Advertisements
Chapter 41 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   41 / 48

120K to 123K   out of 143.7K words

yar ba Uwarki Ba Mutuniyar kirkir ce ba,ana ta Dariya,Suna Cikin Rawan ne sai ga Bahijjat da Matar Salisu yayan Barkat sun leko Sunan Hafsah ta karbesu Hannun Bibbiyu,Bahijjat Ta gane sai ita Bahijjat din ce tamata Bayani matar yayansu,sai Bayan mangariba suka tafi.

Sai Bayan Isha"i Gidan ya Ragu ya Rage Daga Mariya sai Zannira sai Anty Hadiza da Subai Jidda bata zo ba Daman Nazifi yace bazata samu zuwa Suna ba,Auwal sai Dare ya leko Yace Daga gidan Mahaifiyarsa yake Mamarsa tazo garin Har tazo tayi ma Mama barka Shine ya Rakata gida Daganan ya Biyo ta nan, nan Subai ke Tambayansa wai Aure tayi achan Niger din..? Yace mata eh har ta Haihu Wajen uku bata dai Dade da yin Auran bane,Dayake Auwal din yana waya da Mahaifiyarsa sosai kuma tana yi mai Sako,Gidan kakaninsa ma yana zuwa Suma suna Zuwa Wajensa Lokaci Bayan lokaci.

Abdullahi bai Shigo gidan ba sai Wajen 9:30pm na Dare yana Shigowa da Mashin Dinsa Dakin Barkat ya Fara kallah ya ganshi a kulle Ransa ya kara wani baci,yaji wani Abu ya tasomai Daga kasan Ransa Har ya Daidaita zaman mashin dinsa ya Sauko Abun ya kasa sakinsa,Dakyar ya leka Dakin Hafsah suka gaisa da su Anty Hadiza,Su Subai suka gaisheshi ya amsa Yana Fama dasu Amira da su Muhsina wadanda suka Rukumkumeshi,suna mai oyoyo Haka ya kwashesu har Bedroom din Hafsah ya isketa zaune gefen gado Tana Bama Noor Nono Tana ganinshi ta sakarmai Mirmishi Tana Fadin"Abban Noor.."

Gefenta ya zauna yana Fadin"Nidai Ban yarda ba gaskiya ana ta yima Uwata Tawaye..Daddy yayi mata Baba wada ma Haka kema yanzu Abban Amira ya bace Daga bakinki Na koma Abban Noor ne.."Yafada yana wani kwabe Fuska lokaci Daya yana kallon Hafsah Wacce Dariya ta kamata Ganinsu Amira yasa ta korasu Wajen Anty Hadiza,Suna Fita ta Ciro Noor Daga Nono ta mikama Abdullahi Lokaci Daya Tana Fadin"Meke Damunka...?

Kai Tsaye te jefamai Tambayan karban Noor yayi yana Fadin"Me kika gani..? Ya suna ya Hidima..?
Kafadarsa ta Dafa tana Fadin"Lafiya lau Alhamdulillah...Allah Abban Amira wani Abu na Damuka naga Ranka abace ne..? Kallonta yayi ido Cikin ido kafin ya kada kai yana Fadin"Shiyasa nake fada bayan Mama da Umma kece mace ta uku datafi kowa sanina...Karki Damu Bawani Abu ne Gajiya ce ina yin wanka naci Abinci zan wartsake.."Mikewa Hafsah tayi tana gyara Wuyan Riganta Lokaci Daya tana Fadin"Bari na saka Subai ta Hada Maka Abinci..Dakin Barkat din zaka zauna..?

Kai ya gyada mata Lokaci Daya yana Fadin"Koma ki zauna In na Fita zan mata mgana ta Bani abinci karki damu kinfini Bukatar Hutu.."Komawa tayi ta Zauna tana Fadin"Kawota toh kaje kayi wanka kaci Abinci ka kwanta Sannu.."Mikamata Noor yayi ya mike yana Sakin Siririn Tsaki Lokaci Daya yana Fadin"Bari naje...Sai da Safe.."Hafsah tace"Allah Tashemu Lafiya..plz Abban Amira kaci Abincin ka kwanta ka Huta kaji ko..? Dukawa yayi ya Sumbaci goshinta yana Fadin"Insha Allahu Matar Abdullahi.."Itama Martanin Mirmishin ta maidamai Har ya Fice Daga Dakin,Tana jinsa yana Cema Subai ta kawomai Abinci Dakin Barkat yana Jiranta Daganan ya Fice Dakin ya Bude ya Shiga wanka ya Shiga ya gasa Jikinsa kana ya Fito ya saka Jallabiya Ya iske subai ta kawonmai Abincin,Ya zauna yaci kadan,ya ture ya koma ya kwanta akan kujera yana kokuwa da Bacin Ransa yana Tunanin ba Shakka Barkat bata sanshi ba,sanin da tayi mai ba wani mai yawa bane,domin Data sanshi bata yi kokarin Saba Umarninsa ba.

Haka ya kwana Cikin Bacin ran Barkat,Da safen ma kafin Ya tafi Office Cikin ABU din ya Shiga kuma ya Jima ammh Bai nemi Barkat din ba Daganan ya wuce Wajen aiki,ita kuma Barkat ta Damu Bayan Har Dare taga Abdullahi bai kirata ba,Taso ta kirashi sai kuma ta Fasa,Da sukayi mgana da Bahiya ta gayamata Abunda ya Faru Fada ta Hau mata ta nuna mata bata kyauta ba,mijinta ne ya isa da ita ne,Shiyasa yace ta koma Jin Bahiya ta bata Rashin gaskiya yasa sai ta Sauko,ta yanke Shawaran zata koma,ganin Yammah tayi sai ta bari sai da Safe,Bayan ta gama Abunda zatayi ta Ta Hayo Mota Ta Dawo Lokacin Data Shigo Gidan ma Kaskon karshen ake soyawa na Naman suna,Tuni sun gama komai,Gaishesu tayi suka amsa banda Subai Datake nata wani kallo Dakin Hafsah ta Fara Shiga ta Dauki Noor suka gaisa Sai ga Anty Hadiza ta Shigo nan Hafsah ke nuna mata Anty Hadizan tace yayarta ne,Barkat din ta kara gaisheta ta amsa Cikin Sakin Fuska tana kallonta tana ganin kamarsu da Hafsah din.

Ta dan Jima Dakin Hafsah din kafin ta Fito zuwa Dakinta,makulli ta saka ta Bude ta Shiga Dama Daga ita sai yar jakarta Data sako Littafan karatunsa kaya kuma bata zo da ko Daya ba sai Hijabi Tunda tana da wasu anan gida da yawa ma,Tunda ta Shiga Daki ba wanda ya karajin motsinta sai da aka gama girki mariya ta leka ta kai mata ta amsa sai kuma zuwa chan Bayan an Raba Naman Mariya ta mika mata ta karba tayi godiya an Dibar ma Abdullahi sai Hafsah da yara,sai Mama da ita da su Inna Abu,da goggo Habiba sai Ammi da Daddy sauran kuma suka Raba ma kansu sai na Mokota Zuwa La'asar sun gama komai kowacce tayi wanka sai Shirin Tafiya Zannira gidan Mama ta wuce da nasu Maman Bayan sunyi sallama da Hafsah kan gobe zata wuce,Anty Hadiza ma Gidan Ammi tayi itama Goben zata koma,Subai kuma Ta nan sai Bayan mangariba Mijinta zai zo Daukanta saboda yara,Auwal ma yazo Hafsah ta bashi nashi,ya karba yana ta Godiya Subai yabi da mijinta yazo Daukanta zasu ijiyesa agida.

Gida ya Rage Daga Mariya sai Hafsah sai su Amira Barkat na Cikin Dakinta ko motsinta Ba"a ba yau Abdullahi da Wuri ya Shigo Gidan Ana yin Sallar Isha"i Barkat na Jin Shigowarsa kuma ya yada Zango Dakin Hafsah Duk da yaga Dakin Barkat din da Hasken Wuta,Hafsah ta nuna mai komai yadda aka raba yace yayi kyau nashin ta ijiyemai anan ne yace mata Eh nan take Fadamai Barkat ta Dawo kuma an bata nata bai ce komai ba Ganin haka ita Hafsah bata kawo komai ba,Ta shiga nuna mai Kayan Sunan data samu tare da bayanin Sunan wadanda suka bata yana ta gani yana godiya da saka albarka nan Dakinta yaci Abinci,dayace zai yi wanka Hafsah ta kalleshi tace"Abban Amira kaje Dakin Barkat mana Kayi achan..? Ai yanzu ka zama nata Har sai nayi Arba"in ni da Noor mun kara Samun Lafiya.."

Hararanta yayi Lokaci Daya yana Fadin"injiwa..? Wannan Tsarin ki ne ba nawa ba Malama.."Yafada yana Tura Kofar Toillet,ya shige yayi wankansa ya Fito ya saka Jallabiya,Yazo ya Dauki Noor ya Fita zuwa Falo yana Biye ma su Amira suna wasa da Noor tana Hannunshi.


Barkat kuwa Shuru Shuru bata ga Shogowar Abdullahi ba gashi taci kwalliya tana Tashin kamshin Tun Tana saka Ran Shigowarsa har ta Fara Sarewa wayarta ta Dauka ta Kirashi bai Daga ba ta kara kira bai Daga ba Kira na uku ne ya Kashe mata kiran Gabadaya,Baki Barkat ta Bude Hawaye na Cika mata ido Kishi ya Turniketa Domin Acikin Ranta tana Tunanin Duk Fushin da Man yake akanta Saboda Hafsah ne kan kujera ta Fada tana Sakin kukan Daya taso mata Daga kasan Ranta.

Hafsah kuwa ganin ana ta Kiran Abdullahi bai Daga ba yasa ta Zargi wani Abu kai Tsaye ta kalleshi Tana Fadin"Kawo Noor Abban Amira kaje Ka kwanta ka Huta..Ke Amira maza kije kiyi Fitsari keda Amir kuje ku kwanta Wajen Anty Mariya.."Jin haka yasa suka Shige Cikin Bedroom Din har suna Rige Rige.

Abdullahi ya gane Nufunta sai dai bai Tanka mata ba ya mika mata Noor din ya mike Lokaci Daya ya Dauki Wayarsa yayi mata Sallama ta rakashi Har Kofar Daki,yana Fita ta maida kofar ta kulle ta koma Daki Afili ta Furta.."Hmmm yau Barkat ta taba yan Maza..Allah ya Kyauta kiga Masifar Abdullahi yau."


Tana Kwance kan kujera bayan ta gama Kukanta ta Share Hawayemta,taji Shigowarsa Da Sauri ta tashi Tana kallonsa Shi kuwa Ransa ya Hade Tamau kawai ya Rabata zai wuce da Sauri Tasha gabansa Lokaci Daya ta Fada Jikinsa tana sakin mai kukan Shagwaba Lokaci Daya Tana Fadin"My Man ka sakani kuka..?

Tafada tana kara lafe mai Bisa Jikinsa,Haushi ya kara kamashi Da Sauri ya saka Hannu ya bambareta Daga Jikinsa Kai Tsaye Yana kallonta itama Shi take Kallo ta wani karya wuya,gefenta ya Raba zai Shige Cikin Bedroom din tayi Saurin Riko Hannunsa Tana Fadin"Plz mana my Man Am Sorry...!

Ta Fada tana wani karya Murya,Da Sauri ya waigo Cikin Fusata yana Fadin"Sake ni Don Allah...! Yafada cikin kakkausan Murya Da sauri ta Sakeshi Tana kallonsa karamin Tsaki yaja yana Fadin"Ban da Tsabar kin Raina ma kanki wayau Ashe kinsan Abunda kika aikata Tunda kike bani Hakuri..? Ya fada yana Tsare da ido Da Sauri tace"ba haka bane My M..."

"Dakata Don Allah..."Yafada Lokaci Daya yana Dagamata Hannu Da sauri Barkat ta Kama bakinta ganin yadda yake jifanta da wani kallo lokaci Daya yana Fadin"Har ni na baki Umarni nace miki ki Dawo Gida Jiya da Safe ammh Tsabar kin Rainani baki Daukeni a matsayin Mijinki Tunda Har zance ga Abunda Zaki yi ammh Kika nuna min iyakata Tunda sai yau zaki kwaso kafafunki ki Taho Toh kin makara da kin sani baki Dawo ba Domin da Dawowarki da Rashinsa Ni awajena Duk Dayane Barkat....Sai dai ina So ki san Wani Abu Guda Daya Wlh Tallahi kinji ma na Rantse miki Ba wata ya macen da Zan Aura tana karkashina kuma na Bata Umarni taki bi,ko kuma ina mgana tana min gaddama ko kuma In bada Umarni taki bi tace Ita sai Ra"ayinta za"a bi Toh bazamu Shirya ba..Ni agidana Namiji ne kuma Jajirtattace ne,kuma mai Fada aji kuma mai iko ne kuma mai Fada ne Wajen matarsa ke bama Ke da kike matsayin matata ba Bama Hafsah Da Take matsayin matata ba Wlh ko Kannena Dake Gidan Auransu ina Saka Musu Doka kuma su Bi,kuma na basu Umarni su bi Ballatana ke da kike karkashin Ikona,Toh Baki isa ba Karatun ma da kike yi Ra"ayina ne in yau nace Kin gamashi Wlh Ko Duniya zasu Taru akaina baki isa ki Komata ba Wlh,Baki sanni ba ko..? Hmmm ki Tambayi Hafsah Zata Fadamiki kowaye ne Indai kina son zaman Lafiya ki Bini a sannu ko kuma Wlh Ranki yayi ta Baci indai Bazaki san Abunda kike yi ba.."

Ya karishe Fada yana nuna ta da yatsa Lokaci Daya yana Sakin Numfashi,Afusace ya juya ya Shige Cikin Bedroom din ya Hau gado ya kwanta yana Jin Haushinsa akan Barkat ya Ragu ita kuwa da ido ta rakashi Har ya Shige,Jikinta a sanyaye ta koma ta Zauna kowani Dakika maganganunsa suna mata amsa kuwwa Cikin kunni Afili ta Furta"Topha..!


*Domin Biyan Kudin Karatu akan Littafin Ra"ayi ne ko Buri..? Zaku iya Tura kudin karatunku ₦200 Kachal akan wannan asusun bankin 0552179550...JAMILA UMAR GTB,Sai a turo Shedar Biya ta wannan layin wayar 09069067488,In kuma Katin Waya ne zaku iya Turowa ta wannan Layin 09027767783 kai Tsaye Bayan Mutum ya Dauki Hoton katin...Ga masu Bukatar VIP zasu Biya ₦500 ne ta Lambar asusun Dana bada a sama....! Mutanenmu na Niger kuma Zaku iya Tuntumbar My Jika aglan Nissa ta wannan Layin +22794131747....Sai kunzo Masoyana*




*Shakira...*
4/9/21, 2:00 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!


*037*




"Ta Dade zaune maganganun Abdullahi na mata amsa kuwwa acikin kunnuwanta,Mamaki ya kamata wani irin Bakin Kishin Hafsah ya mamaye mata Rai Tana Tunanin ba saboda komai Abdullahi ya gaggayamata wadanan mganganun ba sai Saboda bata zo Sunan Hafsah ba In ba Haka ba Me tayi mai da zafi da zai gayamata Haka.

Kishin Hafsah ya Tsaya mata arai Ta kasa Sukuni sai tayi yunkurin tashi ta bishi Ciki sai kuma Ta Fasa,sai da ta Sassaita kanta kana ta mike ta Bishi Cikin Bedroom din Zuciyarta Cike da Kishin Hafsah me Tsanani na ganin yadda Ta kama Zuciyar Abdullahi komai zai yi ko mgana zai yi sai ya ambaceta.

Koda ta Shiga ta iskeshi kwance yayi kwanciyar D'aida'i Bisa Gadon Idanuwansa na kallon Rufin Dakin,Yana ganin Shigowarta ya Juya baya Lokaci Daya yana gyara kwanciyarsa,Karisawa tayi Cikin Tafiyar kasaita zuwa gabansa ta Rankwafa Tana Fadin"My Man..! Tafada Tana kallonsa Ganin ya wani Lumshe ido Kamar mai Barci.

Kara Karya Murya Tayi Tana Fadin"Am Srry kayi Hakuri Bazan kara ba..Kuma a think in ban zo Sunan ba wannan karon akwai Next Time ko..? Tafada tana kallonsa Ganin yaki mgana yasa ta Dora Hannunta saman Kirjinsa Tana Shafawa,Karaf kuwa ya Bude Idanuwansa ya Sauke akanta Lokaci Daya ya Saka Dayan Hannunsa ya Dauke nata Hannun kafin ya mike Zaune batare Daya mata mgana ba Yaja Filonsa ya Tashi zai Fice Daga Bedroom din,Da Sauri Ta Mike Zata Biyoshi Tana Fadin"My Man...!

Bai bari ta karisa mgana ba ya juyo a Fusace Yana kallonta lokaci Daya yana Nunata da yatsa yana Fadin"Kinga..? Kinsan Allah..? In kina son kanki da arziki kada ki Biyoni in kuma baki ji ba Kika Sake kika Biyoni kina Damuna Wlh Tallahi zan Fita na bar Miki Dakin nan in kuma na Fita bazan Dawo ba sai dai gobe..!Yafada Cikin Kakkausan Murya ya Fadi Haka Lokaci Daya kuma yana jan wani Dogon Tsaki ya Fice Daga Bedroom din yana Fadin"Banda Iskancin Banza da Raini Miye na Damuna na kwanta ina jin Barci..? Kin gama  yin Laifin da gangan kuma ki Dawo kina son Rainin min Wayau..wlh baki isa ba ba wacce zan auro Tana karkashina tace bazata bi Umarni ba.."

Galala Barkat tayi Tana Bin Abdullahi da kallo har ya Bar mata Dakin Ajiyar zuciya ta Sauke kafin ta koma Gefen gado ta Zauna tana Fadin"Jar Uba..."Kawai ta iya Fada tana mamakin yadda Abdullahi ya Rufe ido yana Nuna mata nashi Kwanjin akan kowacce mace,ammh sai ita tasakashi Mizani kan Duk Saboda Hafsah ne yake mata Haka,Tashi Tayi ta Shige Tailot tayi wanka ta Fito Tayi Shirin Barci sai Lokacin ta Leka Falo ta ga Abdullahi kwance kan Doguwar kujera yana Barci ta Dade tana Kallonsa kafin ta kada kai ta koma Ciki ta Hau gadon ta kwanta Bayan ta Rage Wutar Dakin Barci ya saceta ne da Tunanin Irin Abunda ya wakana Tsakaninta da Abdullahi.

Al"amarin Abdullahi bai kara Bata Tsoro ba sai da Asuba Tunda ya Tashi yayi wanka yayi alwala ya Fice Zuwa Masallaci bata Kara ganinshi ba,yana Dawowa Dakin Hafsah ya Shige yayi kwanciyarsa kawai Itama Hafsah taso tayi mgana ammh ganin yadda yake ta wani Fushi yasa ta kama Bakinta,Saboda bata so Ta Shiga Abunda ba Ruwanta,Balle ta san Halin yan kayanta yanzu sai ya Sauke mata Gabadaya Fushin Barkat din akanta,Dalilin Haka ne yasa Ta Tattara Ita da Noor ta koma Dakin yaran,Ta kwanta Su Amira kuma Suna Kitchen tare da Mariya tana Dafa Abun karyawa.

Tun Barkat na Jiran Dawowar Abdullahi Har ta gaji da Jiransa Tatashi tayi wanka,ta Shirya Cikin doguwar riga na Wata Shadda,Wajen karfe 8am na safe ta Fito Daga Dakinta zata gaida Hafsah a Tsakar gidan suka Hadu da mariya suka gaisa su Amira ma suka gaisheta Ta amsa Tana Tambayansu bazasu Hadda bane sukace an basu Hutu Tare dasu ta Shiga Dakin Hafsah din.

Hafsah na Cikin Bederoom dinta Tana Shirya Noor bayan tayi mata wanka Abdullahi na kwance yana ta Barci yau asabar kila ba inda Zashi ne sai anjuma,Daga Cikin Dakin Hafsah ta amsa Sallaman agurguje ta Shirya Noor din ta Fito,suka gaisa da Hafsah Din Barkat ta karbi Noor a Hannun Hafsah tana mata Wasa,Su Amira nata Hayaniya sai Hafsah tace su Natsu Kada su Tashi Abbansu na kwance yana Barci Sai alokacin Barkat ta Fahimci Inda Abdullahi ya yada Zango bayan ya Dawo Daga Sallar Asuba,Nan da nan Kishi ya Turniketa sai dai bata nuna ba tadai yi yake kawai,Jin haka yasa su Amira suka Fice zuwa Wajen Anty Mariya itama Barkat din bata Dade ba ta mikama Hafsah Noor ta Fice Zuwa Dakinta zuciyarta Cike da Kishin Hafsah Tana ganin itace Silan Rashin Jituwa Dake Tsakaninta da Abdullahi Hafsah ne Sila.

Da Mariya ta gama Breakfast ta Mikama Hafsah nata ta sakama yaran sai na Abdullahi,Sai Hafsah tace ta Dauki na Barkat ta mika mata,Sai ta Dauka Tana Shiga sai ta isketa kwance tana ta kuka Mariya Abun ya bata mamaki Bayan ta ijiye Farantin kayan karyawan ta karisa gareta Tana Fadin"Anty Barkat lafiya kuwa..?

Sai Lokacin Barkat taji Shigowar Mariyan,Da sauri ta mike tana Share Hawayenta ammh Ta makara Mariyan ta Riga ta gani,Kokarin kakalo Mirmishi Tayi Tana Fadin"La bakomai wani Abu ne ya Fadamin Cikin ido.."Kallonta Mariya tayi tana Zama gefenta aranta tana Fadin sai naji Kwal uwar Daka Kafadarta ta Dafa Tana Fadin"Haba Anty Barkat...Nifa kamar kanwa nake gareki,domin kin gayamin Damuwarki wani Abu ne..? Kar ki manta yayana fa kike Aure...?

Kallonta Barkat tayi Tana wani Tunani Acikin Ranta Da kamar Bazatayi mgana ba sai kuma ta Bude baki tana gayama Mariyan Abunda ya Faru tana gayamata tana Kuka ta karishe Tana Fadin"Daga karshe Har cewa yayi bazan koma na karishe Jarabawana ba ammh wannan bai Dameni ba nasan Zence ne kawai yake bazai iya Hanani ba.."

Kallonta Mariya Tayi kafin tayi wani Dariya na Zaki gane Kuranki Lokaci Daya ta Dakata tana Fadin"Mganar ya Abdullahin ne zencen banza..? Lalle bama kisan wanene Mijinki ba naga alama.."Barkat tace"Kamar ya..?bangane ba..?

Mariya ta gyara Zama Tana Fadin"Eh mana mamaki naji da kikace wai mganar ya Abdullahi Zence ne kawai..Shine nace baki san waye mijinki ba..Wlh In ya Fadi mgana baya Sauyata Kaifi Daya ne in yace Eh...Eh ne,in yace A"a A'a din ne Wlh Ina mai Baki Shawara ki Bashi Hakuri in Allah yasa kina da Rabo ya Sauka Daga Fushinshi ya kyaleki ki koma Kada ki bata Shekarunki a Banza,In kuma kika Zauna kina Tunanin Fade kawai yake,Toh ina mai Tabbar Miki Bazaki Taba komawa makaranta ba Ballatana ki samu Damar karisa Jarabawarki.."

Ido Barkat ta Zaro Tana Fadin"Eh..Dama Haka yake.."Mariya tace"Ya Abdullahi yafi gaban Hakama..Shi mai Iko akan Kannensa,kinga ko su Anty Zannira Umarni yake basu Subi..Ballatana mu da muke gida,Baya son gaddama yana son Abashi Girmansa yana son a Girmama mganarsa baya son Raini sam..Kinga Anty Hafsah ita zaki Tambaya zata gayamiki Wanene Ya Abdullahi Tsautsauran Ra"ayi Gareshi ba kowa zai iya zama Dashi ba sai mai Hakuri.."

Idon

41 / 48