Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
kare sai wani kanin babansa kadai ya Rage Baba isuhu sai ya"ya da jikoki, Lariyace ke kare mata tana Fadin Aure tayi achan ammh ba wanda ya yarda da Ita.
Bayan Shekara da Tafiyarsu Kawarta da suka Tafi Tare ta Dawo da Tarin Dukiya ita take Fadama Lariya irin kudin da Hajiya sa"a tayi da kuma Riban Datake samu wajen sana"arta Ita kanta Lariyar ta samu Abun Duniya Sosai na Dogayen Rigunan da Sa"ar take aiko mata Dashi Tana Saidawa kafin kace ma Sa"a ta maida kanwarta mai kudi,ana kuma Cikim Hakane Allah yayi ma Mijin Lariyar Rasuwa kuma bata Taba Haihuwa ba kawai sai ta koma tana zaman kanta Bayan an bata Gidan data gada na zaman Takaba,ta koma Chan tana Cigaba da sana"o'inta Kuma suna mgana da Sa"arta ta waya ita ta bata Shawaran ta Fara Fita Dubai tana Saro kaya kada kudaden su Darkane a hannunta da wannan Shawaran tayi amfani Lariya ta Fara zuwa Dubai saro kaya kafin wani Lokaci sunan Lariya mai kayan Dubai ya Fara Shahara,shekara Biyu Tsakani ta Biya kudin Hajji taje Saudiya achan suka Hadu da yar"uwanta Hajiya Sa"a bata iya ganeta ba saboda yadda ta Sauya ta Chanza kuma Tabbas Tana cikin Daula Rayuwa Domin Tana auran wani Mai kudi ne Balarabe ammh Baya som Haihuwa kuma sai da sukayi da Sharadi Kafim auransu suka je aka Juyama Sa"a mahaifa ita kuma saboda Tarin Dukiya ta yarda ta Aureshi baDomim komai ba Saboda tana so Ta gina da kanta kafin ta rabu dashi ta koma Nageria ta Dauko yarta su Zauna tare.
Komai Hajiya sa"a ta samu to Na Jidda ne,Kowani sako zatayi ma Lariya akwai sakom Jidda,ita kuma Lariya bata mika Sakon ga Jidda saboda tataba zuwa gidan Sau Daya da kayan Sakon da Hajiya sa'a kema Jiddan Ammh da Mama ta karbi kayan da ta sake komawa sai ta maida mata da kayan tace Yayansu yace baza ta karba ba Abun ya bata mamaki ammh sai bata Fadama Sa"ar ba bata so Hankalinta ya Tashi,Sai ta Cigaba da ijiye komai awajenta Tana Jiran sai Hajiya sa'ar ta dawo sai ta Fadamata komai acikin Hakane har Ita Lariyan ta Gina katon gida ta tare to da zata taren sai tazo ta Roki mama Ta bar Jidda taje shine data kwana bayan ta Dawo Abdullahi ya Fara fada Sosai saboda Gaskiya ana Rade raden wai Hajiya sa"a karuwanci take a Saudiya tana Turoma Kanwarta kudin Tana kasuwanci bama haka ba Tarbiyan mace bata mace bace sai Tsayayyan Namiji ballatana Jidda Datake da Bala"in Rawan kai da Fi"ili.
Ashe itama Hajiya sa"a tana aiko da Kudi ana Tamfatsa mata, wani katom Gida a chika gari,ta Hannun Hajiya Lariya,Domin tana Shiryan Shiryan Dawowa ne,cikin Lokaci kadan Dayake da kudi Ginin gida ya kamallah aka saka komai na alatun Rayuwa achan Saudiya Hajiya sa"a tana so ta Tsinke Auranta da wannan Balaraben kuma sai abu ya gagara suka Fara Hayaniya Domin yace shi bazai sake ta ba,tayi tayi ammh kuma yaki Dole Dawowarta Nageria ya samu Tsaiko sai da ta Shekara 20cir kafin ta Sako kafarta acikin kasarta ta Haihu Shima Dalilin Rasuwar Mijin nata,bata baro kasar ba sai da aka Raba Dukiyarsa aka bata nata sauran kuma yan"uwansa da ya"yansa suka Raba Ita dai Saudiya ta mata komai na Rayuwa Shiyasa data Dawo Nageria bata ci Kaichio ba sai ma Cigaba tana Tunanin Data zauna acikinta Allah kadai yasan ya Rayuwarta zai kare a wulakance.
Tana Dirowa Hajiya lariya taje ta Daukota Direct gidanta suka Wuce already dama Hajiya lariya ta samo megadin dake gadin gidan Bayan kwama Biyu kuma da Dawowar Hajiya sa"a,Ta sa Hajiya Lariya ta samo mata yan aiki Guda Uku Biyu yan Matasa Daya Tsohuwa sai da tayi Sati Daya da Dirowa kana ta Shigo samaru Cikin Sabuwar Motarta Kiran Jeep,wacce Tun Tana Saudiya ta Turoma Lariya kudi ta Siya mata,Lokacin data isa Babbam Gidansu,kafin afara wata mgana ta Dinga musu barin kudi Sai kika ji bakin kowa Tsit,Baba Isuhu ne Duk da Haka sai da ya maganta,yayi mata Fada Sosai ta kuma Rantse da Allah Aure tayi ba zaman karuwanci ba, Gidansu Mamansu kuwa duk irin Cin mutumcin da suka Tanadar mata ta Rufe bakinsu da kudi Matansu kuma ta basu Tsaran kayayyanki Bayan kwana Biyu kuma ta Dawo ta saka aka Buge garun gidan aka sauya na zamani ta kuma ta Bisu da kudi Domin su ja jari sai kaji baki Shuru sune mai ke Yada ai Sa"a aure Tayi achan Saudiya kuma Daman tazo musu da Hotunan Auranta da mijinta sun gani kuma sun yarda cewa auran tayi Duk da dai mutanan anguwan suna ta gulman yawon iskanci Taje bata damu ba yanzu kawai Burinta bai wuce ta Dauko yarta Jidda ba wacce Rabonta da ita Tun Sadda ta yayeta.
Lokacin Datama Hajiya Lariya mganar kan tana so su Shirya su Shiga Cikin Zaria Wajem marikiyar Jidda tana so ta karbota Aranar ne ta gayamata komai ta kuma nuna mata Uban kayan Data ke aikoma Jidda da bata kaimata ba, sai dai ta ijiyesu,Hajiya sa'a Haushi ya kamata Tana chan Tana Tunanin Rayuwar yarta ta inganta ammh Shine za"a gayamata mganar Banza Ko Dawowarta Rabin Tsarabanta na Jidda ne Har Mota ta bada Odar a kawo mata so take ta Inganta Rayuwarta Sosai yadda Zata ji Dadin Rayuwa Ba kamar ita data sha Wahala ba.
Cikin Bacin Rai Hajiya Sa'a ta kalli Lariya tana Fadin"Wani irin Shanshanci ne wannan Lariya.? Shine kika Boyemin wannan Abun mai matukar muhimmanci..?Kin fa san cewa Komai da nakeyi Duk Dukiyar dana Tara saboda Jidda ce na Dawo ina so na inganta Rayuwarta amatsayina na mahaifiyarta Tunda Tun dana Haifeta bayan na yayeta bata kara Jin Dumin Uwa basai dai na ganta a Hoto wanda kike Turamin,sai yanzu ammh kuma kika Boyemin wannan Abun mai girma..?
Hajiya Lariya Ta rausayar dakai Tana Fadin"Kiyi Hakuri Yaya Abunda yasa ban Fada miki ba Tun Lokacin bana so a Hankalinki ya tashi ne.."Wani Wawan Tsaki Hajiya sa"a ta Saki kafin tace"Ita Karimar ce tafada miki cewa Bazasu karbi komai ba..? Ko ta manta ni Sa"a ni na Haifi Hauwa"u da Cikina..?Tafiyata Saudiya ba Dadewa naji Labarin mutuwar Alhaji Usman wake Daukan nauyin yata..? Nasan Tana chan tana Shan wahala ya zama Dole yau ba sai gobe ba naje na Dauko yata ta Dawo Hannuna Har Abada.."
Hajiya lariya tace"Ba ita bace taki karba Cewa tayi yayansu yace Jidda bazata karbi komai Daga wajenki ba Domin bata Bukatarsa.."Hajiya sa"a tace"Yayansu kuma.? Waye kuma yayansu..?
Hajiya Lariya tace"Oho ina na sanshi Banta ba ganinsa ba ammh ai na gayamiki na zan tare a sabon Gidana naje da kaina na Roki karimar sanna ta bari Jidda Ta Biyoni Dare yayi mata sai ta kwana baki ga yadda ta kirata tana mata Fadan ta Dawo gida yayansu na Fada ba, Danaga Jiddan ta Rude ne yasa na Tambayeta wanene sai take Fadamin wai ko yayansu wama..? yauwa Abdullahi tacemim kamar Shine Babba inaga shi ke Dauke dasu gabadaya Domin Jiddan na gayamiki makaranta mai kyau take kuma bata Cikin Wahala gaskiya.."
Hajiya Sa"a ta koma Ta zauna Dabas Tana Dafe kai kafin tace"Inaga Yaron Matarshi ta Farko ce daman naji labarin Yana da Babban yaro namiji Shima ba"a gidan taHaifeshi ba Shiyasa ban sanshi ba..."Hajiya lariya tace"Nima dai ban taba ganinsa ba
Hajiya Sa"a tace"Ki Shirya muje Gidan...Ko da Karfin Dukiya data Sharia sai yata ta Dawo Hannuna ina so na Jiyar da ita Dadin da ban Jiyar da ita ba A baya ba..."
Daga haka Tatashi tana wani Taku Mazaunanta na Juyawa Ta Shige Cikin kayattacen Bedroom dinta Hajiya Lariya ta Bita Da kallon Tsausayin ganin Ta Cikin bacin Rai.
*Shakira..*
4/9/21, 1:56 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*
*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!
*020*
"A Ranar su Hajiya Sa"a basu samu Tafiya ba sakamakon Tana Cikin bacin Ran Rashin gayamata Abunda ke Faruwa da lariya batayi ba Shiyasa ko Waya Datace Zata Turo kudi a siyama Jiddan lariyan ta Hana,ta kawo mata Excuse din cewa Ta bari sai ta Dawo har yanzu Jidda Yarinya ce ko waya sau Biyu suka Taba Mgana da ita Lokacin da tazo Tariyan Sabon Gidan Ita Lariyan Abunda yasa bata maida Hankali ba Saboda Tana chan tana kokarin Tattara Dukiyarta waje Daya ta Dawo gida Shiyasa bata maida kai akan Lamarin ba ballatana Har ta Fahimci akwai mtsala.
Sai washegari Ranar Talata Tun wajen karfe 11am na Safe Hajiya Sa"a Ta Biya ta gidan Lariya ta Dauketa acikin bakar Jeep dinta Saboda bazata iya gane gidan ba gaskiya Rabonta da cikin gari Tun Ranar da Usman Direba ya saketa Rabonta da kafarta ta Taka Babban Dodo to tana Yaye Jidda Bayan an maidota ta Bi kawarta suka Tafi Saudiya.
Da suka Shigo anguwar Hajiya Sa"a Taga Chanje Chanje dadama Na Gidajen zamani da kuma Cigaban Rayuwa Tace ma Lariya in ita kadai ce bata iya gane ko"ina,Bata gama mamaki ba sai da Lariya ta nuna mata gidan Tabishi da kallo acikin Ranta tana Fadin am samu Chanji Domin Abdullahi ya gyara gidansu Sosai bama samfarin Ginin Baya bane wannan na zamani ne.
Siririn Gilashin Fuskarta ta zare Tana Bin gidan da kallo Ta Madubin Motarta Cikin mamaki Tace"Lariya gida nan ya Sauyamin Sosai in ni kadai nazo ban iya ganewa.."
Hajiya Lariya tace"Eh gaskiya kam Yaya ai Shekarun fa da yawa ba gidan ba Duka anguwanma an samu Sauyin Yanayi Ballatana ma Gidan gaskiya ko bayan Rasuwar megidan bai Lalace ba Yayannasu ya tsaya akan gidan Sosai.."Kai kawai Sa"a ta kada kafin ta Daidaita parking a kofar Gidansu Abdullahi.
Firfitowa sukayi Lokaci Daya Hajiya sa"a na gyara zaman mayafin kanta Tana sanye ne da wani leshi mai ubansu kyau da Tsada ta Saka mayafi har kanta sai wani takalmi mai Tudu Hannayenta suna sanye da zabban Zinare harda Wuyanta da Awarwaro,Fuskarta kuma tana Sanye da wani medicated Glass dan karami na karin karfin gani ko na gayu ne bansani ba,Sai karamar jakarta mai kama da pos dake rike hannunta wanda wayarta ke Ciki sai key din Motarta makale a Yatsanta na Hagu.
Area din take bi da kallo,ba yalwar Mutane saboda Safe ne ma"aikata Duk sun Tafi aiki Yara na makaranta magidanta kuma sun Fita neman Abun bama iyalai Hajiya sa"a Ba fara bace ammh Tana da kyau daidai misali yar kimanin Shekara 46 aduniya ce kallo Daya zaka mata ka Fahimci ta goge a Duniyanci da kuma Bariki idanuwanta suna Bude ne sosai Daga ganinta tayi Shige Shige Sosai Domin Hancinta yana Dauke da Huji ne,sai bakinta dake Jere da Hakoran Makka Har guda Biyu,ita kanta Hajiya Lariyan Shigar alfarma tayi Sosai in ka gansu zaka Fahinci Yaya da kanwa ne saboda suna Tsantsan kama da juna.
*****
Mama na Cikin Daki Tun da tagama Sallar Walha ta Zauna tana addu'o'inta bata Tashi ba,gidan ba kowa Daga ita sai Jidda sai Auwal dake dakinsa yana Barcin asara Mama tayi Tashin Duniyan nan ya tashi ya Tafi Shago Tunda yau bazashi Makaranta ba ammh yaki Fitowa ko Karyawa bai yi ba Sai kawai ta Fita batunshi Mariya kuma Ta tafi asibiti Tun safe in aka Turata.
Jidda na Tsakar gida tana Wanke wanke yan kwanukan da suka Bata ne da kayan karin safe,Taji sallama kamar Daga saama Da Farko bataji ba sai da Hajiya Lariya ta Daga murya ta kara Maimaita Sallaman,kana Jidda taji ta Dago da kanta Daga saman yar Kujeran Tsakar gidan Data ke kai sai kawai taga taci karo da Lariya Baki ta Bude harda Hanci Tana Bin ta da kallo Cikin kayattacen Mirmishi Hajiya Lariya tace"Jidda..."
Da Sauri Jidda ta mike Tana Fadin"La.! Anty Lariya kice...? Tafada Cikin murna tana Rufe bakinta kafin ta Zura da gudu ta Fada Jikinta Tana murnan ganinta Hajiya Sa"a Dake bayan Lariya Hawaye suka Cika kwarmim Idanuwanta,na ganin Tilon yarta wacce Rabon ta da ita Tun Tana da Shekara Biyu da wani Abu aduniya,Jidda Dake Rumgume da Lariya idanuwanta suka kai kan Hajiya Sa"a Dake baya Tana Binsu da kallon Sha'awa,Da Sauri Jidda ta Saki Hajiya Lariya Ta matsa Gaba Tana kallon Hajiya Sa"a Cikin Bugawar Zuciya,Idanuwanta kamar zasu Fado kasa,Kamar Mommy ta take gani,wacce bata taba ganinta ba sai dai a hoto Lariya ce Taga yadda suke kallon Juna Dukkansu yasa Ta Rike ma Jidda Hannu ta Jata har gaban Hajiya Sa"a Ta Dauki Hannuwansu ta Hada waje Daya Tana Fadin"Jidda kin gane ta..?
Bakin Jidda ya kasa Mgana kawai sai Hawaye sharr Hajiya Sa"a ta kasa Hakuri kawai sai ta jawo Jidda ta Rumgumeta tana Fadin"Kinga ne ni Hauwa"u..?nice Mahaifiyarki Nice Ummanki.."Tafada Cikin wani matsanancin kuka itama Jiddan Rumgumeta tayi Lokaci Daya ta Fashe da kuka Cikin Shakakiyar murya take Fadin"Mommy...!!!!
Mama Dake Daki Taji kamar Mgana Sama sama da kuka ko Hijabin Jikinta Bata Cire ba ta Fito Tsarkar gidan Tana Kiran Jidda sai kuma tayi Turus ganin Jidda Rumgume Jikin wata mata Dukkansu suna kuka Cikin mamaki tatako gabansu Tana Fadin"Subnallahi Jidda lafiya..? Wacece wannan.?
Hajiya Lariyace ta Waigo Suka Hada Ido Cikim Mamaki Mama tace"A"a Hajiya lariya ce.."?Lariya tayi Mirmishi Tana Fadin"Eh mune karima."Tafada tana kallon Jidda da Hajiya Sa"a wanda suka saki juna Lokaci Daya suka Bi Juna da kallo Cikin Shauki da Soyayyar Uwa da yarta Mama Ta bisu da kallo Cikin mamaki kafin ta samu Zarafin mgana Hajiya lariya tace"Karima kin gane wacece wannan kuwa..?
Mama tabi Hajiya Sa"a da kallon Mamaki wacce ta kara Rumgume jidda kamar ta maidata Ciki saboda So da kauna Cikin Girgiza kai tace"Ban gane ba gaskiya."Ta fada tana kara Kallon Hajiya Sa"an Tana so ta Tuna inda ta san Fuskarta ammh sam ta kasa Tunawa Hajiya Sa"a ne da kanta ta Dago Jidda Daga Jikinta Ta kalli Mama Tana Fadin"Karima baki ganeni bako..? Sa"adatu ce Sa"a mahaifiyar Hauwa"u."
Ido Mama ta zaro kafin tace"Sa"a.?kice haka.? Ikon Allah Ba Shakka sai yanzu na ganeki ina ta kallonki Araina ina cewa kamar Sa"a kamar ba ita ba.."Hajiya Sa"a tayi Mirmishi Tana Fadin"Nice karima..Ai Shekarun da yawa ne.."
Mama tace"Duk da haka dai kin Chanza Sa"a kin kara kiba kamar bake ba Wlh ku Shigo Ciki kwa Tsaya Daga waje ke Jidda Shigo Dasu Ciki mana Tsiyana Dake wauta wani zubin.."Tafada tana Wucewa Daki da Sauri Hajiya Sa"a Tayi Mirmishi Lokaci Daya Tana Riko Hannun Jidda wacce Bakinta yaki Rufuwa saboda Murna,gefedaya kuma Hawaye Duk ya gama wanke mata Fuska.
Dakin suka Shiga suka samu waje suka zauna kan Daya Daga Cikim kujerun Falon,Jidda na nanike da Hajiya Sa"a kamar zata koma Cikinta sai kallonta take tana jin wani Farinciki acikin Ranta na yau gata ga mahaifiyarta wacce ta Haifeta,Mama kuma kitchen ta koma ta Dauko,musu Ruwa da Lemo,ta sako Cikin wani Babban Faranti ta Hado da kofuna ta kawo musu kana ta zauna suka kara gaisuwa.
Mama tace"Ikon Allah Sa"a yaushe agari..? Tun lokacin akace kin Tafi Saudiya..? Hajiya Sa"a tace"Eh Wlh Last week na dawo..Abubuwa ne sukamin yawa yasa ban samu zuwa ba sai yanzu.."Mama tace"Ikon Allah Ai kinsha na Saudiya wajen Shekaru ashirin fa.."Mama tace"Gaskiya kam.Bayan Tafiyata naji Labarin Rasuwar Mahaifin su Hauwa"u ya karin hakuri karima.?
Mama tace"Umh kedai bari..Hakuri da godiya kafin Rasuwarsa har gidanku yaje nemanki akace kin Tafi Saudiya..'Hajiya Sa"a tace""Eh wlh Haka Lariya take Fadamin..Allah ya jikansa da Rahma ya yara..? Yaran daya bari su nawa ne ma..?
Mama tace"Ameen Ameen..Su Shida ne,gasunan duk sun Girma.."Hajiya Sa"a tace"Allah sarki...Allah ya baki ladan Rikonsu kema..'Mama tace"Ameen bakomai..Kusha Ruwa mana Lariya.."Hajiya Lariya tamurmusa taDauki kofi ta Tsiyaya Ruwa tasha Kadan ta ijiye Mama kuwa sai kallon Hajiya Sa'a take Cikin mamaki da ganin yadda ta chanza Daga gani kudin sungama zauna mata Cikin sakin Fuska Mama tace"Kin dawo gabadaya ne ko zaki koma chan Sa"a..? Kamar naji an ce Kin yi aure achan ne ko Lariya kema kika Fadamin kuwa..'"
Hajiya Lariya Tace"Eh Tayi aure achan mijin ya rasu ne..Shine ta Dawo gida gabadaya."Mama Tace"Ayyah Allah Sarki..Allah yaJikansa da gafara kin dawo kenan gabadaya..? Da yaranki kika Dawo ko suna chan wajen Dangin Ubansu.."?
Hajiya Sa"a tayi Dariya Tana Fadin"A"a ai ban haihu ba..."Zaro ido Mama Tayi Tana Fadin"Baki Haihu ba.? Kai Sa"a kodai kin Tsaida Haihuwan ne..?
Hajiya Sa"a Tace"a"a ...kawai Allah ne bai kawo ba."Tafada tana Dariya Mama tace"Hakane kuma..Komai dama na Allah ne kice sai jidda kadai ta Fari kuma Auta Dama ga Jidda da son Jiki yau dai an ga Mama an manta Dani.."Tafada tana kallon Jidda,Wacce tayi Dariya ta Sinne jikin Hajiya Sa"a Lariya ce tace"Haba dai...Aiko Taga Mama ke uwartace Har Abada.."Hajiya Sa"a Ta karbe da Fadin"Sosai ma wanda zai Rike maka yaronka Tun yana karami ai Abun ka godemai ne,..Angode Sosai Allah ya saka da alheri.."Mama tace"Ameen bakomai wlh..Ai ni nawa kawai kula dasu ne duk wani Dawainiyarsu yayansu ke yi Ci da shansu makarantarsu,Tarbiyansu da kuma kula da komai namu Wlh Shine Tunda yaronan ya kawo karfi yake Wahala Damu,Sai dai kawai muyi Fatan Allah ya Biyashi ga Tamu laluran gata Iyalansa ammh bai Taba gazawa ba."
Hajiya Sa"a tace"Allah Sarki..Allah ya Biyashi bangane yayan nasu ba Shine Babban su ko..? Mama tace"Eh bazaki ganesa ba gasakiya Domin sai bayan Barinki gidan ne Marigayi ya karbo sa Yaron wajen Hajara ce ta gusai matarsa ta Farko.."Hajiya Sa"a tace"Oh Allah Sarki...Na ji labarinta kuwa.."Mama tace"Wlh kuwa Shine komai namu Shiyasa Lokacin da Lariya ta kawoma Jidda Sako Tace in jiki Taga na maido mata Wlh shi ya Hana Akarba Shiyasa nasan kuma ta gayamiki ko..?
Hajiya Sa"a zatayi mgana kenan Auwal ya Bude labulen dakin ya Shigo yana mutsuke ido Dukkansu suka Dago suna kallonsa Mama takallesa Tana Fadin"Akwana a hantse sai dan Hutu.Sai yanzu aka tashi kenan Alhaji Auwal.?
Dariya ta kama Auwal ya Sosa Kansa yana Fadin"Kai Mama..? Banfa wani Dade ina barcin ba..kuma Yaushe ma nake samun Lokacin barcin in ba yau ba.."Mama ta Harareshi Tana Fadin"Kana fa samu..Baka ga baki bane..,? Mahaifiyar Jidda ce da kanwarta.."
Sai Lokacin ya Dago yana kallonsu Cikin mamaki gaishesu yayi suka amsa suna kallonsa Jidda ya kallah yana wani Tabe baki kafin yace"ji ta kamar wata karamar yarinya sai wani Shagwaba take."Baki ta Tura tana Kallon Mama tace"Mama kinganshi ko..?
Mama tace"Rabu dashi Babban Banza ne,Dole kiyi Shagwaba gaki auta gaki kuma mai uwaye Har Biyu.."Hajiya lariya tayi Dariya Tana Fadin"Ai kuwa ita yar gata ce gaba da gaba.."Auwal ya kada kai yana Fadin"Yar gata ko Shagwabbabiya duk