Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
kafin kowa balle ma ba mganar karin Aure a Tsarina bansani ba ko zuwa gaba.."Ya karishe Fada yana Hura mata iskar Bakinshi kan Dogin wuyanta Zillewa tayi tana Dariya ya taka zai Rikota Kawai Sukaji Hon din Motar Nazifi na neman Toshe musu Dodon kunne Kai Abdullahi ya Dafe kafin yace"Kai Wanchan gayen dan Wutar Ciki ne..Kasan kana son matar taka ka bari ta tafi gida kawai ni ina son yau na zauna naga kwalliyar Hausina Dakyau dakyau ammh yazo ya Takuramin.."Yafada yana wani Bata rai Daidai Lokacin da Nazifin ya kara sakin Hon.
Dariya ta kama Hafsah bata karisa ba Abdullahi ya Rikota ya kara sakata Cikin Jikinsa Na dan wani Lokaci kafin yayi mata Kiss Saman kanta yana Fadin"Miss u...Take care of ur self for me kinji HAFSATUNA.!
Yafada Cikin wata Murya Mirmishi ta sakarmai kafin itama tayi Dage Domin ya Fita Tsawo ta sakamar sumba bisa karan Hancinsa Tana Fadin"Insha Allah U Too..Abdullahi Mijin Hafsatu.."Mirmishi ya sakarmata kafin ya Riko Hannunta har Tsakar Gidan ta Rakashi kana suka saki juna ya Fita Tana Dagamai Hannu,jikinta Duk yayi sanyi Tafiyar ne tazo ba wani Shiri.
Yana Fitowa Nazifi ya saki Tsaki kawai Abdullahi ya Bude gaban Mota ya Shiga yana Fadin"Mallam karfa ka Takuramin wlh..Kaja Tsiya sai na koma Abuna.."Ko kallonsa Nazifi bai yi ba ya Fizgi Motan da Gudu sai da Abdullahi yayi gaba ya Dawo Cikin mamaki ya kalli Nazifi yana Fadin"Shin wai ni nace ka mari Sakinar ne har tatafi Gidansu..? Yau ga Shawarakin Banza Yana neman Hushe haushin wata akaina..'Ba Abdullahi kadai Daya Fada ba Hatta Nazifin sai da ya kyalkyace da Dariya suka Hada Hannu suka Tafa suna Cigaba da Dariyansu irin na Shakikan abokan da Shakuwa da yarda da Juna ke Tsakaninsu.
*Janafty..*
4/9/21, 1:53 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:@JamilaUmar351*
*Dedicated To:My Habibaty Aisha Idris Abdullahi..!*
*009*
 "Koda misalin karfe 10am da wani Abu na safe,tayi ma su Abdullahi a Babban Falon gidansu Sakina Dake Kofar Nasara acikin Birnin kanon Dabo Tumbin Giwa.
Tun Zuwansu Megadi ya Shiga Ciki ya sanar da isowarsu Shi yayi musu Jagora zuwa Cikin Setting Room din,Suna nan zaune mai aikinsu ta Shigo da kayan Tabawa ta kuma sanar dasu Hajiya da Alhaji suna sama su Dan Jirasu suna Saukowa yanzu.
Nazifi ya karkata kai yana Tambayan Sakina Mai aikin tace musu Sakina ta Fita tare da,kawarta Rukayyah zuwa wajen Shopping,Daga haka ta Fice ta Barsu nan,Abdullahi Dake gefe kawai sai ya Maida kansa jikin Cussion din Kujera Lokaci Daya yana Bin kayattacen Falon da kallo Wanda yaji kayan alatun Rayuwa Duk da ba wannan ne Zuwansa na Farko ba ammh yana da Tabbacin an sauya kayan Falon Domin bai taba manta Zuwansu na Farko Dashi da Nazifi Tun Lokacin kafin Auran su da Sakinar ne.
Tun suna Hira Jefi Jefi Har suka Gaji Kowa ya Fiddo wayarsa yana Latsawa ba wanda ya Lekosu Ran Abdullahi ya Fara baci ya Tsaki Siririn tsaki yana Kallon agogon Fatan Dake Hannunsa Cikin kosawa yace"Mutumina ka ko kalli agogo karfe nawa yanzu..?
Nazifi Dake latsa wayarsa ya Dago yana kallon Shima agogon Fatan Dake daure a tsitsiyan Hannunsa Cikin waro ido yace"Kai pass 11 fa mutumina Nake gani.."?
Abdullahi ya sauke Numfashi yana Fadin"Ko dai masu Gidan basu san da zuwanmu bane..? Nazifi yace"Wani irin basu sani ba...Baba ya fadamin ya fadama Mahaifin sakinar muna tafe yau insha Allahu Wulakanci ne kawai da Rainin arziki irin wanda Nake gaya maka.."Ya karishe Fada Cikin Bacin rai da kosawa Lokaci Daya kuma yana Lalubar Lambar sakina wacce bai yi Niyyar ma Kiranta ba kwata kwata Domin Tun Bayan Abunda ya Faru basu waya da Juna ba bai Kiranta ba bata taba kirashi ba.
Lokacin da wayarsa ta Shigo Wayar sakina Daidai Lokacin da tayi Hon kofar makeken Gidansu Cikin Bakar Motarta Camry,Rukyyah kawarta na gefenta Suna Taba Hira Jefi Jefi,Bata Duba wake kiran nata ba Sai da Ta Daidaita Motar a parking space kuma alokacin ne ta ci karo da Motar Nazifin Batayi mamaki ba Domin Da Safe Abba ke sanar da ita zuwan Nazifin yau in Allah ya yarda.
Lokacin Data Dauko wayar har kiran nashi ta katse Ganin irin Mirmishin Data saki ganin Shine mai Kiranta yasa kawarta Rukky tace"Yadai Qawata..? Sakina tace"Wannan dan Wahalan ne mana...."Rukky tace"Wa.? Nazifi..?
Sakina tace"Shi mana Bana gayamiki Abba Dazu yake gayamin sunyi mgana da Babansa yabada Hakuri ba kuma yace yau zai Turo Shi Nazifin yazo ya bada Hakuri Da kanshi ba.."Rukky tace"Dama ai na gayamiki Zai zo da kafarsa..Waya Fada mishi ana Taba mace irinki wacce ta mallaki Komai na Rayuwa a zauna lafiya..? Ai Dolensa yazo yayi ladabi ya bada Hakuri Don Ubansa.."Wani kallo Sakina ta watsa mata kafin tace"A"a nan fa Daya Rukky Bana so komai zaki yi karki zagi mijina Domin bazan Dauka ba...Har yanzu ina Son kayana Atoh..."Rukky tace"Allah baki Hakuri Qawata kaina Bisa Wuya.."Tafada tana Dariya Itama Mirmishin Sakinar ta saki kafin ta kashe motar su Bude Murfin Mota suka Fito Booth ta Bude Rukky ta tayata Daukan Ledojin Datayo Shopping Domin gobe zata koma Abuja wajen aikinta.
Cikin Gida suka Shiga,Dakin Sakinar suka yada zango Direct Sakinar bata zauna ba kayan Hannunta kadai ta ijiye ta kalli Rukky tana Fadin"Bari na leka saman Abba..Kila bai sauko wajen Nazifin bane inaga Dalilin Kiran kenan.."Da kai Rukky ta amsa mata ita kuma ta Fice da Sauri Zuwa sama Inda Dakunan Barcin iyayen nata yake.
Bata kai ga karisawa ba suka ci karo da Mahaifiyarta Cikin Mamaki Hajiya ke fadin"Lafiyar ki kuwa..? Har kun dawo Daga Shopping din..?
Sakina tace"Eh Hajiya ina Abba yake..? Hajiya tace"Yana Dakinsa yana Shiryawa wani Abu ne..? Baki Sakina ta Tura kafin tace"Hajiya bai san Nazifi yazo bane..? Wani Harara Hajiyar ta sakar mata kafin tace"Ya sani sai me..? Ke wai meke damunki ne Mutumin Daya Daga Hannu ya mareki ke har yanzu yana Ranki..? Mahaifinki yanci yake son kwatar miki ke kuma kina wani Sakarci.."
Kai Sakina ta Dukar Tana Fadin"Nifa Bance komai ba Hajiya...Kada dai yaga an Shanyashi ne kuma ina jin kamar ba Shi kadai bane.."
Hajiya tace"Hmmm Sakina kenan..Kina da Wahala in Namiji zaki Dinga ma Haka wuce ki Sauka kasa ga Abban naku nan Fitowa ai gwara amishi haka yasan kina da Darajarki ammh har yaushe Kamar wannan yaron da bai Wuce dan aikin Gidanki ba zai Daga Hannun ya marar mana ke mu kuma sai mu Zura ido..? wlh dole ya gane bai da wayau in sakarci ne ke damunsa.."Ta karishe fada Cikin zafi Da kuma Bacin rai.
Sum sum Sakina ta Sauka kasa tana Waiwayan Hajiya wacce ta Juya zuwa Dakin mahaifin sakina tana Cigaba da Fadan yadda Sakina take nuna son Mijinta karara
Nazifi kuwa ganin ya kira Sakina bata Daga ba yasa bai kara Kiranta ba,Abdullahi kuwa Ya gaji da zama bini Bini sai ya Duba agogo yana sakin siririn tsaki Shi kanshi Nazifin Ransa ya gama Baci Cikin kunar rai yake fadin"Abdullahi kaga Abunda nake Fadama ko..? Wlh na yardan ma kaina nayi sakacin da Sakina da iyayenta suka Rainani yanzu Fisabillahi meye amfanin wannan Wulakanci ko dai basu san waye yazo ba ya dace suyi mai Abunda suka mana..? Ya fada idanuwansa suna Chanza launi alamun bacin rai.
Numfashi Abdullahi ya Fesar yana Fadin"Abun dai ba Dattako aciki..Arzikin kadai ake Tutiya Dashi ba kima..Ai ko bakomai sai su Duba kai Surukinsu ne har yanzu akwai Aure tsakanin ka da yar"su...'Nazifi ya kada kai bai ce komai ba Saboda Takaichin Abun yana cin Ransa.
Shuru ya kara Biyo Bayan maganganunsu kafin Chan Abdullahi ya muskuta Ruwan Gora da aka ijiye musu basu Taba komai ba ya jawo ya Tsiyaya a wani karamin Kofi yasha Sai da ya koshi kana ya Sauke Kofin kasa yana Hamdala acikin Ransa,Cikin Kosawa ya sake Kallon Nazifi bayan ya kai Duba zuwa ga Agogon Hannunsa yana Fadin"Kai Nazifi wannan zaman ni kam ya isheni wlh...12 fa yanzu Fisabilillahi Ko da bamu da Abunyi sai mu zauna Haka balle ma sun sani mu da aikin yin mu Dukkanmu.."
Nazifi ya saki Huci kafin yace"Wlh Ba domin ina Tsoron Fadan Baba ba,da Tuni yanzu mun kusa ida Zariya kajima na Rantse maka sai dai su Fito suga mun kara Gaba Wulakancin ya isa Haka.."Abdullahi yace"Nifa nama ga Kokarinka in nine yadda nake da Zuciya da Fushi da Tuni na sakar musu yarsu Su jika susha Bazan iya Daukan wannan Iskanci ba..."Nazifi yace"Shiyasa nake gayamaka karka yarda kayi irin sakacin danayi Mutumina Abunda kake yi Shine Daidai.."
Abdullahi yace"Ai ni Matata ba irin Matarka bace..Iyayenta suna da Kudi ammh kuma susan Dattako..Wlh ba karya ko ganin Ido ba Hafsatu bata taba sa"in sa Dani ba kuma ban taba saka mata Doka ta karya ba Ballatana har na Dinga Fada tana Fada ina wannan karya ne Nida kai Nazifi akwai Bambamci ka yarda bakayi Sa"a ba kawai.."Nazifi ya goge Zufa yana Fadin"Ok ban yi Sa"a ba ko..? Toh ka yi sake ka gani Wlh sai ta maka Abunda Sakina ma batamin ba.."
Abdullahi yace"Ai banki Taka ba Mutumina kaima ai mganarka nakan Hanya ko yayane gwara ka Rika Nuna ma mace kai ne Shugabanta yafi ka zauna Komai sai Abunda ta tsara maka."Nazifi ya Bude Baki zai yi Mgana kenan Sai ga Alhaji Badamasi mahaifi ga Sakina ya Sawo kanshi Falon Cikin Shigar Shadda harda Babbar Riga Tun da ya Shigo kamshin Turaransa ya gauraye Falon.
Da Hanzari suka Mike Tsaye suna Kallonsa Kan Daya Daga Cikin Kujerun Falon ya Zauna ya wani Harde Kasa Dukkansu sukayi suna Gaisheshi ya amsa Fuskarsa ba Walwala Dukkansu sukayi Shuru suna jiran Suji me zai ce musu,Sai da ya Dauki Dogon Lokaci kafin yayi gyaran Murya yana Fadin"Ashe mahaifinka kadai keda Kima acikin Idanuwanka ko Nazifi..?
Yafada Cikin Gadara da wani Rainin Wayau,Abdullahi ya Dago ya kalli Nazifi Shima ya kallesa kafin Nazifi ya Dago kansa yana Fadin"Ba haka bane Abba....Wlh...! Ba haka bane to ya ne..? Ya katseshi Cikin dan bacin Rai Lokaci Daya ya Cigaba da Fadin"Kira nawa nayi maka kana gani baka Daga ba..?kuma koda baka gani ba in kazo kagani bazaka iya kirana Back kaji Dalilin Kiran nawa ba..?
Ya karishe Fada yana Kallonsu Dukkansu Abdullahi kuwa mamaki ya Cikasa sai kallon Alhaji Badamasi kawai yakeyi Nazifi na bashi labarin Rashin Kirkin Surukansa bai taba zaton Abun nasu yakai haka ba Nazifi kuwa Ransa Dama chan yana bace ne yasa kuma ga wannan mganganun,sai kawai yayi mai Shuru jin Shurun yasa Alhaji Badamasi ya Cigaba da Fadin"Koda yake ai bazaka Daga Kiran ba kasan Abunda ka aikata Kasan Allah ba Domin mahaifinka ya Kirani yana Bani Hakuri ba da Tuni sammaci ya iskeka Domin bazan Lamunci wani Sakarai Dagachan bangaren yana Dukan min ya"ba wanda ko Ni Dana Haifeta ban Dake ta ba ballata wani Chan Bare bazai Sabu ba.."Yafada Cikin Nuna yadda Abun ya batamai rai.
Nazifi dai kansa na kasa bai ce komai ba ganin Haka sai Abdullahi ya Dago kansa yana Fadin"Abba hakuri za"ayi Abun duk bai kai haka ba..Kuma in Nazifi nada Laifi itama Sakinar Danata Laifin ko miye bai dace Tana karkashinsa Ta Dinga Nuna kamar ita ke Auransa ba Yakamata Shima Abba aduba wannan mtsalar.."Yafada kansa Tsaye da mamaki Alhaji Badamasi ke kallonsa Domin don sani ya san Abdullahi Domin ko gaisuwan Surukai tare suka zo ammh bai Taba tsammanin Haka yake da Tsaurin ido ba.
Alhaji Badamasi yayi Shuru kafin yace"Naji mganarka ammh ai banga Bambamci ba Domin yasan Diyar wanda ya Aura..Sakina tayi karatu bama a kasar Nageria ba Taya yake Tsammanin zata zauna bazata yi aiki ba..? Kuma in ta samu aikin yasan yanayin irin wannan aikin Tunda yaji yagani Dole kuma yayi Hakuri da yanayin Tsarin Tunda Shi yaji kuma ya gani.."Ya fada Cikin Halin ko in kula Abdullahi suka Kalli Juna Shida Nazifi kafin Abdullahi ya kada kai yana Fadin"Duk da Haka dai Abba ya kamata adubi..Shi Aure ba Abun wasa bane Ibada ne wanda in Suka Rabauta kansa Dukkansu sai Su samu aljannah ta wannan Hanyar Abun Dubawar Shine koma miye ai Shine mijinta ya kamata ta Rika bashi Girman da Allah ya Riga ya bashi.."Alhaji Badamasi yayi kasakai yana Kallon Abdullahi da Sauraransa aransa yana Fadin wannan yaron ya Cika iyayi da Sanaben Tsiya ba Tsoro acikin Ransa ballatana wani Fargaba.
Cikin Dakewa yace"ok...Shikenan.Dukkansu sai su Taru su gyara...ammh Dole ya barta In wani aikin ya taso bana son wani Hayaniya Tunda yasan yanayin aikin Matarsa.."Nazifi ya Kada kai yana Fadin"Ayi hakuri Abba Insha Allahu haka bazata kara Faruwa ba.."Alhaji Badamasi yace"Shikenan ya wuce Tunda kazo ka bada Hakuri...ammh mgana ta karshe Kar ka kuskura ka sake Saka Hannu kace zaka Daki sakina in wannan karon na kauda kai In ka sake wlh zan Rufe ido naci Mutumcinka.."Yafada Cikin kakkausan Murya.
Nazifi ya Dake yana Fadin"Naji Abba ammh itama Sakinar ku ja mata kunni ai yakamata amatssyina na Mijinta in wani Tafiya ya kamata ta Dinga neman izinina ba Wai ta Rika Bani Umarni ba.."Yafada Shima Cikin Dacin Rai,Alhaji Badamasi bai ce komai ba ya Daga wayarsa kawai ya Kira Hajiya tana Dagawa yace"Ki Turomin sakina Shashen baki yanzu nan.."Daga Haka ya katse Kiran Falon ya Dau Shuru na wani Lokaci.
Ba"a Jima ba sai ga Sakina tayi Sallama acikin Falon Tana sanye da Doguwar atamfa na wani material da mayafi,Sau Daya Nazifi ya kalleta ya kauda kai Bai kara ba itama kallonsa tayi Dagashi Har Abdullahin kana ta isa kusa da Abbanta ta zauna Tana Fadin"Gani Abba..Hajiya tace kana son ganina.."
Da Hannu ya Nuna mata Nazifi yana Fadin"Mijinki ne yazo ban Hakuri da Bikon ki,na jamai kunnan kar ya kara Dukanki in kuma ya kara zan Dauki mataki Sai kuma Shima ya kawo nashi Korafin kan baki Neman izininshi kan wasu abubuwan sai dai kawai ki Rika sanar Dashi Kai Tsaye.."Sakina ta Dago kanta tana kallon Nazifi wanda yayi Saurin Dauke kansa Jim tayi kafin tace"Abba ina Fadamai..Ko wannan ma Tafiyar na sanar Dashi Shine yace Bazani ba kuma in zai Fadi gaskiya ina nataba zuwa Ban gayamai ba..?
Tafada tana kallon Nazifi wanda Shima ya kalleta ido Cikin ido na wani Lokaci Abba yace"Toh kai kaji Abunda tace Cikinku bansan waye mai gaskiya ba..? Ba Nazifi kadai ba Hatta Abdullahi sai da ya Dago kansa yana kallon Daga Uban har yar yana Jinjina kai Cikin Dacin Rai Nazifi yace"Me zan karu dashi in nayi miki karya Sakina..Tun da mukayi Aure Baki Taba bani Girmana a matsayina na mijinki ba ki Bude baki yau wata Tafiya ta kamaki kice min Nazifi Ranar kaza zamu Tafi kaza ina neman izininka..? In kuma kin Taba sai ki sanar dani..?
Ya karishe Fada yana Sakarmata Idanuwansa Itama kallonsa Take kafin ta sadda kai Kasa tana wasa da gefen Mayafinta Alhaji Badamasi Daya gano yarsa bata da gaskiya Cikin Borin kunya yace"Shikenan..Ke sakina ki gyara Kinji ko..? Daga Abdullahi har Nazifi da kallo suka Bisa kawai Ganin yana Shirin mikewa yasa Nazifin yace"Abba ina da wata mgana..?
Komawa yayi ya zauna yana Fadin"Ina Sauraranka kayi Sauri Domin ina da Taro zan Fita ne.."Kai Tsaye Nazifi yace"Bazan Hana Sakina aiki ba..Ba kuma zan Hanata taka duk inda take so awannan kasar ba saboda ni nayi sake Haka ta faru..ammh ta sani Dolenta ta Rika zuwa Gidana na Kaduna tana Weekend dinta Bai zama Dole ina matsayin mijinta kuma ace Kullim sai dai ni na Rika kwasan Jiki ina Binta ba mganar gaskiya na gaji bazan iya ba.."Sakina ta Dago tana kallonsa kafin tace"Wani gida aciki naka ko wanda Abba ya bamu..?
Kai Tsaye yace"Nawa dai..Shine ai mallakina wanda Abba ya baki kuma wannan mallakin ki ne.."Cikin Zafi ya Fadi mganar wanda yasa Alhaji Badamasi yayi Tsai yana kallon Nazifin Ganin yadda ya Hade rai Allah na ganin Bashi da Burin ganin Auran sakina ya Mutu Domin Duk Cikin ya"yansa Sakina tafi kowa Dacen Mijin kwarai sauran Daga yan Iska sai Marasa Tarbiya gadai Dukiyar ammh ba Tarbiya Shi kuma Nazifi gashi dai bamai kudi ba ammh dai Akwai Hankali da Tarbiya Shi kuma Abdullahi yaji Dadin Mganar Da Nazifi yayi domin Shi ya bashi Shawaran ya kamata ya Bar gidan da mahaifin sakina ya basu ya koma nashi Shine Mutumcinsa.
Kafin Sakina ta samu Damar mgana Abba ya Rigata da Fadin"Shikenan zata Dinga zuwa ba Shikenan ba..."Yafada Cikin Son kauda zencen kan Nazifi na kasa yace"Shikenan Abba.."Alhaji Badamasi ya mike yana Saba Babban Rigansa Lokaci Daya yana Fadin"Sai kuje kuyi ta Hakuri..Kadai ji Abunda na Fada maka Banason na karajin Zencen Duka.."Nazifi yace"Insha Allahu.
Sakina tayi zaraf tace"Abba ina son yayimin lamani sai bayan na koma Abuja Ranar sati sai na koma Kaduna din.."
Kafin ma Abba yayi mgana Nazifi ya Rigashi da Fadin"Allah kiyaye Hanya...."Jin Haka yasa Alhaji Badamasi bai kara mgana ba Su Abdullahi suka mai sallama ya Fice Daga Falon,Ganin haka yasa Abdullahi ya mike yana Fadin"In kun gama ina Mota.."Daga haka kawai ya Fice Domin mganar gaskiya ya gaji da zaman Gidan.
Da kai Nazifi ya amsa mai kafin yace"Ok Nima ganinan Zuwa..."Daga haka ya maida kallonsa kan Sakina Wacce ta kafeshi da ido Tana kallonsa ganin Duk ya Rame ganin Sun kwashi Wajen Mintuna Biyar ba wanda yace ma Dan"uwansa komai yasa Nazifi ya Mike yana Fadin"Mu zamu koma Tunda baki iya gaisuwa ba ko..?
Itama Mikewar tayi Tana Fadin"Baka so na gaisheka bane..
kai da kake Kallona kana Kauda kai.."Yana Shirin mgana yaji wani masallaci Dake Kusa da Gidansu Sakina ana kwala Kiran Sallah ido ya Fiddo yana Fadin"Har Azahar tayi..? Lalle mun kwashi zaman Rashin Dalilin agidan nan...Toh mu zamu Dauki Hanya...Gobe zan Koma Bakin aikina."Daga Haka kawai ya saka kai ya Fice Cike da mamaki take Binsa da kallo kafin Daga Bisani ta tabe baki ta Shige Cikin gida aranta tana jin ko ahaka aka Tsaya ita keda Riba.
Yana Fitowa basu Tsaya ba kawai ya Bude Bangaren Direba ya Shiga ya Zauna Dama already Abdullahi na gefen mai zaman Banza Motar ya Tada lokaci Daya ya saki Hon megadi ya wangale musu get suka Sulala waje Sai da suka Daidaita Motarsu kan Titi ne kana Abdullahi yace ma Nazifi.."Har kunyi sallaman ne..?
Tsaki Nazifi yaja kafin yace"Wani sallama Fitowa nayi na barta ta Tsaya mulkinta kila Jira take itama na Bata Hakuri kamar yadda na bama Ubanta.."Ya karishe Fada Cikin bacin Rai kai kawai Abdullahi ya kada kafin yace"Ka tsaya muyi sallah in kaga masallaci kan Hanya Lokaci yayi.."Ok kawai Nazifi