Advertisements
Chapter 36 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   36 / 48

105K to 108K   out of 143.7K words

mai Wani Abu ba,Shi kuma abangaransa Baya Fahimtar Komai.

Siyayyah kayan Haihuwa kuma Anty Hadiza ta Turama kudin Tace ta Siyamata Harda Turaman Atamfa da less,adinka mata Daga Chan ta aiko mata Dashi Abdullahi ma ta bama kudin ya Turama Anty Hadizan sai Lokacin Take gayamai Kudin da Daddy ya bata ya saka albarka kuma ko Afuska bai Nuna Wani Abu Itama sai ta Share kawai ta ijiye kudin Dama akwai Abubuwan Datake son Siya Bayan Allah ya Sauketa Lafiya.

*****

*Bayan Wata Daya..*

Alokacin da Bikin Abdullahi da Barkat ya Rage Saura Kwana Goma Sha Hudu kenan ma"ana Sati Biyu yau asabaar akuma yau Din ne za"aje kai kayan Auran Abdullahi Zuwa Gidansu Barkat din.

Azuwa wannan Lokacin Tuni Abdullahi ya kamallah Gyaran Gidan Dakin Barkat an kamallah komai an Fitar da Bayi da komai anyi Fenti ya sauya mata Kofa Bedroom din ma Ya sanya mata Kofa gidan Gabadaya ya Sake mai Sabon Fenti mai Tsada,,Kicthen ma Ya kara Gyarashi an Saka musu Sabon Cabinet,Kayan Hafsah gefe ta mai Dashi Ta barma Barkat kusan Rabi da kwatan Kitchen din Har ma Abdullahi yayi mgana tace kar ya Damu Su da ba zama zasuyi ba,Lokaci Kadan zasu koma Sabon Gidansu yadai kyaleta ne kawai Saboda Baya son matsa mata ganin Halin Data ke Ciki na Cikinta ya Shiga Wata Tara ma"ana Watan Haihuwansa kenan Duk Ta Kumbura ta zama a lallaba.

Iyayen Barkat din da kanwarta Bahiya sunzo sun Duba Dakin nata Ranar Hafsah ma tana Ciki batama Son da Zuwansu ba Sai da suka kariso kana Abdullahi ya Kirata ya gayamata Dakinta ta Fara Saukesu ta kawo musu Ruwa suna ma cewa ta barshi Ganin Halin Data ke Ciki,Taki basu Jima Sukace sunzo Duba Daki ne Ta Shiga Ciki Ta Dauko Musu makulli Ta mika musu Suka Fita Basu Wani Jima ba Suka Leko suka mata Sallama Tare da Bata makulli ta amsa Tana musu Fatan Zuwa Gida Lafiya Domin batayi Girki ba kwance Take Tana Fama da kanta.

Bangaran Ita Barkat din kuwa da Hafsah basu Taba ganin Juna ba Sai dai ita Barkat din Tataba ganin Hafsah a hoto a wayar Abdullahi ammh ita Hafsah ko kusa wannan bai Dameta ba,Su Amira kuwa ai sun zama yan Gidan Anty Domin yasha kai su Wajenta su mata Wuni Ranar da basu da makaranta,sai yammah yake zuwa ya Dawo Dasu da Tsaraba Niki Niki Suzo Suyita Murna Suna Labarin Anty ta basu kaza Anty tace musu kaza Mommy Anty BARKAT na gaisheki Sai dai kawai tayi yake toh me Zatace..? Gefe kawai ta koma ta zama yar kallo,Dama Barkat din Shiryen Shiryen Fara Jarabawa Suke Bayan Bikin da kwana Goma Zasu Fara Jarabawar first Semester.

Koda aka kawo kayan Akwatunan Gidan Mama Zannira ta Saukesu Biyar na Barkat guda Daya kuma na Hafsah ne,Sai da Abdullahi yazo ya gani kana yace Mama su Shirya wadanda zasu je su kai kayan na Hafsah kuma ya Dauka yakai mata ta Karba Tayi Godiya yace mata ta Shirya yakai ta Gidan Mama Taga kayan Barkat Din sai ta Nuna mai Bata iya Zuwa Batajin Dadin Lallabata yake Shiyasa ya kyaleta da kuma Hankalinsa yanzu yana kan Auransa kawai.

Mama ta Kira Ammi da kanta ta Fadamata Ammi kuma ta mata alkawarin zata zo a kai kayan da Ita Umman Sadiq tace sai Biki Zata zo Subai ma da Zannira ta Kirata cewa tayi Wlh baza taje ba Tana Taya Kawarta Hafsah kishi Da Abdullahi yaji labari Wani Dogon Tsaki yaja yace Su kyaleta Dama Baya gayyartata,Hatta da Nazifi wannan karon Baya goyon Bayan Abdullahi kan Wannan Auran Koda yaushe sukayi Waya sai yayi mai Complain din komai nashi ya Tsaya Saboda wannan Auran Shi bakomai ya Rasa ba Wajen Matarsa Hafsah ba,Gashi yanzu Ginin nashi ya Tsaya Shagon ma yanzu ba wasu kaya Duk Sun kare ba kudin Sarowa ga Hidiman yau da kullum albashin ma ba wani mai yawa bane Tunda Duk Wata Suna Cire Bashinsu 10%,In Nazifi yama Abdullahi wannan mganar basu Rabuwa Lafiya sai Abdullahi ya Fara Fada Shi kuma ya Fita Batunshi Domin Shi yanzu ya samu kwanciyar Hankali Sosai Jidda Taci Jamb Dinta yana ta ma kokarin Sama mata addmission a Kasu ne ta samu Gurbin karatu,Bangaran Sakina kuwa Tana ganin kwarewar Ruwan Bulla agidan Nazifi Alhaji Badamasi yayi Fada Sosai Lokacin da Sakina ta gayamai ta koma Gidan Mijinta Hajiyarsu Kuwa Takaichi kamar ya kasheta ammh Sakina Ta Nuna tana son Mijinta bazata iya Rabuwa Dashi ba,Dole suka saka mata ido Abaya sai Tayi Sati Uku bata zo kaduna ba ammh Ganin kamar Jidda Tafi ta Morewa sai ta koma tanayin kwana Goma Zuwa Sha Biyu Tana Dawowa Domin Tana Chan ne ammh Gabadaya Hankalinta na kan Nazifin Da Jidda na ganin yadda Jidda ta mallake Nazifin Karamar yarinya da ita ta iya Makirci da Yadda zata maida Namiji ya Dawo karkashinta.

Ranar da za"a kai kayan Abdullahi Har da Hajiya Sa"a tazo Mama ta Kirata Domin Tun Bayan Auran Jidda komai ya Daidaita Suna Mutumci yanzu Sosai,Ammi ma tazo sai Inna Abu da Zannira sai Mariya Data yi Rantsuwan sai Taje su kenan suka Tafi sai Inna Talatu,Amota Biyu Sukayi kayan Amotar Hajiya Sa"a aka saka Ta Dauki su Inna Talatu da Inna Abu da Mariya ita kuma Zannira suka Shiga Motar Ammi Suka Tafi Sai da suka je Gidan kana Ammi ma Taga ai Tasan Gidan Marigayi Alhaji Shehu basu da Nisa Sosai tama san Hajiya Amina Domin sun yi zaman Zuwa Islamiya ajinsu Daya Tun Lokacin Su Hafsah Suna yara.

Am musu Tarba na Girma da karammawa Matan wan Babansu Barkat din Da Makota suka karbi kayan Suna ta saka albarka Ruwa kawai suka Sha Sauran kayan Toye Toyen a Mota aka saka musu Ammi Sun gaisa da Hajiya Amina Sosai Shine har take Tambayanta Dama Abdullahi Dan'uwansu ne Dariya kawai Ammi Tayi Inna Abu ce tace ai Mahaifiyar Matarsace kamar Uwa Take garesa Kowa yayi mamaki Sosai nan kuma suka kara Tabbatar da an zama Daya Mariya kuwa sai kwakwa take Taga Amarya bata ganta ba taga Dai Bahiya da Bahijjat,Aina tana Sch,Barkat kuma Bata Gidan Tana Makota Saboda kunya Duk Da Karatun ma Jarabawarta Take tayi Ganin Lokaci Nata karatowa

Da zasu Tafi 10k suka basu Tukwaici Da Farko sunki Karba Sai da Suka ga basu Ji Dadi ba kana suka Karba Sun Koma Gidan Mama Suna Tadin Kirkin Gidansu Barkat din,Zannira dai sai Washegari zata koma Inna Abu kuma da inna Talatu ana Dawowa suka Nufi Gida su aka bama ma 10k din Ammi da Hajiya Sa"a sunfi karfin kudin sukace bazasu karba ba itama Hajiya Sa"a ta Jima nan Gidan Mama Suna Hira da Ammi Nan ma Tayi mangariba kana ta koma Gida Ammi kuwa tana nan Har Dare har sai da Abdullahi yazo ya isketa Bayan sungaisa yayi ta mata Godiya tace bakomai da Zata tafi sai Gobe Abdullahi yazo Gida ya Sameta yace mata Insha Allahu.

Sai bayan da yan kawo kaya suka Tafi ne Barkat ta Dawo Gidan Bata ga kayan ba sai Chan Dare bayan Kowa ya watse sai isu isu Hakika kayan Sunyi Daidai Ruwa Daidai Kurji,Bayan tagama ganin kayan Ta Turama Abdullahi Sakon Godiya da Jinjina yaji Dadi Sosai acikin Ranshi yana Tunanin in ya samu kudi zai karama Barkat din kaya Har ga Allah Daya na Cikin Wadata sosai sai ta samu Abunda ma yafi Haka.

Shiryen Shiryen Biki Duka ya kamkama Ammh yafi Yawa ta Bangaran Gidansu Barkat din,Domin Hafsah dai Ta kanta Take yi Tana Jiran Haihuwa ne yau ko Gobe Gidan Mama kuwa Subai ce Daman bai Son Bidi"a abiki To wannan karan Tana Taya kawarta Kishi ko Gidan Maman batazo ba Da Zannira tayi mganar Fitar da anko Subai tace Wlh bazasu yi wani anko ba Mariyama tace Wlh bawani ankon da zasuyi Dole ta bar Mganar,Sai dai Tana Kiran Hafsah awaya suna mgana Sosai tana kara kwantar mata da Hankali Tazo Gidan Hafsah Taga kayan da Abdullahi yayi mata ta Dauki Wasu ta kai mata Dinki sauran Ta bar mata Kudin Hannunta kuma tace ta adana In Ta Hauhj Lokacin zasu koma Sabon Gidansu sai ta kara Wani Abun Hafsah tayi na"am da Shawaran Subai Sosai Domin Ita Din kawace ta Amana agareta.

Ana Saura Sati Daya Bikin Dangin Barkat Suka zo suka mata Jeren kayanta Masha Allah itama Taji kaya Sosai,sai wanda ya gani,Sun Jera komai yadda ya kamata Kitchen din ma sun Sun Jerama Barkat din Abunda ya Samu Domin Kicthen din yayi musu kadan gaskiya,Basu Damu ba Sanin Daman Barkat din ta Fada musu zamansu anan na wani Lokaci ne da zarar ya kamallah Gininsa zasu koma Sabon Gidansu a Gra Shiyasa ma Sauran kayan Barkat din Duk ba"a zo Dashi ba Fridge kadai aka Zo mata dashi Sauran gas dinta da Sauran kayan amfani agida aka barsu sai Zasu koma Chan Gida sai tayi mgana akai mata kayanta chan cikin Sakewa Ranar da suka zo Dankin ma Hafsah Bata nan Tatafi awo Subai ce da Mariya Ya Kira suka zo Agidan Mama akayi musu Abincin Dama yayi musu Bayanin Hafsah bata nan Tatafi awo ammh haka Suka Dinga Surutun wai kishi ne yasa Ta bar Gidan Hafsah kuwa Daga Asibiti Gida ta wuce taje ta kwanta Sai Da Ammi ta matsa mata ne ta koma Gida Lokacin yan Jeren ma sun Tafi Subai ma ta koma Gida Mariya ta iske agidan da yara sai da ta Dawo da Abdullahi ya Shigo Gidan ya maidata Gida ita ko Dakin ma bata kallah ba Tunda ma Sun kulle Abunsu sun Tafi da makullinsu Abdullahi Dai na da wani Ammh bata Damu dama tace zata ga Dakin ba Shima bai Damu Daya ce mata komai ba ammh yaso ya mata Masifan kan gidan Ammin Data Biya ammh ganin ta Hade Rai yasa Dole yayi Shuru da bakinsa.

Ammi da Daddy 100k suka bama Abdullahi suka ce ya Kara ba yawa yaji kamar ya saka kuka Yaji kunya Sosai,Kuma ya kara Tabbatarma kansa Iyayen Hafsah Dabam ne,Mutane ne masu Dattako da Sanin ya kamata Yazo Gida yana Gayama Hafsah yace Tatayashi Godiya Wajensu Daddy Ta Kira ta musu Godiya Daddy yayi Ta lallashinta Ta Tabbatarmai da bata tada Hankalinta ba,Haka yaje ya sanar ma Dasu Mama,Mama ma ta Kira Ammi Tana ta Godiya Har Umman Sadiq sai da Ya gayamawa itama ta Kira Ammi Tana mata Godiya acikin Ranta Tana Tunanin Abdullahi ya bata kunya na yarda iyayen yarinyar nan suka Daukesa ammh Sai da yayi Sanadiyar Damuwar yar"su.

Da su yayi amfani ya Siya kayan Abincin da za"ayi Hidima Na Gidan Mama da gidanshi 30k kuma ya bama Barkat na Walima da Hidimar Biki,Sauran kuma ya bama Auwal ya Dan Saro kaya Haka,kada Shagon ya Durkishe ba kayaTunda katinan Biki da kayan da zai Saka Nazifi yaji da Barayin,Umman Sadiq ana Saura kwana Biyar Biki ta iso Goggo Habiba kuma Ana Saura kwana Hudu Tazo ta Buhun Masara Dana gero Harda na Shinkafa da Sauran su kuka da kayan kauye irin su kayan Miya da Sauransu Umman Sadiq kuma Shinkafa kawai tazo Dashi da kudi Ta Damkama Abdullahi Zannira kuma ita Tace zataji da Sauran Cefenan Gida da Abubuwan da za"a Bukata Subai kuwa bama wanda ya ganta agidan Mama tana Gidan Hafsah.

Sai ana Gobe Bikin Jidda ta iso,Sakina kuma Dataji labari Dadi Taji Domin Tunda akayi mata Kishiya toh ayi ma Uban kowa ma ta kuma yi alkawarin sai ta Kira Hafsah tayi mata Murna Taga ya zataji, Zannira ma aranar tazo Saboda Uwar Mijinta ba lafiya ammh Taji Sauki Shiyasa tayi Tsaiko Ya"yan Goggo Habiba su Jamila ma Duk sun iso,ammh Suna zuwa Gidan Hafsah suka yada Zango Har da Madina Tazo Daga malunfashi da kannen Nazifi Duka Suna Gidan Hafsah Dasu Mariya,Zannira ce kadai agidan Mama Tana Taimakawa da wasu abubuwan Tunda Itama Maman zatayi Taron nata.

Gidan Abdullahi kuma Su Subai ne sai Anty Hadiza da tazo,Ita da yan Biyunta,sai Jidda dasu Jamila da Mariya Suke ta Bidirinsu Domin Su Debema Hafsah kewa kuma Ba laifi sun Debemata kwarai Domin sai da Bikin yazo Gabda kana Taji Damuwarta ta karu Nazifi Tare da Jidda suka zo Suna Chan Tare da Abdullahi agidanshi Tunda nan din ya Cika,Su Amira da su Muhseena suna Tsakar Gida suna ta Wasa bawani Taro ne Hafsah Zatayi ba isu isu ne sai makota kuma da ba"a rasa ba.

*****

Ranar asabar Daya ga Watan Goma Shekara ta Dubu Biyu da Ashirin da Misalin karfe 11am na Safe Duban Mutane suka Shaida Daurin Auran Barkat Shehu da angonta Abdullahi Usman Direba akan Sadaki mafi Dataja lakadan ba ajalan ba,Daurin Auran da"aka Daurashi a Sabon Gari Gidan Wan Babansu kenan

Daurin Auran Daya masu Hallatar manyan Mutane kama Daga abokan karatun Abdullahi Abokan aikinsa da kuma abokansu Tun na yara Shida Nazifi,Ga Jama"ar Salisu  Data Baba wada mijin Goggo Habiba ma yana Wajen Daddy ma yaje Daurin Auran Auwal da Tawagan Abokansa Mijin Zannira Da Mijin Subai ma sun Hallaci Daurin Auran Hatta da yan Gidansu Hajiya Sa"a Suma sun Je Daurin Auran Gaskiya Ya samu Jama"a sosai Wanda zai iya Misalantashi dana Farkonsa,Bakin Abdullahi baya Rufuwa Saboda Farincikina,Dashi Da Nazifi Suna Sanye ne da kaya iri Daya Farar Shadda Riga da wando Har da Babbam Riga Wacce Taji aiki da Hular zanna Bukar akansu Abunda sai Wanda yagani., ana Gama Daura Aura ya Fito da Wayarsa ya Turama Barkat Sako da Cewa

_Alhamdulillah Now u are Officcialy Mrs Abdullahi Usman Direba..Allah ya bamu zaman lafiya.._

Barkat na Cikin kawayenta da yan"uwanta agidan da suke zama Ba ita ta Bude Sakon ba wata kawartace Nusi abokiyar karatunta Ta Bude Sakon ta karanta afili nan da nan suka saka mata Ihu da Cewa,itama sai Hawayen Farinciki Tana Hamdala aranta da yau Allah ya Cikamata Burinta ta zama Matar Abdullahi Barkat tasha Kwalliya Sosai Tayi kyau ainun Sunyi anko na Less mai kyau Sunsha kyau Su Bahiya Suna ta Rawan Jiki abu nasu mganin a kwabesu Aina dai Ita kadai ce Tayi Missing Tana makaranta kuma Babu Halin Tataho Tana Chan Tana Cizan yatsa.

Su Abdullahi kuma Daga Wajen Daurin Aure Shagalinku sukaje sukayi Reception Wanda Nazifi da wasu abokansu suka Dauki Nauyinsa kuma na kowa da kowa ne Harda iyaye irinsu Baba Wada dasu Daddy, Suma Sunje sunci sun Sha kuma Suna Addu"an Allah yabama Ma"aurata zaman lafiya Daganan dai iyayan suka kama kansu Abokan ango da ango kuma suka Nufi Gidan iyayen amarya suka Shiga Har Ciki Suka gaisa ana ta Nuna Ango kowa kagani yana Son Barka ne Daganan Gidan dasu Barkat ke zama Suka Nufa chan aka je akayi ta Hotuna kala Abokan ango na ta ma Abdullahi Shakiyanci Suna Fadin ya More Duka Matansa ya Hada yara kanana yana Morewarsa Baya mgana Sai dai Mirmishi kadai Domin yau da Barkat ta Tabbata matarsa yana jinsa kamar yana yawo a gajimare ne sai Wajen 3pm da wani Abu suka Baro Wajen Bayan su Nazifi sun Jadaddama Kawayen Amarya cewa karfe 5pm na yammah zasu zo Daukan Amarya Daganan Gidan Mama suka Nufa,Chan suka Iske su Ammi dasu Goggo Habiba Su Hajiya Sa"a da Hajiya lariya dasu Inna Abu Suma sunci kwalliyarsu Gidan Cike da mutane makota da yan"uwan Har Cikin Gidan suka Shiga Abdullahi Daya Ga baiga Zannira ba ya Tambayeta Mama tace Dazu Tatafi Gidansa Sai Lokacin ya Tuna yau tun Bayan Wayar da Sukayi da Hafsah bai kara Kiranta ba Sabewa yayi zuwa Waje ya barsu Nazifi na gaisawa da su Umman Sadiq ya Fita ya Kebe kanshi ya lalubo lambar Hafsah ya Kirata ammh Har Tagama Ringing bata Daga ba Kira Wajen Hudu yayi mata Bata Daga ba Sai Ranshi ya baci ya maida akalan Kiran nashi ga Zannira Bayan ta Daga sun gaisa tana mai Murnan an Daura aure lafiya Ya katseta da Tambayan Hafsah tace bari ta Duba mata Suna Ciki ita da su Subai koda Ta Shiga ta isketa tana Sallah ne sai ta gayamai batare Dayace komai ba ya Datse Kiran yana Sauke ajiyar Zuciya.

Bangaran Hafsah kuwa Wacce Taci Kwalliyarta Cikin Wata Super mai Tsada Cikin Wanda Ammi ta Dinko mata ne na Fitar Biki Shiyasa ko kayan Abdullahi na Fadar Kishiya bata Bi ba Tunda ta samu kaya Hatta Anty Hadiza tayo musu anko Atamfa da Leshi kala Biyu,Dinkin Doguwar Riga tayi Saboda Cikinta Su Amira kuwa Yan kanti Abdullahin ya Siya musu bama Shi suka Saka ba Shaddan da Subai ta Dinka musu Hardasu Muhusina suka Sanya,Tun Bayan Da Gari ya waye Hafsah gadai Ta nan ne su Mariya da su Jidda Manyan mata suna Waje suna Girki Suna Hiran Yawancin Hiran Sakina ne Jidda na Bada labari Subai na Dariya jin wai Sakina na Fadan wai Nazifi ya Daina kula da al"amarinta Hafsah na Ciki Tana jinsu Domin acikin Kirjinta Wani Nauyi Take ji Subai ne Data Shigo ta Fahimci Halin Data ke Ciki ta Dinga Lallashinta ta matsa mata ta Shiga tayi Wanka ta mata kwalliya da Safe Wani Less ta saka ammai Dinkin Buba suka zo Suna ta Daukanta hotuna Domin dai su Debemata Kewa Anty Hadiza kuwa kallon kanwarta kawai take Tsausayinta na kama Su suka Taimaka Wajen Rage mata Damuwa ammh Lokacin Da Ta tabbatar da an Daura Aure Sai da Tayi kuka Kishi ya Taso mata Tailet ta Shige tayi mai isarta kana ta Fito ba wanda yace mata meyasa tayi kuka Domim Kuka ai Dole ne,Su dai sun gama abinci sun kwashe a kololi kowacce Taci wanka sun koma gefe makota dai sun Shisshigo Allah Sanya alheri.

Lokacin da Abdullahi ke Kiran Wayar Hafsah Tana Hannunta kuma Tana gani Taki Dagawa Kuka ya kawo mata Wato sai yanzu ma ya Tuna da ita Tailet ta Shige Tasha kukanta kana Ta Dauro alwala ta Fito ta Tada Sallar la"asar ganin Lokaci yayi,kuma Data idar Zannira ta gayamata sai tace wayar bata Hannunta bata gani ba,Sai kawai ta Share Zencen.

Hudu da Rabi Abdullahi ya Kira Zannira yace Yanzu su Nazifi zasu Dauko Amarya,Tace Shikenan Shi ya Kira Mama ya gayamata yace Gidanta za"a Fara kawota Daganan sai su kaita Chan nan ma ta sanar ma su Ammi Suka Tashi suka Fara Shirin Tarban Amarya Tun Hudu da Rabin Su Nazifi da Sauran abokan suka Tafi Chan

36 / 48