Advertisements
Chapter 12 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   12 / 48

33K to 36K   out of 143.7K words

ya Barta zuwa suna Toh.."Subai tace"Yace in ta nemi izini ya yarje zata zo...In kuma ta karamai irin na wannan karon yama Rantse bazataje ba...."Mariya tace"Kuma ya gama mgana Wlh..Kaifi Daya nan ba"a sauyata.."

Zanniratu tace"Ni wlh na zata ya sauya..ashe Hali na nan..Don ma Hafsah mai hakuri ne da yanzu anji kansu.."Mariya tace"In batayi Hakuri ba ya zatayi Anty..? Ya Abdullahi ya wuce Duk Tunaninki kan Ra"ayinsa da Jin kansa da isarsa uwa uba kuma Masifarsa kowa neman Tsari yake da Ita Har ya Auwal kuwa.."

Zanniratu tace"Allah ya kyauta..ni Lokacina Abunsa bai kai Haka ba Ko domin ina kiyaye masa ne,Ammh nifa Lokacin kan Samari munsha Fama dashi Sosai Sai da nayi Aure kuma Komai ya kare.."Mariya tace"Yanzu ai Jidda ce ke shan Wahalarsa.."Nan ta Shiga Basu labarin Abunda ya Faru Ranar har Yaya Nazifi ya kwaceta.

Subai tace"Wai ni Nazifin ya suka kare da wannan yar Jinkan matar nashi..? Tanan tana aikin nata a Abujan kenan..? Mariya tace"Eh gaskiya tana Abujan..kwanaki naji inna Abu tazo suna mganar da Mama kan cewa Tana Abuja sai dai in Yaya Nazifin ya samu Lokaci yaje mata Weekend.."


Zanniratu tace"Tabdijam...wannan wani irin Aure ne anyi ba'ayi ba kenam.."Subai tace"Ke Duk Abunda ya Faru shi yajama kansa...Auran jari yayi sai kuma yaga karshensa.."Mariya tace"Haka ake ta Fadi ma a anguwa..mudai shuru muke aminin ya Abdullahi ne karka Tofa mgana takai mai Shima irin ya Abdullahi ne akwai son Girma.."Gabadayansu suka Sheke Da Dariyan Nishadi da ka gansu kaga yan"uwa Da suke tsananin Son Junansu Jaririyar na Hannun Subai Shi kuma Saleem na Hannun Mariya sun kule Cikin Bedroom Falo kuma Kanwar mijinta ne sai wata yar Dattijuwa da uwar mijinta ta Turo mata ta zauna mata na sati Tunda aiki aka mata.

Bangaren Hafsah kuwa Har Abdullahi ya Dawo ya Isketa batayi Girki ba kuma ko wanka bata sake ba Tun kayan Shirin Zuwa kaduna barka ne ajikinta.

Bayan Sallar Isha"i ya Dawo koda ya Shigo Amir yayi barci sai Amira ta Rugo tana mai oyoyo ya Tarbeta ya Dauketa yana Tambayanta Amir tace yayi barci Sun kariso Tsakiyar Falon inda Hafsah ke zaune tana latsa wayarta Amira tace"Abba ina jin yunwa..".

Kai Tsaye Abdullahi ya kalli Hafsah Cikin mamaki yana Fadin"Baki yi girki bane..? Amira ke kukan yunwa fa kina jinta ."Batare da ta Dago ba tace"Ban girka ba.."Galala yayi yana kallonta kafin yace"Saboda mene..?kai Tsaye Hafsah tace"Bakomai kawai Ra"ayi.."Shi yama manta Abunda ya Faru da safe Cikin kulawa yace"Baki lafiya ne..?

Kai ta girgizamai kafin tace"lafiyata kalau..."Jin haka yasa ya gane Rainin Wayau ne kawai, kawai sai ya kada kai ya Sauke Amira yana Fadin"Kinga Mamata bari na fita na siyo miki abinci ban Riko muku komai ba na manta.."Sauketa yayi Lokaci Daya yana Barin Falon tana jinsa yakara Fita Da mashin din nasa batare daya ma kara kallon Barayin Datake ba.










*Shakira...*
4/9/21, 1:54 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Janafty*❤️

*Dedicated To:My Habibaty💞Aisha Idris Abdullahi..*!

*Godiya Tare da Jinjina mai Hade da Fatan alheri zuwa gareku Dimbim Masoyana na Nesa Dana kusa,Hakika naga Salon Soyayyarku ga wannan D'an karamin Labarin nawa mai Taken MASIFAFFAN MIJIN HAFSATU...❤️,Ina godiya Sosai ga Sharhinku da kuma Kayattacen Sakonninku Na Soyayyah da kauna zuwa gareni Nagode Sosai Allah ya saka da alheri Godiya Gareku Masoyana na Wattpad da kuma WhatsApp,Allahu ya bar Zumunci Janaftyshakira nayi musu Son Kauna Mara iyaka...*

*012*

 
"Tana nan Zaune har ya Dawo Dauke da Ledoji Guda Biyu,Koda ya Dawo Amira tayi barci Tashinta yayi ya bata Ledan mai Dauke da gasshiyar kaza,sai Take away din Jalop din Shinfaka sai Fura.

Sai da yaba Amira taci ta Koshi kana yaci Sauran ya Tada ita yakaita Tailet tayi Fitsari ta wanke Hannunta da Bakinta Da kanshi yakaita Dakinsu ita da Amir Daya Rigata yin Barci Hafsah na Zaune yazo ya wuceta ko kallo Bata ishesa ba itama Haka Bata kara Bi ta kansa ba sai ma ta Kishingide kamar mai Barci Saboda Bacin Ran Abunda ya mata Haka kurum Taji bazata iya Controling Din Fushinta akan karfin Ikon da Abdullahi ke nuna mata Lokaci Bayan Lokaci ba.

Sai wajen 12am na Dare kana ta mike ta Tattara Lodojin da suka barsu nan Tsakar Dakin ko Kazar basu Cinye ba da Shinkafar,Ta kwashe komai ta Kai Kicthen ta saka Cikin Fridge din Kana Ta Rufe Kitchen ta Dawo Daki ta kashe Wutar waje ta kashe na Falon Lokaci Daya ta Kulle kofar Falon Dakinsu Amira ta Shiga ta gyaramusu kwanciya Hade da yi musu addu"a,kana ta Fito ta Shiga Bedroom dinsu ta iske Tuni Abdullahi ya Dade da yin Barcinsa mamaki ya kamata wato Ita ke kidanta Tana Rawanta bai ma Damu ba kyafci tayi ta Shiga Taiolet Tayi wanka Lokaci Daya ta Dauro alwala tazo Tayi Shafa"i da wuturi Ta Dauki Filo ta Jefa kasa ta kwanta Bayan Ta Dauki Blanket ta Rufu Dashi.

Da asuba da Abdullahi ya tashi yaga Hafsah a kasan Cafet Tana Barci Mirmishin Takaichi yayi acikin Ransa kuma yana Fadin zan koya miki Hankali Hafsah ko Kallonta baiyi ba ya Shiga Toilet yayi wanka Tare da Dauro alwala yazo ya saka Jallabiya ya tsallake Hafsah zuwa masallaci sai bayan ya Fita ne Hafsah tatashi itama ta Shiga tayi wanka tazo ta Tada salla,Ganin har wasu masallatan sun Tada sallah.

Bai Dawo masallaci da wuri ba Sai da Haske ya bayyana koda ya Dawo Tagama komai hatta su Amira sun Shirya Jiransa kadai suke shima Sama sama ya Shirya ya kwashesu zuwa makaranta Dagachan ya wuce wajen aiki,Haka Zamansu ya kasance Hafsah ita ta Dauko Tsiyan sai Abdullahi ya nuna mata yafi ta sanin kan Tsiya Shima kawai ya Fita Batunta yayi Banza da ita bai ma Nuna yasan me take ma Fushi ba.

Dole kanwar naki Hafsah ta watsar da Tsiyan nata ganin Uban gayyar dai bazai Kalleta ba Ballatama ya bata Hakuri Ranar data Fara gaisheshi da safe kafin ya amsa sai da ya murmusa Lokaci Daya yana Fadin"Lafiya lau Hausi...Kin gama Gaban dani..? Shagwabe mai kawai tayi Lokaci Daya da Hararansa Batace komai ba Shima kawai sai ya Biyemata Kamar Babu Abunda ya Faru,Ganin yasa Hafsah ta Sakankace cewa Abdullahi zai barta Zuwa Suna.

Ana Gobe Suna Subai"a ta Kirata awaya Tana gayama ta Gobe ne zasu Tafi sunan Saboda Mama tace su Tsaya su Tafinma da Anty Zanniratun Sako Zuwa Gobe,Tace mata Su Hadu gidan mama Gobe da Misalin karfe 8am na safe Nan Sukayi sallama,nan take Hafsah ta Kira Ammi tana Fadamata itama kuma Tace zata Turo Direba da sako ya kawomata ta kaima Zanniratun In ta samu Lokaci ko Bayan suna Hafsah zata Rakata Taje ta mata barka.

Zuwa Yammah Ammi ta aiko Da sakon Atamfofi Guda Biyu masu kyau da Tsada sai Babban pampers mai Guda 50,Da Rigan yarinya mai kyau itama Hafsah tayi ta Jin Dadi,tace ta Huta Siyan wani abu sai tace ita Da Ammi kuma Daman ta sani Harda natan Ammi ta Hado sanin ba wata sana"a takeyi ba Duk da Babu Abunda ta nema ta rasa Abdullahi ya Tare mata gaba da baya Sai dai Abunda Ba"a Rasa ba.

Abdullahi na Dawowa ta kwaso kayan Tana nunamai Ya amsa ya gani yayi Godiya nan yake gayamata ya bama Mama 15k ta hada ta siyan ma Zanniran wani Abu sai a aikamata Dashi,Danashi dana Hafsah nan tayimai Godiya Bata gayamai Zuwa Zencen Sunan gobe ba sai da zasu kwanta kana ta gayamai bai ce mata komai ba yace Allah ya kaimu Sai da safe Bayan ta gama Shiryawa Ranar ma bashi ya Kai su Amira makaranta ba Mai mashin dinsu ya kaisu Yana kallon Hafsah tana ta Shiryawa sai da Tagama Shirya kayanta Cikin Karamin akwatinta na Kayanta kala Daya da Hijabi wanda zata Sauya na gobe sai sakon Ammi.

Abdullahi ma Shirin Fitan yake Domin ya gayamata Za"a Fara Ginin Gidanshi na Gra,Domin har an kawo Siminti da Bulo,da kasa Tun Shekaran jiya zai Fara Biyawa Yayi mgana da ma"aikatan kafin ya wuce wajen aiki,Subai"atu sai kira take tana Fadin Hafsah tayi Sauri Gata Gidan Mama.

Sai da ya Bari ta saka Hijabi kana ya kalleta yana Fadin"Wai ina zaki ne naga kina saka Hijabi..?Cikin Dariya Hafsah tace"Kaima da wata mgana..Yau ne fa Sunan Zannira baka ga Subai ma Sai Kirana take ba Suna Gidan Mama suna Jirana."Kai Tsaye yace mata"Au kin gama Fushin Dani ne..? Yafada yana kallonta kai Tsaye jin haka yasa Jikinta yayi sanyi tayi galala tana kallonsa yana Saka Takalminsa Sawu Ciki yake Fadin"Babu inda zaki...Tunda har ni nan zan Hanaki Abunda iko na ne ammh ki Nuna min ban yi Daidai ba ki Dauki gabadani na kwanaki Kidaina Dafa abinci kina ma ya"yanmu Horo da yunwa Saboda Ni na Haifesu ko..?

Yafada Lokaci Daya yana mikewa Ido ya sakarmata ganin Har Hawayen Idanuwanta sun Fara Zubowa Cikin Bacin Rai ya Cigaba da Fadin"Kyaleki nayi naga iya Gudun Ruwanki...naga inda karshen Tsiyanki zai kai ashe Babu inda zai kai...Na bari ne dama sai kin gama naki ni kuma na Fara nawa..Suna ne Bazaki ba..Sai na gani Tsakanin Hafsah da Abdullahi wanene ke Auran wani.."Yana gama Fadin Haka ya kwashi Jakarsa da Key din Mashin sa ya Fice yana Fadin"Yau ma ki Dauki Gaban dani..Karki Dafa komai ki bar yaran da yunwa kinji ko.."

Daga haka ya fice ya barta nan Taaye tana Tsiyayan Hawaye,Tana Jinsa ya Fito da mashinsa ya Fice Bata san sadda wani kukan bakinciki ya Turniketa ba,Ta Fada kan gado kawai ta sakeshi wiwi kamar karamar yarinya wani Bakinciki da Takaichi na cin Ranta da Zuciyarta Tana Cikin kukan ne Taji karar wayarta Ta Dago kanta Shabe Shabe da Hawaye ta Jawo Jakarta Inda tasaka Wayarta ta Bude ta Dauko sai taga Ammi ne ke Kiranta da Sauri Ta Daga Kiran Lokaci Daya Ammi na Fadin"Hafsah kun tafi ne..?

Jin Haka yasa wani kukan ya kara Zuwarma Hafsah kawai sai ta sakarma Ammi kuka Cikin Firgici da tashin Hankali Ammi ke Fadin"Innalillahi...Hafsah meya faru..? Ina Abdullahin..?ko wani Abu ne ya Faru daku..?

Duk atare Ammi ta Jero mata wadanan Tambayoyi,Ammh Hafsah ta kasa mgana Saboda kuka Cikin Tsawa Ammi tace"Dallah kiyi mgana lafiya kike ma mutane kuka..?
Jin haka yasa Hafsah tace"Ammi..Ya hanani zuwa Sunan ne..."Tafada Cikin Shesshekan kuka Wani Karamin Tsaki Ammi Taja Lokaci Daya tana Fadin"To Shine kuma Abun kuka..? Nifa har kin saka gabana ya Fadi Allah yasa Daddynku yana Barci kila da kin saka Jininsa ya Hau in yaji wannan Shirmen naki.."Cikin kuka Hafsah ta kara Fadin"Ammi Ranar fa Haka ya hanani zuwa barka yauma har na Shirya yace bazani ba.."Ammi tace"Sai me.
? Sai me in ya Hanaki..? Inace ba kanwarsa bace da suke Uba Daya..? Yafi ki son kije wajen yar"uwansa kuma yahanaki sai kiyi Hakuri ki zauna Ranar daya Lamunce miki sai KiTafi Hafsah.."Cikin Takaichi Hafsah tace"Ammi Su Subai na chan gidan Mama suna Jirana kuma kowa zai je Ammi sai ni kadai sai ya Hanani.."

Ammi tace"Tsiyana Dake sakarci Maman Hamzana,Suna yafi Mijinki ne..? Kuma na Tabbata wani Laifin kikemai Shiyasa ya Hanaki Zuwa Sunar ko...?

Shuru Hafsah tayi taki mgana Jin Haka yasa Ammi tace"Hmm ni na sani..Meyasa Hafsah wani Lokacin kin cika Wauta ne..! Karfa ki manta ke matar aure ce wacce ke karkashin mijinta akullum ina gaya miki Aljannarki Tana karkashin Kafar mijinki ne,sai ya Daga Zaki Shiga,kuma Aure Bautar Allah ne,Kuma Shi Aure dan Hakuri ne kinga in kikace bazaki yi Hakuri ba Wlh zaki Sha Wahala ne kawai Hafsah.."

Tura baki Hafsah tayi kafin tace"Toh ni Ammi me nake mai..Iya Biyayyah Wlh ina yi da Hakurin da kikace.."Ammi tace"Toh in kinayi me ye na kuka Saboda yace bazaki suna ba..? In kina yi sai kiyi Hakuri  ki Share Hawaye dama ai Aure ya gaji Haka.."Cikin Marairaicewa Hafsah tace"To Don Allah Ammi ki Kirashi ki Rokeshi Da Allah da Annabi ya barni naje.."Ammi ta Rike Baki Tana Fadin"Ni Jikar Hadiza..? Rufamin asiri Abdullahi na ganina da kima Ina Ruwana da Shiga Hurumin da ba nawa ba..? Yanzu bamu da iko akanki Hausi Kin bar karkashin ikonmu Tun Ranar da igiya uku ta Hau kanki kikabar Karkashinmu Zuwa karkashin Mijinki,Saboda haka yafimu iko Dake.."Bakin Hafsah kamar ya Fado Tace,"Kai Ammi yanzu dai baki Kiransa ko..?

Ammi tace"A"a wlh karya da Ciwo..Na kirasa nace mai me..? Haka kurum Jama kai Raini da lalacewa sai na Kirashi nayi mai mgana kan Abunda yake da iko akansa..?ko Babanki yaji labari sai ya batamin rai bakisan kwanciyar Hankalinsa da nawa Ba Yana da Nasaba da Kowaccenku tana zaune lafiya Gidan Mijinta ba  kuma Dukkanku kun yi sa"an Mazaje na gari ya"yan albarka Da Dangin Mijin na gari nan Shekaran jiya Abdullahi yazo yana gayama Babanki Ya siya Fili a Gra har zai Fara Gini Dukkanmu muka sakamai albarka kinsan anyi..?

Ta karishe Fada da Sigan Tambaya Hafsah tace"Bansani ba Ammi..'Ammi tace"Toh Ina laifinsa...kiyi maza ki Share hawayenki ki kirasu kice su tafi Baxaki samu zuwa ba In Ya dawo kin Lallabasa in ya barki bayan suna sai Ki rakani muje mu mata wuni mu Dawo.."Hafsah tace"Shikenan Ammi nagode..Ki gaida Daddy in ya tashi..Anty Hadiza Shuru bata Haihu ba..?

Ammi na Dariya tace"Sai ki kirata kice mata taki Haihuwa..inaga Cikinta da Sauransa bai wuce wata Takwas bafa Girman ciki ne da ita irin na Walid ne..'"Hafsah tace"Na kosa ta Haihu naje Kano na Rabu da Zuwa Kano Ammi Tun sanda Anty Hadiza ta Dawo Daga Saudiya.."Ammi tace"Toh shine me..? baku na waya da juna ba..?

Hafsah tace"Eh Ammi.."Ammi tace"Toh banga Abun Damuwa ba..Kowa ya zauna agidan Auransa yaci gaba da Bautar Aure.."Baki kawai Hafsah ta Tura Ammi Kuma ta Fara Fadin"Umm.Auta..Autan Zinariya Autan Hamza kuma Maman Hamza..Kuma kanwar Hadiza Ko Hausi.."Jin Kirarin Ammi yasa Hafsah ta manta bacin Ranta ta Shiga Dariya Ammi bata kashe wayarta ba sai da ta tabbatar da Hafsah ta saki Ranta.

Suna gama Waya da Ammi Hafsah taci karo da Kiran Subai"atu wajen Guda Biyar Lokacin tana waya,Da sauri ta Kirata Tana Daga Kiran Subai tace"Wai Gimbiya matar Ya Abdullahi ko kin Fasa zuwa ne..? Kefa muke ta Jira Har yanzu baki kariso ba..?
Cikin sanyin Murya Hafsah tace"Ku tafi kawai Subai...Bazan samu zuwa ba..'Cikin mamaki Subai tace"Bangane mu tafi ba kawai..? Ko Ya Abdullahin ya hanaki ne..?

Hafsah tace"Eh yace bazani ba..Ku tafi kawai in kunje ku gaisheta,Kuyi Hakuri da bata muku Lokacin danayi Kuma Don Allah in zaku iya ku Biyo ku karbi sakon Ammi ku kaima Zanniran.."Subai tayi karamin Tsaki kafin tace"Bansan Meyasa Ya Abdullahi ke haka ba sam..."Hafsah dai Shuru tayi batayi mgana ba Subai tace"Shikenan in da yuyuwa zamu Biyo..Baya dai kyautawa.."Tana jin Mama na Tambayan me yafaru Subai na Fadamata yadda Hafsah ta Fadamata bata tsaya Jin me Mama ke Cewa ba ta kashe wayarta kawai.

Tana nan Zaune Har su Subai"a suka kariso basu wani Tsaya ba Ta basu sakon Ammi da 3k cikin kudinta Data ke dashi tace su kaima Zanniran,Har waje ta karasu Ita da Direban Mahmud ne,sai Jidda,Da inna Abu sai Inna Talatu wata kanwar Mama ce,Tana Daga musu Hannu suka kule ma ganinta kana ta koma Cikin Gida ta Shiga Falonta kenan Wayarta ta sake neman agaji,Tana Dubawa taga Umman Sadiq ce ta Daga suka gaisa Kana Umman Sadiq ke Tambayan Hafsah ya Suna..?

Hafsah tace"Bata je ba tana gida..? Cikin mamaki Umman Sadiq ke fadin"Kina gida?toh saboda mene baki je sunan ba..? Ko ba yau bane Sunan Zanniratun..?

Hafsah tace"Yau ne Umman..Har na Shirya sai yace bai yarda naje ba..Su Subai"atun ma sun wuce yanzu.."Umman Sadiq bata Jira cewar Hafsah ba kawai ta yanke Kiran ta Kira Abdullahi Lokacin yana Office yana Tsaka da aiki yaga Kiran Umman Sadiq bayan ya Daga sun gaisa kai Tsaye tace'"Meyasa kake Tauye Yarinyarnan ne Abdullahi..?

Jin Tambayar nata yayi ta mishi bambarakwai cikin mamaki yace"Wata yarinya kuma Umma..? Cikin Takaichi tace"Kaniyarka nace..Kaji ko..? Nace kaci Gidanku Abdullahi.."Jin Haka yasa ya natsu yana Sosa kansa Cikin Lallashi yace"Umma kiyi Hakuri Don Allah bangane inda mganarki ta Dosa bane.."Umman Sadiq tace"Miye Dalilinka na Hana Hafsah zuwa Wajen sunan Zannira Kowa ya tafi sai ita kadai..?

Jin haka yasa ya gane bakin Zarensa Ransa ya baci wato Kararsa Hafsah takai kenan lalle Cikin Saukar da kai yace"Umma ki kyaleta Hafsah ta Fara Rainani ne.."Umman Sadiq tace"Toh kai waye da baza"a Raina ka ba..! ? Ka Fita daga idona na Rufe Abdullahi banda mugunta ka Hanata zuwa suna sunan ma na yar"uwanka kowa ya tafi sai ita kadai.."Kansa na kasa yace"kiyi Hakuri Umma.."Bata Damu ba tace"Bawai mganar Hakuri bane kayi maza ka Kirata awaya ka bata Izinin tafiya yanzu kafin yan Tafiyan su mata Nisa kaji ma na gayamaka..'Ransa amatukar bace yace"Naji Umma Shikenan zan yi yadda kikace.."kyafci tayi Lokaci Daya tana yanke Kiran wayar yabi da kallo yana Sauke Numfashi acikin Ransa kuma ayyana Yadda Hafsah ta fara ganin gadon barcin harda zai Hanata zuwa waje ta Kira Umma takai kararsa

Ita kuwa Hafsah batasan aikin da Umman Sadiq tayi ba Tana Zaune tana latse latsen wayarta Sai ga Kiran Abdullahi sai da gabanta ya Fadi da sauri ta Daga ko Sallamanta bai amasa mata ba, yace mata"Kin kyauta Tunda bakin ki ya iya kai karana..Sai ki Shirya ki tafi Allah ya Kiyaye Hanya Hafsahtu.."Jin haka yasa tayi kalan Tsausayi kafin tace"Wh Allah ban kai karanka wajen kowa ba..Umma ce.."Wannan damuwarki ce ban ce kimin wani Dadin baki ba ki Shirya ki Tafi kawai Malama.."

Yafada yana Shirin yanke Kiransa da Sauri tace"Toh don Allah na kwana sai gobe na Biyosu mu dawo.."cikin kulufuwa yace"Bama kwana Daya ba in zaki iya bari ma sai ta yaye Yarinyar Duk Dayane awajen Abdullahi..Tunda kin nuna ni ban isa dake ba Hafsah ai babu kuma Abunda zan kara cewa Duk Abunda kika yanke Daidai ne.."Shuru tayi batare Datayi mgana ba Shima bai Jira cewarta ya Datse kiran Tsalle ta Buga Tana Murna nan da nan ta Kira Subai tace Suna ina ne..? Tace yanzu suka wuce Danmagaji, Nan Hafsah tace su Jirata gatanan zuwa Cikin mamaki Subai tace"Ya barki ne..? Hafsah tace"Eh Umma ta kirasa ku jirani yanzu zan hau adaidai nazo na sameku.."Cikin Jin Dadi Subai tace"Yauwa har naji Dadi sai kinzo...Direba Don Allah samu waje ka faka.."

Dama kayanta na Shirye Hijabi Kadai ta Zura ta Dauki Jakarta da key din Gidan sai karamar Jakarta na Tafiya ta Rurrufe ko"ina Tana Kulle gidan ne sai ga Almajirinta yunusa Kudi ta bashi tace bata nan sai gobe zata Dawo,Tana Fitowa ta samu

12 / 48