Advertisements
Chapter 27 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   27 / 48

78K to 81K   out of 143.7K words

damu Madam..Watarana ma ke da kanki zaki Cinyar dani ko..? Sunne kai Tayi Tana Dariya Saukowa yayi kasa ya tankwashe kafa ya Fara Cin Abinci Jefe yana Jefama Jidda Tambaya tana Bashi amsa kafin kace me suna Hira Sai gashi ya Tada Filet din Abinci Jidda ya kallah yana Fadin"Kai..Duk ni na Cinye wai..?

Dariya ta kama Jidda ta Saki Jiki Tanayi Shima yana Tayata,Tashi yayi ya koma Bisa katifar yasata matsar da kayan abinci,Kana yace ta Dawo ta zauna Tun Jidda na nokewa har Daga karshe ta saki Da Nazifi yana ta bata labarai Na makaranta da yadda Rayuwar makaranta yake da kuma na ma"aikatansu,Sai ga Jidda ta Zage suna ta Shan Hira Cikin Love,Basu ankara ba sukaji Kiran Sallar La"asar Nazifi ya saki Baki yana Duba agogon Fatan Dake hannunsa kafin yace"Baby La"sarfa nake gani.."Kai ta kauda Tana Mirmishi mikewa yayi a kasalance yana Fadin"Bari naje nayi sallah nazo na tafi..Naga alaman in na Biye miki yau kwanan zaria zan yi ko..?

Mikewa tayi Tana gyara gyalanta Tana Fadin"Nifa ba Ruwana.."Nazifi yace"Naji ba Ruwanki..Ni da Ruwana.."Yafada yana kallonta Tare suka Fito Yace Taje Cikin Gida ta Zubomai Ruwa abuta Haka taje Ta ga Mariya atsakar gida tana ganinta ta Shiga Mata Dariya Ita kuma Jidda tayi mata Banza,Ta dibi Ruwan ta kai mai nan kofar dakin Auwal din yayi alwalan tana Tsaye kana ya mika mata,ta koma Ciki Shi kuma ya wuce masallaci.

Koda ta koma Duk Dariyan Mariya Bata kulata ba Mama ce tace"Autana Ya tafi ne yayan naki.?Tana Tura baki tace"A"a sai ya Dawo Sallah.."Daga haka ta Shige Daki kana ta Fito itama alwalan tayi tazo tayi sallah Sai ga Su Jidda harda kara Shafa Hoda ana gyaran Fuska Mariya ta Shigo ta ganta sai tayi kamar bata ganta ba,Tana gyara zaman mayafinta taji karan wayarta Data barta nan kan gado tana Daukowa Taga Bakuwar lambace ta gane Shine tana Dagawa yace ta Fito yana Jiranta.

Data koma sallama kawai sukayi Ya Bata 10k,kana ya bata 2k ta kaima Mariya da Farko taki amsa sai da ya kalleta yana Fadin"Miye haka..? In Abdullahi yayi miki kyauta Haka kike mai..?

Jin haka yasa tasa Hannu Bibbiyu ta karba tana mai godiya Tasata yayi ta Rakashi yama Mama sallama ya bata 5k ta karba tanata sakamai albarka Jidda ma Ta ba Mariya nata itama tana Godiya Sallama sukayi da Mama ya Fito Har Kofar Dakin Auwal Jidda Ta rakashi kana yace ta koma Daganan in ya isa gida zai Kirata sai ga Jidda kamar zatayi Kuka da zai Tafi,Ta Dade tsaye nan bayan Tafiyarshi kafin ta koma Cikin Gida.


Yana Fita gida ya koma ya ma Su Baba wada Sallama ya basu Abunda zai basu ya wuce Wajen Biyar ya Dauki Hanyar Kaduna Zuciyarsa Cike da Farincikin samun Hadin kan Jidda.

Baba wada ne ya Shigo Da Daddare yama Mama Bayanin komai da kuma sanya Lokacin Auran Mama tayi ta saka albarka Koda Baba wada ya Kira Jidda ya gayamata bataji wani iri ba,Tunda Shi Nazifin ya gayamata bata dai Nuna ba,Baba wada yaFita ba Dadewa sai ga Kiran Nazifin Sai ga Su Jidda an haye gado ana kashe Murya mariya dai na gefe Tana ganin Abun mamaki da Auwal ya Dawo Falon Mama suka Dawo mariya na Radamai Abun mamakin Data gani yana cin Abinci yana Fadin"Hegiya jidda...Taga Salon manya.. Wanda ba irin na yara ba..Magulmaciya.."


Yafada yana Dariya,sai da Mama ta taka musu burki kana Suka yi Shuru ita ko uwar gayyar ma Bata sani ba Tana Cikin Daki Suna waya sai mai Shagwaba take yana Biye ma Tabaran Shagwabanta da kuma Yarintar,Dama yana komawa wanka kawai yayi ,sai sallah ya koma ya kwanta abinci kuma Tun Abincin dayaci azaria Cikinsa ya Cika koda ya Dawo wai Sakina Indomie ta Dafa don ta Raina ma kanta wayau Barinmata yayi ko Kallo ma bata ishesa ba Tunda ya Shige Cikin Dakinsa bata kara ganinsa ba Shiyasa ya samu dama Yana Biyema Kwailar Amaryansa Yana sata sakin jiki Dashi kuma ba laifi ta Fara sakin Jikin Dashi...



*Domin Biyan Kudin Karatu akan Littafin Ra"ayi ne ko Buri..? Zaku iya Tura kudin karatunku ₦200 Kachal akan wannan asusun bankin 0552179550...JAMILA UMAR GTB,Sai a turo Shedar Biya ta wannan layin wayar 09069067488,In kuma Katin Waya ne zaku iya Turowa ta wannan Layin 09027767783 kai Tsaye Bayan Mutum ya Dauki Hoton katin...Ga masu Bukatar VIP zasu Biya ₦500 ne ta Lambar asusun Dana bada a sama....! Mutanenmu na Niger kuma Zaku iya Tuntumbar My Jika aglan Nissa ta wannan Layin +22794131747....Sai kunzo Masoyana*



*Janaftyshakira...*
4/9/21, 1:58 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!


*026*




""Adaran Hira Tsakanin Nazifi da Jidda Tayi Tsawo sosai,Sai Biyema Tabaran Jidda yake da Shagwabarta saboda yana so ta saki Jiki Dashi Sosai Kuma ta Fara Sakin,Sai gashi Dukkansu Suna Jin Dadin Hirar.

Cikin Hirar ne Nazifi ke Tambayata wata mgana ne tace zata gayamai Ta waya..? Cikin Sangarta tasakomai mganar Cigaban karatunta,Domin har Ga Allah taji Acikin Ranta zata iya Auran Ya Nazifi mtsalanta Daya Shine karya Hanata Cigaba da karatunta Shine Tashin Hankalinta,Shi kuma yace mata ta bari sai anyi Auran in yaga Yadda Take bashi kulawa Sosai kuma Ta Dauki alkawarin komai bazai Sauya ba nadaga kulawar Datake bashi,Toh Zatayi Ilimi har sai da kanta Tace tagaji Jin haka yasa ta Dauki Murna Sosai Tana mai Godiya Basusan iya Lokacin da suka Dauka Suna waya ba Har mariya Datake Duba littafanta Ta Gaji Ta kwanta ta bar jidda sai Araund karfe 2pm na Dare sukayi Sallama kowa ya kwanta Ransa Cike da wani Annuri wanda ke Fitowa Daga kasan Ransu.

Washegari Kuwa Tun Wajen karfe 10am na safe sai ga Hajiya Lariya da Hajiya Sa"a ransu a matukar bace Alokacin gidan Babu Kowa Auwal ya Tafi makaranta mariya kuma Tatafi asibiti Mama ce kadai atsakar Gida Jidda Tana Falon Mama Tana Goge kayanta Suka Shigo ko karba Sannu da zuwan da Mama ke musu basu yi ba,Hajiya Sa"a ta Fara gaggayama Mama mgana Son Ranta Tana Fadin Don ba Ita Ta Haifi Jidda ba Shiyasa zata yarda akashe mata Rayuwa Tana yi Hajiya Lariya na Tayata,Jidda naji ta Fito da Sauri ganin Mama na kuka itama sai taFara kukan Tana Rokon su Hajiya sa"an kan suyi Shuru ammh ko Sauraranta ba wacce Tayi...

Iya Kokari Mama Tayi wajen Fahimtar Dasu,Ammh suka ki Fahimta Daga karshema Hajiya Sa"a tace Tazo Tafiya da yarta ne Babu kuma wanda ya isa yayi mata Aure,Tana ji Tana gani Hajiya Lariya taShiga Cikin Dakinsu Jidda ta Hado mata kayanta ta Fito Da Farko Jidda Taso Tayi Tirjiya ganin mama na Sharan kwallah ammh kuma Sai Mama tace ta Bisu ba komai Jidda naji nagani Hajiya Sa"a da Hajiya Lariya suka Tasata Har Cikin Mota sai Chika gari.

Suna Fita Mama ta koma Cikin Daki Taci kukanta Ta Share Hawayenta kana ta Dauki Waya ta Kira Abdullahi yana Office ta gayamai Abunda ya Faru Ransa matuka ya baci Cikin Fushi yace"Don Allah Ki Daina Bata Ranki abanza Mama..Nafi karfin na Tsaya ina Sa"insa da Wannan matar...Karki Damu Yadda ta Dauki Jidda da Hannunta Haka zata Dawo da ita kuma Mganar Auran jidda da Nazifi Wlh bazai Taba Tashi ba sai dai in Dayansu yau ya Fadi ya Mutu kafin Lokacin.."Mama ta Share Hawayenta Tana Fadin"Shikenan ammh baka ji irin manganganun Datake Fada bane..Tana ganin kamar wai don Jidda ba yata bace Shiyasa na yarda Za"ayi mata Aure.."

Mirmishin Takaichi Abdullahi yayi yana Fadin'Eh Ba ke kika Haifeta ba..Ammh kin mata Abunda ita Datake uwarta bata Mata ba ta, ita da ta Tsallake tatafi wayon Gantalinta shine yanzu Take da wani Bakin mgana..?karki Damu Mama...Kinfita iko da Jidda kuma da izinin Lahi sai kin Aurar da ita kuma Jidda yata ke gareki har gaban Abada.."Da wadanan kalaman na Abdullahi yasa Hankalin Mama ya kwanta Sukayi Sallama.

Sun gama waya ba Dadewa Sai ga Sallaman Baba wada Dashi da yara,da kwalayan minti da Biscuit,Sai goro Nan Mama ta tarbesu Cikin Fara"a Bayan sun gama gaisuwa ne ya gabatar mata kayan Saka Ranar Jidda sai kuma Sadakin Mama batayi mgana ba Ta Kira Abdullahi Ta gayamai sai yace Tabama Baba wadan Waya Dashi Sukayi mgana yace Baba wada ya Rike Sadakin a Hannunsa Tukunnah,Kwalayen Mintin kuma Da Biscuit din Yace abarma Mama Hakki ne Dama su Gani kuma su Raba ma wanda ya kamata yaji kuma ya sani.

Bai wani Jima ba ya mata Sallama ya Tafi Abdullahi shi da kanshi ya Kira Zannira yace in ta samu Dama gobe tazo Gida kan mganar Jidda,Tace insha Allahu zata zo ko bata kwana ba Haka ya Kira Subai ma ya gayamata,Goggo Habiba ma Sunyi mgana tana ta Saka albarka Itama ya Bukaci ganinta Gobe in ta samu Dama tace Insha Allahu Tana tafe,Umman Sadiq kuma Mama da kanta ta kirata ta gayamata,Tayi ta Murna tana Saka albarka Tana yabon kwakwayan Halayyar Nazifin Abunda kuma yasa Abdullahi bai Kira Ita Umman ba ya bari ne sai Su Mama sun Raba kayan Sa Ranar daman yana sa Ran zuwa gusai Weekend dinan Sai ya wuce mata Dashi yayi mata Bayanin komai.

*******

Da Abdullahi ya koma Gida Da Daddare yayi ma Hafsah Bayanin komai itama Tayi Fatan alheri da Safe kuma da zai Fita yace in Tagama Abunda take ta Shirya Taje Gidan Maman,Saboda Maman tace ya kamata Hafsah din Tazo Tunda Duka anzama Daya.

Lokacin Dayake gayamata Tana Tsaye Kofar Dakin tane Shi kuma yana Tsakar gida yana Duba Mashin Dinsa Dataki Tashi,Ya Dago kansa yana cema Hafsah.."Kinga fa inaga yau sai dai na Bar mashin din nan gida ta samu mtsala..Zan kira Auwal in ya Dawo makaranta Yazo ya Dauka yakai min wajen Bakanikan nan na kofarDoka.."..

Hafsah na Tsaye tace"Ayyah ba Jiya Lafiya lau ka Dawo da ita ba.."Kai Tsaye yacemata'Halin karfe Nasara kenan bashi da Tabbas.."Yafada Lokaci Daya yana Sakarmata Idanuwansa Lokaci Daya ya gano Ramar Datayi Shi bai sani ba Dayake baya samun Zama In ya Fita aiki Tun safe sai Dare ya Dawo a gajiye barci wani lokacin Har asabar kuma yana Shiga makaranta Lahadi ce Kadai Ranar Hutunsa Daya kamata ya Zauna agida kuma Baya zaman Saboda Hidimomi Da yawa.

Cikin Bacin Rai ya kara kafeta da Ido Yana Fadin"Hafsah..Wai meke Damunki ne..?kinga yadda kika Rame kuwa kin Lalace Don Allah miye haka... ? Zazzabin Daren ne har yanzu bai sauka ba ko yaya..?

Yafada Yana kallonta Cikin Bacin Rai,kai Hafsah ta Saukar Cikin Sanyin Jiki,Bataso ta Tadama Abdullahi Hankali ammh ita kanta taasan Bata da Lafiya Wuni Take kwance kasala Ciwon kai da Zazzabin Dare ammh bata bari ya sani ba,Gashi bata iya wani cin Abinci Shiyasa Duk Ta Rame ganin Taki mgana yasa kawai ya Kada kai yana Fadin"Dole gobe muje asibiti adubamin ke..Wlh ban yarda Dake ba baki da lafiya ammh baki san gayamin Duba Don Allah yadda kika Rame sai kwarmin ido..? Yafada yana Sakin karamin Tsaki Lokaci Daya yana Tura Mashinsa dinsa gefe key din ya mikamata yana Fadin"Auwal zai zo ya karba...In yazo ki Bashi 3k Cikin kudin Dake Hannunki.."

Da To ta karba Shi kuma ya Rataya Jakarsa ya Fice tana mai Fatan adawo lafiya Har ya Fice Tana Tsaye nan kofar Dakin,Kasala ce ta Lullubeta a kasalance Ta Juya ta koma Ciki,Kan gado ta koma ta kwanta komai batayi Tunanin kaudawa Don ma Allah ya Taimaketa su Amira Suna gidan Ammi Jiya Datazo suka Saka kukan sai Sun Bita tace abata kayan makarantansu Tatafi Dasu,Ita Kanta Ammin sai da Tambayeta ko Bata lafiya ne..? Tace lafiyanta lau ammh ai duk wanda yasan Hafsah in ya ganta sai ya gane tayi Rama Sosai.

Sai dataga 12pm na Rana ta wuce kana Dakyar ta iya Rarrafawa Tayi wanka ko Shara batayi ba Dama Safe Tea kadai Abdullahi ita batama Shan ba Fatan  tsaki Taji Tana Bukata kawai,Ammi ta Kira tace Don Allah ayi mata Tana Gidan Mama a aiko mata Dashi Tunda Ammi Taji Haka aranta tace Arina wannan Ramar naki Hafsah Toh Allah ya Raba lafiya kulle Gidan Tayi ta samu mai adaidaita yakai ta Gidan Mama Koda Ta isa Har Sun kariso Zannira da Subai" sai Goggo Habiba nan aka Shiga gaisawa suma Suna ta mganar Ramarta ammh sai tace bakomai.

Sai da sukayi sallar azahar kana Mama ta gabarar musu da kayan saka Ranar,Su zannira suna ta saka albarka Subai kuma Harda Guda Daman Tun zuwansu suna Tambayan Jidda mama ta gayamasu yarda akayi da kuma Abunda Abdullahi yace Suma basu Damu ba sukace Susan karya Take bazata iya Ja da ya Abdullahi ba,Raba komai sukayi su Diban ma Mama da Danginta sai nasu,Na goggo Habiba sai na Umman Sadiq,sai na Ammi Sauran kuma na makota ne,Sai na Hajiya Sa'a da ita kanta Jiddan Wanda Baba wada yabata Umarnin a Cire musu.

Direban Ammi Daya kawoma Hafsah Fate akabama Sakon Ammi ya kaimata Sakon na Zuwa Hannunta sai Kiranta Tana ta Fatan alheri da saka albarka,La"asar nayi goggo Habiba ta koma Bayan Ta Shiga Gidan Inna Abu sungaisa Zannira kuma sai gobe zata tafi,Subai ma Da Wuri tatafi Saboda yau mahmud din yake Dawowa Daga wata Tafiya Da yayi,Hafsah kuma tana kwance Tun Bayan Data idar da sallar la"aar ta kasa Tashi Tatafi gida tanan nan Har Auwal Ya Shogo bayan ya Huta yaci abinci ya karbi key din gidan Dana Mashin ya Tafi yaje ya Dauki Mashin din yakaita gyara Chan ya barta sai zuwa gobe da yammah za"a gama gyaran.

Abdullahi kuma Sai da ya Tashi Daga Office yabiyo Gidan Mama ya iske Hafsah kwance Mama ta Fara mai Fadan meyasa basu je asibiti ba Yana Latsa wayarsa yace"Mama kinsan Halin Hafsah kuwa daTaurin kai..? Wlh ta Rainani Har sai nawa zan mata magiya tayarda muje asibiti a gwadata aduba Aga meke damunta ammh bani da wannan kimar idanunta sai Abunda Taga Dama Shi zatayi ."Ya karishe Fada Cikin Bacin Rai Zannira ce ke bashi baki Tana ma Hafsah Fadan kamar wata karamar yarinya sai ta Rika zama da Ciwo Bata dai ce komai ba,Dakyar ta Rarrafa tayi sallar Isha"i Aka zubamata Tuwo ta Faraci ko Loma Biyar batayi ba Zuciyarta ta Fara Tashi sai amai nan ta Fita Waje tana Sheka shi Abdullahin na Tsaye gefenta Duk Hankalinsa ya Tashi ya kalli Mariya yana Fadin"Ke bani Ruwa.."Da Hanzari ta Diba takaimai ya kamata ya wanke mata Bakin yajata zuwa Dakin Mama tama kasa zama sai Kwanciya kawai Tayi ajikinsa hawaye na Bin gefen Idanuwanta Hankalin Abdullahi dasu Mama ya Tashi Mariya na Waje tana Share Inda Hafsah tayi aman Zannira ce tace Yakamata Atafi asibiti agani.

Mai Adaidaita Abdullahi ya saka Auwal ya samo musu Dashi da Mama Suka Tafi Asibitin ko Acikin Napen ma Kan Cinyar Abdullahi take ta lamgwabewa kamar wacce bata da Jini,Abdullahi Fada kawai yake yana Fadin"kinga Abunda nake gudu ko Mama..?Yanzu don Allah miye amfanin wannan..? Bayan ku iyayena ina da wacce ta Fiyemin ita ne..? Itace komai nawa..Ciwonki nawa ne Hafsah Domin sai da Bazakarki da lafiyarki nake iya Rawa Nima ammh kalli yadda kika maida ki..?Don Allah jibi fa Mama..?

Yake Fada kamar yayi kuka Asibitin Dan Fulani Dake kan Fage suka kaita Suna zuwa aka karbeta aka bata gado bayan an Dibi Jininta da Sauraran Gwaje Gwaje,Drip aka sakamata da Alluran Barci Tunda Jikinta ba kwari in kaga Abdullahi kamar Shine bai da Lafiya Rana Daya Duk ya Fada kamar bashi ba,Ko Abinci bai iya sakama Cikinsa ba Tun karin Safe,Zannira yakira ya Fadama an basu gado,sai gasu Ita da Auwal sun zo Asibitin Har zuwa Lokacin kuma Hafsah bata Tashi ba Suna aaibitin sai Wajen Sha Biyu Saura Suka Tafi Tare da Abdullahin ya wuce gida su kuma suka wuce gidan Mama Gida ya kwana Shi kadai Tun safe ya Kira Ammi ya gayamata Halin da ake Ciki,Shi kuma Wanka kawai yayi ya Hado mata kaya Dazata sauya sai Abun bukata irin kayan Tea da Sauransu Fulas din Ruwan zafi kuma Daga Gidan Mama an zo Dashi koda yaje asibitin ya iske Ammi da Daddy da Inna Abu sunzo,Ga kayan karyawa nan Daga gidan Mama sai Wanda su Ammi suka zo Dashi,gaisuwa sukayi Sukamai yamai Jiki Lokacin Hafsah na barci Bata tashi ba, Bai Jima ba ya wuce Wajen aiiki Daganan Tunda yayi kokarin ganin likita akace ya Hau ra sama Shi kuma yana Sauri ya makara yaasa bai Tssya ba yace sai ya Dawo.

Zuwa yammah asibitin ta Cika da Mutane Dayake suna Vip ne sai aka samu Wadatar waje,Saboda Ciwon Hafsah yasa Zannira bata koma Aranar ba,sai Washegari Subai ma Tazo,Akuma Ranar ne Likita yabama Abdullahi Takardan sakamakon gwajin Hafsah inda yamai albishir din Tana da Ciki har na Tsawon wata uku Sai Murna da Farimciki Abdullahi ba kunya yazo yana Fadama su Ammi da Mama suma sukayi ta Allah ya Raba lafiya Ammi tace Daman ita ta Zargi haka Tun Farko ganin kamar irin Ramar datayi Lokacin Cikin Amira.

Sai dai Hafsah ta Shafe kwana Hudu a asibiti kana aka Sallameta ta koma Gida,Saboda yanayin karfin Jikinta sai Ammi ta bata yar aikinta Guda Daya Harira tazo Tana kula da ita,Su Amira kuma Suna wajenta,Kwana Biyu da Sallamota sai ga Umman Sadiq tazo ta Dubata kwananta Daya ta Juya Bayan Mama ta bata kayan saka Ranar Jidda Tayi ta Fatan alheri.

Sai da Hafsah ta kwashe Wajen sati Biyu kafin ta gyagice ammh fa Har yanzu Jikin ba karfi bata iya wani aiki mai karfi wannan Dalilin ne yasa Abdullahi ya kara Rokon Ammi Data bar musu Harira ko Wata Biyu Tayi Zuwa Lokacin da Cikin Hafsah zai yi kwari Ammi ta amince,Sosai Hafsah ta samu Hutu da Jin Dadi ga Abdullahi na kula da ita yana ji kamar kan wannan Cikin ne zai Taba Haihuwa Hatta da Nazifi yazo Dubata Dayazo ne ma Tana Daga Cikin Daki Taji Nazifin nabama Abdullahin Labarin suna Waya da Jidda Sosai Domin ma yace mata zai je Chan Gidan mamar nata kuma bata musa ba Duk da Tanuna Tsoron Ita Hajiya Sa"an Abdullahi yayi Tsaki yana Fadin"Karka Taka kaje ko"ina..Na bari ne Hankalina ya kwanta ne..Kwananan Jidda zata Dawo ko Taki ko taso.."

Da haka Suka Cigaba da Tattaunawa mganar kafin su Fita Tare Abdullahin bai Dawo gidan ba Sai Dare.


******

Bangaran Jidda kuwa Ta Shiga Takura Sosai Domin Hajiya Sa"a tayi Tsaye so take Ta Hana wannan Auran

27 / 48