Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
ya wuce Duk Tunanin mai Tunani akansa Wlh.."Haka tai ta Mganarta Tana Cin Dariya Hafsah na Fadin ita bata ji Dadi ba Ta Dankara mata Zagi ta kashe Wayarta ita ta Kira Zannira Dake Kaduna ta Fadamata komai itama dai Hakan tacen Domin Yaya Abdullahi ba bakonsu bane sunfi Kowa sanin macen da zata iyi zama dashi Sai ma Hakuri Over irin na Hafsah Sun Dade suna mgana kafin Zannira tayi Allah ya kyauta su Kashe Wayar.
*****
*Bayan wata uku..*
Tafe Tafe Tun Barkat na Jiran Tsammanin Kiran Abdullahi ko Wayarsa har ta Fara Sarewa Gashi Kimanin Watan Cikinta Watansa na biyar kenan yana gabda Shiga na Shidda kenan har ya Fara Fitowa tana Shirya Shiryan Fara Zuwa awo,Allah ya Taimaketa sun gama Final Exams dinsu ta Dawo Gida ammh ba Abdullahi ba Dalilinsa Tun Makota na Dauka Abun wasa har suka Fara Zunden Barkat ta Kaso Auranta ta Dawo Gida Tun ana gulman awaje har kuma aka Fara Shigowa gida ana yada ma Hajiya Amina da mgana wannan Dalilin yasa Jininta ya Hau har sai ta kwanta a Asibiti a Dalilin Barkat din Wanda Tayi ta kuka Ammh kuma ta Kasa zama ta Fahimci gaskiya har yau har gobe laifin kan Hafsah take Dorashi ba"a kanta ba Hajiya Amina tayi Kokarin Salisu ya kara Tuntubar Abdullahi kan Mganar Barkat ammh yace bazai iya ba Tunda Har yace abarta ba yanzu zata koma ba sai ta Zauna sanda yayi Ra"ayin ta koma sai ta koma in kuma zaman ya kare Daman Haka Allah ya kaddara Dole Hajiya Amina ta bar mganar ammh Acikin Ranta tana Fargaba da Addu"an Allah yasa Kada Auran ya Tsinke gabadaya.
****
Bangaran Jidda kuwa Cikinta ya Tsufa,Haihuwa ko yau ko Gobe,Gida Nazifi ya maidota wajen Mama Dama Abunda yasa bai kawota Tuntuni ba lectures Da suka Fara ne, sai da suka samu Hutu kana ya Dawo da ita Gidan Mama ta Haihu Duk da Tun Watanin Baya ya kamallah Sabon Gidansa Su Subai dasu Hafsah da Mariya suka Gyara mata sabon Gida Aka kwaso kayanta suka Jera mata su,Gida fa yayi kyau sai wanda yagani Gini ne ginin zamani mai kyau da Tsari,Sakina kuwa Dataji Labari kamar ta Mutu Domin Nazifi ya sanar da ita Gida Mallakin Jidda ne, sai dai akwai Daki Daya na Saukarta in taje Zaria,wannan Abun yayi mata Ciwo Dama Tunda Jidda ta samu Ciki Sakina ke Cikin Wani Hali ballatana yadda taga Nazifi ya Dauki Burin Duniya da wani So da kulawa akan Cikin Jidda Shi da yan"uwansa da Danginsa Rawan kafa yake da Rawan Jiki in ka ganshi sai ya baka Tsausayi bai taba Haihuwa ba wajen Shekara goma da Auransa sai wannan karon Dole kuwa ya Nuna Murnansa afili,Sakina kuwa sai Lokacin Nadaman Hana kanta Haihuwa ya Shigeta ta koma asibiti aka Bude mata bakin Mahaifa,Domin Taji itama Tana Bukatar ta samu Ciki Ta haihu Kodomin Mijinta ya Dawo kallonta da Daraja wanda ta Riga ta Zubar dashi Tun abaya,Yanzu ta Daina Biyema kallon Rayuwar wasu kawayen nata,ta koma kallon makomar Rayuwarta,Aikin gwammati kuma ya Fara fita kanta Domin bata da Natsuwa Rana tsaka taje kano Ta Dukama Alhaji Badamasi tana kukan kan ya nema mata Transfer ta koma NTA kaduna tacigaba da aikinta kusa da Mijinta tagaji da yawon Datake Tsakanin kaduna da Abuja,Mamaki ya kamashi Sai dai Lokacin Shima bai mata gaddama ba,Domin yaga Ishara yayyin Sakina Guda Biyu da kanwarta Suna Gida Auran ya Mutu Shiyasa baya Fatan ya sake wani kuskuran da Sakina Za"a sakota itama tazo ta Shiga Layi Ita kanta Hajiyar tayi Sanyi ta Fahimci Barno gabas take Cikim Wata Daya komai ya kamallah sai dai kawai Ta jema da Nazifi Takardan Tare kuma da Rokonsa ya rakata Gidan Tibin Nta Kaduna Taje tayi Report yayi mamaki Sosai sai dai bai Nuna mata ba Shi ya kaita Tayi Reporting Ta Koma aikinta Tana Zuwa Tana Dawowa, Shi kanshi Nazifin haman sai yafi mai kwanciyar Hankali Tunda bazai ce bayason matarsa ba yana Sonta Har gobe zamansu ya Daidaita Tunda ta Roki gafaransa kuma ya Hakura da Saka Bakin Jidda ko Gidan Mama da Nazifin ya Kawota Tare da Sakinar ne Suka zo Dauke da kayan Haihuwa kamar za"a Bude Shago.
Ita kuma Maman bayan kawomata ita sai ta Nuna ya kaita Wajen Mahaifiyarta ta Haihu awajenta,Saboda Hajiya sa'a Ta Nuna mata kawaici Sosai Tana Bukatar yarta kusa da Ita Nazifi bai yi Gaddama ba Suka Tafi Harda Maman chan Chika garin Suka kai Jidda sai dai kuma Hajiya Sa"a taki karbanta tace Mama uwace gareta Har Abada Ta koma wajenta ta Haihu Dole Mama ta Dawo da ita Gida,Abdullahi Dayaji labari wannam karon dai bai saka baki ba Kowa yayi mamaki Jidda ta Dawo Gida Haihuwa ya Abdullahi bai ce komai ba Shi kuwa Daman Nazifin ya nemi Shawaransa Tun kafin ya kawota Din ya Nuna mai Haihuwan Fari tana Bukatar wani Babba kusa da ita Abdullahi yace ba matsala ya kawota wajen Mama ta Haihu bayan ta Haihu in lafiya kalau ba Wata matsala ta koma Gidanta ayi Suna ta Cigaba da wankanta ko Inna Talatu zataje Ta zauna da ita.
Haka kuwa akayi Jidda kwananta Goma da zuwa Gidan Mama Allah ya Sauketa lafiya a Asibitin Chika ta Haihu kuma Alhamdulillah Daga ita Har Jaririyar nata Suna Lafiya Dayake Haihuwan Dare ne sai Washegari Hajiya sa"a taje ta kwaasosu zuwa Gida kafin kace me agidan Mama ya Cika da yan Barka su Hafsah dasu Subai suna Ji suka Taho Su Umman Sadiq dasu Goggo Habiba ta waya aka sanar dasu Inna Abu kuwa ita ta wanke Jinjiriyae tas aka Nadeta Cikim kayan sanyi masu kyau,Jidda kuma Mama tashiga da ita Bayi ta gasata Sosai Mariya na Gida Duk da ita ake Hidima Domin tagama makaranta sunyi Final Exam suna Jiran sakamako.
Nazifi bai samu zuwa ba sai Washegari da Safe,shi da Sakina suka zo ganin Ni"imar da Allah ya basu Nazifi baki yaki Rufuwa Lokacin Daya Dauki Jinjiran ya Rumgume sai da yayi Kwallar Farinciki Nan take yayi mata Huduba, da Sunan Goggo Abu Zainabu Abu mai Tagwayen suna kowa yaji sai yaji Dadin wannan Sunan Sakina ma ta Dauki Jaririyar tana santi Kamar tayi Kuka Jidda na Fadin kema Anty Sakina Allah zai kawo naki,Subai na gefe ta tabe baki acikin Ranta tace Daga baya kenan.
Suna Gidan Abdullahi yazo Gidan Shima ya Dauki Jinjiran yayi mata addu"a Nazifi yace Sunan Inna Abu taci yace Allah ya Rayata,Nan suka barsu ya Dauki Hafsah Da yara suka koma Gida,Gidan Mama Wuni yake da Mutane yan Barka,Ana gobe suna da Zannira tazo Suka Hadu da Hajiya Lariya da Ammi,da Maman da su Hafsah dasu Subai da Jamila diyar Goggo Habiba,Umman Sadiq dai bata zo ba tadai yi sako.. Da Sakina wacce tazo Tun safe za"ayi suna da ita suka Dunguma sai sabon Gida inda za"ayi suna,chan akayi Badali ana ta Hira Subai chan ta kwana Ammh Hafsah Gida ta koma Tunda Uban gayyar bai bari ba Ranar suna kuma anyi Shagali Sosai sai wanda ya gani Jidda da Zainab zeezey sunyi kyau har sun gaji da kyau Hajiya sa"a da Danginta sunyi Rawar gani Domin akwati Guda Tayima Jidda Da ita da kayan Jaririya Mama tayi nata kokarin ita dasu Subai Hakama Gidan Inna Abu suma sunyi iya nasu Kokarin Angon Karni ma yana garin Shima Sakina kuwa Kaya tayi ma Jidda da Zeezey Abun sai wanda ya gani Anata Godiya wasu sai ta koma ma Basu Tsausayi Irin Su Zannira ammh Subai cewa Tayi ko alama bata Bata Tsausayi ba Domin Duk Abunda ya Faru da ita ita Taja.
Ko Ranar sunan ma Abdullahi hana Hafsah kwana yayi,wai Zata kwaso ma Noor Mura Dole ta Koma Gida ammh ta Bar su Amira nan Tunda su Muhsina suna nan sai Washegari ta koma Sukayi Soye suka Raba zuwa yammah kowa ya Watse,Harta Mama Gida ta koma Tun Shekaran Jiya Inna Talatu ne Daman zata zauna da Jidda Sakina kuma sai Gobe zata koma Saboda aikinta,haka suna ya Tashi Lafiya Kalau sai dai Fatan Allah ya bama Jidda Lafiyar Shayar da Zainabu wacce suke ma alkunya da ZEEZEY..!
*****
Rayuwa tayi ma Barkat kunci Domin Tafara sarewa da Jiran Tsammani na zaman Jiran Abdullahi ya nemeta taji Shuru sai ta Fara Tunanin bafa zai nemeta ba,so yake kila Har sai ta Haihu Tana Gida Hankalinta ya Fara Dawowa Jikinta Data ga ma anyi mganar Auran Bahiya da Bahijjat wanda za"ayi Rana Daya,sai ta Fara Tunanin ya kamata ta nemi Mafita bata son ta Haihu agida ko Saboda Hajiya Amina Da tadata Hankalinta sosai akan zamanta gashi ta gama makaranta ba inda take Zuwa Dole Damuwa da kunci su Taru su mata yawa.
Cikinta na Da wata bakwai ta Fara zuwa awo wanda Salisun yadauki Nauyin komai,Har kuma ga yau Abdullahi bai kara mai mgana kan Barkat ba kuma bai Tako yazo ba,Duk da sun sha Haduwa sai dai kawai su gaisa Shi Abdullahi baya mai mganar Shima Kuma Salisun yana jin kunyar Tada mganar Tunda ga yadda suka Rabu Shiyasa Shima ya Zubama Sarautar Allah ido,ko Hajiya Amina Datake cewa salisun Kirashi agayamai matarsa zata Fara zuwa awo Shi ya hana yace A kyaleshi ai yana sane Barkat din na Dauke da Cikinsa in yana Ra"ayinta Har yanzu zai waiwayeta Dole Suka zubama Sarautar Allah ido ammh Shi kanshi Salisu zaman Barkat din ya Fara damunshi Tun baya Damunshi yanzu.
Tun Cikin Barkat na Wata Bakwai Har ya Shiga wata na Takwas ba wani Labari Daga Bangaran Abdullahi sai Hankalinta ya Tashi ta Tsorata Ta Fara Tunanin ko Baya sonta ne yanzu ta sakama kanta Tunani yasa Jininta ya Hau sai da taje asibiti suna ta mata Fada bai kamata tana saka Damuwa aranta ba Tana da Tsohon Ciki Toh ya zatayi Damuwa ta zama Dole Tunda Man dinta ya Juya mata Baya bai Taba Waiwayanta ba kwatakwata.
Bangaran Abdullahi kuwa yana sane da Watannin Cikin Barkat Tun sadda Salisu ya kawomai Takardan gwajin Cikin,bai manta ba,yana ta Shirrinsa Allah ya Taimkesa Watan Shekaran Jiya ya gama Biyan Bashin Dayaci awajen aiki,ya gama Biya ba Dadewa ya samu karin Girma ya koma Office mai Girma albashinsa ya karu sai kawai ya Kira Ma"aikata ya Zube musu kudi aka Cigaba da aikin gidansa Yana son kafin Wata Biyu Su Tare acikin Sabon gida zuwa yanzu kuma yaji ya gaji da zaman wannan gidan.
Batare da sanin ko Hafsah ba yaje da kanshi yakai ma Mama kudi Naira ₦30k yace taje kasuwa ita da Inna Abu suyi Ma Barkat din Siyayyah kayan Haihuwa da ita da Abunda zata Haifa Watan gobe zata Haihu Mama Tayi mamaki Har ta kada baki Tace"Kai kuwa Yayansu kayi Hakuri ka Dawo da ita Dakinta mana Tunda dai Zuru"a ta Shiga Tsakani..!
Mirmishi yayi ma Mama kafin yace"Zata Dawo Mama karki Damu..Zata Dawo Insha Allahu ammh in ta Bukaci Hakan fa.."Mama Tace"Bukata na nawa kuma Abdullahi..? Yayanta sau nawa yana Binka Har fa wan Babanta ya Kiraka ya Rokeka ta koma Gidanka kaki yarda.."Kai Tsaye yace"Sun Rokeni ta koma Mama ban karyata ba..Ammh ita fa..? Tataba Kirana awaya ta bani Hakuri..? Bata taba ba Mama kinga kenan har yanzu tana Sha"awar zaman Gidan ne.."
Mama ta Rike baki Tana Fadin"Au..Tunda ta koma bata nemeka ba..? Kai ya kada yana Fadin"Yawuce wai Mama gashi ina Fadamiki.."Mama ta kada baki Tace"Lalle...Bata da Hankali..,sai hakuri yarinta ne ke Damunta bazata taba ganewa ba ita ko Tsausayin Mahaifiyarsu Bata ji.."Abdullahi yace"Bata ji Mama Datanaji Da Tuni Ta Dawo Gidan Mijinta..Ba wani yarinta ki kyaleta Dani Take Zencen.."
Dole Mama tayi Shuru da bakinta ammh Abun ya bata mamaki sai da ta Tsegunta ma Inna Abu,itama tace ya kyale yar iska Tunda bata da Hankali Tare sukaje kasuwa sukayi Siyayyar Kaya Da yawa Bayan sun Dawo Mama ta Kira Abdullahi tace yazo ya gani yace basai ya gani gobe su Dauka su Tafi Gidansu Barkat su kai musu,Mama tace toh washegari kuma suka Shirya ita da Inna Abu sukaje gidansu Barkat dim suka kai,Wannan kayan da su Mama suka kawo Shi ya kara Dawo da Barkat Cikin Hayyacinta Mama da bata Shuru ta saka aka Kira mata Barkat din ta kalleta yadda ta Rame sai Ido da Katon Ciki Tace"Ni kuwa y'an nan da kin Ijiye wani Abu Kin bama mijinki Hakuri yazo ya Daukeki kin koma Dakinki Kin Haihu achan yanzu ke ko Tsausayin Mahaifiyarku bakyaji Kina gida da Tsohon Ciki Haka dai gaskiya Hakan bai yi ba, ya kamata ki kira Mijinki ki bashi Hakuri ku Daidaita kanku ki koma Dakinki ki Haihu.."Inna Abu ta amshe da Fadin"Toh Karima in banda ma Rashin Hankali komai miji yayi maka ko Dukanka yayi Tunda Zuru"a ta Shiga Tsakani ai kayi kokari ka gyara auran ka koma Dakinka kada kana yaronka Dakai afara kirgamaka Aura Allah na Tuba Duk da bamu san meya Hadaku ba ammh ai girman kai ga mace agidan Auranta baya kaita ko"ina sai Nadama gwara akoma aje ayi ta Hakuri yafi zaman gidan.."
Hajiya Amina ta muskuta tana Fadin"ku gayamata kila ta jiku...Gata nan Ni da yayansu ba Abunda bamu gayamata ba ammh bata Sauraremu ba,Girman kai Daman ina zai kaita bagata nan agida ba,Shi Namiji daman har ka nuna mai ka isa bai nuna maka iyakar ka ba..Wlh yamim Daidai Dayayi Banza da ita in Tagaji da zaman gidan sai ta neman ma kanta mafita na Cire Bakina akanta Abunda ta zabama Rayuwarta Shine Daidai.."Tafada Cikin Bacin Rai Hakuri su Mama suka Cigaba da Bata Sun Jima agidan kafin su Tafi,Suka bar Barkat ta koma Daki Tana ta Kuka Nadama ya Shigeta Lokacin Daya da Som komawa Gidan Mijinta,Su Mama Daganan Gidansu Barkat din Gidan Ammi suka Biya suka gaisa kana suka gayamata Daga inda suke,Ammi tayi ta Jajanta lamarin Tare da addu"an Allah ya Daidaitasu,sun Dade sai bayan mangariba suka Tafi Bayan Ammi ta rakasu da Abun arziki.
Hafsah bata san Anyi ba Domin Abdullahi bai gayamata ba sai Washegari da sukayi waya da Ammi take cemata Jiya su Mama sunzo,Sai Hafsah tace Allah sarki,Sai Ammi tace mata Daga Gidan su Barkat suka Biyo Sunje kai musu kayan Haihu Cikin mamaki Hafsah Ta ke Tunanin Kenan Cikin Barkat din ya Tsufa Lalle ba mamaki Tunda ga Noor tana Cikin Wata na Goma ne,Abun bai wani bata mamaki ba sanin Ko Zencen Barkat din Abdullahi bayason Tayi mai kuma Tunda ya Roketa kan Haka bata kara ba ta kama Kanta ammh Tana Addu"a Duk indan Tayi sallah Allah ya Daidatasu bata son Auran ya kare Saboda ita da Zuciya Daya Ta Zauna da Barkat kuma yadda bazataso Auranta da Abdullahi ya mutu ba itama bazata so Na Barkat din ya kare ba in tayi Duba Hadisin dayace mu soma Yan"uwanmu Abunda zamu soma kanmu.
Abdullahi bai gayama Hafsah ba sai da akayi kwana Biyu kana ya gayamata,Sai ta Nuna mai Bata sani ba,Tayi kokarim tace wani Abu sai yaki bata Dama yace Tadaina Damuwa in Barkat ta Damu Zata Dawo Dakin Mijinta in kuma bata gaji da zaman Gidan ba yanzu ta Fara,Dole ta kama bakinta sanin Halin Abdullahi na kaifi Daya Da kuma Tsattauran Ra"ayi wanda bai sanshi ba shiyasa yake da Bahagon zama.
Bangaran Barkat kuwa Taga fa ba Sarki sai na Allah Hatta da Bahiya Data ke goyon bayanta yanzu ta Daina Shawara suka Hadu suka suka bata kan ta Cire wani Girman kai da isarta ta Kira Abdullahi Ta bashi Hakuri su Daidaita kansu,Tunda dai ta Riga ta Fahimci Girman kai da isa bazasu Sata Cin wani Riba agidan Auranta ba,,Wajen Sati Daya suna Ta Kokarin Bata Shawara,ita kanta Barkat din an kawo Gabar da bazata iya Jurewa ba Dole ta ijiye wannan Girman kan nata da isarta ta Kira Abdullahi Lokacin Wajen 10am na safe ne yana wajen aiki Lokacin Daya ga Kiranta Dariya ta kusa kamashi sai ya kanne ya Murmusa afili ya Furta waya gaya miki Borno gabas Take yarinya..Wlh bamai iya Ja da Abdullahi sai Allah Daya Hallicesa.
Yana gani Tana ta Kira ajere ajere yayi mata Banza sai ma ya saka wayar a Silent Hankalin Barkat ya Tashi ganin bai Daga Kiranta ba Su Bahiya suka kara lallashinta kan ta Cigaba da Kira Ranar Wuni tayi Kiranshi Har ya tashi aiki Daya Duba Adadin Kiran 76 missed calls Tayi mai Kai ya Girgiza acikin Ranshi yana Fadin yanzu kika Fara Har ya koma Gida bata Hakura da Kira ba,Tun Hafsah na Shuru Hardai tamai mgana kan wake Kiranshi Baya Dagawa sai yace mata wani Dan Rainin Wayau ne taa kyaleshi ya Cigaba da Kira jin Haka yasa ta kama bakinta kuma Har Acikin Ranta bata kawo Barkat bace ballatana ta iya wani Abu akai.
Wasa Farin Girki Wajen kwana uku Barkat ta jera kullum sai Tayi ma Abdullahi Over 100 Missed calls Baya Daga Kiranta Taci kuka Sosai su kansu su Bahiya masu Tausanta sun Sare wannan karon,Bahijjat ce ta kawo Shawaran Kiran Nazifi abokinsa Sai Barkat tace bata da Lambarsa Bahiya tace ta Kira ya Salisu baazai Rasa ba Haka kuwa akayi Barka ta Kira Salisu tace ya Turamata lambar Nazifi Tunda yaji Haka aranshi yace Tagaji da zaman Gidan kenan bai Ce komai ba ya Tura mata Ta Kira Nazifi,Lokacin Da Daddare ne baya gida ya Fita masallaci Jidda ce ta Daga Kiran Dayake Watanta Biyu ta koma Kaduna Saboda sun koma makaranta Tare da Inna Talatu suka koma Saboda kula da Zeezey Tunda Sakina na Zuwa Wajen aiki Weekend ne kadai suke zama agida.
Lokacin da Jidda ta Daga Kiran bata gane Barkat bace ta Dai gayamata Yana masallaci Suka Rabu kan in ya Dawo zata gayamai Daya Dawo sai ta manta sai zuwa chan ta gayamai An kirashi kuma Koda ya Duba ganin baisan mai lambar sai ya Share gashi kuma Dare yayi,sai da safe Barkat ta kara Kiranshi Lokacin yana wajen aiki sai da tayi mai bayanin kanta kana ya ganeta Tana kuka Tana Rokonshi kan ya saka Baki Abdullahi yazo ya Dauketa ta gaji da zaman Gida Hakanan ta Kirashi yafi sau Shurun masaki bai Daga Kiranta ba,Nazifi yayi ta Lallashinta ya kuma yi mata alkawarin zai Kirashi yayi mai mgana Suna gama mgana ya Kira Abdullahi yamai mgana ya gayamai yadda Sukayi da Barkat din,Dariya Abdullahi