Advertisements
Chapter 34 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   34 / 48

99K to 102K   out of 143.7K words

ita ammh Awaya zai Kirata Tace Shikenan.

Sai da ya Duba Ya ga Barcin Hafsah yayi Nisa, kana ya koma Falon ya kira Barkat din Bayan ta Dauka Sun Gaisa Tatambayi Hafsah Dasu Amira,shi kuma yana Tambayanta karatunta tace Alhamdulillah,Tunda Tana makaranta bata koma agida ba Har Bahiya ma Taje gida Weekend ita bataje ba Saboda Basu gama Test dinsu ba,Dayake ana Saka musu Interval sosai.



Gyara Kwanciya Abdullahi yayi yana Kiran Sunan Barkat Jin sa Cikin Serious Tone yasa itama ta Natsu Cikin Sanyin murya yake Cemata"Barkat kinsan dai ni bamai karfi bane.Kinsan inda nake aiki..Kuma kinsan Ina da Mata da ya"ya Biyu sai kuma Cikin na uku..Bayan Haka ina da Nauyin Iyayena Data kannina Bayan Ta iyalaina Da kaina..Kuma kinga ni ba yaro bane da zan Tsaya ina ta Yaudaranki Hakika kinmin kuma ina Son ki zama abokiyar Rayuwata in kin amince zaki iya Zama Dani acikin Gidana da muke Lallabawa Dani da matata da ya"yana Zuwa gaba in komai ya Daidaita na kamallah Gidana sai mu koma..In kin amimce ni kuma nayi Miki alkawarin nan da Wata Daya zan Killaceki agidana a matsayinki na Matata..!


Zuciyoyi Biyu ne Suka Buga alokaci Daya Zuciyar Barkat ta Buga da Farinciki mara Misaltuwa zuciyar Hafsah kuma Dake Tsaye Kofar Bedroom dinsu ta Buga ne da Fargaba da mamaki Hade da wani Kishi Daya Taso mata Daga kasan Ranta Bakinta ta Dafe kada Kukan Daya Taso mata ya Fito,Tana jinsa yana Fadin"Alhamdulillah.....Zan gabatar da mganarmu gobe Wajen Aminin Mahaifina Dake Matsayin Uba garemu...Yadda mukayi Dashi zan sanar Dake..."


Baya Taja da Sauri Saboda kada Yaji Motsinta Da Sauri ta Tura Kofar Tailet ta Shiga tana maida Numfashi,Kasa Tsayuwa tayi jin kamar Dan Cikinta na Juyawa,Kasa ta Sulale Hawaye suna kwarayomata Lokaci Daya Tana jin wani zafi acikin Ranta Fitsari ne ya Tada ita ta Farka Sai taga Bata ga Abdullahi ba Abun ya bata mamaki Ta sauko Daga kan Gadon zata Falo sai ta Fara Jin mgana Sama sama Shine yasa ta Labe Daga Kofar Bedroom Daidai Lokacin Dayake ma Barkat wannan Bayanin zufa ya ketoma Hafsah kasan Bayin Ta Sulale Fitsarin Data ke kokarin Rikewa ya kwace mata nan kasa ta Sakeshi Lokaci Daya tana Fashewa da kuka Jin Motsin kamar Shigowar Abdullahi Cikin Dakin yasa ta Dafe Bakinta kar ya ajiyota ammh acikin Ranta maimaita kalmar Aure kawai atake Lokaci Daya da mamakin yadda Abdullahi ya iya Boyemata wannan Bakon al"amarin....!


*Domin Biyan Kudin Karatu akan Littafin Ra"ayi ne ko Buri..? Zaku iya Tura kudin karatunku ₦200 Kachal akan wannan asusun bankin 0552179550...JAMILA UMAR GTB,Sai a turo Shedar Biya ta wannan layin wayar 09069067488,In kuma Katin Waya ne zaku iya Turowa ta wannan Layin 09027767783 kai Tsaye Bayan Mutum ya Dauki Hoton katin...Ga masu Bukatar VIP zasu Biya ₦500 ne ta Lambar asusun Dana bada a sama....! Mutanenmu na Niger kuma Zaku iya Tuntumbar My Jika aglan Nissa ta wannan Layin +22794131747....Sai kunzo Masoyana*



*Janafty...*
4/9/21, 1:59 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*


*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!



*032*



"Cikin Tafiya a hankali ya Shigo Cikin Bedroom din,Sadaf Sadaf Saboda kada Hafsah ta Farka kan gadon ya kwanta Lokaci Daya yana Laluban gefen da Hafsah ke kwance yajita Wayam sai ya mike Zaune yayi amfani da Hasken Wayarsa ya Haske Gadon yaga Bai ganta ba sai ya Fara Waige Waige kafin ya mike Tsaye Wutar Dakin ya kunna ya Haske ya Gauraye Motsin Dayaji a Tiolet yasa ya saki ajiyar Zuciya sai yanzu Zuciyarsa ta bashi Tana Bayi ne.

Gefe Daya kuma na Ransa na Wani Tunani kodai Hafsah Tajishi yana waya ne..? Anya kuwa..? Duk sai ya Tsargu Jin Shuru bata Fito ba yasa ya karisa Kofar Toilet din yana Kiran Sunanta Jin Motsinsa da Kiran Sunanta Dayake yi yasa tayi Kokarin Dafa Bangon Bayin ta Mike Tayi Saurin kwabe Rigar Barcin Jikinta ta jefa Cikin kwandon kayan wankinsu Dake Cikin makewayin,Ta yi Sauri ta Zari Towel Dake Rataye saman Wata igiyan Dake Daure Daga sama acikin makewayin.

Taba Kofar yayi yana Fadin"Wai Hafsah me kike Cikin Toilet da wannan Daran..? Kina lafiya kuwa..? Dakyar ta iya Bude baki tayi Gyaran Murya Lokaci Daya Hawaye na kara kwaranyomata Jin Datayi yana Kokarin Bude kofar yasa ta Kamfaci Ruwa a wani karamin Kofi Daga Cikin Bambin Dake Bayin ta Watsa ma Fuskarta Saboda Kada Abdullahi ya gane tayi kuka..

Bude kofar Tailet Din yayi ya Shigo Lokaci Daya yana Bin Hafsah da wani kallo na kamar bai yarda da ita ba ita kuwa sai Tayi Tsuru Tsuru Da sadda kai kasa Saboda kada ya Fahimci Wani Abun Shi kuma mamakin ganinta Da Towel ne ya kamashi Cikin mamaki yace"Ya naganki Haka kuma..? Wai lafiyarki kuwa..? Ko baki lafiya ne muje Asibiti..?
Da Sauri Hafsah ta Girgiza kai Tana"A"a Lafiyata Kalau...Fitsari ya Tadani sai kuma naji Zafi Shine nace bari nayi wanka kila naji Dadin Barci.."Tafada tana Kauda kanta ganin irin kallon Dayake mata.

Cikin Tsareta da ido yace"A'a...Taya zaki yi wanka Awannan Lokacin..? Pass 12 fa kuma kinga bake kadai bane Hafsah Ko zaki bar wankan nan ne Na Samu Ruwa da Karamin Zani na Dinga Shafa miki Ajiki Kila kya samu Barci.."kai ta Girgiza Tana Fadin"Don Allah ka barni nayi zan fi samun natsuwa..Kaga kuma Bayin Daki ne fa.."Tafada Lokaci Daya tana Jan Botiki ta Fara Zuba Ruwa da kallo ya Bita wani Tunani na Shiga Ransa kafin ya kada kai ya Fice Lokaci Daya yana jawo mata Kofar makewayin.


Da kallo Ta Rakashi mai Cike da kunci kafin kukan Datake Rikewa ya Fito ta Sakeshi Gabadaya ammh Tanayi tana saka Hannu kada Abdullahi ya jiyota,Dakyar ta iya Wanka wanda Watsama Jikinta Ruwa kawai Tayi,sai kuma Tsarkin Fitsarin Data bata Jikinta Dashi,Alwala ta Dauro Domin Ta Tabbata Barci bazai Taba Daukan ta ba gwara ta kai kukanta ga Allah kila ya yaye mata Damuwa...!

Tana Fitowa Ta iskeshi kan gado yana Jiran Fitowarta Kai Tsaye ya kalleta yana Fadin"Kin Fito..? Yake tamai Lokaci Daya tana gyadamai kai,Wardrope dinta ta Nufa ta Bude ta Dauko Wata Doguwar Riga ta saka da Hijabi Ta Dauki Darduma ta Shimfida Cikin mamaki yake Binta da kallo ganin zata kabarta Sallah yasa ya Katseta Lokaci Daya yana Fadin"Me zaki yi kuma..? Badai sallah ba..?

Kai Tsaye tace"Eh salla zanyi.."Cikin mamaki yace"Sallah..? Baki sallar Isha"i bane kafin ki kwanta..? Hafsah tace'"Nayi..Na kasa Barci ne Shine nace bari kawai nayi alwala nayi Sallah koda Raka"a Shida ne.."Abdullahi dai kallon Hafsah kawai yake kamar Wata Bakuwa ganin Tana mgana Bata son kallonsa.

Cikin Tsuramata ido yake Fadin"Yanzu fa Farkon Dare ne Hafsah...Ga Jikin ki yayi Nauyi ke baki Tsausayin kanki ne..? Allah ma ya sani Saboda haka bar zencen Sallar nan maza kizo ki kwanta..'Yafada yana nuni da bata Umarni,Kai ta Sadda tana Fadin"Bari to nayi Shafa"i da wuturi Domin banyi ba barci ya kwasheni.."Tafada Batare Data Saurareshi ba ta kabarta Sallah Da kallon mamaki kawai ya Bita acikin Ranshi yana Tunanin kodai Hafsah taji Wayarsa da Barkat ne..? Ammh in Taji ai bai ga alama ba sai dai yana Tunanin kodai bata da lafiya ne..?

Yana nan zaune yana kallonta tayi Idar da Salla Raka"a uku ta Zauna Lokaci da mike kafarta kanta na kasa tana kokarin son maida Hawayenta kada Abdullahi ya gani,shi kuwa yana ta lura da ita da Duk wani motsinta Yana kallonta ta Daga Hannu Tana addu"a Hawaye sun Fito Daga Cikin Idanuwanta Saukowa yayi Daga kan gadon ya Tsaya agabanta yana Fadin"Hafsah..Lafiyanki kuwa..? Kina addu"a kina kuka..?


Jin Haka yasa tayi Saurin Dago kanta Lokaci Daya tana Dangwalo Hawaye tana Fadin"Kuka kuma..? A"a Digon Ruwa ne inaga Abban Amira.."Jinta kawai yayi yana Binta da kallo ganin yadda take kokari wajen Tashi yasa ya saka Hannu ya Dagata cak zuwa kan gado ya kwantar da ita ya Lullubamata Bargo bayan ya Ciremata Hijabin Jikinta Kallonsa Tayi kafin ta kakaro Mirmishi tana Fadin"Nagode.."Mirmishi yayi mata kafin ya Kashe Wutar Dakin ya koma ya kwanta Abayanta ya Zuro Hannuwansa ya Zagayeta Tsakanin Cikinta ajiyar Zuciya ta Sauke Lokaci Daya da wasu Siraran Hawaye suka Zubomata Kalaman Abdullahi nayi mata lugude acikin Ranta kasa Motsi Tayi Saboda kada ya Fahinci Halin Dayake Ciki Bata son ya Fahimci ta san komai Tunda dai bai yi Niyyar sanar da ita ba Duk da ko Tana matsayin matarsa...Ta Dade Batayi Barci ba Tana Tunanin Halayyar Da Namiji Shi kuwa Tana jin Saukar Numfashinsa akan Dokin Wuyanta alamun Barci ya kwasheshi ita kuwa sai gabanin Asuba kana Barci ya iya kwasanta Barci mai Cike da Rudani Da Damuwa.

******

Washegari ma Tana kallonsa Tun Safe yana ta Shiri Su Amira ma Kiran mai mashin Dinsu yayi yace yazo ya kaisu Shi yana Sauri Tun 7am ya Fita ko karyawa bai yi ba yace mata Suna da Meeting a office kallonsa kawai take bata yarda Dashi ba Haka kurum acikin Ranta taji Cewa Wajen Baba wada zashi Kan Mganar Dataji yanayi Jiya,Hawayenta Ta Share kawai ta koma ta lafe kan gado Bayan Mai Mashin Dinsu Amira yazo ya Tafi Dasu kwance kawai take Ammh gabadaya tana jin kanta kamar ba ita ba in ta Tuna wai Abdullahi zai kara Aure.

Illai kuwa Abdullahi na Fita Gidan Baba wada ya nufa ya Fara zuwarmai da mganar,Shi kanshi Baba Wada yayi mamaki Karin Auran na Abdullahi sai dai kuma bai isa yace Don me zai kara Aure Tunda Allah ya Hallartamai Baba wada yace ba Damuwa in Ya tsara komai sai ya kira Mijin Goggo Habiba Su tafi gidansu Barkat din neman Auran Abdullahi yace ya bashi nan da kwana Biyu zai kirashi a waya su Karishe,Da haka suka Rabu da Baba wadan ya Karisa Gidan Mama itama ya zauna ya gayamata yana son ya kara Aure ba Mama kadai Dake zaune ba Hatta da Mariya Dake Cikin Dakinsu Tana Shirin zuwa asibiti,sai da ta Razana Mama ta maimaita Kalmar Auren Da Abdullahi yace zai kara yafi a kirga Cikin nuna ma Abdullahi kamar yayi gaggawa ya bari zuwa Bayan Hafsah ta Haihu ammh sai Abdullahi ya nuna mata Babu komai Ba matsala,Jin haka yasa Mama taja bakinta tayi Shuru kafin ya Tafi sai yace Ma Mama ta Rufe mganar kar kowa yaji Saboda Bayaso mganar takai kunnin Hafsah Don bai gayamata ba Ya bari sai komai ya kamkama uwa uba kuma Cikin Dake Jikinta Baya so Hankalinta ya Tashi.

Bayan Fitarsa Mariya Ta Fito Daga Dakinsu Tana Fadin"Mama Aure naji ya Abdullahi na mganar zai kara ko..? Mama ta kada kai tana Fadin"Hmm Haka yace Nima Abun ya bani mamaki Aure haka Cikin gaggawa..Ni Wlh ban taba kawoma yayanku Aure yanzu ba.."Mariya tace"Tabdijam...Lallenema Toh Mama a ina zai Sakata..? Bai fa gama Gininshi ba Bikin Jidda ya Tsaida komai ga Anty Hafsah da Tsohon Ciki Mama Gaskiya Ya Abdullahi yayi gaggawa.."Tafada Cikin Jin Haushi kamar za"ayi ma kishiya.

Mama tace"Nima shi nagani...Naga Yadda yake Mganar kamar yana son Auran kusa ne ko wata yarinya ce kuma Oho Donni ko Da zence banji Labarin yana neman Aure ba.."Mariya dai ta Rike baki kawai Tana Jajantama Lamarin Haka Auwal ya Shigo ya Samesu yana Tambayan lafiya Mariya ta Koramai Jawabi ido ya Zaro yana Fadin"Aure..? Kan bala"i ita Wacce yarinyace zata kawo kanta..Nifa ina ganin mai iya zama da ya Abdullahi Bayan Anty Hafsah da Wahala Wlh..".

Mama tace"Atoh..Tazo dai ta gani..In Zasu Daidaita in batayi Hakurin Hafsah ba ko"ina bazasu jeba za"a fara jin kansu.."Nan ne dai suka Hadu Suna Ta Tattauna mganar, Karyawa sukayi Mariya ta Fice Zuwa asibiti Auwal ma wanka ya Shiga Domin yana da Class karfe 9am na Safe suka bar Mama Tana Janjanta Abun Cikin Ranta na Tsausayin Abdullahi Daya Jajibo ma kansa Aure

Abdullahi kuwa Sai da yaje Office ya Kira Nazifi yamai Bayanin komai Nazifi ya Cika da Mamakin Jin har yanzu Abdullahi bai bar mganar nan ba Cikin Rashin son yarda Nazifi yace"Kai mutumina anya Abun bai yi kusa ba..Kaga da baka gama gininka ba..Ga Hafsah nada Nauyi Duk kai kadai fa..! Ni ina ganin da kabar mganar kara Auran nan zuwa gaba.."Abdullahi yace"Karka Damu Duk na mata Bayani ta Fahimta..Ta yarda zata Zauna agidana Zan gyara Dakin Da nake ijiye Mashin Dina kafin Zuwa gaba na karisa gina na..Nidai yanzu ka Kira Salisu kai mai Bayanin komai.."Nazifi yayi ajiyar rai kafin yace"Shikenan bari na Taboshi naji.."suka rabu akan yadda sukayi zai Kira Abdullahi ya gayamai.

Nazifi ya kira Salisu Engr.Bayan sun gaisa Nazifi ya koramai Jawabin Komai Salisu bai yi mamaki ba sai ma Farinciki Daya Cikasa Dama Tun ganin Da yayi ma Abdullahi a asibiti yazo Duba Barkat yake ta addu"a aransa Allah ya Tabbatar da Zarginsa Domin Har ga Allah Zai mata Sha"awar samun Nagartattacen Miji irin Abdullahi,Sun Rabu da Nazifi kan anjuma da yammah zai je Gidansu ya samu Hajiya Da mganar ,daganan zai samu Wan Babansu yayi mai mgana Wanda Daman Bayan Rasuwar Mahaifinsu Shi ne ya zama kamar komai nashi.

Salisu ya samu Hajiya Amina Dayaje Gidan Da Daddare ya labarta mata komai nan take Shaidamai Bahiya tazo da labarin Abdullahin na zuwa Wajen Barkat a makaranta,Tayi Murna Sosai tace yaje gidan Wan Baban nasu yamai bayani bai samu ba Sai Washegari yaje yamai Bayani Shi kuma yace Abdullahi ya Turo magabantan Ammh zai Kira Barkat din yaji ta Bakinta kuma ya Kirata wanda taji Abdullahi ya kara Shiga Ranta ganin yadda ya Fada mata kuma ya aiwatar ba kunya tace ta amince Shi kuma yace yana Jiran Wakilan Abdullahi.


Salisu Nazifi ya kira ta waya ya gayamai Shi kuma yace zai kira Abdullahi Suyi mgana,Bama Kiransa yayi ba Washegarin Ranar yazo Zarian ya kawo Jidda ta Rubuta Jamb suka Hadu da Abdullahin yamai bayanin komai jin Haka yasa Abdullahi baiyi Wasa ba suka Tafi Kasuwa Dashi da Nazifi suka Siyo Goro da kwakayan Biskit da Minti da Tabarma dasu Dabino ya Rakashi Atm ya Ciro Kudi 150k Dama Kudin Albashinsa ne ya Ijiyesu ne zai ba Hafsah tayi Siyayyah Suna,toh ganin maganar tataso sai ya Kwaso kawai yana Tunanin Daukan Loan awajen aikinsa yayi Hidimar Biki da gyaran inda Amarya zata zauna Gefe Daya kuma ya Sallami Hafsah kartazo ta Haihu bai Siyan mata komai ba.

Daya ma Nazifi wannan mganar kamar yace wani Abu sai kuma ya Fasa yana Tunanin kodai Asiri Shegiyar Barkat din nan tama Abdullahi ne,Daya Birkice akanta Aransa kuma yana Ji ba Lalle su Shirya da Abdullahi ba Domin Abdullahi bazai iya zama da macen Datake da jin kai da isa kamar Barkat ba.

Gidan Mama suka Fara kai kayan Tagani ta saka albarka Lokacin Jidda na gidan Bayan ta Dawo Daga Jamb din Tabiyo gidan Mama Labarin Auran Abdullahin Har ya Shiga kunnanta Daganan Gidan Baba wada suka Kai mai ya gani ya saka albarka Abdullahi ya Damkamai kudin Hannunshi Duka yace Duk Abunda suka Nemi So yake suyi zuwa Daya ayi komai agama..Shi ya Kira Mijin Goggo Habiba yamai Bayani kuma yace zai Shigo Garin Ranar da Baba wada ya Tsara zasu neman mai Auran ita kanta Goggo Habiba Tayi ta Fada Dataji labari Tana Fadin Abdullahi bai kamata yayi Aure a irin wannan Lokacin ba..

Abdullahi ya Dakatar dasu Baba wada yace gobe Shida Nazifi zasu Tafi Gusai Sai ya gayama Umman Sadiq tukunnah in ya Dawo sai su Tafi kuma Duk abunda ake Ciki Barkat na sane Domin Abdullahi na gayamata,Nazifi nan suka kwana agidansu Shida da Jidda Washegari kuma Tun Safe suka Dau Hanyar Gusai Hafsah Kuma Tuni ta Fawallama Allah komai ko afuska bata Bari Abdullahi ya Fahimci tasan Wani Abu kan karin Auransa ba Ko Zuwansa Gusai bai gayamata ba cemata yayi kaduna zashi Shida Nazifi bata kawo komai aranta ba tamusu Fatan Dawowa lafiya.

Sun Isa Gusai Lafiya da Misalin 11am na Safe Umman Sadiq tayi mamakin Zuwansu kwatsam Haka sai dai bata Nuna ba sai da suka Huta suka sha Ruwa kana Abdullahi ya Sadda kai yana karanta ma Umman Sadiq mganar karin Auransa a karkace Take kallonsa kafin tace"Aure fa kace Zaka kara Abdullahi..? Anya kana da Hankali kuwa..?

Shuru kawai yayi kansa na kasa Nazifi ma Dai baiyi mgana Ba Cikin Fada Umman Sadiq ta Cigaba Da Fadin"Ina Daukan ka mai Hankali Ashe kai Sakarai ne bansani ba kai in banda Rashin Hankali yau ko kyautar Mata aka baka sai ka amsa..? Ka manta Halin Dake ciki ne..? Ina zaka sakata awannan karamin Gidan da kuke Ciki..? Bama kokarinka na ka gama gini gidanka ka Tare kai da matarka ta Haihu achan ba kokarin kara Aure kake kai Abunka ko..? Toh ban amince ba ba kuma zan lamunta da wannan Auran ba yarinya da Tsohon Ciki kasa Hawan jini ya kamata ba.."..

Tafada Tana kokarin Tashi Da Sauri Abdullahi yace"A"a Umma karkiyi Saurin yanke Hukunci..Ita yarinyar ai Tasan ni bamai Wani kudi bane sai Rufin Asiri kuma nayi mata Bayanin komai ta Fahimci..Zata Fara zama dakin Dake kusa da Hafsah kafin na Karisa gini na mu koma Gidanmu Umma mganar Hafsah kuma Da amincewarta Umma zanyi wannan Auran.."Ya Fada suna Hada ido da Nazifi wanda yayi Kur yana kallon Abdullahi yadda ya Shararama Umma karya alhalin Suna Hanya ya tabbatarmai da bai gayama Hafsah komai ba Tukunnah.

Umman Saddiq tayi Shuru tana kallonsa kafin ta kalli Nazifi Tana Fadin"Gayamin gaskiya Nazifi Shin da sanin Hafsah kan wannan Auran.? Nazifi ya Sadda kai yana Jin kunya yin karya gefe Daya kuma yana jin Idanuwan Abdullahi masu Cike da Tsammani a kansa Cikin karfi Hali yace"Eh Umma..Inda bata amince ba kema kinsa Abokina bazai Taba rikoto Aure ba ayanzu.."Yafada yana Takama Abdullahi yatsu Cikin Takaichin karyan Dayasa yayi ma Umma Shi kuwa Abdullahi ajiyar Zuciya Ya Sauke jin Nazifi bai Tona mai aasiri ba.

Umman Sadiq tayi Shuru kafin ta kada kai Tana Fadin"Naji..Wata yarinya ce wai ma zaka Aura..? Nazifi ne yace"Yar Tudun Wada ce...A makaratar ABU samaru suka Hadu kanwar abokinmu ne Salisu Umma.."Umman Sadiq tace"Kenan itama Digirin Take yi..? Nazifi yace"Eh Umma ammh Tana Shekaran karshe ne ta kusa Gamawa"Umman Sadiq ta Tabe baki Tana Fadin"Naji...Sai dai bazan amince da mganarku ba sai na Kira Hafsah Dakaina na Tambayeta Domin Haka kurum naji Ban yarda Daku ba.."

Daga Abdullahi Har Nazifi sai da Gabansu ya Fadi suka kalli Juna..Umman Sadiq na Lura dasu Tatashi ta Shiga ciki ta Dauko Wayarta Tazo ta Kira Hafsah kuma ta saka wayar a Spekear kowani karan Shigan

34 / 48