyin Amarya Saboda haka Dole komai ma al"ada sai Nazifi ya Cikasa,da kansa ma ya Kirashi Sunyi mgana har ya Turo da kudin Goro da Dabino da Tabarma sauran kayan kuma Hade da Sadaki yace in zai Shigo Ranar lahadi in zai Shigo zai Zo Dashi Ba yadda Abdullahi ya iya Dole ya amince ammh yace ajirashi Zuwa gobe zai yi mgana da kannensa kuma yana so yaje Chan Danja ya sanar ma Goggo Habiba,saboda ko bakomai Kamar Uba take garesu Tunda ba wani wanda zasu nuna yau nasu na Bangaran Mahaifinsu Duk Allah ya karbi Rayuwankansu Ko Bata Shiga Cikin Sha"anin magabata ba Mijinta yana Shiga Tunda Shima kamar Uba suka Daukesa,Da haka suka Rabu da Baban Wada,kan sai Ranar lahadin in Nazifin yazo.
Washegari ta kama Asabar din Farkon mako Tun wajen Karfe 10am na Safe Mijin Zannira ya kawota Ita kadai yaran kuma chan ta barsu gidan iyayen mijin,Daga ita sai Maryam wacce suke Kira Ihsan,Har Ciki ya shigo ya gaida Mama kana ya wuce Samaru dama Daurin aure wani abokinsa akeyi Duk dashi ma yasa ya Dauko Zanniran suka Taho Tare,Da motar Haya zata Shiga,Tana zuwa ba Dadewa ta kira Subai tace mata gata ta kariso itama Bata Dauki Lokaci ba sai Gata,Mama Taji Dadi sai ina zata saka Dasu take,Gidan Daman babu Kowa sai Su Amira Suna makarantar Hadda Duk da bama Gidan suka kwana ba,sai dai Daga Haddar ne zasu Dawo ta Gidan Maman, Auwal ya Fita Shago Tun Safe Mariya kuma Tatafi Asibiti jidda ce kadai kuma Tun Safe tana kwance Bata Tashi ba.
Zannira ita ta kira Abdullahi tagayamai isowarsu yace su Jirashi Yana Cikin Makaranta Ammh yanzu in yagama Abunda zai yi zai kariso,Mama taso ta Fara kyankyasa musu Da suka Tambayi me ya Faru Jidda ke kwance Tataso kuma tana wani Tura baki,Sai mama tace Babu komai Bata jin Dadi ne Allah ya Sauwake kawai suka mata Suka Shiga Hiransu Cikin Hiran ne Ma Subai ke Fadin Daga gidan Mama Wajen Hafsah zata ta karisa wunin Ta Dubata Domin Jiya suna waya tace mata Bata Jin Dadi Jin Haka yasa Zanniran tace kafin Baban waled ya Dawo sai ta Bita Suje su Duba Hafsah din Har Mama tace bata sani ba Itama Jidda ke Fadamata Ammh Tace Da Sauki Abakin Abdullahi dai basu Ji ba.
Sai Wajen 12pm na Rana Abdullahi ya Shigo Gidan,Lokacin ma Sauri yake Zashi Danja Saboda haka Bayanin a gurguje yayi musu sai sukaji mganar kamar almara Subai Tayi murna Harda Rangada Guda,hararanta Abdullahi yayi yana Fadin"Ke miye haka..? Ke meyasa baki da Girma ne sai na Jikinki..??"Tana Dariya Tace"Murna Nake yaya..Abu namu mganin akwabemu Dama kwanaki Lokacin Haihuwar Anty Zannira da muka je gidan Wlh naji Ya bani Tsausayi har ina ce ma Hafsah da ina da yarinya Data isa Aure dana bashi Ashe Allah ya amsa Ban bashi yata ba zan Bashi kanwata kai Masha Allah Allah ya sanya alheri.."Gabadayansu suka amsa da Ameen Ameen Sauran Bayanan Mama yace Ta Fada musu,Shi zai wuce Danja Gidan Goggo Habiba Fatan Dawowa Lafiya sukayi mai ya Fito Tsakar Gidan nan Mama ke Tambayansa Ashe Hafsah bata ji Dadi ba ...?
Yana Duba agogon Fatan Dake Hannunsa yana Fadin"Eh Wlh Mama kinsan Halin Surukarki Sai a Hankali da Zazzabi take kwana Duk Dare da Zarar yammah tayi Shikenan in kuma gari ya waye sai Ki ganta kamar ba ita ba Kuma taki yarda muje asibiti sai dai ta Dinga Shan panadol."
Mama tace"Asha..Aikuwa gwara kuje asibiti adubata agani yafi ayi ta Shan mgani agida.."Yana Ficewa yake Fadin"Haka nake so ...Zuwa Ranar Monday kafin na Tafi aiki zan kaita mugani.."Fatan Allah ya sauwake Mama tayi Shi kuma ya amsa da Ameen ya Fice yana cema Mama sai ya Dawo tace adawo lafiya Su Zannira kuma na Ciki suna kara Tattaunawa Subai uwar Rawan Jiki,Kuwa harda Fadin anko kala Uku zasuyi kuma ya Abdullahi sai yayi Hakuri Domin zasu sha Bidi"a fa,Mama dai sai Dariya Take Jidda kuma na Jinsu taki mgana sai wani cin mgani Take Ganin Haka yasa Subai ta Fara Zolayanta da Amarya kawai sai ta saka musu kuka Cike da mamaki suke kallonta,tashi tayi ta Shige Cikin Dakinsu tana kuka Nan Mama ke Fada musu kukan Datake yi wai bataso ita karatu zatayi.
Subai ta saki wani wawan Tsaki Tana Fadin"Kar Allah yasa ta so mana Mama...Ke acikin abokan ya Abdullahi akwai wani Sa"anki ne..? Kindai ga Matarsa in auran kyau ne ko na ilimi bazaki Nuna mai ba gwara ma ki Saka Ranki Cikin salama mganar aure Babu Fashi Ehe.."Jin haka yasa Jidda ta kara Volume din kukanta Ita Abunda ke karamata Takaichi Shine Kowa ya tashi mgana sai yace wai Nazifi yafi karfinta toh Dama ita tace tana sone balle adameta da mgana,Ba wanda ya kara Bi ta kanta sukayi ta Hiransu Daga gani Abun yayi musu Dadi kwarai..
Wajen La"asar suka Tafi Gidan Hafsah suka isketa kwance ammh Dai taji Sauki Sun dan Juma suna ta Tattauna mganar Jidda sai da Mijin Zannira ya kira waya yace gashi gidan Mama kana suka Mata sallama suka Tafi,Daganan Subai bata koma Gidan Mama ba gida ta wuce Zannira ce ta Koma gidan Mama sukayi sallama Mama tace Su Shiga gidan Baba wada ta gaishesu Haka akayi ita da Mijinta suka Shiga Sun yi Sa'a Baba wadan na nan suka gaisheshi zannira ta Hada ta yi musu Allah Sanya alheri Bakin Inna Abu yaki Rufuwa 5k mijin Zannira ya bama Baba wada ya karba yana ta Godiya Gabda Mangariba suka Dauki Hanyar Kaduna,Mariya ana kiran Sallar mangariba ta Shigo Gidan Dayake Daga Asibitin bayan an tashi gidan wata kawarta ta wuce Sanin Halin Ya Abdullahi in ba da irin Haka ba Baka samun Zuwa ko"ina.
Tana Shigowa Mama tace yanzu Zannira suka Fita,Ta ciji yatsa Sosai Taso su Hadu,sai da sukayi Salla kana Mama ke Bata labarin Abunda ya Faru,Mariya tayi ta Ma Jidda Dariya afili ta Furtamata tana Tayata murnan Samun gwarzon miji irin Ya Nazifi Shi kuwa Auwal Daya Dawo Ana maida mgana ma Haushi Duk ya isheshi Ko mganar ma Bayaso yace a kyaleta mana ta kawo wanda yafi Ya Nazifin Tunda ita bata da Mutumci.
Bangaran Abdullahi kuwa ya isa Gidan Goggo Habiba ta Dinga ina Zata Sakashi Fura ta saka asiyomai ta Damamai,Da Zogala da kuli ta kwadantamai yaci yasha Furan ya Hada da kwadab zogalan ita ya Fara korama Bayanin Halin da ake Ciki Tayi Murna Sosai Domin Nazifi Mutum ne nagari,Tunda duk yawancin Zuwan Abdullahi Tare da Nazifin suke zuwa Gaskiya bashi da laifi,Goggo Habiba da kanta ta aika aka Kira megidan nata Alhaji mamuda,yazo sukayi mgana da Abdullahi Shima ya saka albarka yace Insha Allahu gobe zai zo ya samu Mallam wadan sai su Tattauna,Sai wajen karfe 5pm na yammah ya Baro Garin Saboda Bayaso yayi Dare Bisa Hanya gashi Saman Mashin ne.
****
*LAHADI..*
Lahadi karshen Sati kenan Abdullahi na kwance yana Barcin gajiya Misalin karfe 9am na Safe sai ga wayar Nazifi nan yake Gayamai Gashi Bisa Hanya zai Fara Zuwa Gida ne in sun gama Mgana dasu Baba zai karisa gidan Mama su gana da Jiddan.
Abdullahi yace"Ok..Mutumina sai ka iso Nima ina kwance ne ammh yanzu zan Tashi nayi wanka sai na Fito.."Daganan sukayi Sallama da sai sun Hadu.
Tashi yayi Ya Lalubo lambar Mama ya Kirata Bugu Daya ana Biyu ta Dauka suka gaisa Bayan ya Tambayeta ya Kiriniyar su Amira tace suna makaranta sai Itama ta Tambayeshi ya jikin Hafsah yace tana ma waje tana aiki Taji Sauki tace Allah kara lafiya ya gaisheta Daganan ya Ssnar da ita Zuwan Nazifi Saboda haka ta bama Jidda waya zai yi mgana da ita.
Ba Musu Mama ta Mikama Mariyar wayar tana Fadin"Mariya mikama Jidda waya Yayanku ne ke son zai yi mgana da ita.."Da Sauri Mariya Dake latsa wayarta ta ijiye Ta Karbi ta Mama ta Shiga Dakinsu Jidda na kwance kamar mai Barci nan kuwa ba Barci take ba,Mariya ta Daka mata Duka Tana Fadin"Sai ki tashi Ya Abdullahi zai yi mgana Dake ta waya.."
Dama Tana jinsu Tundaga Falo Cikin Tura baki ta mike tana Fadin"Shine kuma sai kin Dake ni..? Wayar mariya ta sakar mata kan Jikinta Tana Fadin"Bani Dukanki..? Kaji yar rainin Wayau..gashi dai yana dai jinki.."Daga haka ta Fice Daga Dakin ta barta Cikin Mutuwar Jiki ta Daga Wayar ta kara kunni Lokaci Daya tana Sallama,Ko Sallamarta bai amsa yace"Ke Jidda kina jina ko..?
Tace"Eh ina ji.."Cikin Kakkausan Murya yace"Ki Shirya yanzu Nazifi zai kariso...Ki gyara Dakin Auwal ki Saukeshi achan kinji ko..? Cikin Hadiye Miyau mai Zafi tace"Tom yaya.."Shuru tayi Shi kuma yace"Kun karbo Nama yau..? Tace bata sani ba Ajiyar zuciya yayi yana Fadin"Kaima Mama wayar na mata mgana .."Mikewa tayi Cikin Kasala ta Fita Zuwa Falo Mamar bata nan tana Tsakar Fita tayi ta mika mata Wayar tana Fadin"Gashi zai miki mgana.
"
Tana Bata wayar ta Juya ta koma Daki Mama ta kara akunni Tana Fadin"Abdullahi Mgana kake..? Da sauri yace"Eh Mama..ki saka Auwal ya karbo muku Nama mai Dan yawa ko mariya sai ta kama mata Tayi abinci haka,Duk da ba lalle bane yaci ammh akaron Farko dai ta karramashi,In da kudi a Hannunki ki Bata ta Siyo Ruwa da lemo in nazo sai na maida Miki Mama.."Kai Mama ta gyada Tana Fadin"Shikenan.."
Daga Haka suka yanke Kiran,Nan Mama ta Shiga Daki Tana gayama Mariya,Abunda Abdullahi yace Mariya ta kama Baki Tana Fadin"Au shine Dalilin Da naga Bakinta ya kusa kaiwa kofar Kibo .?Mama tace"Shine.."Tafada tana Dariya Suna Cikin haka sai ga Auwal ya Shigo Mama ta gayamai Sakon ya Abdullahi yace bari yayi wanka sai da yayi Wanka kana ya Fita Bayan ya karbi 1k hannun Mama ya Siyo Maltina guda Biyu sai Fanta Guda Daya da Ruwan gora sai Naman daya karbo Dayake suna da komai na kayan abinci yana Dawowa ya Fita Bayan ya barma Mariya makullin Dakinsa.
Mariya Bata bi ta kan Jidda ba Tatashi ta Fara gyara Dakin Auwal din ta Share Tsaf,tayi Mopping dinshi,Ta saka Turaran Wuta ta Rufo kana ta koma Barayin Girki,Jalop din Shinkafa ta Dora,Dama suna da Kabeji da Caras,sai Green Beans,Risho ta kunna