Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
Hudu yace itama ta Shiga ta Fita Uwar amarya sai Nuna Nazifin ake,ana ga ango chan Mutane natama Abdullahi Allah sanya alheri,basu wani jima ba Saboda mata Sunyi yawa Suka Fito Daga Gidan,Daga nan Kofar gidan Baba Wada suka koma Inda Daga gefe suka saka Babbar Tabarma suna Zaune Shida Mijin Goggo Habiba nan suka zauna suka kara gaggaisawa Shi kuma Nazifi sai ya zame Jikinsa dashi da wani abokinsa suka Tafi Gidan da Jidda ke Zama,Suna zuwa sai ga Auwal ya Shiga Har Ciki ya Fito da Jidda ga mai Hoto ya Shiga Daukansu Da su Mariya da Sauran kawayen Amarya,sai Gabda mangariba suka baro Wajen suna zuwa sukayi alwala Suka Shiga sallah bayan sun Fito ne Suka Fara kokarin Daukan Amarya Tunda Tawagar Hajiya Sa"a sun iso tundazu Gidan Mama.
Zannira ce ta Kira Wayar yaya Abdullahi ya Dauka sukayi mgana akan Abasu Mota zasu kai Jidda chan wajen Hajiya sa"a ta mata Nasiha suyi sallama Tunda su nan kowa yayi nashi,Harta shi Abdullahin yayi mata nashi Nasihan sai yace su Dakata Sauran abokansu na Anguwa su iso da Motocin su gama dai Kimtsa ta da komai da sunzo aka Fito da ita zasu kaita gidan Inna Abu Wajen Baba wada in yagama Mata Nasihan sai su wuce Dukkansu Chan Shika garin in sun Dawo Daganan sai Dakin Auranta basai sun Daawo ba,Da haka suka Kashe wayar,Bayan sungama Mgana ne ya ja Nazifi Gefe suka Tattauna yace hakan Daya Tsara yayi,yanzu Duka Motocin zasu iso.
Yana Kokarin Maida wayarsa aljihu ne yaga Alamar Sakon akan wayarsa sai ya Dakata ya Bude kamar yadda ya Zata ne Itace Domin Tun Ranar daya Rage mata Hanya koda yaushe sai Turomasa Sakon MorningMassges,da kuma na Good nite,sai na Jummat"mubarak kuma kowani Lokaci Zata saka Sunanta a kasa,Yana ta mamakin ina ta samu Lambarsa Lokacin kansa yayi Zafi da wannan Sha"anin Shiyasa bai Taba bin takai ba yana ganin Sakom nata bai Taba dai maida mata Reply ba,yau kamar kullum ga Abunda Ta Rubuto.
_I wish you a Hearty Congratulation on This occasion...may Ur Life always Shower you with such Happy and Succeessful Moment...Allah ya Sanya alheri...ya kuma Basu zaman lafiya Ameen....BARKAT SHEHU..._
Mirmishi yayi Yau dai na Farko ya Maida mata da Reply din Ameen Nagode Barkat.."Barkat bata Taba tsammanin Abdullahi zai maido mata amsa ba,sai kawai ta ga Sakonsa Tsalle ta Buga adaki Ta Fada kan Littafanta na makaranta Wanda ta Dauko Tana karatu Saboda sun Kusa Fara test ne a makaranta,Rungume wayarta tayi Tana jin wani Farinciki na Ratsata Bahiya ce ta Shigo Dakin Jiya Ta Dawo Weekend ganin Barkat Cikin wannan Halin yasa ta Rike baki Tana kallonta kafin tace"Anty Barkat lafiya kuwa..?Hajiya tace lafiyarki kike Ihu ke kadai..?
Sai Lokacin Ta Dawo Cikin Hayyacinta Ta Bude Lumsassun Idanuwanta akan Bahiya kafin ta yunkura Ta mike ko kallon Bahiya batayi ba ta Dauki Wayarta Ta Tura kofar Tailet ta Shiga ta Rufo Kofar Batare da tabama Bahiya amsa tambayanta ba ganin haka yasa ta Tabe baki ta Fice Sanin ko Zata Shekara Tsaye Barkat bazata bata amsan Tambayanta Datayi mata ba...Barkat kuwa Kofar Tailet ta Jingina Dashi Tana ta Murnanta Lokaci Daya tana Fadin"Alhamdulillah.."Dama Abakin Hajiya taji Zencen Auran kanwarsa Da Nazifin Lokacin da ya Salisu yazo da safe yana Fadamata Daurin Auran na 11 na safe ne,shiyasa ta Turamai sakon Allah sanya alheri.
Su Goggo Habiba da Umman Sadiq da Inna Talatu sai Ammi suka kai Jidda Nasiha wajen Baba wada,Yayi mata Nasiha Sosai Shida Mijin Goggo Habiba,Daganan gidan Mama suka maidata tayi mata Sallama suka Rumgume juna suna ta Kuka Dakyar aka Bambare Jidda tana kuka aka Fita da ita Lokacin Sauran abokan sun iso da Motocin,Abdullahi shi ya amshi key din Motar Nazifi yace zai Dauki Jidda da kansa ya kaita Dakin Auranta Saboda haka Motar aka Sakata Daga ita sai Ammi sai Umman Sadiq da Goggo Habiba Dangin Hajiya sa"a Dama da Motocinsu suka zo Sauran Motocin kuma Kawayen Amarya su Rumana su Mariya suka Shisshiga Subai"atu kuwa da Hafsah Motar wani Ishaq suka Shiga Dayake Duk yan anguwa ne Zannira kuma Wata mota ta samu ita Dasu Jamila,Motoci a kallah sun kai goma Dayake anyi Abun da Tsari ne,ba Tururuwa kowa ya samu Harda kannen Nazifi Sun samu Shiga.
Gidan Hajiya Sa"a suka Fara Zuwa Abdullahi kadai ya Shiga da Mota,sai Danginta da Shigo da Tasu,Ciki yau ne karo na Farko Daya Taba zuwa Gidan,yana Cikin mota yace Su Goggo Su Fita da ita Don Allah Minti goma su Fito Haka kuwa akayi Basu wani Jima ba yan Nasiha ne da Sallama Dama kuma ta mata,suka Fito da ita,Abdullahin ma Tana kiran Umman Sadiq ta waya yana cewa su Fito
Tafiya zuwa gidan Amarya Tawagar ta kara yawa Tunda Har dasu Lariya Suna Zuwa kofar gidan Jidda ana Kiran Sallar Isha"i,Abdullahi da kanshi ya Rike Hannun Jidda har kan gadon Auranta,ya zaunar da ita ya Dafa kanta yayi mata addu"an Zaman lafiya Daganan ya Fice Su Ammi kadai ya Jira su da ya Dauko ya maidasu da kanshi Chan yaga su Hafsah da Subai"atu sun Fito Daga Mota Abunda Ya bashi mamaki ganin Hafsah Da gyale Ransa ya Baci Kamar ya Fito ya mata mgana sai kuma ya faasa Domin Rabonsa da ganinta Tun Shekaranjiya Banda ta Rainasa ta san Bayason mayafi Shine ta saka ga Cikinta ya Fito,ko kafin ma ya Fito sun Shige Gidan kawai sai yayi kwafa yace Zasu gamu,Su Umman sadiq ganin Dakunan kawai sukayi suka saka albarka suka Fito Abdullahi ya maidasu Daganan Ammi ya Dauka ya maidata gida Anty Hadiza Tun dazu tatafi Saboda Su Abdulwaseen suna ta Rigima bai Shiga ba ya Juya Ammi nata mai godiya.
Yana komawa yaga gida wayam Ba wasu Mutane Duk an Tafi Gidan Amarya ya Shiga Cikin Gida yasa aka Kira masa Mama Yake Tambayanta Gidan Amarya wanchan Zugan zasu kwana..? Mama tace Eh aiko Abdullahi yace ba wacce zata kwana Wayar Zannira yakira yace su Tattaro kaf dinsu su Dawo gida in ba Haka ba Ransu ya baci Zannira ta Fara mgana kan kawayen Jidda zasu kwana yace ba wacce zata kwana Tunda ba Farillah bane Ango zai kwana Dakin Amarya Saboda Haka Wlh ko su Tarkato su Dawo ku kuma in yazo Dukkansu bazasu ji da Dadi ba,Mama dai batayimgana ba ganin Tunda yace ba wanda zai kwana da gaske yake sai Fada yake yana Kiran su zannira Manyan banza ko kunya Sunje Gidan kanwarsu zasu kwana,Zannira ta kara kiran Abdullahi tana Fadamai Duka Motoci Sun Tafi yace su Tako akafarsu Tsautsayin Dayaasa suka Shiga Ciki Suka zauna Har suka kai Dare ya Dawo Dasu.
Sanin Halinsa yasa Zannira na Fada kowa ya Fara Shiri Dama iyaye Tuni suka kama kansu suna ganin gida suka Shige Motoci aka koma Dasu Daganan ne ba Motar Data Dawo,Da Jidda taji labari sai kuma ta kama kuka, Subai"atu takalleta tana Fadin"Hakuri fa zakiyi...Laifin Yaya Abdullahi ne Shi a komai sai ya Nuna iko..Don ina laifi Don yabarmu mun kwana na yau kadai mun Rakashe kawai kawai yacewai kowa ya koma gida.."Ta fada irin Abun bai mata Dadi ba Mariya tace"Hmmmm...Aini Abun ya bani mamaki Wlh.."
Rumana tace"Gaskiya Yayan nan naku ya kwafsamana toh ke Qawata kin Shirya kwana da angon ne..?kawai sai Jidda ta saka Kuka Zannira tace"Kima yi Hakuri Da wannan kukan..Domin kinsan bamai Tsallake Umarnin yaya Abdullahi kinsan yazo gidan nan yaci mana ba karamin aikinsa bane.."Hafsah na gefe tana Dariya Subai kuma sai Tura baki Take Jidda dai taga da gaske suke Tafiyan zasu yi ta Kara Volume din kukanta Tana Rike Mariya,Mariya ta Fizge Hannunta itama kamar ta koka tana Fadin"Sakeni Jidda kinfi kowa sanin Halin Yaya Abdullahi Wlh nima ba Ragamin zai yi ba.."Dole Jidda Tana ji tana Dukkansu Harda kannen Nazifin Suna ta Dariya Kawayenta ma kaf Zannira ta Taro suka fito Suka bar Jidda na kuka Zannira tace tataso ta Rufe gida kafin ango Ya kariso Dakyar ta taso ta Rufe Gidan Tana kuka.
Sun Dade awaje Zuga Guda ba Abun Hawa Dole suka Fara Bin Hanya,ko Masu Napep babu ballatana wasu su Rage,Hafsah ga Ciki ga Tafiya Dukkansu Sun gaji Subai"atu tace Hafsah ta Kira Abdullahi yazo ya Taimakesu Tace bari ta gwada Data Kirashi sai da Tagama Bayaninta kana yayi Tsaki yace Waya kaisu..? Gidan Amarya ai na yara ne da suka je suna ganin waje sai su Fito a Dawo dasu ammh suka Share kafa,ai yanzu sai su Dandana Tafiyar kasa.." Daga haka ya kashe waryarsa,Dole Kowaace ta Wasa kafarta Sauran kawayen Jidda suka samu Mashin Sukayi Gida Rumana ne da Mariya da kanwar Mijin Subai Ke ta Shan Tafiya basu iso gida ba sai Goma Saura Suka iske Abdullahin da Nazifin a kofar gida,Saboda Haushi ba wacce ta kallesu kowa ta maida kanta gefe Hafsah kuwa Dakyar ta kawo Bayanta da kafarta sai Ciwo Suke Dariya ta kama Abdullahi Dayake akwai Wuta Haske ya Gauraye wajen Haka ya ga Fuskar ko wacce ba Fara"a Auwal ma na Zaune da Abokansa Sai da yayi Dariya afili ya Furta ya Abdullahi yayi Tsiya.
Suna Shigewa ya kalli Nazifi yana Fadin"Ango Sai ka Tafi gidanka Sai Allah ya kaimu gobe..Nima gida zan karisa nayi wanka na kwanta na gaji.."Hannu Nazifi ya bashi sukayi musabaha kafin Suyi Sallama bai Tafi da Motarsa ba Makullin Mashin din Abdullahi ya Karba wacce ke Hannun Auwal,ya Tafi da ita Motar kuma ya barma Abdullahi Shima bai Tafi da itaba Nan kofar Gidan Baba wada ya bar Motan ya Hau Mashin Din Haya zuwa Gida.
Shi kuma Nazifi kofar Doka ya Tafi ya Siya kayan Sanyi da kuma Kaji Guda Uku,Sai ya Dawo Gida ya Dauki karamar Jakar kayansa Dayazo Dashi Daga kaduna Sauran Sabbin Dinkinsa suna wajen Tela sai Gobe zai kamallah Misalin Karfe 11:pm da wani Abu na Dare ya Shiga Gidan Daman yana da Makullin gidan a Hannunsa Budewa kawai yayi ya Shiga da Mashin ya Faka kana yazo ya Rufe Gidan ya Taka ya Tura Kofar Falon ya Shiga da Sallama Jin Shuru yasa Direct yayi Cikin Bedroom din Jidda Dake a tsorace Manne Abayan Kofar Bedroom dinta Tajiyo Shigowarsa Lekowa tayi ganin Shine yasa yajita kawai ta Fadkmai Bisa Jikinsa Kadan ya Rage Dagashi har ledojin basu yi kasa ba ya Zame ledojin a kasa ya saka Duka Hannuwansa ya Riketa ajikinsa yana Fadin"Kinga..Bar wannan Tsoron am Here for u..kinji ko..!"
Yafada yana Shafa Bayanta Zuwa Kugunta alaman Lallashi.
*Domin Biyan Kudin Karatu akan Littafin Ra"ayi ne ko Buri..? Zaku iya Tura kudin karatunku ₦200 Kachal akan wannan asusun bankin 0552179550...JAMILA UMAR GTB,Sai a turo Shedar Biya ta wannan layin wayar 09069067488,In kuma Katin Waya ne zaku iya Turowa ta wannan Layin 09027767783 kai Tsaye Bayan Mutum ya Dauki Hoton katin...Ga masu Bukatar VIP zasu Biya ₦500 ne ta Lambar asusun Dana bada a sama....! Mutanenmu na Niger kuma Zaku iya Tuntumbar My Jika aglan Nissa ta wannan Layin +22794131747....Sai kunzo Masoyana*
*Shakira...*
4/9/21, 1:59 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*
*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!
*030*
"Shagwabe mai Tayi Tana Fadin"Ka Barni sai Tsoro nake ji Gashi ni kadai agida..."Tafada Cikin Tabara da sangarta Shiko Nazifi Tunda yajita acikin Jikinsa Komai nashi ya Chanza yanzu din ma Dakyar ya iya Lalubo amsa da zai bata da cewa"Am so Sorry My Jidda bada gangan bane...Kinji ko..?
Ya Fada Yana Shafa Bayanta Cikin Wani Salo Saurin Sakinsa Tayi jin yadda yake Shafata kallonsa Tayi Ido Cikin ido kafin Tace"Kai ne ka sa Ya Abdullahi ya Korarmu su Anty Mariya da kawayena ko..? Tana Fada sai ga Hawaye Tuni Nazifi ya Rude yaga Amarya na kuka ya Rikota Zuwa Jikinsa yana Fadin"A"a Wlh bani bane...Bansan ma sanda ya aikataba..."
Tana Tura baki tace"Toh meyasa da ka sani baka Hanashi ba....Kuma Bakace su Dawo ba..?"Mganar sai da ta kusa Sakashi Dariya sai ya kanne yana Fadin"Nayi iya yina yaki ya Fahimceni kinsan Halin yayan naku kaifi Daya ne...In ya karkace ko Hafsah bata iya maidashi Daidai Ballatana ni..."Yafada yana Dagota Lokaci Daya yana Share mata Hawaye.
Ganin yadda Tayi da Fuska yasa yaJata gefen gado yana Fadin"Meye na Fushin..? Keda zaki yima Farinciki gaki ga Angonki.."Wata Uwar Harara Ta makamai Data Sanyashi Dariyan Dole mikewa yayi ya Cire Babban Rigan jikinsa Saurin Kauda kai Tayi Tana Share kwallarta Rigar saman ya Cire ya Rage Dagashi sai Vest da Dogon Wando,Kallonta yayi yana so yayi Dariya sai ya Fasa Cikin alamun Lallashi yace mata"My Jidda tashi muje muyi wanka.."
Jin Haka tayi Saurin Haurawa Chan Tsakiyar Gadon Tana Fadin"Ni nayi wanka na..."ta Fada Tana Tura baki bai Damu ba ya Kada kai yana Fadin"Orly ni bari nayi.."Daga haka ya Shige Tailet bai wani Jima ba ya Fito Ruwa na Diga ajikinsa,ita kuwa Har ta Fara gyangadi Daga Zaune bai Tasheta ba sai da ya Sauya kaya Zuwa Jallabiya yaje Kitchen ya Dauko Filet da Kofuna yazo ya Saka musu kaza Guda Daya Kofunan kuma ya Zuba musu Madaran,kana ya Haura saman gadon yana Tashinta Dakyar ta iya Tashi Barci yaci Idonta Gajiyar Biki ne,Mayafinta ya Zare mata ya zaunar da ita kan Cinyarsa yayi Kokari Taci kazan Taki Ci Dakyar ta yarda taci kadan ya Bata Madaran tasha shima kadan Sai Lallabata yake ita kuma tana ta Shagwaba tana Tura baki bayan Sungama ta sake Komawa kan Gado ta kwanta Shima ya kwashe komai yamaida Kitchen.
Dakyar ya iya Lallabanta ya Rakata Bayi tayi Brush Ta Yi alwala Shima yayi suka Fito ya Shimfida musu sallah Jidda sai Cewa take tana jin Barci Shidai yana ta aukin Lallashinta,Harsuka Idar Da sallar yayi musu addu'o'i Duk da bai Tswaita ba,Suna Idarwa ta Haye gado kallonta kawai yayi Akwatin da"a kazo mata dashi ya Duba ya Dauko mata Rigar barci Shima an sha Daga kafin tatashi tasaka Shidai nashi lallashi ne da Ban baki Da farko yaso ya kyaleta ne ganin ta gaji ammh kuma sai yaji bazai iya ba Harta Fara Barci Tajishi kusa da ita TunJidda na Dauka Abun Sharan Fage ne haryazo ya Fara wuce Tunaninta Da Farko a irin Salon wasan daya Tafi da ita ta saki Jiki Tana Jin Dadi ammh kuma da Gangara tatafi sai ta Fara kuka tana Neman Taimako ammh ina Lokacin gogon naka bai ma Jinta yana Kokarin Shiga wata Duniya ta Dabam Duk da Yajita a matse ne tsam ammh bai iya Saurara mata ba Haka ya Dinga Tura kai Tun yana Waje waje har yazo ya Shige Ciki gabadaya ya Cigaba da aiki ba kama Hannun yaro.
Ba karamin Jarumtar Yarinyar yagani ba Sosai Duk da Tasha kuka da Koke koke Yaga Kokarinta kwarai Sai ya Tuna Lokacin Daran Farkonsu da Sakina Irin yadda ta Dinga kuka kamar wacce ya yanka tana mai Allah ya isa wai ya yagata Lokacin ma ai ita ba yarinya bace,Ammh kalli Jidda yarinyace karama ai ta iya Daurinyan Daukansa Duk da yana na Farko nan ko baisan karatunsu Subai bane da Hafsah na karta nuna gazawarta Ta nuna Jarumtarta Yana karama Mace a Daraja Sosai a idon mijinta.
Adaran ya Taimakamata Dama yaga Ruwan zafi a Flaks Dashi Yayi mata amfani Yadai Sha Shagwaba ne da Tura baki har ya Godema Allah Bayan ya gama gasata yayi mata wanka ya Nadota Cikin Towel ya kawota kam gado Shima ya koma ya Samu Tsarki ya Fito koda ya Fito Har ta koma Barci,shima Wandonsa Gajere ya Zura ya koma Kusa da ita ya kwanta yana Sauke Numfashi Lokaci Daya yana Jawota Jikinsa ita kuma sai ta kara lafewa Lumshe ido yayi kamar mai barci ya Tuna irin Kiran da Sakon Cin Mutumci da Zagin Da Sakina ta Dinga aiko mai Jiya Shiyasa ma ya kashe Duka wayoyinsa ya bama Banza ajiyarta Abunda kuma yake kara Bashi mamaki Dama wai yana daWani Daraja a idon Sakina ne..? Bai taba Tunanin don Yayi Aure zata iya Daga Hankalinta haka ba,Shi kuma yayi alkawarin Barinta Da aikinta ne ya Daina mata Korafi sai asamu zaman Lafiya.
Har Zuwa Washegari da Shagwaban Jidda tatashi Shidai Nazifi sai aikin Lallashi yake yana Saka mata albarka Tunda shi ya Kira Ruwan yana gidan bai iya Fita ba sai Bayan La"asar da su Zannira suka zo da su Hafsah kawo mata Sauran akwatunanta da wasu kayan sai kayan Su Cincin da Sauransu sai Lokacin ya samu Fita,Kowa yaga Jidda sai ya Fahimci dai Taji maza Domin abun ba Sauki Sai wani Sunne kai Take tana wani Sanyin jiki ba wanda ya Nuna mata wani abu sai dai sun kara bata Wasu Shawarwarin da zasu Taimaka mata Sosai kan zamanta kewarta.
Sai Dare suka bar gidan chan suka bar Mariya da Rumana su kuma da su Goggo Habiba zasu Tafi suka Bisu Subai"a tace kada a kuma irin na Jiya,suma su Mariya basu Dade ba suka Tafi Su Hajiya Lariya suka bi suka Rage musu Hanya sukabar Jidda ita kadai Tana yan kananan kuka Nazifi kuma Suna tare da Abdullahi Ana idar da Sallar mangriba suka Rabu Abdullahi ya Shiga Gidan Mama Shi kuma ya Wuce gidansa wajen yar Shagwabansa ai kuwa koda yaje ya sameta Tana ta kukan an barta ita kadai Sai da ya zauna yana ta aikin Lallashi yau dai Babu Abunda yayi mata Suna Jinya ne ammh ya Nannadeta Cikin Jikinsa Sunyi Barcinsu Cike da Soyayayyah da kauna.
Ranar Monday kuma yan biki duk sunWatse Domin Tun Safe Zannira ta koma Kaduna ita da yaranta Mijinta ya Turo Direba ya Dauketa Goggo Habiba ma Ta koma Dama ya"yanta Tun Jiya suka Tafi Jamila ce kadai ta Tsaya zasu koma Tare,Su Inna Talatu ma Duk sun koma Umman Sadiq ne kadai ta Tsaya sai Zuwa Laraba ammh Tuni abokiyar zamanta ta koma jiya ita da Zahra,Gidan ya Rage sai su Hausi da Subai"atu Sun Share kafa sun Zauna wai sai Gobe zasu koma Su suka Taya aka Gyara gidan aka Kankanta inda ya kamata Dayan Dakin Suka koma Suka Dasa Hira Suna Shewa Hafsah da Ciki Gaba Subai kuma Tana karkace sai Zuba Take Suna Dariya.
Abdullahi Shi Duk azatonsa Hafsah ta koma Gida Ranar yaje aiki,Daya Dawo ya Biyo ta gidan Mama da Su Amira da Su Muhsina ya Fara cin karo Daganan ya gane basu koma Gida ba mamaki ya kamashi yana Bayyana Rashin Hankalin Yaranan subai da hafsah bai Shiga gidan