Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
da Martabana Daga yau Zaki iya zama a Abuja Har Abada Sakina Ban damu ba Ranar da kika samu Lokaci sai ki Lekomu a hakan ma Wlh mun gode.."Yafada yana yar Dariya.
Ganin yadda ta kafeshi da manyan idanuwanta ne baki Bude ta kasa mgana yasa kawai ya Mike yana maida Wayarsa aljihu Leda Daya ya Dauka Cikin Ledojin yana Fadin"Ga shin nan ki Dauka kici karki Dinga aiki ba Abinci acikin ki Hakan Illah ne ga Lafiyanki ni kuma Bana son Abunda zai Tabamin Lafiyan Uwargidata Ran gida.."Yafada yana Cije baki Gaba yaci zai Shiga Dakinsa kamar mai aljanu haka Sakina tayi Wurgi da System din gabanta Ta Hada da Katinan Auran Tayi Fatali Dasu Cikin Zafin nama ya waigo yana kallonta ganin yadda Take Huci Tana kallonsa Mamaki ya Kamashi ya Bude baki yana Fadin"Lafiyarki kuwa..?
Cikin Wani Gadara da Takama tatako Zuwa gabansa Tana Fadin.."Ni kake kallon Tsabar idona kana Fadamin zaka kara Aure Nazifi Wada..? Tafada tana Nuna kanta Cikin wani irin Bacin rai Abun ma sai ya Bashi Dariya,Har sai ya Murmusa gyara Tsayuwa yayi yana Fadin"Kamar ya..?Toh ke wacece da baza"a gayamiki ba..? Da kiji Daga Bakin wani fa..? Au gwara kij Daga Bakina.."
Ya Fada yana kallonta Kankance Ido Tayi Tana Fadin"Ni sakina Badamasi nice yau kake cewa zakama Kishiya Nazifi..?kishiyarma Da wata karamar yarinya kuchaka kazama Wacce bata..."Saurin Dakatar da ita yayi Lokaci Daya yana Daga mata Hannu Cikin bacin rai ya Fara mgana"Don Allah ya isa haka Sakina me ta miki da zaki Rika kiranta da wadanan Sunayenan..? Ina Ruwanki da ita..? Ai ban Dauka zaki Nuna kin Damu ba Don zan kara aure ba Sakina na Dauka Bayan Dukiyar iyayenki Da aiki babu wani Abu mai muhimmanci acikin Rayuwarki..Na zabi nayi Aurena ne na samu kwanciyar Hankali ke kuma ki Zauna da aikin Gwamnati na Har Abada Wlh bazan kara Korafi ba..ya kamata kisan mganar da zaki Dinga Fada malama.."Yafada yana kokarin Juyawa Cikin Wani Hargagin kuka Sakina taci kwalan Nazifi Tana Fadin"Wlh baka isa ka wulakantani ba kamar ni zakace zakama kishiya..? Kishiyar ma da wata yar isk..."Bai bari ta kai karshen Mganarta ba ya Yarda Ledan Hannunsa ya saka Hannu ya Finciki Wuyansa Lokaci Daya yana Ture Sakina Baya tatafi ta Fadi Saman Cafet tana gunjin kuka Ransa yayi bala"in baci Cikin kakkausan Murya ya Nunata yana Fadin"Ke yar gidan Uban waye da baza"ayi miki Kishiya ba..? Sakina wadanda suka fiiki komai da komai ma an musu Kishiya kuma sun Zauna Dole Ballatana ke..Kin yi karya ki Hanani Abunda Allah ya Riga ya Hallatamin Kuma Wlh in Bakin ki ya kara Budewa kika zagi Jidda ko kuma kika Kara Rikemin Wuyan Riga wanchan karom mari kikasha wannam karon kuwa sai na barki kwance saboda Duka Abaya nayi Hakurin duk wani iskancinki keda iyayenki Saboda nasan Laifina ne ammh banda yanzu da wata ta Riga ta Nuna Nima ina da Darajata kamar ko wani Da Namiji..'Yafada yana sakin mata Huci kamar wani mahaukaci ganin haka sai ta Firgita ta Shanye mganarta Ledan kazansa yaDauka ya Shige Dakinsa Lokaci Daya da Banko Kofa Cike da Bori Sakina ta Mike ta isa Jikin Kofan Tana Bugawa tana kuka ta Hadawa da Zagezage Harda Abdullahi take ta zagi Yana Ciki yana Jinta ammh sai yayi kunan Uwar Shegu da ita gefe Daya kuma yana Tunanin dama Har yanzu sakina na sonsa..?
Bai san iya Adadin Lokacin Data Dauka awajen ba Shidai bayan ya gama cin gazansa ya Kora da Ruwa yayi Shirin Barci ya kwanta ya Toshe kunne da Ear phone suna waya da Jidda suna mgana kan jeren da za"aje yimata Gobe yabama Banza ajiyarta Har ya gama wayarsa ya kwanta yayi barci Daganan bai kara Jinta ba.
Ita kanta Sakinar bata san iya adadin Lokacin Data Dauka akofar dakin Nazifi ba gajiya tayi taja Jikinta zuwa Dakinta ta Fada kan gado ta kara sakin wani marayan kuka,Abun na Zuwar mata Daga karkashin Zuciyarta ne,Tana Tunanin har ita Nazifi zai ma wannan Wulakancin wai kishiya..? Ita kaf cikin kawayenta ba macen da aka tabama Kishiya sai ita kuma Dukkansu ma"aikatan gwannati ne yanzu in wannan labarin ya Fita Abun kunya ne awajenta Babban ma Abun Takaichi yadda Abun yayi mata ZAFI har ga Allah tana son Nazifi kuma Bata kaunar wata mace ta Kusance shi,Uwa uba kuma ya Rasa wazai aura sai wata kazamar yarinya kanwar abokinsa Take nan Tsanar Abdullahi ya kamata duk ko a Baya Duk acikin Abokan Nazifin Tafi kowa ganin Girmansa ammh Dalilin haka sai Taga bakinsa Tana Tunanin Shi ya Hada Nazifin da Jidda Tunda a iya saninta Nazifinta bai da Ra"ayin Tara mace Fiye da Daya.
Kwana Tayi kuka Dama Tana Hutun sallah,Tun asuban Fari ta Shirya kanta da karamin akwatinta acikin Zuciyarta Tana Tunanin Abunda zata yanke Shine Daidai Tunda ta Kira Abbanta ta gayamai komai kuma ya bata izinin Tahowa gida Allah barshi Sai ya zaba ko Ita ko Amaryansa Hajiya na gefensa Tana Fadin Tsiyan Dan Talaka kenan Bai iya samun Waje ba ammh banda Haka har Shi Nazifi ya isa yama Sakina Kishiya,Wajen Misalin 6am na safe yana Zaune kan Darduma yana azkar Yaji Tashin Motatanta Domin yau bai je masallaci ba ya makara,agida yayita ko Gizau bai yi ba ballatana yayi kokarin Tashi ya Bita acikin Ransa kuma yana ma Jin Dadin haka Dama da Rashin Ta da ita din Duk Dayane awajensa.
Bai Fita ko Kofar gida ba yana Gida Kazan da Siyo mata Jiya ko Tabata batayi ba yaji Dadin haka ya Gyara zama yaci Abinsa Lokaci Daya kuma yana kallon Talabijin Cikin Nishadi,yana ganin Kiran Alhaji Badamasi yaki Dauka sai da ta katse kana ya Kirashi Abun mamaki ko gaisuwansa bai amasa ba ya Rufeshi da Fada kamar yayi wani laifi wai don me zai kara Aure..? Abun sai ya bashi mamaki bai Tankaba sai da yace Toh sakina Ta Dawo gida sai ya Zaba ko Ita ko Amaryansa.
Wannan karon bai iya Shuru ba,Sai ya Tanka yace"Ammh Abba meya kawo wannan mganar..? Aure fa Sunnar ma"aiki ne,kuma kasani Da Biyu ma yace mu Fara Bantaba Jin inda akace namiji ya zauna da mace kwara Daya Tal ba..Sai dai in Hakan Ra"ayinaa ne..Kuma Lokacin da zan Auri sakina Bamuyi daku Cewa bazan kara Aure ba Ballatana wata mgana ta Fito Mganar Na zaba ko Ita ko Jidda Wannan kuma Ra"ayinta ne Lokacin da mukayi Aure ban mata Dole ba ita Taji ta gani yanzuma Da kafarta ta saka Kafa ta barni so in Taga Dama ta Dawo in bata ga Dama ba ta Zauna bandamu ba Domin har gs Allah ni bance tatafi ba..mganar gaskiya kenan.."
Jin Haka yasa Alhaji badamasi ya saki Baki kawai yana Sauraran Nazifi bashi kadai ba Harda Hajiya da Sakina Dake gaban iyayenta Wayar a speaker yasa Nazifi bai Jira Wani mgnaba ya yanke Kiran,ko ajikinsa sakina kuwa Dataji kalaman Nazifi sai Ranta ya kara Baci Ta mike Zuwa Dakinta Tana Jin wani Kuka yana Taho mata Daga kasan Ranta Duka iyayenta suka Bita da Kallon Tsausayinta...
*******
Yau lahadi Tun Safe Yan Jere suka Tafi,Zannira Wacce Tun Jiya ta Sauka ita da Tawagarta,Sai Subai"atu da Hafsah sai Inna Talatu,Da Hajiya Lariya da Goggo Habiba wacce Itama Tun Ranar Jumma'a take gidan Mama Umman Sadiq ne sai gobe zata iso Ita da gayyarta.
Tun Wajen 10am na safe suna Famwaki Kuma ba laifi karamin Flat mai kyau Nazifin ya kama Sosai gidan yayi kyau 2 bedroom sai Kichen aciki da Tiolet awaje kuma akwai Rijiya da Bohol,sai Tailet din Waje da Filin Tsakar gida kafin yammah sun gama Gyara ko"ina Dama Tun Jiya kayan Suka iso,Gida yayi kyau Masha Allah,Kalan gidan Ash And Black,Abun sai wanda ya gani Kowa yayi Bajintarsa Sosai Sai Dare suka koma Gidan Mama Duk da basu da yunwa Daga gidan Inna Abu aka kawo musu abinci,Sun gama komai kayan gara ne,kadai ya Rage Shima Abdullahi yace asaurareshi Zuwa Gobe Duk Dama Goggo Habiba tazo da Buhun Masara Biyu,Dana Dawa sai Buhun Danyan Shinfika Shiyasa Abun yazo da Sauki.
Amarya Jidda Tana Chika gari gidan Mamarta Hajiya Sa"a ita da Mariya da Rumana kawarta Tun Ranar jumma"a suka Tafi,Ana Chan Hajiya Sa"a ta Gayyato Wata Hajiya Laila a saudiya suka Hadu Tana gyaran Amare Sosai Take gyarata Gefe Daya kuma tana Tsumata da kayan Mata Washegari kuma Ta aika da Sakon Turaran Wutan Dana Daki Dana Jiki,sai Glass din Da kuma Kayan Gara komai Buhu,Da kwalayen su Taliya da macaroni da Indomie,Koda Abdullahi yazo ya gani bai yi Mgana ba,Dayake yanzu suna da Fahimtar juna da Hajiya Sa"a din Taga uwar bari Har Waya suna yi,Yanzu din ma sai da ta Kirashi Ta gayamai yayi mata godiya kayan Abincin Daya kawo kuma Sai yace Mama suyi amfani Dashi a gida.
Sai Ranar alhamis Jidda ta Dawo Gidan Mama Hajiya Sa"a agidanta Zatayi Taronta ita da Danginta,Gidan Mama ya Riga ya Cika da Baki Umman Sadiq tazo ita da Zahra ta zama Budurwa Ta kai Shekara 10,Harda Abokiyar zamanta tazo,Sai Su Ammi itama tana Zuwa Takai Dare sai ta koma Gida Hafsah kuma Abdullahi ya Hanata kwana Komai Dare gida take komawa,Harira kuma ta koma gidan Ammi ganin Jikin na Hafsah da Sauki tana iya yin aikinta da kanta.
Ranar Jumma"a Nazifi ya Tattaro ya iso Bayan ya Dauki Hutun Sati uku Daga wajen aikinsa na Amarci Makaranta kuma Ba lalle bane ya Shiga Tunda sai wani Abu ya Taso,Da yammah kuma Su Jidda sukayi Walima Wanda Subai"atu da Zannira suka Hada,Akofar gidansu Abdullahi akayi Walimar aka saka Kanufi da Kujeru aka gayyato Malama Safiya muhammed Ba"are tazo Tayi wa"azi ga ma"aurata,An Raba kofuna da Kananan Qur"ani sai Carbi da Dabino Wanda Auwal ya Dauki Nauyi,Zuwa Dare baki Sun Cika gidajen Biyu,ya"yan Goggo Habiba su Jamila sun Diro Anty Hadiza ma Tazo,Gidan Inna Abu ma ya Cika da Dangin Su na uwa Dana Uba sai Hidimar Biki ake ganin haka yasa ya Tattara sukabar anguwan Shida Abdullahi zuwa gidansa Tunda Hafsah Tun Jiya tayimai Yaji ko Ganinta bai yi ba Da ita dasu Amira balle yace ta koma gida Suna gidan Mama sai Bayan Biki.
Achan ne Nazifi ke bama Abdullahi Labarin Abunda ya Faru Tsakaninsa da Sakina Abdullahi yayi ta mamaki ammh kuma sai ya Shanye mamakinsa sanin Halin mata yafi haka,Ya dai Bama Nazifi Shawaran karya saketa Ya kyaleta in ta gaji zata Dawo,da kafarta Nan suka kwana Dayake Duk yawancin Tarin Abokan nasu Daya ne,Duk da kowa yayi gayyarsa Both Nazifin da Abdullahin.
*Domin Biyan Kudin Karatu akan Littafin Ra"ayi ne ko Buri..? Zaku iya Tura kudin karatunku ₦200 Kachal akan wannan asusun bankin 0552179550...JAMILA UMAR GTB,Sai a turo Shedar Biya ta wannan layin wayar 09069067488,In kuma Katin Waya ne zaku iya Turowa ta wannan Layin 09027767783 kai Tsaye Bayan Mutum ya Dauki Hoton katin...Ga masu Bukatar VIP zasu Biya ₦500 ne ta Lambar asusun Dana bada a sama....! Mutanenmu na Niger kuma Zaku iya Tuntumbar My Jika aglan Nissa ta wannan Layin +22794131747....Sai kunzo Masoyana*
*Shakira...*
4/9/21, 1:59 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*
*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!
*029*
*YININ BIKI...*!
"Yau ta kama Asabar ne wanda yayi Daidai da Ranar Daurin Auran Jidda da Angonta Nazifi Tuni Kowani bangaren gidajen ya kaure da Sha"ani Tare da Shagalin Biki ba Gidan Mama ba,ba gidan Inna Abu ba,kuma Ta ko"ina Area su ta Dinke da Jama"a Tunda dama Duk anguwa Daya ne sai Taron Mutane yayi yawa Sosai.
Bangaran ango kuwa Tun Wajen 9am na Safe suka Baro Gidan Abdullahi Cikin Shigar Shadda mai Ruwan Sararin samaniya Riga da wando Duka Harda Babban Riga,Kala Daya sukayi Hatta Takalmi da agogo Wanda Shi Abdullahin ya Dinka musu Shi kuma Nazifi sai ya Siya musu Hula zanna Bukar mai kyau da Tsari.
Shagalinku Hotel suka Nufa Inda Sauran abokan Nazifin suka Sauka Abokan aikinsa Wadanda Suka zo Daga Kaduna sai Wadanda sukayi karatu Tare,chan suka Bata Lokaci sai Gabda Daurin Auran kana Motocinsu suka Shigo Cikin Gari,Dama a masallacin kusa da Gidan Baba Wada za"a Daura Auran da Misalin Sha Daya na Safe Koda suka isa Waje ya Dinke da Jama"a ba Tsaka Tsinke Dakyarsuka samu Hanyar Shiga Cikim Masallacin.
Karfe 11:10am na safe Shaidu suka Shaida Daurin Auran Hauwa"u Usman Direba Jidda da angonta Nazifi Wada kan Sadaki mafi Daraja kuma lakadan ba ajalan ba,Ayayinda Baba wada ya zama Wakilin Amarya Shi kuma Mijin Goggo Habiba Ya zama Wakilin ango Daurin Auran Daya samu Dimbin Hallatan Mutane Daga Waje Waje dadama Ciki akwai abokan aikin Abdullahi da abokan karatunsa Haka bangaran ango ma akwai abokan aikinsa Daga kaduna da Wasu Daganan Zaria,da abokan Auwal da Tsofaffin abokan Baba wada Dama na Mahaifinsu.,sai kuma Dangin Hajiya Sa"a na Uwa Dana Uba Duk sun mata kara Sunzo kwarai da gaske Taro fa Yayi Taro Abun sai wanda ya gani da idanuwansa Harda Salisu yazo Daurin Auran kuma Dashi Bayan Daurin Auran suka yada zango a Usmaniya Restaurant Dake kongo Zaria akayi Reception.
Bangaran Amarya kuwa agidansu Rumana kawarta suke zama,Dayake abinci aiki suka kai akayi musu Ba wanda ya Wahala Hatta Drinks Nazifi ya kawo musu Tun Safe mai kwalliya tazo ta gwangwajesu,sai wanda ya gani Amarya Jidda tayi kyau Har Gaji da kyau,Da Safe Shadda ta saka Wacce Duka Gidajen Biyun Sukayi ankonta Da gidan Mama da gidan inna Abu Sukayi ankonta kowa ka gani Dashi,Daga Cikin Gida kuwa Su Hafsah da su Subai"atu ke kai da kawo Abinci anan aka Dafa Tuwon Shinkafa,da Shinkafa da Wake,Sai zobo da Ruwa Suma Din Biki yayi Biki Tuni Kowa yaci wankansa yana ta Warwarsawa su Hafsah makotansu Mama sukaje sukayi wanka Suka Shirya Daman Kayansu da komai da komai yana gidan Bayan sunyi Wanka Sunyi kwalliya suka Dinga Daukan Hotuna Su da ya"yan Goggo Habiba su Jamila kowacce ta yarda ya"ya suna chan Gidan Mama suna Shan Biki,Subai"atu dai bata da yarda zatayi Saleem na Tare da ita Taso Ta makalama mahmud da yazo Daurin Aure Shi kuma ya gudu yaki karbanshi,Zanniratu kuma Tana Wani Daki Tare da Dangin Mijinta da suka zo mata Biki Subai"atu kanwar mijinta ne Tana Tare da kawayen Amarya.
,Su Ummi kuma sunzo har sun Tafi.
Ita kuma Hajiya Sa"a da Tawagarta Suna gidanta chan Take nata Taron sai zuwa yammah yan chan zasu Taho akai amarya dasu.
Nazifi Suna wajen Reception ya Ciro Wayarsa yaTurama Sakina Sakon... *Alhamdulillah...An daura Aure..Yau na Tabbata Miji ga Hauwa"u...Fatan Allah ya bamu zaman lafiya.......*Ya Turamata da gayyah ya nuna mata ya zabi Jidda Fiye da ita aikuwa Tana gani Sakina ta Fara kuka Tana Fadin manganganu Tunda Ta Dawo Gida bata da kwanciyar Hankali ko wajen aikinta Bata koma ba Tun Tana Tunanin ganin Nazifi har ta Daina Ta Shiga Damuwa Sosai kullum sai kuka Bata taba Tunanin haka take son Mijinta ba sai wannan gabar Kawarta Rukky Ita Hajiya ta Kirata tazo Tana Bata baki Bayan ta karanta Sakon Nazifi Sakina na kuka Tana Zagin Nazifi da Abdullahin da Ita kanta Jiddan Rukky ta Bude Baki Tana Fadin"Wai ina ce ba wannan abokin nashi da kuke Mutumci da matarsa bane Nazifin ya auri kanwarsa..?
Sakina na kuka tace"Eh Shine...Hafsah ba.."Rukky tace"Kinji ko..? Wlh itama da Hadin Bakinta In banda Munafunci ai babu yarda za"ayi Ace Mijinki zai auri kanwar Mijinki bata sani ba in gaskiya ne ta Kiraki ta Fadamiki mana.."Cak kuka Sakina ya Dauke idanuwanta Jajir take kallon Rukky kafin kawai ta Zabura kan Dressing mirror ta lalubo wayarta Jikinta na Rawa ta lalubo Lambar Hafsah ta Kirata.
Hafsah na chan ana Hotuna da ita Taji wayarta Dake Cikin aljihun Rigar Shaddarta ta Dauki Ringing Dama Doguwar Riga Tayi mai aljihu saboda Cikinta Daya Fito,Sosai ya sakata kiba yanzu Duk yawancin kayanta sun mata kadan,Tana Daukowa ta Duba taga Sakinar Nazifi sai da Gabanta ya Fadi ammh kaucema Hayaniya sai tamatsa Gefe ta Daga Kiran,Abun ya bata mamaki Dataji Sakina na kuka tana mata mgana kan cewa Har da ita aka Taru akaci amanarta Wajen Tusama mijinta kanwar Mijinta Data rasa Mijin Aure,mganganu dai gasunan masu alama da Cin mutumci da Zagi Duk kawaicin Hafsah Sai da Ranta ya baci Jin Tana Neman Zagar mata miji sai kawai ta yanke Kiran Ta juyo ta Dawo sai ga Subai"atu Cikin mamakin gani Chanjin Fuskar Hafsah take tambayanta Abunda ya Faru ita kuma ta gayamata wata uwar ashar Ta lailayo ta Lafta kafin Tace"Kata'i lalle nema Matarnan ta Cika yar iska yo ke kuma sai kika ce mata me..?
Hafsah tace"Me zan ce mata..?biye mata zanyi muyi ta Hayaniya..?kashe wayata nayi.."
Subai"atu ta Ciji yatsa kafin tace"Nayi Takaichin Lokacin Data Kira wayar bani na Daga ba wlh da sai ta Raina kanta..Dama tana son Mijin nata don Durun ubanta Take wulakantashi..? Ta kwantar da Hankalinta mun ma kanwarmu karatun komai Wlh sai ta Bata mamaki Shegiya kota ma Abujan ne ko Kadunan ita ta sani..."
Hafsah tace"Ohon mata..Ammah ai maganganunta ba ilimi sam..Ina ma ji Wata a kusa da ita na Tayata Allah kyauta asan Kishiya akwai zafi ammh sai ka samar ma kanka Natsuwa.."Subai"atu Tayi Tsaki Tana Fadin"Kar ma ta samar kanta...Ubanta zataji Wlh..Gata ga aikin Abuja nan Miye nata na Damuwa bashi ta Rike ba da Sai ya Rika bata Abunda Namijin Duniya Ke bama mace Shegiyar ashe Tasan Kan Abun Wlh naso kaduna Jidda zata Fara zama mije mu Baje Iskanci Da sai ta kusa Mutuwa saboda bakinciki.."Hafsah tace"Kai..Sai kuma ba chan bane..Kidai ki kama girmanki Yaya
kike ba kawar amarya ba.."
Subai tayi Shewa kafin Tace"Tudu Biyu nake Takawa gani Yar amarya kuma Wlh Ta wani Bangaran kawar Amarya ce.."Dariya Hafsah Tayi Tana Fadin"Shegiya..Allah ya Shiryaki."Ta wuce Subai tabi bayanta Tana Fadin"Ameen Harda mai Ciki ma.."Hafsah na Jinta tamata banza ganin haka yasa Ta Bita tana Tsokanarta Ga Hotunanta sunyi kyau ko ta Turama Yaya Abdullahi ne ko kallonta Hafsah batayi ba sanin Shakiyancin Subai yafi gaban haka.
Sai Wajen La"asar kana Abdullahi da Nazifi suka gama Sallaman mutanensu,Daganan Cikin garin Suka Dawo Suka Shiga Gidan Inna Abu,su ka gaishesu ,kannen Nazifi sai Tsiya sukaima nan ya tsaya sukayi Hotuna suna Fitowa suka Hadu da Auwal nan ya Dake sai sun Tsaya Sunyi Hoto Domin mai Hoto Guda ya Dauko nan ma Sun Bata Lokaci,Kana suka Shiga Gidan Mama suka kai gaisuwan iyaye,Duk da gidan yana Cike ne,Mama kuwa Sai Shiga take tana Fita Abdullahi yayi mata kala