Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
ina da Ra"ayi..Insha Allahu sai na kara Aure wannan karon Tsakani ga Allah zan nemi aure na bazan yi irin na Farkon wajen neman Cikar Burina da Auran jari ba."
Abdullahi yace"Yo daman ai Duk wanda ya Hau motar kwadayi...! Nazifi na Dariya ya karisa mai da Fadin"Karshensa Tashar Wulakanci..Kuma nagani Domin Ta kaini ni harda Tashar ma Nadama da Danasani..'Dariya ta kama Abdullahi sai Da ya Duke,Nazifin na Tayashi Cikin Nishadi,Sun Dade awajen kafin su baro wajen Suna Hanyar Zuwa Cikin gari sai ga Kiran Mama Lokacin misalin Daya Saura ne na Rana yana Daga kiran Bayan sun Gaisa tace mai ga Hajiya Sa"a ta iso Tana son ganinshi Yace gashi nan zuwa
Bayan sun gama Wayar Abdullahi ya saki Numfashi yana Shafa Kanshi Nazifi na Driving ya Dago yana kallonsa Cikin Kulawa yace"Lafiya kuwa Mutumina..? Abdullahi ya yamutsa Fuska yana Fadin"Ina fa Lafiya..! Mahaifiyar Jidda ce ta ke son wai na bata Jidda ta koma Wajenta da zama Tunda ni ko Mama mun gaza.."Cikin Mamaki Nazifi yace'Mahaifiyarta wacce ta Haifeta..?
Abdullahi yace"Eh mana..."Nazifi yace"Toh ba kwanaki mun Taba mgana dakai kace min ita da Mahaifiyar Auwal Tun Tuni basa garin ba,sai naji kamar kace min Tana Saudiya Tun Bayan da aka anso Jidda ko..?" Kai Abdullahi ya gyada yana Fadin"Eh Mun taba mganar dakai..Wai ta Dawo ne Shine take son karban yarta ta koma Hannunta.."Nazifi yace"Ji wata mganar Banza..wannan ma ai Rainin Wayau ne.."
Abdullahi yace"Kaima ka gani..Kwanaki tazo ta Dauketa taje wajenta ta mata kwanaki Shine yanzu take son Daukanta gabadaya alhalin ba gidansu take zaune ba Gida ta gina Tana zaman kanta.."Nazifi yace"Koda ma Tana gidansu ne Cikar kamalar Yarinya ai gidan Ubanta ne, ga Mama araye kaga Har sai Ta Dauki Jidda ta koma Hannunta..? Haba wannan ai bai kamata ba sam.."
Abdullahi yace"Hmm barni da Ita zan mata Bayanin da su Baba suka kasa mata.."Nan ya koramai Bayanin Abunda ya Faru Ranar da tazo Tafiya da jidda kai Nazifi ya kada kafin yace"Na yarda wani Lokacin Mata Tunaninsu kalilan ne wlh.."Abdullahi yace"Ah sosai ma kai sai yau ka sani.."Daidai Lokacin da suka kawo kofar gidansu Abdullahi gaban Jeep din Motar Hajiya Sa"a suka Faka tasu sai da suka Firfito kana Abdullahi ya kalli Motar yana Fadin"Ina jin ma wannan Motarta ce.."
Da kallo Nazifi yabi Motar kafin yace"Ah Lalle,Da gaske kam Tatara Abun Duniya.."Abdullahi yace"Na banza ne ni awurina..kai mutumina mu karisa masallaci muyi sallah gashi chan ana kira.."Da haka suka wuce masallaci Suna Hira alwala suka Dora suka Shiga masallacin sukayi Salla kana suka Fito anan suka Hadu da Baba wada Abdullahi ya gayamai Zuwan Hajiya Sa'a Baba Wada yace Mama ta aika gida an gayamai Dukkansu Daga masallacin suka Dunguma zuwa Cikin Gidan Mama
Da sallamarsu da Jidda suka Fara Cin karo a tsakar gida Ita da Mariya Suna zaune kan Tabarma Suna ta Faman Latsa wayar Jiddan,Dukkansu suna Sanye ne da Dogayen Riguna Dinkin Rariya iri Daya wanda Subai ta taba Dinka musu ne,Suna jin sallamansu Sukayi Saurin Boye wayar kansu na kasa suna gaishesu,Ko kallonsu Abdullahi bai yi ba ya Dauke kai Nazifi ma kallo Daya yayi ma Jidda yaji gabansa ya Fadi Wani Lokacin Abun na bashi mamaki yadda indai yaga Jidda sai Zuciyarsa ta amsa Baba wada ne ya tsaya suka gaisa yana ta Zolayansu.
Dakin Mama Abdullahi yayi Sallama Inda yaga Takalma yana Tunanin Hajiya Sa'ar tana Ciki Daga Ciki Mama ta amsa ya Tura kai ya Shiga Nazifi ya Biyo Bayanshi Da Baba wada,Kusa da Mama Abdullahi ya Zauna Nazifi kuma ya samu Chan gefe Ya zauna kan Kujera mai zaman mutum Biyu,Mama kuma ta mike ta Bama Baba wada wajen da tatashi ta mishi sannu da Zuwa ya amsa yana Tambayanta ya yara.
Hajiya Sa"a Ta Fara gaida Baba wada Lokaci Daya Tana kallon Abdullahi,wanda ya Dauke kanshi sama yana wani Daukan Kai Kawai Ranta ya bata Shine Abdullahi Domin Tabbas kwarjinsa ya Daketa ashe ma yaro ne karami ba wani Babba ba yarda Take Tunani Mama ce ta Kalli Hajiya Sa"a da Lariya tana Fadin"Ga su sun kariso..Ga yayan nasu Jidda Abdullahi wannan abokinsa ne Dan wajen Mallam Wada ne.."Ta fada tananuna kowa Kai Hajiya Sa"a ta gyada tana Fadin"Masha Sannunku..Abdullahi ina gajiya..? Nazo kwanaki baka nan nasan karima ta Fadamaka zuwana da Abunda ke Tafe dani.."
Abdullahi ya Dago kanshi yana Fadin"Basu Fadamin komai ba..Sun dai sanar dani kinzo kin Tafi da Jidda zata miki kwana Biyu.."Da mamaki kowa yake kallonsa Shi kuma ya Hade Ransa Baba wada yayi Mirmishinsu na Manya yana Fadin"Kega Sa"a Bamu gayamai komai ba..Mun bari ne keda kanki ki sanar dashi sai ku Fahimci Juna.."
Hajiya Sa"a ta gyara zaman mayafin dake Jikinta Tana Fadin"No problem Daman kan Mganar Hauwa"u ne, kwarai da gaske da nazo naga Hauwa"u na yaba sosai da irin Rikon da naga anyi mata kuma naji Dadi Sosai,sai dai kuma ina Son Don Allah a matsayinka na Yayan Hauwa"u wanda ke matsayin Uba gareta kai da Mallam Wada kumin lamani na Karbi Jidda ta Dawo Hannuna Saboda Chan Saudiya Danayi Aure har Mijina ya Rasu bam Haihu ba Jidda ita kadai ce yata anan Duniya Na Dawo Nageria da zama na Dindin ina Bukatar zaman Hauwa"u awajena Kodon Shekarun da muka kwasa bama Tare Saboda wasu Dalilan da Allah ya Tsara.."
Falon yayi Shuru Abdullahi kadai ake Saurara wanda yayi kasake kawai yana kallon Kasan Cafet din Dake Dakin Mama Mirmishi ne ya kwace mai kafin yace"Acikin mganarki ya kamata ki Gane amsarki aciki kafin ki Dora wata mgana sai da kikace a matsayina na yayan Hauwa"u kuma Uba gareta Nida Baba wada kinga kenan Jidda tana da gatan da Ko kotu kike je ba wanda zai baki Rikon Jidda ta koma Hannunki..."ya fada kai Tsaye yana kallonta ido Cikin Ido Hajiya Sa"a tayi tsai Tana kallonsa Lariya kuwa acikin Ranta Fadi take dama Daga ganinsa zai yi Taaurin ido...
Baba wada dai yayi Shuru bai ce komai ba Saboda ba"a kawo gabar da zai yi mgana ba,Nazifi kuma ya maida Hankalinsa kan Wayarsa ammh kuma gabadaya Hankalinsa na kan su,Hajiya Sa"a ta muskuta Tana Fadin"Ai nasan kuna Raye..Kuma zaku iya Rike Jidda Fiye da yarda zan Riketa Sai dai kuma kuyi Duba da Duk Tsawon Shekaruna nan bana Tare da ya"ta baku Tsausayina a matsayina na Uwa wacce take Bukatar yarta a kusa da ita ba....?"
Kai Tsaye Abdullahi yace"Ana Tsausayinki mana..Kice baki Tsausayama kanki ba Hajiya to be Frank kin san kina son zama da y'arki ki ka Tsalleketa koda Tana gidan Mahaifinta ki Lula wata uwa Duniya ki ka manta da ita ?.Kawai sai yanzu Farat Daya kizo kice zaki karbeta Don Allah ke kina ganin ya Dace..?na Dauka ko baki Jidda nayi kunya bazai barki ki karbeta bawai ina miki Gori bane No ina gayamiki gaskiya ne Ban gaza ba Mama ma bata gaza ba tana iya bakin Kokarinta kuma koda Mahaifinmu ya Mutu ya barmata Amanarmu Duka Tana Hannunta ne Ta Rainemu har muka kai iyanzu kina ganin ba Rashin adalci bane kizo Daga Sama kawai kice zaki karbi yarki..? Baki Tsausayama wata Uwar da ita Bata taba Haihuwa ba kuma ta Sadaukar da Lokacinta da kuruciyarta wajen inganta yaran da bama ita ta Haifa ba..? Itama Shin ba abar Tsausayi bane..?
Yafada yana kafe Hajiya Sa"a Da ido wanda mganganunasa suka Shigesu Baba wada kai kawai yake Gyadawa alamun gamsuwa Mama kuwa na gefe tana Sharan kwallah acikin Ranta tana Godema Allah daya bata D"a kamar Abdullahi Duk da ba ita ta Haifeshi ba.
Falon ya Dauki Shuru Lariya ce tayi mgana wannan karon Da cewa"Ammh ai Itama Yayar sai ku Duba Rauninta..Taya zataji alokacin ga Sakin miji daga baya kuma akazo aka Rabata da yarta alokacin bata da wani Abun da zata iya yi akai zuwanta kuma Saudiya wannan Nufin Allah ne dama Allah ya nufi zataje chan kuma Har tayi Aure.."Mirmishin Abdullahi ya saki kafin yace"To waya ce ba Nufin Allah bane.."Komai da kika gani nufin Allah ne,Saboda haka Itama Jidda zamanta agidan Ubanta Daya mutu ya bari wani Nufi ne na Allah Mganar gaskiya ba zan tsaya kuna Fada ina Fada ba saboda mu ba Sa"anin Juna bane..Kunsan Allah..? Bazan iya baki Jidda ta koma Wajen ki da zama ba Sai dai zan miki alfarma ta karshe duk bayan kowani Wata zata Dinga zuwa ta miki kwana Biyu Ke mahaifiyarta ce ban isa ,na Raba tsakaninku ba,kuma nayi miki alkawarin duk Abunda kika Siya mata a matsayinki na uwa gareta bazan Hanata amfani Dashi ba,ko waya da kika Siyamata na barta dashi Domin Dama Abunda yasa kika ga ban Siyamata ba abaya saboda bata yi candy ba ammh Tunda yanzu tayi Shikenan bazan Hanata karban komai Daga gareki ba Nagama Mganta ko ya kagani Baba..?
Baba wada yace"Hakan Shine Daidai Abdullahi..Abunda yasa Tun Farko ban saka baki ba kenan Sanin wannan Bukatun na Sa"a bamai yuyu bane gaskiya in akayi hakan Ba"ayi ma Karima Adalci ba."Abdullahi ya mike yana Fadin"Nima shi nagani..Duniya sai ta zagemu..Mganar gaskiya kenan Ba zan maida Rikon Jidda ahannunki ba ba Saboda komai ba Sai saboda ke macece mai Rauni kema baki wuce wani ya baki Tarbiya ba kinga kuwa ke bazaki iya bama Jidda Tarbiyan Data kamata ba.."
Daga haka ko Wucewar Hajiya sa"a bai Jira ba ya kalli Nazifi yana Fadin"Muje mutumina.."Daga haka ya Fice Nazifi ya Maramai baya,Hajiya Sa"a da Hajiya Lariya suka Bisu da kallon Mamaki Baki Bude,suna Fita suka ga Jidda ta Rabe Jikin Mariya Tana Sharan kwallah wani kallon Banza Abdullahi ya Wurgamata Dole ta Shiga Taitayinta wani Dogon Tsaki yaja kawai ya Zura Takalminsa ya Fice Nazifi ya maramai Baya.
.
Acikin Dakin Mama kuwa Baba wada ne yace"Kinji dai Hukunci Da ya yanke..Kuma ina Bayansa Hajiya sai kiyi Hakuri yarki dai bamai Rabaku ammh ki barta gidan Ubanta ki Rika zuwa ganinta Lokaci bayan Lokaci itama zata Rika zuwa tana ganinki bashikenan ba.." Hajiya Sa"a ta Dukar da kai Tana jin Wani Daci acikin Ranta bata samu bakin mgana ba Lariya ta Bude zatayi mgana Baba wada ya Dakatar da ita da Fadin"Kinga ya isa..Wani Cece kuce duk ba namu bane..Mu ba yara bane kuma na Tabbata munsan Abunda ya Dace damu..'Daga haka kawai Shima ya mike yanama Mama Sallama ya Fice,Mama ta Sunkuyar da kanta Kawai batayi mgana ba Hajiya Sa"a ta saki ajiyar Zuciya ta mike Tana Fadin"Tashi mu Tafi Lariya..."
Lariya ta mike Tana saba Jakarta Mama ma ta mike tana Fadin"Kiyi Hakuri Hajiya Sa"a..."Da Hannu ta Dakatar da ita Tana Fadin"Ba sai kin ban Hakuri ba Karima ba Laifin ki bane..ammh ina so ku sani ni Sa"a ni na Haifi Jidda da Cikina Bayan na Sha wahalan Dakon Cikinta na Wata Tara na Sha wahalan Naguda na Haifeta kuma na Shayar da ita Daga jikina na Tabbata koni ban nemeta ba ita Zata nemeni Saboda haka bawanda ya isa ya Rabani Da ya"ta..Muje Lariya.."
Daga Haka Ta ja Hannun Lariya suka Fito Daga Dakin ganin Su haka yasa Su Jidda suka mike daman suna Jin Abunda ke Faruwa kuka Jidda ta saka Ta Rike Hajiya Sa"a wacce Taji kamar itama ta Fashe da kukan kanta ta Shafa Tana Fadin"Stop crying my Dota..Ba wanda ya isa ya Raba wannan kaunar da Allah Ya dasa Tsakanin uwa da ya...Ki zauna anan dim Insha Allahu zan Rika zuwa ina ganinki Lokaci Bayan Lokaci."Tafada tana Share mata Hawaye Zuru Jidda ta mata ido Kafin kuma ta saki Mirmishi Rumgume juna sukayi Lariya Da mama da Mariya suna kallonsu Cikin Sha"awa.
Kudi ta Dunbuzo Daga Cikin Jakarta bata ko san nawa bane ta Mikama Jiddan Tana Fadin"Zamu mgana ta waya kinji ko..? Da kai Jidda ta amsa Tana Fadin"Nagode Mommy.."Mirmishi ta mata ta Shafa kumatunta Tana Fadin"U are wlcm y Darling Dota.."Hannunsu Rike da juna Har Zaure kana suka Rabu ta Daga musu hannu kana ta koma Cikin Gidan Duka Kudin ta Damkama Mama,Mama taki karba tace ta ijiye kudinta sai ta Bama Mariya tace ta ijiye mata.
Achan waje kuwa Abdullahi da Nazifi suna tsaye wajen Motar Nazifin sai gasu sun Fito Kallo kallon sukama Juna Abdullahi ya Dauke kansa Gefe kamar bai gansu ba kai Hajiya Sa"a Ta kada ta Bude Motarta ta Shiga Bangaran Direba lariya ta Shiga Bangaran mai zaman banza suka Tada Motarsu sukayi Reversr suka Dau Hanya sai da suka kule kana Nazifi yace"Allah ya kyauta..ammh matar nan ta Cika karfin Hali
Ajiyar zuciya Abdullahi ya Sauke yana Fadin"Kabari kawai harga Allah Zuciyata bata kwanta ba..Ni ban isa na Raba uwa da ya ba..Ko yayane suna Tare wani abun ma ba sani zan yi ba ina Tsorin Jidda ta samu sake sai Allah Wlh Nazifi ina Cikin Damuwa inda ace yau ina da wanda zan iya bama Jidda ya Aura wanda na yarda da nagartansa ko Bashi zan iya ci Wlh nan da wata Biyu na aurar da ita Hankalina zai Fi kwanciya.."
Yafada yana Bayyana yadda Abun ya Damesa asaman Fuskarsa,Nazifi yayi Shuru yana kallonsa Kafin yace"Gani...Zaka bani Auran Jidda...?
Da Sauri Abdullahi ya kalleshi kafin yace"Dillah mu daina wannan wasan Dakai.."Nazifi yayi Dariya kafin yace"Am not Joking abokina indai zaka bani Auran Jidda ni kuma na maka alkawarin Auranta nan da Wata Biyu na killaceta agidana ni kadai.."da wani rin Sauri Abdullahi ya Rikeshi yana Fadin"Are u Serious Mutumina..?"
Nazifi yace"Wlh Tallahi..Am Serious...Kaji ma na Rantse..."Rumgumesa kawai Abdullahi yayi yana mai Bayyana Farincikinsa afili Shima Nazifin Rumgumesa yayi kafin Lokaci Daya su saki Juna Abdullahi ya kalleshi Cikin Fara"a yana Fadin"Zan fi Farinciki in ka sanar dani ba wai saboda na Furta haka bane zaka auri jidda zan Fi Jin Dadin in ka Furta kana Son Jidda So na Aure..!!!
Mirmishi Nazifi ya Sake kafin ya Riko Duka Hannayen Abdullahi yana Fadin"Haba Mutumina Ni din ne baka sani ba..? In Abu bai min bani da Kwana kwana Direct nake Fadama kowa ma waye koya muke Dashi..Kaji ma na Rantse Maka har ga Allah ina Jin Jidda acikin Raina ba Tun yanzu ba Abokina..."
Abdullahi ya kalli Nazifi yana Fadin"Alhamdulillah naji Dadi kwarai...Ba Domin komai sai Domin Na yarda Dakai abokina kuma na Tabbata zaka auri Jidda ka Riketa Kamar yadda ni zan Riketa na kula da ita.."Nazifi yace"Insha Allahu Mutumina...Karma abari ya Huce muje ni dakai yanzu mu ma Baba mgana ayi komai cikin Lokaci Dama Mata nake nema kuma na Riga na samu agidanmu ma.."
Dariyar Jin Dadi Abdullahi yayi yana Fadin"Hakane..ammh Wani Hanzari ba gudu In Salisu engr.yaji Labarin kanwata zaka aura anya bazai ji Haushi ba..? Yace Kaki kannesa kuma ni na baka kanwata..?Nazifi ya Dafa kafadan Abdullahi yana Fadin"Come on Mutumina...Salisu bai da wannan Halin sam..Ko kwanaki ma naje gidan na gaida Hajyarsu,tayi Rashin Lafiya har ta kwanta asibiti naje gidan na gaisheta Duka yaran na gansu ammh kamar Karamar da Babbar ban gansu ba suna Makaranta karka damu kanka Dani da kai mun zama Daya salisu bazai taba wani Tunani akan hakan ba infact ma ni nace ina so ba Turamin kayi ba.."
Abdullahi yayi Mirmishi kafin yace"Allah yasa..."Daga haka suka Dunguma zuwa gidansu Nazifin akofar gidan suka iske Baba wada suna mgana da wani makocinshi gefe suka koma sai da suka gama kana yazo ya samesu kan Dakalin kofar gidan suka Zauna su uku kafin Nazifi ya Fara korama Baba wada jawabi Abdullahi ya karisa kafin su gama Bakin Baba Wada yaki Rufuwa,Cikin Farinciki yace"Masha Allah..Alhamdulillah kai gaskiya naji Dadin wannan Labarin naku..Kai...Abu yayi Dadi dama na Dade ina son wannan Zumuncin Dake tsakanin Gidan Abokina marigayi Usman Direba da nawa gidan ya kara Haduwa ta Hanyar Autarayyah Allah bai yi ba sai wannan karon Hakika naji Dadin wannan mganar Sosai.."Yake Fada yana Bayyana Farincikinsa Haka suma Sun Dade suna tsara yadda komai zai kasance Nazifi yace baisan a dauke Lokaci mai Tsawo Sai aka bar mganar kan Abdullahi Yace Sadaki kadai Yake Bukata wajen Nazifi Tuwona maina ne Abun,Sun Dade suna mganar kafin Daganan Abdullahin sukayi sallama da Nazifin da Baba Wada yayinda suka Shiga Cikin Gida Shi kuma baima koma Gidan Mama ba Mashin Din Haya ya hau zuwa gida Zuciyarsa Fes.
Bangaran Baba Wada Da Nazifi kuwa suna Shiga Cikin Gida Baba wada ya Labartama Inna Abu Halin da ake Ciki,Guda ta Rangada tayi Juyi kafin tace"Ahayye...Abu namu mganin akwabemu..Ni uwar amarya kuma uwar ango ka Biyasheni Nazifi Wlh sai yanzu zan Tabbatar da zakayi aure ina gayamaka Har mai asharalle zan kira ya bugamana kidaa da waka Ni da Karima.."Karamin Tsaki Baba wada yaja yana Fadin"A"a bamai Asharalle ba ki kira Mai amada ne..Kullum bakya girma Abu baisan me kikeson ki zama ba.."
Yana Fada ya Bude labule ya Shige Cikin Dakin ya bar Nazifi da Inna Abu tana ta sakamai albarka Shi kuma yana Dariya yana Jin wani Farinciki yana Tsirgamai Har Cikin Ransa na Wannan Auran wanda bai ma san Sadda bakinsa ya Furta zai auri Jidda kuma Baya jin Nadamar haka sai Farinciki.
Nan yayi La"asar yaci abinci kana yayi sallama da iyayensa ya Dau Hanyar Kaduna Zuciyarsa na wani irin Fari yana jin wani Farincikin da baisan Daga ina yake Fitowa ba..."
*Domin Biyan Kudin Karatu akan Littafin Ra"ayi ne ko Buri..? Zaku iya Tura kudin karatunku ₦200 Kachal akan wannan asusun bankin 0552179550...JAMILA UMAR GTB,Sai a turo Shedar Biya ta wannan layin wayar 09069067488,In kuma Katin Waya ne zaku iya Turowa ta wannan Layin 09027767783 kai Tsaye Bayan Mutum ya Dauki Hoton katin...Sai kunzo...*
*Shakira...*
4/9/21, 1:57 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*
*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!
*Intelligent writer' asso...*
*023*
"Haka Abdullahi yajema Hafsah Cikin Wannan Farincikin Wanda ya kasa Boyuwa Daga saman Fuskarsa,Tayi ta mamaki ganin Wannan Fara"a kamar me,Data Tambayeshi sai yace mata Bakomai koma miye zata ji Daga Baya.
Su Amira kuwa Auwal ya Dawo Dasu Bayan ya Dawo Daga Shago,Shi Abdullahi yama Manta Dasu ya Taho Shi kuma yana Dawowa Shago Mama tace ya Daukesu Amira ya kaisu Gida,ya Dade sai Wajen goma yayi musu sallama ya koma Gida Bayan yayi Dinner dinsa anan Suna ta Hira da Hafsah Abdullahi ko yana Ciki ya kwanta gajiya ta Saka Barci ya Daukesa da wuri.
Washegari Inna Abu ta kasa Zama sai da ta Shiga gidan Mama ta Fara Zegunta mata Hakika Mama tayi murna ammh acikin Ranta Tana Tunanin Jidda ne,ganin ai babu Soyayyah Tsakanin Nazifin da Jidda Tayaya wannan Halin zai yuyu,Koda yake