Advertisements
Chapter 22 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   22 / 48

63K to 66K   out of 143.7K words

ce bata san Ya yarinya tayi Fadi tashin girma ba kawai sai yau Rana tsaka tazo tace zata Dauketa ta koma wajenta..? Wannan ma ai ba mganar da zata yuyu bane ai Jiya mun Dade muna mgana da Anty Zannira awaya da Auwal yazo gidana Tacemin ta kira ya Abdullahi tace karma ya Fara yarda Ta Dauki Jidda in kuma Hakan ta Faru sai Allah ance ta gina Katon Gida da Katuwar mota zaman kanta take Ta Dauki Jidda ai kuma sai Abunda muka ji muka gani.."Mama tace"To daman mana..Daga ita har kanwarta Lariya basu da aure..Ita lariyan Dama Tunda Mijinta ya rasu bata kara ba Ance ita Sa,"an Tun Tana Saudiya take mata aiken kaya su take saidawa har ta Fara tsayawa da kafarta Daga Sa"ar Har lariya kowacce tana Zaune agidanta ne.."

Subai"a Tace"kin ji ko Mama..? Ni wlh ko Bata itan ta kwana Biyun Zuciyata bata kwanta ba.."Hafsah ta kada baki tace"Gaskiya kam..Ammh ai ba laifi bane Domin ta Dauketa taje tamata kwana Biyu mganar dai  ta Dauketa gabadaya ta koma wajenta Shine Abunda bazai sabu ba.."Subai tace"Auwal yace Wlh datana da Wani Tsayayyen Saurayi kawai ya Abdullahi ya Aurar da ita Shikenan Gardama ta kare.."

Mama tace"Wlh nima Kamar ya Shiga Raina haka nace..Toh Babu sai Tarkacen Yara kanana Daga ita Har kawar nata Rumana Sai Tarin yara wadanda ba auransu zasu yi ba banda su Lalatasu.."Nan suka cigaba da Hira kan zence Dukkansu sai Dare suka Tafi Abdullahi yazo ya Dauki Hafsah bayan ya Dawo Daga Makaranta ita kuma Subai Mashin ta Hau ta koma Gida nan Hafsah ta barsu Amira gobe Suna da Hadda.

Hafsah bata ma Abdullahi mgana ba sai da sukayi Shirin kwanciya Tana Tsaye gaban madubi tana Daura igiyan Rigar barcinta Yayin da Abdullahi ke kwance kan Gado yana latse latsen wayarsa Hafsah ta kallesa ta Cikim madubi kafin tace"Abban Amira Ina so na maka wata mgana ammh bansani ba ko zaka karbi zencen.."

Bai Dago ba yace"Wata mgana ce.? Cikin Kulawa tace"Wata yar Shawara ce kadan..ammh karkace nayi maka Shisshigi kan Abunda ya Shafeka.."Dagowa yayi ya kafeta da ido Cikin mamaki kafin Cikin Dakewa yace"Hafsatu... "ta waigo Cikin Dari Dari Tana Fadin"Na"am..
"kai Tsaye yace Mata"Zo nan...'Yafada A muryansa Babu alamun wasa sam.

Jikin Hafsah sai yayi sanyi ta marairace Murya Tana Fadin"Me nayi Abban Amira...? Ido ya sakarmata Lokaci Daya yana ijiye wayar Hannunsa gefensa yana Fadin"Nace ki zo nan ko..? Ya fada yana Tattara Naman goshinsa Cikin Dar dar ta Fara taku zuwa garesa kowani Taku Daya in Tayi sai Zuciyarta ta Raunana Shi kuma kowani Takun ta Daya sai yaji wani iri acikin Ransa balle yadda Hasken Farin watan Dayake Hudowa ta Window din Bedroom din suna Hasketa gabadaya Sai yaji Zuciyarsa da gangar Jikinsa na Tsalle Lokaci Daya.

Tana Zuwa Gabansa ta tsaya tana Kifkifta ido,hannu kawai ya saka ya Jawota ta Fado kan Cinyarsa Ido ta zaro Tana kallonsa Shi kuma ya Hade Ransa Tamau yana Binta da wani Sanssayar kallo Cikin Sha"awa da kauna Kanta ta Dukar Bazata iya Jurema kallonsa ba Hannunsa Daya yasa ya Dago Habarta Suka Hada Ido Cikin Sanyin murya ammh mai Cike da bacin rai yace"Shekararmu nawa da Aure Hafsah..? Kai tsaye ya jefamata Tambayan Cikin narkewan kallonsa Tace"Shekara bakwai Cikin na Takwas.."Kai ya Rausaya kafin yace"Duk a iya tsawon Wannan Shekarun da muke zaune a karkashin Inuwa Daya Hafsah ashe baki yarda dani ba..? Kina min wani kallo Dabam wanda ni ban sani ba..?.

Nan da nan Taji Hankalinta ya Tashi Cikin muryan kamar zatayi Kuka tace"Abban Amira....!!!Shiiii...Ya Dora mata yatsa a saman Bakinta Lokaci Daya yana kallonta Idanuwa ya Lumshe kafin ya Bude a kanta yana Fadin"Karki cemin komai...In ba baki yarda dani ba taya Domin kin bani Shawara kan wani Abu Daya Shafeni ya Shafeki Kuma kice kar naga kin min Shisshigi..? Na taba miki iyaka akomai nawa Hafsatu..?
Ya karishe Fada Cikin nuna Mganarta batamai Dadi ba,Sai yanzu ta gano laifinta Idanuwanta suka kawo kwallah kawai sai ta Sulale kan Kirjinsa ta Kamkamesa Shima Bayanta ya Zagaye da Hannayensa suna Jin Bugawaer Numfashin Juna kafin ya Cigaba da Fadin"ai ni na Dauka ni dake mun zama Daya..Abunda ya Shafeni ya Shafeki kema Abunda ya Shafeki ya Shafeni Domin zaki bani Shawara kan wani abu sam bai Dace ki kawo kalmar Shisshigi Hafsatu Bazan Boye miki ba Raina ya Baci Da mgaanarki.."

Yafada yana Sakin Huci Kara Kamkamesa Tayi alamun ban hakuri kafin Tace"Ba Haka nake Nufi ba Abban Amira..Ammh Tunda baka ji Dadi ba am Sorry Baran kara ba Insha Allahu.."Kanta ya Sumbata yana Fadin"Bakomai ya wuce..Inda nake kara Som Matata Hafsatu Bayan Mahaifiyata Hajara tafi kowa sanina da Fahimtata.."Taji Dadin zencensa kawai sai ta murmusa ta kara gyara kwanciya saman Kirjinsa Tana Fadin"I Love u Abban Amira..."

Tudun Hips dinta ya Shafo Cikin wani Shauki yana Fadin"Me too...Ummin Amira..."Yafada yana kara kwantar da kansa saman kanta yana jin wani natauwa da Farinciki yana Shigarsa,Sun Dade ahaka kafin ya Dago yana Fadin"Umh..ina jinki Wata Shawara ce Matata zata Bani..? Kam kasuwancina ne ko kan karatuna..? Ko kuma Tunatarwa kan Zamantakewarmu ko kuma Ta iyayenmu da Makotanmu..?

Hafsah nadaga kwancen Tace"Kan Zamantakewarmu da kannenmu ne Abban Amira..Mganar Jidda ce nake so nayi maka Duk da baka Fadamin ba.."Ajiyar Zuciya ya Sauke kafin Yace"Bagashi da ban gayamiki ba kin ji Labari..? Hafsah ta Dago Daga Jikinsa Tana Fadin"Ammh ai ba Daga bakin ka ba ko..?

Kai Tsaye yace Mata "Eh Ammh Ko baki ji Daga Bakina kinji Daga bakin makusantana..Ya kamata ki Fahimci Lokacin da Abu ya gama Batamin Rai ban cika son ina Tattauna mganar da wani ba nafi son Abarni ni kadai nacigaba da Nazarin Bacin raina ni kadai U know me Hafsah..Ban cika som ina Raba miki Fushin da ba naki ba zan iya zuwa na kawo miki wannan mganar kila ki Fadi Mganar da batayi Daidai da Ra"ayina ba kinga kuwa zamu samu Matsala har takai mu ga Abunda Zuciya bazata Dauka ba Shiyasa Tun Farko ban miki ma mganar ba sam Bana so Fushina ya Shafeki ne.."Yafada yana kallon kwayar idanuwanta Ido ta kada kafin tace"Hakane...Ammh ni banga Abun Damuwa ba Abban Amira Tunda dai tace Sati Daya zatayi mata zata Dawo da ita ba Tafiyar kenan ba.."

Annurin Fuskarsa ne ta Dauke na wani Lokaci kafin yace"Haka kike gani..Banga laifinki ba Domin baki da Tunani irin nawa,,baki san Abunda hakan Zai Haifar ba.."Hafsah tace"Duk da haka ni Damuwar da kasa aranka ce ta Hanaka komai bana so Abban Amira.."Cikin wani irim kallo yace Mata"Me damuwar ta Hanani..? Uhm..?

Cikin Kallon Juna ido Cikin ido tace"Ta hanaka kula matarka mana.."Ta fada Cikin Shagwaba da Tabara sai ta bashi Dariya Har sai da ya Murmusa kumatunta yaja yana Fadin"Kaji matar nan kawai kice kina Bukatar mijin ki ba wai ki Tsaya kina kwanana ba.."Kan kirjinsa ta Sunne kanta tana Fadin"Ai gaskiya ne..Tunda mganar nan Tataso baka kulani kuma kasan nayi kewarka ko.?

Tafada tana yawo da Hannunta saman Kirjinsa Bankare mata yayi Lokaci Daya yana sakin Siririyar kara kan yace"Nima nayi kewarki Fiye da yadda kike kewata Hafsatu kawai dai kinsan In Zuciyata bata da natsuwa gangar Jiki bai da ikon Aiwatar da wani abu koda kuwa Gangar Jikin yana Tsanain Bukatar Abun."Yafada yana fara yawo da Hannunsa a Gadon Bayanta Cikin wani Salo Ta Dago da kanta Tana kallonsa kafin tace"To yanzu gangar Jikin tana so..?kuma zuciya ta Hana ko..? Kunnanta ya kaima Cizo yana Fadin"kinganki ko..? Ko Zuciyar bata so Dole tayi Hakura yau na Morema Kayana ko..? Dariya tayi Ta kara makalkaleshi Shima Dariyan yake kafin Lokaci Daya ya Dagota su Hade bakin Juna.

Wannan Daran Sun Shayar da juna Zumar Soyayyar Washegari koda ya Tashi kamar bashi ba da Annurinsa ya tashi bai je aiki ba Sakamakon yau asabar sai Wajen 11am na Safe ya Shiga Cikin makaranta,bai dawo ba sai Dare Daya Dawo Daga makaranta Gidan Ammi ya Biya ga gaidasu kana ya Bi ta Gra inda gininsa ke Ta Tafiya,Koda ya Dawo Hafsah Taji Dadin ganinsa,Ya Rage nuna Damuwarsa ko afuskarsa nan kuwa kawai yayi kokarin nuna mata komai ya wuce nan ammh acikin Ransa Jira kawai yake Ranar Talata tayi yaga Shin Hajiya Sa"a zata dawo da Jidda kamar yadda tayi alkawari..? In bata Dawo da ita ba Ya Rantse da Allah in ta saka wasa sai yayi karar ta akotu.


******

A bangaran Jidda kuwa Tana chan Cikin Jin Dadin Rayuwa Aranar da suka Tafi kai Tsaye Chika gari suka wuce katon Gidan Hajiya Sa"a Suna zuwa Ta kaita Daki na musamman daaka kawatashi Domin ita komai na kayan alatun Rayuwa kama Daga na Amfani zuwa na sakawa an Tanadarma Jidda murna kamar ta kasheta Hajiya Sa"a da kanta ta Shiga ta Hadama Jidda Ruwan wanka Ta Taimaka mata ta Cire kayan Jikinta ta Shiga wanka Ji take kamar ta lasheta Saboda so da kauna.

Bayan ta Fito wanka Ta iske Hajiya Sa"a ta Fito mata da wasu Ubansu Riga da Sikat na yan kanti masu kyau da Tsada,Jidda ta Dinga Dagawa Tana Murna Domin agida Ya Abdullahi baya Barinsu saka Riga da wando koda Sikat yan kanti yanzu zaiFara Fada gashi ita kuma Tana son Daman Harkan gayu da wayewa Dama ne kawai bata samu ba,Ta saka kayan kenan Sai Ga Hajiya Sa"a Ta Shigo Dayake Sun Ijiye Anty Lariya agidanta kafin su Wuto nan.

Hajiya Sa"a da kanta Taja Jidda gaban Madubi ta gyara mata Fuska Taga kanta yayi Datti tace gobe zasu Fita ta gyara kanta da Jikinta,Falo ta jata kan Dinning ta Iske an Cika Teburin da kayan Ciye Ciye da ShayeShaye da Abinci kala lala,Hajiya Sa"a da kanta ta Bama Jidda abinci abaki Tana ci Tana kallonta kamar ta lasheta,sai da suka gama cin abincin kana ta jata zuwa Daya Daga Cikin kujerun Falon,suka Zauna kana ta Kira yan aikinta ta gabatar musu da Jidda a matsayin yarta kwara Daya da Allah ya bata Duk suka gaishe da Jidda Cikin Girmamawa,Daganan ta Jata ta zagaya da ita ko"ina na Cikin Gidan Tana nuna mata Jidda sai Bin ko"ina Take da kallo Tana Tunanin yanzu wannan Gidan na Mahaifiyarta ce Lalle Allah Abun Godiya.


Ranar kwana sukayi Hira Tsakanin Hajiya Sa"a Da Jidda,Daki Daya suka kwana sai asuba suka kwanta Sai da Hajiya Sa"a tabama Jidda Labarin Auranta da Mahaifinta da Haihuwarta zuwa komawarta Saudiya da Auran datayi Duka kuma ta karyata Rade Raden da akeyi na cewa karuwanci Takeyi achan Saudiya ba Aure tayi ba Ta Daukoma Jidda albulm din Hotunansu da Tsohon Mijinta na Chan Saudiya,Jidda tayi ta kallon Hotunan Mamanta a Saudiya Tana Jin wani Farinciki Itama Labarin Komai na Rayuwarta ta Bata da irin Takuran ya Abdullahi a garesu Tana Rumgume Jikin Hajiya Sa"a take bata Labarin irin Rikon da Mama tayi musu Kamar ita ta Haifesu bata Taba Nuna musu bambamci ba ko kadan,Hajiya Sa"a Tana ta Sauraranta acikin Ranta kuma Tana Tunanin yadda zata karbi yarta ta Dawo wajenta Har Abada.

Sai da jidda ta kwana Biyu a gidan basu Fita konan da Chan ba,Har ta Fara Chanzawa ta samu Mayuka masu kyau da Hutu bata komai sai Ci ta kwanta abincin ma abaki Hajiya Sa"a ke bata so take ta sangartta,Ranar data kwana uku suka Fita Gidan Su Mahaifiyarsu ta kaita suka ganta sai mamakin Girmanta suke nan suka wuni sai Dare suka koma Gida Dayan Washegarin kuma Suka Tafi Babban Gidansu Babansu,Shima nan din sai Mamakin Girman Jidda Suke yi ganin ta zama Budurwaa bakin Jidda Yaki Rufuwa ganin ashe itama yar Dangi ce,Tafi jin Dadin Rayuwarta Wajen Mamarta Saboda ta samu Saken Rayuwa Sosai ta saka kayan data keso ta kuma ci Abunda take so Ra"ayinta Shine Ra"ayin Hajiya Sa"a tayi alkawarin bata Dukkan wani kulawa da jin Dadin Rayuwa wanda bata ba ta abaya ba.

Basu kai Dare ba suka Biya Gidan Hajiya Lariya chan suka kai Dare,washegari kuma Ta kaita gyaran kai da gyaran jiki aka mata Gyaran Kafa da kuma na gashi nan da nan sai ga Jidda ta Fito tayi Ras da ita kana suka Shiga kasuwa tayi mata Siyayya kamar za"a Bude shago komai na Bukatar mace na mata ta Siya mata,Daganan kuma suka wuce Gidan Hajiya Lariya Suka Dunguma Gabadaya zuwa Shagon wani mai dinki ya gwada Jidda kana Suka koma Gidan Hajiya Lariyan Tare,da zasu tafi ta Dauko mayafai masu kyau da tsada wajen Kala goma ta Bama Jidda,tace asha kwalliya lafiya kamar Jidda zata Sume saboda Dadi Dama tana Bala"in son saka gyale,Gashi kuma Burinta ya Cika ta Rumgume Anty Lariyan tana ta mata Godiya.

Ana gobe Satin Dayan da Hajiya sa"a tayi alkawarin Komawa da Jidda aka kawo Sabbin Dinkunanta na atamfofinta da lesuna Masu kyau da Tsada da material kaya wajen kala ashirin,sai Takalma da jakunkuna da Anty Lariya tazo Dashi,Da farko Hajiya sa"a ta nuna batason Rabuwa da jidda zata Riketa a hannunta komai zai Faru ya Faru lariya ce ta nuna mata kar tayi hakan Saboda in Tayi haka batayi Daidai ba ta bari su maidata Daga baya sai suyi mgana.

Da wannan mganar yasa Hajiya Sa"a Ta Fasa Gudurinta ammh bata maida Jidda ba sai da ta kwana Goma awajenta kana ta Maidota gida da kaya Niki Niki kamar za"a bude wani karamin Boutique,Tare kuma da Siyan mata Wata Faskekiyar waya Samsumg Jidda Tana ji kamar tayi ta Flaying a sama saboda Murna,Motarta kuma ance bata iso ba sai sati na sama Da yammah ne suka kawota Lokacin Mama bata nam Tana gidam Inna Abu Mariya ce kadai agidan itama Daga asibiti ta Dawo ko Unform dinta bata Cire ba Taji sallaman almajirai suna ta Shigowa da kaya bata gama mamaki ba Sai gasu sun Shigo Tana kallon Hajiya sa"a tun kafin Taga Jidda ta gane mahaifiyarta ce saboda kamarsu Da taga Jidda sai da saki baki ganinta Cikin Shigar wata Doguwar riga baka tayi Rolling da mayafinsa sai wata karamar jaka da bakin Takalmi,sai Wayarta Dake Hannunta tana ganin Mariyan tayi Tsalle ta Rumgumeta tana murnan ganinta itama Mariyan ta Rumgumeta tana murnan ganinta Ko Daki Hajiya Sa"a da Lariya basu Shiga ba jin Mama bata nan,Sallama sukayi da Jidda Hajiya Sa"a tace Zata Dawo Ranar Lahadi saboda ta samu Abdullahi agida,jidda har da kuka da zasu tafi sai da Hajiya Sa"an ta Rumgumeta tana lallashinta da mata Alkawarin Zata Dawo Ranar lahadi ta Dauketa.

suna Fita ba Dadewa sai ga Mama Jidda ta makalkaleta tana Murna Ta jasu Daki Tana nuna musu kayan da Hajiya tayi musu,sai wata leda ta Databama Mama Daya,sai karama kuma ta bama Mariya tace inji Hajiya Sa"a Da mariya ta Bude nata Doguwar riga sai Less guda Daya da Takalmi sai Saitin Turare na Olive,Mama kuma atamfofi ne Guda Biyu sai leshi daya da Takami sai Turaran miski Dana Jiki,Mama ta karba tana ta Godiya ammh mamaki ya kamasu ganin Uban kayan da Jidda ta Dawo dasu Haka ta Dinga cema Mariya ta kara wani abun in tana so Mama ta Hana tace abari sai Yayansu yazo ya gani nan da nan Jidda ta bata rai sanin Halinsa,Ranar kwana sukayi ita da mariya Suna latsa wayar Jidda Cikin Sha"awa da Burgewa.


_Ga Masu Bukatar Fara Biyan kudin Karatu akan Littafin RA"AYI NE KO BURI...? zasu Biya kudi akan ₦200 kachal Ta wannan Asusun bankin 0552179550...JAMILA UMAR GTB,Sai a turo da Shaidar Biya ta wannan Layin 09069067488...in kuma Katin Waya ne sai a dauki Hoton katin a turo ta wannan layin 09027767783...Sai kunzo..._


*Anitha...*
4/9/21, 1:57 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!



*Intelligent Writer"s asso....*



*O22*


"Abdullahi baisan Hajiya Sa"a ta Dawo da Jidda ba sai da Safe Daya je kai su Amira Makarantar Hadda Jiya Dare yayi kuma mai mashin dinsu Mashin dinsa ya samu Mtsala bai samu zuwa ya Daukesu ba,Bayan ya kaisu sai ya Biya Gidan Mama nan ne ya iske Jidda Mama kuma ta Tattaro duka kayan Harda da wanda Hajiya Sa"an tayi musu aike ita da Mariya da wayar data Siyama Jiddan ita kanta.


Tsab ya gama kallon Komai Wayar na Hannun Mama bai karbeta ba yadai kallah ya kada kai,yace ma Mama Ta maida ma Jidda kayanta su kuma Sun gode Ba Mama kadai ba Hatta Jidda sai da Taji mamaki Domin Tana Daki Tana Kukan Rabuwarta da Wayarta sanin Ya Abdullahi bazai barta da wayar ba sai gashi kuma ya basu mamaki gefe kawai ya koma yana latsa wayarsa Gefe Daya na Zuciyarsa kuma yana ta Nazarin wasu abubuwan.

Ya Dade gidan Mama sai da yasha Koko da kosai kana Ya tafi,bayan Mama ta zubamai Kosan tace ya kaima Hafsah sanin Tana son kosai Sosai,yana Hanyar komawa Gida Nazifi ya kirashi awaya yace yana gobe yana Hanya zai Shigo,Yana so yaje ya Duba Gininsa ya kara ma Shugaban ma"aikatan kudi,Shima Abdullahi yace Dama Zai je Shima wajen nashi ginin Duk da nashi yayi nisa har an kai Linter kuma anyi Rufin sama Dana Ciki.

Koda ya koma Hafsah ta gama Komanta tayi wanka Shima wankan yayi a gurguje yayi Breakfast ya Tafi Makaranta Yana da karatu Karfe 11am,Hafsah sai Murna take Taga Kosai Shi taci da Buredi tasha Ruwa,Abdullahi bai Dawo Gidan ba sai Dare,Shago ya Biya atudun wada Shiyasa yakai Dare,Washegari kuma Tun karfe 9am na Safe Sai ga Nazifi Agidan Abdullahi ma Dukansu suka karya ya Jirashi yayi wanka ya Shirya ya bar Mashin Dinsa Nazifin ya Daukesa a Motarsa suka Fita.

Wajen Ginin Nazifi suka Fara Biyawa Shima ginin yayi Tsawo Sun Dade a wajen Sosai Kafin su Tafi Chan Gra,Nazifi yayi mamakin ganin yadda Ginin Abdullahi yake Tafiya da Sauri Haka yanayin Tsarin ginin ya Burgeshi Flat uku ne aka Hadashi Cikin Bangare Daya aka Fitar da Babban Falo,Daga hannun Dama Akwai Koridon da zai sadaka da Wani Dan madaidaicin Falo,sai 2bedroom da Kitchen,Hakama Daga Hannun Hagu Shima sai Haka Tsarinsa yake sai Daga Yammah ma Shima sai dai Shi karamin Falo ne sai Bedroom guda Daya da Kitchen nan ne na Megidan kenan.

Nazifi ya kalli Abdullahi yana Fadin'"Anya mutumina kodai da Sabuwar amarya zaka tare ne..? Hararansa Abdullahi yayi kafin yace"Dillah ni kyaleni nagaji da maka Bayani in Kara aure na Cikin kaddara na zan kara ammh ni ayanzu bani da wannan Ra"ayin Domin Babu Abunda Hausina ta rage ni Dashi Ballatana naji ina Sha"awar Kara aure.."Nazifi ya murmusa Lokaci Daya yana Fadim"Ni

22 / 48