Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
Dandara ba ta kara Binsa ta saka Hannun kenan zata Rikosa yayi saurin kaucewa yana kallonta Lokaci Daya yana Fadin.."Ina Kika ijiyemin Jallabiyoyina..? Yafada yana kallon Gefe Saboda Shigar datayi Domin wanke Laifinta ya kusa yin Tasiri a tare da shi.
Batare Da tayi mgana ba ta matsa gefensa ganin haka yasa Shima ya matsa hade da Juyamata Baya,Mamaki ya kara kama Hafsah aranta tace Abun Babba ne,Jallabiyansa ta Daukomai mai Ruwan toka tana Fadin"Gata ko na chanzo maka wata ne..?
Bai mata mgana ba illah ido Daya Zubamata lokaci Daya yana mika mata Hannunsa tagane Abunda yake Nufi ta mikamai Jallabiyan ta koma gefe tana kallonsa Bai sakata ba ya maidata ya Dauko Baka ganin haka yasa ta Girgiza kai ta Fice kawai Zuwa Kitchen ta Hado ma Abdullahi Dinner dinsa Zuwa Tsakiyar Cafet din Dake Cikin Falon.
Ta kawo mai Ruwa kenan sai gashi ya Fito yana waya Jin datayi yana ambaton Mutumina yasa ta gane da Nazifi yake mgana Yana zama kan Daya Daga Cikin kujerun Falon taji yana Fadin zataji Daga Haka sukayi sallama,Abincin ta Zubamai Cikin Filet tana Fadin"Na saka maka Coslow din ne..? Bai mata mgana ba sai ya Sauko kasa ya Tankwashe kafa Sai ta mikamai Filet din Hannunta zuwa gabansa ta Turamai Dan Vowl din Data saka Coslow din Shi kuma ya saka Cokali ya Diba ya zuba kana ya Fara Cin Abinci gefe ta koma tana kallonsa Sakamakon Ita ta Riga taci nata Tun Dazu.
Hankalinta ta maida kan Talabijin tana kallon Tashar Arewa24,Chan taji yana Fadin"Ashe kun Biya gidan Nazifi yau..? Hafsah ta waigo tana Fadin"Eh wlh..na kira sakinar tace tana gida bata koma ba batajin Dadi.."Kada kai yayi kafin yace"Yan suna..? Gashi kin Dawo na zata chan zaki zauna sai Zannira ta yaye kana sai ki Dawo.."Kai Hafsah ta Sunkuyar Lokaci Daya tana Fadin"Allah baka Hukuri.."Bata Rufe baki Ba Abdullahi ya katseta da Fadin"Shoutup...!!! Gabanta ya Fadi sai ta kara Sunkuyar dakai tana Wasa da adon kwalliyar Rigarta.
Cikin Bacin Rai Abdullahi ke Fadin"Banda kin Rainani Hafsah har ni na ce bazaki je waje ba ki kira Ummata ki kaimata karata ko..? Saboda Umma ke Auranki ko..? Ko kuma Ita Zanniran tafini Muhimmanci ne Tunda kika zabi ki Farantamata ni kuma ki Sabamin ko..? Hafsah ta Dago Tana kallonsa Cikim marairaicewa tace"Allah Abban Amira ba Haka ba..!Ba haka bane To yane Hafsah..?
Ya fada yana Tsareta da mayen Kallonsa mai kama da Tuhuma Cikin Fargaba ta maida kasa tana ajiyar Zuciya,Kada kai Abdullahi yayi yana Fadin"Kinsan meyasa na Hanaki zuwa sunan nan..? Bai bata zarafin mgana ba yacigaba da Fadin"Saboda ki gane ni keda iko dake..Kuma kina karkashina ne..Ina da ikon da zan Hanaki zuwa Sunan komawaye ba Kanwata Zannira ba koda kanwarki ce ko yayarki Ni Abdullahi ina da ikon da zan ce bazaki ba kuma ta zauna ammh saboda ki nuna min iyakata ki ka kira Umma ta Tilastani yin Abunda ban Shirya ba kin kyauta ai gashi kin je kinyi ma Zannira Suna kin Dawo kin barta Chan ita da Mijinta suna zamansu lafiya ke kuma kin Dawo kin Tarar da mijinki wanda kika Nuna ma bai isa Dake ba yayi kyau...".
Maganganunsa sun kashe Hafsah Jiki sai ta kada kai Tana Fadin"Nidai nasan ban Kira Umma na gayamata komai ba ita ta Kirani Tana Tambayanta meyasa banje suna ba sai nace mata kai ka Hanani batama Jira cewata ba ta yanke kiran kuma Harga Allah bansan cewa kai Zata Kira ba da ban barta ba ammh na amsa Laifina Don Allah kayi hakuri.."Yana jinta har tagama mganarta bai Tankamata ba,Ganin yayi mata Shuru yasa ta marairaice tana Fadin"Kaji..? Bazan kara ba Insha Allahu.."
Tafada tana sakarmai Idanuwanta kamar bazai Tanka ba sai kuma ya Dago yana kallonta ajiyar Zuciya ya saki Lokaci Daya yana Fadin"Ya wuce..Ammh kuma karki Fasa biyema mara Hankalin yarinyar nan Subai"atu ni ba irin sakaran Mijinta bane mara wayau ko"ina sai ki ganta tana saka kafa in kikace ita zaki dinga bi Wuyana zaki Sha Allah.."Dariya ta kusa kama Hafsah sai ta kanne Tayi Saurin Fadin"Insha Allahu.."
Ture Filet din gabansa yayi ya mike yana Fadin"Kwashe kayanan ya isheni..Nazifi na muku ban gajiya ya koma sakina ke Fadamai kun zo.."Ta mike tana Fadin"Eh muna amsawa..Sakon Naman sunanka nawajena Zannira tace azo maka Dashi.."Tabe baki yayi yana Shiga Bedroom dinsu yace"Ita kuma gulmanta yayi yawa ina Abunda ya Shafi Abdullahi da Naman suna ko ce mata kikayi mijinki baya Siyan miki nama Shine yasa ta aikomin dashi..?
Yafada yana Tsare Hafsah da ido,Da sauri tace"A"a wlh cewa tayi dai adiban maka kaida Auwal..Ni ba ruwana.."Mirmishi yayi kafin yace"Haka Chan naje Mama na turamin gabana nace wannan ai Shirmen mata ne Naman suna ta Hada suci agida,..."
Hafsah batayi mgana ba ta kama Bakinta Shima bai kara mgana ba ya Shige Ciki ya barta tana kwashe Kayan da yayi amfani Dashi.
*Shakira.."*
4/9/21, 1:55 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*
*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!
*015*
"Allah ya taimaketa wannan karon bai tsawaita Fushinsa ba Bata taba zaton Abun zai zo da Sauki kamar haka ba sai dai kuma Sha"anin na Abdullahi sai Allah Shi madaci ne ga Zaki ga Harbi.
Da safe suna Breakfast Take gayamai Sakon Ammi na Su Amira sai Friday zasu dawo Har ta bashi Labarin Diramar Ammi da Daddy kan su Amira Abdullahi yayi Mirmishi yana Fadin"Sai ki Shirya yau in na Dawo Daga Office muje mu gaishesu Daganan sai mu kaima su Amira kayansu Tunda suna Debema Daddy kewa su Zauna chan Har sai sun gaji dasu sun Dawo dasu da kansu.."Baki Hafsah Ta Bude Cike da mamaki da kuma Farinciki kafin tace"Makarantar Haddarsu fa Abban Amira..?
Yana Tura kwai bakinsa yace"Su Dinga zuwa Dagachan mana...Ko Ammi ma sai ta Tuka mota takaisu yanzu ma karki mamakin ba Direba ke kaisu Amira makaranta ba Itace da kanta.."Hafsah tace"Ammi ai babu Ruwanta...Bantaba mantawa Nida Anty Hadiza Ita ta koyamana Mota Duk da Fadan Daddy ya Dinga yi.."Kai Tsaye Abdullahi ya kalleta yana Fadin"Gashi Anty Hadiza ta Mori koyon Motan nata, ammh ke baki Mora ba har yau baki jin wani iri..?baki jin kamar kin Fita Dabam ko Hausina..? Kin Taso A Katon Gida da kuma motoci ammh kinzo kina Rayuwa a karamin Gida tare da Miji mai Rufin Asiri baida Mota ballatana katon Gida sai dai Mashin baki jin wani irin in kika shiga Cikin Danginki da yan"uwanki..?
Kur Hafsah tayi mai da ido kafin Lokaci Daya Annurin Fuskarta ta Chanza Idanuwanta suka Chanza Launi Cikin karaya da Muryan Kuka Tace"Kana Tamtama da Irin Son da nike maka ne Abban Amira..? Kai ya girgiza mata zai yi mgana ta Dakatar dashi da Fadin"Ko kuwa Irin Tarbiyan da iyayena suka bani ne ka Raina..? Kai ya gyada mata yana Fadin"Karki min mummunar Fahimta Hafsatuna...Ina Tsausayinki ne sai ina ga kamar ban miki adalci ba kamar kinfini karfina na so kaina da yawa da Nuna ina Sonki har na Aureki..".
Ranta ya baci Hawayen idanuwanta Suka zubo Cikin Wata Irin Murya Tace"Banta Tsammanin Zuciyarka zata maka irin wannan Tunanin akaina ba...Tunda na taso agidanmu agaban Ammi a kullum karatunta garemu nida Anty Hadiza Shine mu daina Dubam kanmu ko matsayinmu ko na Mahaifinmu Mu Rika Duban Na kasa Damu mu kuma sani Cewa ko yatsun Hannayenmu ba Daidai bane,Daddy ya karantar damu Gidan Uba Dabam yake da Gidan Miji Abban Amira ya kuma Sanar damu ba Lalle bane Abunda ka samu gidan Mahaifinka ka samu gidan Mijinka ba Ya horamu kam zamu iya Yin Aure mu samu Fiye da Abunda muka samu Daga garesu kuma zamu iya Aure bamu samu Kamar yadda muke samu ba sai dai ya Horemu Da kada mu Raina arzikin wani komai kankantarsa,Mu dai mu kasance masu Wadatar zuci da kuma Dogarai ga kai da kuma Tsayawa ga Allah,Sun kuma Horar damu mu Sani Takala ko mai kudi Duka Daya yayi Su..Tunda ga Ranar Dana Gabatar da kai wajen Daddy ya yi min Nasihan cewa Zabi nagari shine mafi a"ala kuma Ranar da za"a kawoni Gidanka a matsayin Matarka Daddy ya Fadamin cewa Kada na Dauka naje zaman Jin Dadi ne Zaman Aure waje ne na Bauta kuma wajen samun aljanna ce..Saboda haka sai namike tsaye kuma nayi aiki Tukuru Domin wajen samun aljannah ba"a samunsa da waasa.."Ta Dakata tana Share kwallahrta Abdullahi Dayayi Shuru yana kallon Hafsah sai Jikinsa ya mutu ya taso Daga Inda yake ya karisa gabanta ya Duka ya saka Duka Hannunwansa saman Kafadunta ya Dagota Lokaci Daya ya Saka Hannu yana Daukemata Hawayenta yana Girgiza mata kai alamun kartayi kuka.
Kukan ne ya kwace mata ta Fada Jikinsa tanayi,Hannayensa ya saka ya Rungumota Yana sakin Ajiyar zuciya itama Rumgumesa tayi kam Tana sakin Kukanta Bayanta ya Shiga Shafawa yana Fadin"Shiii..Is ok..Am Srry kinji bazan kara wannan mganar ba i promise u.."
Kara Lafewa tayi saman Kirjinsa Tana Fadin"Tunda na Aure ka Abban Amira wani abu bai taba Tsolemin ido ba..Miye Mota..? Bakomai bace a zamana dakai kana Bani Abunda Gidajen masu Hawa Motocin basu bama Matansu ba,Farincikin da kake bani da kulawar da kake bani Nida ya"yana yafi yemin duk wani kawan Duniya awajena kai mai arziki ne Domin ban Taba zuwa wani waje an Raina ni ba..Kana bani Abinci mai kyau da Gina Jiki kana Dinkamin Suturu na alfarma masu Tsada Dani da ya"yana,Kana bani Lokacinka uwa uba kana Saukemin Duka Hakokkina Kana kuma kana Darajamin iyayena da yan"uwana kamar yadda kake Mutumta naka miyefi wannan arziki..? Ni awajena Duk macen Data samu wannan Tagama samun arzikin Duniya sai dai ta jira na Lahira kuma.."Tafada lokaci Daya tana Dagowa ta saka Kwayam idanuwanta Cikin nashi Kashemai Jiki tayi yasa kawai ya kamata ya Rumgumeta Rumguma mai Tsawo kafin ya Dago ta ya Sumbaci lebenta Sumbata mai Tsawo da Muradi kafin ya Dago Habarta yana kallonta Cikin Ido Lokaci Daya yana Fadin"Alhamdulillah..ina godiya ga Allah da samunki A matsayin Matata Uwar ya"yana Hakika na yarda kuma na gamsu Fatana kimin Afuwa da mganata kinji ko...? Hafsatu zata iya ma Mijinta Abdullahi Bawan Allah afuwa..?
Yafada yana wani lumshe mata ido Jikinsa kawai ta koma ta Fada ta Dada kamkamesa Jin Haka yasa ya gane ta Hakura Shima Kara kamkameta yayi yana Shakan Kamshin Turaranta,Sun Dade ahaka kana ya Dagota yana Fadin"Hafsatuna na Makara fa...?Sakinsa tayi Tana Tura baki Dariya kawai yayi yana kallonta Bedroom dinsu suka koma ya Dauki briefcase dinsa da key din mashin dinsa Har waje ta Rakashi kana ta Rufe gidan ta koma Dakin ta Fara kwashe kayan da suka bata zuwa Kitchen.
Bayan Sallar Isha"i Suka Tafi Tudun wada sai dai su Ammi suka gansu kwatsam,Su Amira ma basu wani Damu dasu ba,Suna makale da Daddy da Ammi,su kuma suna Jin Dadi Tunda Gidan ba yara,Hafsah sai wani Shagwaba takema Daddy Ammi ta kalleta tana Fadin"Yau ni naga Abunda ya isheni ni Zinaru..? Uwa tazo ta nanikemin Miji Diyama tazo ta Hau nanikamin miji wai me kuke nufi ne..?
Abdullahi na Dariya yace"Ammi kema sai kija maigidanki gefe kiyi Banza dasu.."Ammi tace'Haka Za"ayi kuwa..Ammh Laifin megidan ne ba Cefene ni kuma na saba Mijina cefene yake min.."Dariya suka saka Hafsah tace"Kai Ammi ina Laifima..?Daddy yace"Kyale Zinaru..So take abarmata ni ita kadai..Alhalin Tunda tayi sabon megida ya watsar dani ni kuma sai na koma wajen amaryata kawai bashi kenan ba.."Dukkansu Dariya suka saka Cikin Farinciki sai wajen goma saura na Dare suka koma Gida Shima Din Daddy ne ya matsa su koma Gida Hakika Sunji Dadi Da Abdullahi yace su Amira su zauna har sai Ranar da suka ka gaji suka maidasu sun kai musu kayan sawansu dana Makarantar Haddarsu dama already kayan makatantar na gidan kafin su Tafi Hafsah Taji Abdullahi da Daddy suna mgana kan Gininsa Daya fara yace mai Har Ginin ya Fara tsawo ammh ya Tsaya sai karshen wata kudinsa Sunyi kasa Taji Dai Suna Ta Tattauna mganar bata saka musu baki ba ganin bada ita suke mganar ba.
Kwana Biyu Tsakani Abdullahi na Office ya Kirata yana Fadamata ta yanzu gaya Transfer din kudi ta account Dinsa,har na Kimanin Miliyan Daya da Rabi Daddy ya Turamai yace ya kara Ahidimar Gini,Murna ya kama Hafsah kuma har ga Allah Taji Dadi Sosai Suna gama Waya da Abdullahi ta Kira Daddy tana mai Godiya yace karta damu Abdullahi Tamkar da ya Daukesa Miliyan Daya da Rabi ba wani abu bane,Don ma bai samu yarda yake so ba 2 million yayi Niyar Bashi Hafsah tayi ta Godiya Da irin karamcin da Iyayenta suka ma Mijinta.
Abdullahi kuwa Cikin Farinciki ya Kira Nazifi Ya gayamai bayan ya Kira Daddy yamai Godiya Mamaki ya kama Nazifi Cikin mamaki yace"Kuma sai ka karba..?Abdullahi yace"eh...In ban karba ba zan maida mai dashi ne Nazifi..? Karfa ka manta bani na Rokesa ba Shi da kansa yayi Ra"ayi ina zaune na ya aiko Min Dashi kuma Hadisi ne ba"a maida Hannun kyauta Baya.."
Nazifi yace"Hmm Duk da Haka Mutumina karka Fara wannan gangancin nima da Haka na Fara kaga Daga irin wannan ana baka kana Karba Shikenan wlh baka da wani katabus nan gaba ma Gidan bazaka iya Tutiya Dashi ba Domin ko wani Abu ya Faru ita Hafsah zata iya Dukan kirji tace da kudin Mahaifinta acikin Ginin Gidanka alokacin kana da tacewa..?Abdullahi yace"Nifa banaki mganar bane Mutumina Abu Daya nakeso ka gane Surukaina Suna da Bambamci da irin Iyayen sakina Tunda na Auri Hafsah ban taba kamasu da Wani Abu na Rashin Dattako ba..Na Shaida su na kuma yaba da irin Tarbiyansu bance maka hakan Bazata Faru ba,Zata iya Faruwa mana Tunda dama mace ita yar Gori ce ko Shekara Dari kayi kana Bauta mata Rana Daya ka kuskure zata iya maka Gori ammh Abunda nake so ka gane Sakina da Hafsah suna da Bambamci kai tun Farko Daman kasiyama kanka ne abokina ni kuma Allah na gani ban Daukan ma Kaina ba Itama Hafsah ta sani Shiyasa take kiyayemin Kan wasu abubuwan.."
Nazifi yace"Ai shikenan Tunda kace haka..Zan Shigo zuwa gobe sai muje naga yanayin aikin Nima ya kamata nazo na Fara gina nawa na Gaskiya din nan.."Abdullahi yace"Gaskiya ya kamata ko Saboda in ka Tara iyali in kunxo zaria ba sai kun Sauka Gidan Baba ba kuna da gidanku..."Nazifi yayi karamin Tsaki Kafin yace"Kai Rabani kaji Mutumina ni yanzu Wlh bana ma Kaunar na Hada Zuru"a Da Sakina kwata kwata.."
Abdullahi ya Rike baki yana Fadin"Subhanallah miye zafi kuma..? Nazifi yace'Bama Abunda Baiyi zafi ba Mutumina kai kafi Kowa sanin Halin Danike Ciki..Nagaji da Hallayar sakina Nagaji da Fama da Ciwon mara kada Ciwon Rashin mace kusa Dani ya kasheni Tunda Sakina tafi karfina na yanke Shawaran Aure zan kara Insha Allahu.."
Abdullahi yace"Topha Aure kuma...? Anya baka Hada ma kanka zafi ba kuwa Abokina.."?Nazifi yace"Bawani zafi..kaji mutumina..Kadai ka bari na Shigo zamu Tattauna.."Daga haka sukayi sallama suka yanke Kiran Duk wani masoyin Abdullahi sai da yaji Labarin alherin da Mahaifin Hafsah Yayi mai Mama da Inna Abu kuwa Har Tudun wada suka je yima Daddy Godiya ya Dinga Fadan meya sukaje Kamar wasu kudi ne masu yawa Mama dai sai Godiya kawai sukeyi,Inna Abu tana ta saka albarka dasu ka koma gida tana bama Baba Wada Labari Tana Fadin kaga gidan karamci da Dattako mallam ba irin Surukan Shashashan Yaron nan ba.."
Baba wada yace"Ina zaki Hada Abu..? Ai Iyayen yarinyar nan mutanan kwarai ne Abdullahi yayi Dacen Surukan kwarai Allah dai ya saka da alheri ya bar zumunci.
Ranar Friday Nazifi ya Shigo Zaria Bayan sunje sun Duba wajen Ginin Nazifi ya kalli Abdullahi yana Fadin"Shege mutumina Gini fa yana ta Nisa.."Abdullahi yace"Kai dai bari so nake nan da Shekara mu Tare...Wanchan ya Fara mana kadan gashi ana ta Tara iyalai.."Yafada yana Sosa Sajensa Dariya Nazifi ya saka ya bashi Hannu suka Tafa suna Gefe Inda suke Tsaye Suna Bin ma"ikatan da Kallo Nazifi ya waiwaya yana Fadin"Katon Gida ne fa anan wajen Mutumina..Ammh naga kamar Flat biyu zaka yi ko..?
Abdullahi yace"Eh 2 Flat ne mana..Daya na Hausina da yara,Sai Dakin baki Daya kuma Nawa ne Megida.."Yafada yana Dariya Nazifi ya kallesa yana Fadin"Kodai...kodai Aure zaka kara ne Abokina.?
Abdullahi ya ware ido yana Fadin"Aure..? Rufamin Asiri ina Lallaba Rayuwa ni da matata da ya"yana..Ban ce maka bazan kara Aure ba Har Abada..ammh Bani da Ra"ayi kila in yana Cikim Kaddarata sai kaga na kara ammh gaskiya For now bani da wannam Ra"ayin Wannan sai kai mutumina.."Nazifi ya gyada kai yana Fadin"Hakan nda kyau....Kai in Baka da Dalilin kara Aure ni ina Dashi abaya a tsarina Mata Daya ta isheni Rayuwa ammh a yanzu dana zauna nayi Tunanin in nace zan Zauna akan Tsarina na Baya ni zan Cuci kaina gwara na Auro wacce zata kula dani ta kuma Sauken Nauyin Hakkin na Dake kanta ita kuma sakina Taje ta Cigaba da aikinta Bazan Hanata ba."Abdullahi ya gyada kai alaman gamsuwa yana Fadin"Hakane kaima ta wannan Bangaren kana da gaskiya..to ka samu yarinyar da kake so ne..?
Nazifi ya kada kai yana Fadin'"No..ni yanzu ba so nake nema yarinya mai Hankali wacce ta Fito Daga gidan Tarbiya wacce zata kula dani da Duka Hakkokina kuma in na saka mata Doka bazata iya Tsallakewa ba ballatana tayi Sa"insa dani kamar yadda sakina ke yi dani.."
Abdullahi yace"Tabbas Hakane..Ammh Duk da haka ya kamata ka Bincika ko wannan karon kuma a kaduna garin gwamma zaka lula ka samo mana wata ma"aikaciyar Gwannatin.."Yafada yana Yar Dariya Tabe Nazifi yayi yana wasa da key dim Motarsa yace"Umh..Allah ya Tsareni nayi da Farko ban ji Dadi ba..In Auran kudin ne sai dai na bawani Labarin in auran mace mai kyau ne da Dirin ciki da ilimin Duka naga Dahir Saboda haka yanzu karamar yarinya zan nema yar Sakandiri na aura in na Ga dama na barta ta Cigaba agidana in banga Dama ba kuma na Hanata gwara mu zauna Hakan zaifin kwamciyar Hankali Da Natsuwa akam Auran irin su Sakina.."
Abdullahi ya Dafa kafadan Nazifi yana Fadin"Toh mutumina ka Dudduba ko Cikin Dangi mana baza"a raasa irin wacce kake so ba.."Nazifi yace"Kai Rabani da wannan aikin...Ni ban san ma wasu yanmata Cikin Dangi ba ba tsayawa Tantancesu nake yi ba gwara na nema agari..kwanaki munyi mgana da Salisu Eng.yace min Yana da kannen mata Har guda Hudu naje na Duba Daya Daga Cikinsu in tayimin Shikenan.."
Abdullahi yace"Toh sai kaje ka Duban Din ba laifi suma gidansu