Advertisements
Chapter 39 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   39 / 48

114K to 117K   out of 143.7K words

na ganka ballatana Har kamin Tausan..? Kaida Tunda aka Fara wannan Hidiman baka da lokacinka kanka ma Ballatana na ya"yanka yanzu ma na san Amaryanka na Chan na Jiranka.."Rufe bakinta Keda Wuya Wayarsa ta Dauki kara ya Dakata ya Ciro ta a aljihu ya Duba Ajiyar Zuciya ya Sauke ganin Barkat ne Kallonsa Hafsah Tayi kafin tace"Ita ce ko..? Karka Damu Tashi kaje Allah tashemu lafiya..'

Tafada tana Kokarin Tashi Da Sauri ya mike ya Taimaka mata Ta mike Tsaye tana Cije baki Shi kuma yana ta mata Sannu,Kamata yayi Ya kaita Har kan Gado ya kwantar da ita Godiya tamai kawai ta koma ta kwanta Tana Sauke Numfashi,Kallonta yayi yana Fadin"Kinci Abinci kuwa..?ko basuyi Girki bane kafin su Tafi..?

Hafsah tace"Sunyi mana Subai ta Dafa Da Rana Akwai Sauransa Shiyasa ba"ayi wani Girki ba.."Kai kawai ya gyada yana Fadin"Shikenan mu kwana lafiya..in kinji Jikinki ba Dadi Juz Call me kinji ko..? Da kai ta gyadamai alamun To,Dukawa yayi ya Sumbaci goshinta kafin ya Fice bayan ya kashe mata Wutar Dakin,Falo ya koma ya Tattara kayan su Cincin din da kular ya kai Dakinsu Amira suma ya Dubasu yayi musu addu"an barci ya Rage musu Fankan Dakin kafin ya Fito Sai da ya kashe Wutar Falon kofar kuma ya Turota ya Rufe kawai Tunda Hafsah ta Riga ta kwanta.

Dakin Barkat ya Shiga ya isketa tayi Fushi Harda kuka yana Shiga Bedroom din tataso ta Rumgumeshi Tana mai kukan Shagwaba wai ya tafi ya barta Riketa yayi Yana Shafa bayanta zuwa kugunta alamun Lallashi,Dagowa tayi Tana Fadin"Shine ka tafi ka barni ni kadai ko .? Alhalin ma naji Shigowarka Nayi ta Jiranka ban ga Shigowarka nan ba.."

Hannunta yaja zuwa kan gado,Suka zauna Kumatunta ya Tallaba yana Share mata Hawaye, Cikin Sigar lallashi yake Fadin"Am so Sorry Amaryata,Kinsan na Fita Nazifi na Jirana Munje gidanku mun gaida Surukai Daganan kuma muka Biya wani Waje,kafin Mu Dawo Gidan Mama kinga Goggo Tana nan bata Tafi ba sai gobe,Umma ma Tana nan fa,Kuma Nazifi gobe zai koma kaduna mgana na Tsaya mukayi mai muhimmanci Domin ba lalle bane goben kafin ya Tafi mu Hadu,Mganar kuma na Shigo Gida Tun dazu Bai kamata ki Damu ba, kinsan Halin Hafsah take Ciki Tsohon Ciki Gareta yanzu ke kinga nayi adalci na Shigo Gidan ban leka Dakin ta na ganta ba..? Kina ganin in kece Zakiji Dadi..?

Yafada yana kafeta da ido Saurin Maida kanta tayi Saman Kirjinsa Tana Fadin"Ni ba Haka nake nufi ba..Kawai na Damu ne kabarni ni kadai gasu Bahiya Tun Dazu,Suka Tafi suka barni ni kadai..'Rumgumeta yayi yana Fadin"Kiyi Hakuri gobe muna Tare...Ba inda zani na Dauki Hutu Sati Daya zamuyu sai kin gaji Dani.."Kara kamkameshi Tayi Tana Fadin bazata Ta taba gajiya Dashi ba Sun Dade suna gayama Juna kalaman Soyayyah,Kafin ya Tambayeta taci Abinci tace taci Wanda aka kawomata Ruwan Wanka yace ta Hadamai zai yi wanka tatashi ta Hadamai ya Shiga wanka Bayan ya Fito ya saka Jallabiya Dare yayi komawa kawai sukayi suka kwanta Suna kamkame da juna Hira Suke Cikin Shauki da Soyayyah,Bai mata komai ba Sanin Tana da Rauni ammh Ta bashi Hadin kai yayi yadda yake so da Jikinta Itama ta Nuna mai Kokarinta Wajen maidamai martani kafin su Nade Cikin Jikin Juna Barci mai Dadi Ya kwashesu suna kamkame da juna.

******

Washegari Tun Safe Hafsah tatashi Hakanan Tayi ma su Amira Wanka tayi musu Shirin Zuwa makaranta,Ta Fita Zuwa Kitchen ta Dafa musu Ruwan zafi,Ta Soya musu Buredi Mai kwai Dashi Suka karya Dakin Barkat din ma yana Rufe ko Motsin Abdullahi bata ji ba ganin yara na neman makara yasa Ta Kira Auwal a waya tace yazo yakai su Amira makaranta yace gashinan zuwa ba Dadewa sai gashi yazo Shi ya Daukesu Zuwa makaranta.

Dakyar ta Daddafa Ta Gyara Dakunanta Lokacin yunusa yazo yayi mata wanke wanke da Sharan Tsakar gida ya Zubar da Bola ya Zuba mata Ruwa,Tabashi Abun karyawansa ya Tafi Nasu Abdullahi kuma ta Zuba musu Cikin Wata karamar kula Ruwan zafi kuma Ta saka musu Cikin karamin Falas Ita Ragowar Shinkafan Jiya ta Dumama ta koma Daki Taci ta koshi tasha Ruwa,waya ta Dauka ta Kira Subai sukayi mgana tayi mata Bangajiyan Biki Daganan kuma ta Kira Ammi suka gaisa nan take Gayamata Anty Hadizan Yanzu zata koma ga Direban Mijinta nan yazo Daukanta nan aka bata ita Sukayi mgana tace kafin Tatafi Zata biyo Suyi Sallama da Hafsah Din Tace tana Jiranta kana Sukayi Sallama.

Basu Jima da gama waya ba Sai ga Anty Hadizan tazo bata jima ba Sukayi sallama Tatafi bayan Tayi ma Hafsah Nasihan Hakuri da kuma bata Shawaran in Taji Wani Ciwo ta Kira Ammi ko Mama ta Fadamata Tunda dai Uban gayyar yanzu ta Amarya yake Har ma Anty hadizan Tatafi Bai sani ba Kofar Dakin Barkat din ma arufe yake alamun basu Tashi ba ko Sun Tashi ma basu Dai Fito ba.

Abdullahi bai Fito Daga Dakin Barkat ba sai Wajen Sha Biyu Saura na rana,Ya shiga Dakin Hafsah yana ta kamshin Turare Cikin Shigar Wata Shadda mai kalan Sararin Samaniya,Hafsah na Ciki kwance Ya shigo ganinta kwance yasa Ya zauna Gefen gadon yana Fadin"Lafiya kike kwance..?

Numfashi Taja tana Fadin"Lafiya kalau..Nadai kwanta ne kawai.."Kai ya Ggyada yana Taba kafanta Cikin kulawa yake cemata"kinga Kafar ta sauka ko..? Batayi mgana ba illah ido kawai Data zuramai,Yadauki Lokaci mai Tsawo yana matsa mata kafan kafin ya Dago yana Fadin"Ina su Amira ne..? Waya kaisu makaranta kinsan Wlh sam na Manta ban kira mai mashin dinsu yazo ya kaisu ba.."

Saurin Janyen Kafarta Hafsah Tayi Ta mike Zaune Dakyar tana Gyara Daurin Zanin Dake Jikinta Bata Dade da yin wanka ba ta Saka Sabuwar Tamfanta ta Riga da Zani,Dankwalinta ya Zamo Da Sauri ya gyara mata Yana mata Sannu ta amsa tana Fadin"Dama ai ban jira kaba..Auwal na Kira yazo ya kaisu.."Kunya kuma sai ta kamashi ya Sosa kai yana Fadin"Wlh na Sha"afa..Ban kuma yi Tunanin kiran Auwal din ba sam...Kiyi Hakuri plz.."

Hafsah tace"Bakomai karka Damu..Ya kwanan Amarya..? Abdullahi yace"Lafiya lau..Ya za"ayi ne ina so na Hadaku ne muyi mgana Gabadaya yaushe kike ganin ya kamata muyi zaman..? Yafada yana Riko Hannunta Lokaci Daya yana Jinginata da Jikinsa Fuskarta ta Saki Tana Fadin"Eh to ka bari Zuwa Da yammah mana..Kaga kila yau ma za"ayi baki ko..? Yana Shafa Tulelen Cikinta da Hannunasa Guda Daya yake Fadin"Eh goggo Habiba tace zata zo Ita da Umma kafin su Tafi..bansani ba Ko yan"uwan Barkat din zasu Dawo.."Hafsah tace"Kila zasu Dawo Suma.."

Bai yi mgana ba Sukaji Sallaman Barkat Din Daga Falon,kallon juna Sukayi Itadashi kafin ya yunkura yana Fadin"Barkat ce tazo gaisheki ne.."Yafada yana mika mata Hannu ta kama ya Taimaka mata ta mike Tsaye ya Gyara mata Dankwalinta da Daurin Zaninta ya Rikota Zuwa Falo Barkat din na Zaune kan Daya Cikin kujerun Falon Tana Sanye da Riga da Sikat na atamfa da mayafinta suna Fitowa ta mike Abdullahi ya kalleta yana mata Mirmishi ita kuma ta ballamai Hararan Wasa Duk Hafsah na kallonsu Ta kauda kai Shi ya Taimaka mata ta Zauna kan Kujera shi da Barkat din Suna Binta da Sannu Sai da Zauna kana ta kalleshi Tana Fadin"Nagode Abban Amira..."

Mirmishi yayi mata bai yi mgana ba Barkat din ta rankwafa tana gaida Hafsah din ta amsa tana Mata ya bakunta,Tace Lafiya lau nan Hafsah ke mata Godiya Taga sako Tayi Mirmishi tace bakomai an zama Daya,Kallon Abdullahi Hafsah Tayi Tana Fadin"Kun karya..? Abun karyawanku na Kitchen fa..Sai hakuri Saboda yanayina Ruwan Tea Kadai na iya Dafawa sai Soyayyah Buredi da kwai.."Mirmishi Barkat din Tayi kafin tace"Ayyah bakomai an kina ma kokari Allah ya raba lafiya.."Da Abdullahin da Hafsah suka Hada baki suka Amsa da Ameen Ameen.

Sun zauna Shuru kafin Abdullahi ya mike yana Kallon Barkat din yace"Ke tashi muje mu karya ko..? Ta mike tana Fadin Toh Waigowa yayi yana kallon Hafsah yana Fadin"Bari naje mu karya..Ya kamata asan yadda za"ayi ko mariya ta Dawo nan ta Rika kwana wajenki Saboda yanayinki Abubuwan suna miki yawa.."Hafsah tace"Da kabarta.Bakomai zan iya ai ina Motsa Jikina.."Yana Shirin Fita Daga Dakin yake Fadin'Bana som wannan gaddaman naki..Karki Kara sakamin baki Abunda ya kamata Shi zanyi.."

Jin Haka yasa bata kara mgana ba har ya Fice ta Bishi da kallo Aranta Tana mamakin yadda Abdullahi ke rawan Jiki kan Wata Mace bayan ita Lalle Rayuwa kenan Maida kanta tayi Jikin Kujera kawai ta Lumshe ido kamar mai Barci,Abdullahi da kanshi ya Shiga Kitchen ya kwaso musu Abun karyawansu suka koma Daki suka Karya,Daganam bata kara jin Duriyarsu ba,Jidda ta Kira Hafsah Tana gayamata sun Wuce taso Ta Biyo kafin su Tafi Ya Nazifi ya Hanata bata damu ba tace Bakomai Allah ya Kiyaye Hanya.

Sai Wajen 2pm na Rana Hafsah Tatashi Ta Dafa Taliya da Miyar Kifi Dama Tun Jiya Subai tayi mata Miyar,Taliyar kadai ta Dafa bata ma iya ci ba Su Amira kuma Ta Kira Auwal yace har ya Daukosu Suna Gidan Mama Zasu taho Gidan Tare dasu Goggo Habiba,Shine yasa ta Dibi Abincin taci kadan Nasu Abdullahi kuma akula ta Zuba Musu Komai Tunda suna Ciki basu kara Fitowa ba,Kofar Dakin nata ma yana kulle ne.

Ta idar da Sallar La"asar kenan Sai ga su Goggo Habiba da Umman Sadiq,Da mariya sunzo Tare da su Amiran da Inna Abu da Inna Talatu Hafsah Taji Dadin ganinsu Sosai ta saka Mariya ta Zubo musu Abinci Suka ci suka Sha Ruwa da Lemo,Inaga Hayaniyarsu Abdullahi yaji ya Fito Zuwa Dakin Hafsah suka Gaisa da su Goggo Habiban Yana Dakin sai ga Barkat din ta Shigo ta Duka Har kasa ta gaishesu Abdullahi ya nuna mata Goggo Habiba da Inna Abu yayi mata Bayaninsu Ya nuna mata Umman Sadiq yace ga mahaifiyarsa Dama Tana ganinta taga Kamarsu da Abdullahi Duk da Daman ai Tasan ba Mama bace ta Haifeshi..

Nan Su Umma suka Taramu suka mana Nasihan Hakuri da zama da juna Abdullahi kuma suka Dinga mai Nasihan yayi adalci,Sun Dan Dade sai gabda mangariba suka Yi Shirin Tafiya,Abdullahi da kanshi ya Fita ya sama musu Abun Hawa Mariya kuma yace gobe da safe zai Kira Mama ya gayamata ta Shiryo kayanta Gobe ta Dawo nan Wajen Hafsah ta Dinga kwana Saboda ta Rage mata wasu ayyukan Su Umman Sadiq suka ce Hakan yayi Domin Ayanzu Hafsah Tana Bukatar Tallafi da mataimaki.

Chan ya Tsaya yayi Sallar mangariba da Isha"i kana ya Dawo Gidan Dauke da kayan Marmari da kuma Naman Soyayye da Danye,Da kanshi yakai Kicthen ya saka a Fridge din Ya kaima Hafsah nata kana ya Shigarma da Barkat nata Sai Wajen 9 da wani Abu sai ga Abdullahin da Barkat din a dakin Hafsah suka isketa tana Tashin Amira tatashi taje tayi Fitsari Taje ta kwanta,Abdullahi ya Tada ita,ya kaita tayi Fitsarin ita da Amir din yakaisu Makwancinsu yayi musu Addu"a suka kwanta kana ya Dawo Falo Daman Daya Shigo ya gayama Hafsah yanzu Yana son zai yi mgana dasu Dukkansu.


Bayan ya Bude Taro da Sallama kana ya kora musu Jawabin Da Hafsah ya Fara Inda ya kalleta yana Fadin"Hafsah ga Barkat...Kanwatake gareki ba Kishiya ba..Na Shaidake kuma ina da Kyakyawan yakini a kanki..Bazaki bani kunya ba,Nasan ki nasan Halinki na kuma san Abunda zaki aikata da wanda bazaki aikata ba..Ki zauna da ita da Zuciya Daya kamar yadda na sani..Ki kama Girmanki kina gaba da ita,In Tayi ba Daidai ba Kina da Damar da zaki Yimata gyara akomai na Cikin Gidanan Saboda haka Don Allah Don Annabi Hafsah ki zama Wakiliyata akomai na Cikin Gidanan Domin kece ni..Nine ke Yau in na samu zaman Lafiya Daga ke ne Hafsaatu..Kinfi kowa sanina Daga Mama sai Umman Kece ta Uku Wajen sanin Abunda ya Shafeni Gabadaya Ina Fatan zaki min wannan alfarman Hafsatun Abdullahi...?

Ya karishe Fada yana kallonta Numfashi ta Sauke kafin tace"Insha Allahu..Bazaka samu Wata matsala Daga barayina ba.."Ta Fada tana gyara zamanta a kasan Cafet dinta,Cikin Jin Dadi yace"Alhamdulillah naji Dadin Haka..Barkat na Dawo gareki..Kindai san ke karama ce acikin mu.Baki Dade da Shigowa Cikinmu ba..Ni ne mijinki kuma ina Gaba Dake,Hafsah kuma wakiliyatace Itama Din kamar yaya Take gareki bawai bana Sonta bane yasa na Aureki ba,A'a ina son Matata Domin itace Rufin Asirina Itace Silan Da kika ganni Har Kikaji zaki iya zama dani a matsayin Abokin Rayuwarki..Nasanta Fiye da yadda na san kaina Barkat..Hafsah mai Hakuri ce mai ladabi ce mai Biyayyah ga Duka Umarnina..Saboda haka ki bita Sau da kafa kar naji kinyi Sa'insa da ita ko kuma ta nuna miki baki Daidai ba kiki jin mganarta,Akomai ki Rika Tunawa ke Karamace Ina Rokon da Allah da Annabi ki Yi mata Biyayyah kamar yadda na sanki dashi in Hakan ta Faru zan Fi kowa Farinciki Domin sai da Zaman lafiyanku Nawa zaman lafiyan zai Dore ina Fatan kema zaki min wannan alfarman..?

Kan Barkat din na kasa tace"Insha Allahu..Nima Daga barayina baza"a samu wani matsala ba.."Abdullahi yace'Nagode..Naji Dadin haka sai Barayin Rabon kwana..Ya za"ayi in na gama kwanakina Bakwai a Dakin Barkat Hafsatuna ya zaku Raba Abun ne..?

Hafsah tace"Sai naga mu barsa a kwana Bibbiyu ko..? Ta Fada tana kallon Barkat din Wacce ta gyada kai Tana Fadin"Eh yayi Anty Hafsah..."Abdullahi yace"Shikenan Sai mganar Girki Wacce keda Miji ita keda Girki kenan ko..? Hafsah tace"Eh hakan yayi.."Abdullahi yace"Shikenan Allah bamu zaman lafiya...Sai mganar Barkat Zata koma Makaranta nan da kwana Bakwai Saboda Zasu Fara jarabawa so nayi ma Mariya mgana zata Dawo wajenki Hafsah da zama ta Dinga Taimaka ki Allah barshi sai ta Rika Zuwa makarantar Daga nan kafin Barkat din ta gama Exams Dinta ta Dawo gida.."Hafsah tace"Allah bada sa"a..Shikenan Nagode Sosai.."

Abdullahi yace"Bana son wannan Godiyar fa..Me nayi miki..? Abunda yake Hakkina ne na Sauke fa.."Kada kai kawai Hafsah Tayi batayi mgana ba Ya mike Tsaye yana Fadin"Dare yayi bari muje mu kwanta...Gobe ina so muje Gidan Mama da gidan Baba Wada ta gaisheshi Har Gida zan kaita ta gaida Ammi da Daddy Insha Allahu..'Hafsah na Zaune tace"Allah ya kaimu Allah bada iko..Sai da Safenku.."

Mikewa Barkat din Tayi tama Hafsah Sallama ta Fita Shi kuma sai da ya Tsaya ya Taimakama ta Mike yakaita Cikin Bedroom ya Ciro mata Rigar Barcinta ya Taimakamata ta saka ya kwantar da ita,kana ya Kashe mata Wuta ya Jawo mata Kofar ya koma Dakin Barkat,Yau din dai bai iya Dagama Barkar din kafa ba Sai Da ya kara Moran Sadakinsa Dakyau Ita kuwa Barkat sai kuka take da Shagwaba shi kuma yana Biyemata yana lallashinta Da Sakamata albarka.

Washegari kuma Kamar yadda Abdullahi yace da Yammah ya Dauki Barkat din Amashin dinsa Wanda Auwal ya Dawomai da ita da Safe,Suka Fara Zuwa Gidan Mama Daganan suka Shiga Gidan Baba wada suka gaisheshi Yayi ta musu Nasiha da saka musu albarka Daganan sai gidan Ammi Chan suka ma jima Ammi da Daddy sun karbi Barkat kamar yadda Suke Karban Hafsah basu bari sun Tafi ba sai Da Ammi ta matsamai Sukayi Dinner,Kana suka yi musu Sallama suka Tafi Daddy nata saka musu albarka da kuma Nasihan zaman Hakuri Ammi Harda kayan kwalliya dasu Tararan Wuta tabama Barkat din ta karba Tana ta Godiya.

Daganan Gidansu ya kaita suka gaida Hajiya Amina,Sai Wajen 10pm na Dare suka Dawo Gidan,Har Suka Dawo kuwa Abdullahi Bama Barkat yake labarin Irin karamcin iyayen Hafsah Da Ga yadda yake bata labarin ta Fahimci yana ganin Girmansu da Darajansu uwa uba kuma Ta Lura Ba karamin Girma da kima ita kanta Hafsah Take dashi a Wajen Abdullahin ba Domin Koya Mganata ta Gifto akanta yabonta yake Tun Tana Jin bata Jin Haushi Har ta Fara Ji Ta gaji da Jin kalmar Hafsatuna kaza Hafsah na kaza ta Rasa gane wani irin Sadaukarwa Hafsah tama Abdullahi Data Riga ta kamashi kam a Hannunta.


Su Umman Sadiq da goggo Habiba Rana Daya suka Tafi Zannirace Ta koma ana gobe zasu Tafi Gidan Mama taro ya tashi kowa ya koma Gidansa Lafiya ana ta Fatan Allah ya bama su Hafsah zaman lafiya.


******

*Bayan Sati Daya..*

Acikin Satin Dayan nan Barkat da Abdullahi sun gwangwanji Amarci Sosai,Domin Daman Hausawa sunce Amarya ko Ta Buzuzuce sai Anyi Dokinta kamar Hakane ya Faru Domin Abdullahi fa yayi Rawan kafa Hafsah sai dai ta kauda kanta kawai batama Cika Fitowa Tsakar Gidan ba,Kamar yadda Abdullahi yace Mariya ta Dawo Wajen Hafsah,Nan take kwana Da safe in ta gama Ayyukan Gidan,Tayi ma su Amira wanka ta Shiryasu,suka Tafi makaranta sai ta gyara Dakunan Hafsah bayan tayi Abun karyawa in tana da Shiga makaranta ta Tafi in kuma bata Dashi ta zauna Wani Lokacin in Tana makaranta Hafsah ke Dafa Abincin Hakanan Tunda Amarya anata Amarci.

Kullum da Safe Barkat din Zata Shigo su gaisa ta Tambayeta ya yara Daganan kuma bata kara ganinta sai wani Safiyar Su Amira dai yam Dakinta ne da sun Dawo makaranta Suna Wajenta Mariya dai bata Shiga sai in Zata mika mata abinci ko kuma Abdullahi ya Kirata Barkat din Tana Girmama Hafsah Domin Anty Take kiranta ammh Kishi kam Tanayi da Hafsah domin Wani Lokacin Tana Jin Haushin yadda Abdullahi ke kula da Hafsah Sosai Tana ganin Fiye da ita Amarya ma.

Ranar da Abdullahi zai bar Dakin Barkat Har wajen 10pm na Dare yana Dakinta yana Lallashinta sai kuka take wai bazata iya kwana ita kadai ba Dalilin Haka yasa ya Umarci mariya yace Taje Dakin Barkat din ta Kwana Hafsah dai batayi mgana ba Tana ganin ikon Allah Barkat din yarinyace da za"a ce tana Jin Tsoron kwana ita kadai,batayi mgana ba Mariya dai na Tura baki Tatafi Dakin Barkat aranta kuma Tana ganin Bariki Wajen Barkat,Falo tace zata kwanta Barkat din Tace Tatashi su Shiga Ciki Tace nan din ya mata bata Damu ba Tashige Ciki ta barta nan Mariya ta Bita da Harara.

Washegari kuma Su Bahiya da Bahijjat kannen Barkat suka zo Tana ta ma Shirin Tafiya makaranta ne,Mariya Hafsah tace ta Cigaba da Girki Allah barshi In Barkat din Tagama Jarabawa ta Dawo sai ta Fara Abdullahi yaji Dadin Haka sosai ya Dinga ma Hafsah Godiya,Barkat din ma bata wani Damu ba Da Abdullahin ke Fadamata sai ma Haushin Irin Godiyar Da Abdullahin kema Hafsah din taji kamar itace Zatayi Girkin.

Ana Gobe Barkat zata koma Cikin makaranta Abdullahi ya koma Bakin aikinsa,Ita kuma Ranar tayi parking din Abunda zata Bukata Littafan karatunta Dama Suna Chan

39 / 48