Author : Zainab Idris Makawa Seenabu Category : Complete Novels
yanzu ya koma ruwa sosai don sai dare yake dawowa indan kuma bai zuwa
aiki ya zauna min falo yaita bakin rai a falo yana jin fada.
Zai sha abinda yaga dama a wurin da nai magana yanzu zaiyi cikina da cin mutunci
da tonan asiri sai ya gaji ya kyale don kan sa.
Wata rana na tafi gaida mahaifiyar shi gwago na mun gaisa dadi dadi da ita sai
kowa yai shiru zuwa can tace dani yanzu komai yai daidai tsakanin ku ko an daina
jin korafin ki.
Nai mamaki dajin wanan magana nata datai min nace da ita dama ai ba korafi bane
fahinta ne akan addini don akwai karancin illimin addini a kan shi.
Nan ta haye tace wai ita nake fadawa magana akan dan ta nihar yaushe aka haife ni
da zan ce zan koya masu addini.
Nidai nai shiru ina sauraren ta har ta gama dama da wuya nazo gidan bamu samu
matsala akan dan ta ba bata kaunar a fadi magana gamay dashi ko kadan .
Ban dade ba nai sallama dasu na juyo zuwa gida da kafa na tako nan na hadu da
wata yar unguwar mu a hanya muka jera da ita muna tafe muna zuba bayeraba na amma
kano aka haife ta ta iya hausa sosao don haka in taga bahaushe take matukar jin
dadi a ranta.
Tafe muke muna hira tana tambaya na yaji da kuka take so nake cewa da ita ina
dashi ai tazo zan bata taji dadi tana ta min godiya.
Tun daga nesa na hango motar shi nasan cewa yana gida sai dai nayi mamakin may
yake yi a gida wanan lokacin haka mun dan tsaya da wata makwabciyar mu suna magana
da Mujida har take ce min yanzu na yi nauyi nabar kitso ko ?
Nai dariya nake cewa da ita na daina ma don maigidan ne ya hana nai mai kitso a
gida .
Ta rike baki tana mamakin halin maza tace shi bai ganin baiwa ne daga Allah na
hanyan samu yai maki zai hanaki samu nan dai muka wasan ce muka wuce ita kuma ta
kama gaban ta.
Mun zo kofan gidan na tura kofan yana bude sai nace ta jira ni a kofa na dauko
mata don kada na shiga da ita kuma ya zama min fitina wurin shi .
Sai ta tsaya a waje tana jirana tana ce min karfa ki shiga mai gida ya rike ki ki
manta dani a waje.
Kunsan yare idan yana jin hausa iya yin gare su shi sai ya nuna yafi bahaushen
iya hausan ma ga kuma mutane suna kallon mu tana jin dadi.
Nidai na wuce ta ina dariyan abinda naji ta fada zuciyana cike da mamakin abinda
ya dawo yi gida da ranan nan haka.
Don dama da sunan zan wuni gida gwago na tafi sai yamma zan dawo ta ban samu
fuskaba do haka nai shawara indawo gida kawai in nemi abinda naci don har na fara
jin yunwa ko.
ZAINABU IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , ,
2️⃣
4️⃣
YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU
PLEASE, , , , , , , , ,
Mun isa garin mu garin mu an shiga sallah magariba kafan mutane ya dauke sosai mota
ya tsaya dani kofan gidan gwagon ummi na.
A nan aka sauke min kayana kaf sai faman tabayana takeyi lafiya kuwa nakai ma
driver ruwa nan dai na fada mata tsaye muka wuce gidan mu.
Nan aka karasa sauke min kayana nai sallama da drever na shiga gida tunda yaran
gidan suka kyala ido suka ganni suka ce ga Safiya nan da nan na cikin daki suka
firfito waje suna min sannu da zuwa.
Dakin Ummina na nufa yayin da aka shigo min da kayan da nazo dashi ciki yar jakar
kayana da tsaraban da nazo masu dashi.
Ni bani sanin cewa na sake masu amma su suna ganin wai na zama wata yar birni
dani take inna wani kishi ya tarsu a zuciyar ta na yadda na canza.
Lafiya kalau suka tare ni sabanin ummina da ta shiga zargin zuwana gani da juna
biyu a jikina kuma.
Mama tazao muka gaisa take tambaya na kowa nace duk suna lafiya take cewa ashe da
sai dai muji haihuwan ki kawai don bamu ma san kina da ciki ba.
Murmushi nai mata kawai muka gaisa ta fita daga dakin ta koma ta aiko min da
abinci daga wurin mama din.
Ban iya cin komai ba sai kunu da na nema don ummina bata rasa kunu a dakin ta.
Baba ya shigo gida daga masallaci yara suka tare shi da cewa safiya tazo baba
cikin mamaki yake tambaya da cewa Safiya ?
Ya nufi daki Ummi yana tambayana nazo lafiya nace Alhamdullahi sai da ya tambayi
kowa har Ahmed din da kan nesa.
Sai kuma ya dakatar yana tabmbaya na da lafiya dai na ganki ke kadai ina mijin
naki yake ne?
Ban ji tsoro shi ba nace dashi yana gida baba ni kadai nazo, kamar zaiyi magana
sai ya juya ya fice dakin na mu.
Yan gidan mu suna baibaiye dani har wani lokaci sannan suka dauke kafan su.
Nasan ba komai yasa sukai min haka sai tsaraban da nazo masu dashi wancan zuwa da
ni tare da yaya sani.
Har lokacin da suka barni dakin ummina na min kallon zargi sai dai batai min
magana ba sai da na dan kimtsa na samu wuri na kwanta don a gajiye nake sosai.
Ban falka ba sai cikin dare na falka da tunane a raina barkatai na yadda zamu
kwashe da mahaifina gashi daga zuwa ba abinda ya fara tambayana sai Ahmed din da
mahaifiyar shi.
Na dade a haka ina tunane sai zuwa asuba wani barcin ya dauke ni kuma har na
makara da sallah sai da ummi na ta ta tadani.
Nayi sallah na fito na gaida iyayyena na koma daki don baba bai shigowa gida sai
hantsi ya fito yake dawowa daga masallaci.
Ummi na samu tayi zaune tana tunane ita kadai a dakin na samu wuri na zauna sai
tace min yar nan lafiya kika zo gida a haka yadda kike nan ?
Kuma ba a samu wani ya biyo ki ba kika biyo hanya ke kadai haka gari ba kusa ba ?
Kafinta gama maganan ta hawaye ne ya cika min ido na cikin kuka nace mata ummi
saki na yayi yau kwana hudu kenan yace na bar mashi gidan shi .
Salati ta saka tare da dafe gaban ta tace yasake ki ka ce fa za tai magana sai
kuma naga ta mike kawai ta fita dakin.
Na bita da kallon tausayi har ta bace min ashe dakin mama ta tafi ta kirata sai
gasu sun dawo dakin cikin rudewa.
Mama a rude take tambayana Safiya may ke faruwa ne wai ni dama tun jiya da kika
zo nake zargin wani abu.
Ban boye masu komai ba duk yadda mukayi na kwashe na fada masu da abinda gwagona
tai min duk ban boye masu ba.
Salati mama ta saka itako ummi na sai kuka takeyi ba tsagai tawa mama ne ta samu
bakin cewa amma in haka Asiya tai muna taci amanan zumunci wallahi sai Allah ya
saka maki.
Inna da yarta ta fadawa taji ummi na kuka kuma mama na dakin mu ta kasa gidin
zama taje ta dawo a tsakar gida don taji may akeyi.
Mama ne ta kirata sai ko gata tazo nan suke fada mata abinda ya faru dani ummi
dai bats samu bakin magana ba sai inna ne tace adai binkita aji gaskiyan maganan.
Tunda naji ta fadi haka nasan zata iya zuga baba a kan maganan don ta wuce nan
kadan ne daga cikin sherin ta.
Shigowan baba gidan yasa suka fito daga dakin mu dakin Inna yake ta bishi dakin
ko may ta fada mashi sai gashi ya fito yana cewa ina Safiyan take.
Nan ya fado dakin mu ya samay mu da ummi na a dakin yace ki fada min gaskiya may
ke faruwa dake ?
Yadda na fada masu mama haka na mayar mashi da maganan tiryan tiryan yana saurare
na har na gama fada mashi komai.
Yace cikin tsawa ke safiya badai gidan nan ba ai na fada maki tun farko kada ki
dawo min gida.
Sai lokacin ummi tai magana tace idan bata dawo ba duniya kake son ta shiga ya
koreta akan karuwa tabar mai gida ina yake son ta tafi garin mutane kai bakai
tunanen haka ba baka gode ma Allah da ya kawo muna ita gida lafiya ba.
Ke Rabi kifita a idona tun muna sheda juna nida ke ke tsaya kiji bazaki zauna
min a gida ba muddin kika kashe auren nan kiji na fada maki.
Ya tashi ya fita yana fada yaya sani ne yashigo gidan yace yaji ance nazo jiya da
dare sai kuma ya samu labarin abinda ke faruwa.
Nan yace ai dama nasan haka zai faru ko ta koma da idona fa na samu ya dauko
karuwa a gidan kuma yaiwa safiya dan banzan duka.
Amma baba ya hana aiyi magana to ai ga irints nan yanzu cikin kuka nace yaya Sani
wanan ba wacce ka sani bane nan na shiga basu labarin abinda suke mun yaya sani
yace kai ina wallahi bai yuyuwa gaskiya.
Dole baba ya canza maganan shi na komawa n ki gidan nan sai dai in yasa yaci
kudin sune yake kamay kamay.
Daganan Inna ta kirashi dakin da yazo, to to ita kuma Inna zata fara abinta
kenan baije ba saida ta sake daga murya ta kirashi ya tafi.
Fada tai mai sosai akan ya canza hali yafita batuna da uwana don ba ysn goyo muke
ba yace ni Inna baruwa na da harkanku na kishi, ni kaunata nake tausayawa.
Fita yayi ya tara kan yan uwan baba suka hada mai mitin din kashi akan ya fada
masu gaskiya in ya karbe kudi wurin gwagona ne yasa bai iya raba aure na da Ahmed.
Nan baba ya kara yin fushi ranshi ya baci sosai ya kumbura sosai yahau yace diyar
su ko diyar shi da zasu tsure shi akaina.
Yamike yana fadin yau yau din nan zan bar shi gidan shi in koma gidan mijina ko
mu bashi gidan shi nida uwata.
Allah ya taimake ni yazo gida sai ga su yaya sani sun shigo yace infito da kaya
na inbar mashi gidan shi in kuma ban komawa gidan mijina mu fita mai gida dani da
ummi.
Fitina ya tashi si yaya sani suka ce mu zauna kada muje ko ina ya shigo har dakin
mu zai doke ni mama da ummi suka taso mai sukace idan ka dake ta da tsoho ciki haka
wani abu ya samay ta sai an daure ka a garin nan.
Sai jikin shi yai sanyi ya dauki kayana dake gefe yafita dasu waje gidan ya watsar
yaya Nura ya kwaso ya dawo dashi ciki yace haba baba wai kodai Safiya ba diya cikin
ka bane ?
Yaringa fa tun tasowan ta bata da gata a cikin gidan nan kamar kowa kun tsane ta
ita da uwar ta may yasa baba kake mata haka kai kayi su İnna suyi ?
Sai jikin shi yai sanyi yabi yaranda da kallon mamaki Yaya Sani ya karasa kwaso
min kayan ya shigo dasu gida.
Ya rasa abinda zai yi ya fice yana fadin sai sun bar min gida yau ita da uwar ta
kowa yai mata tsaye a garin nan.
Nan ne gidan ubanta basu zuwa ko ina inji yaya sani haka kawai ka bayar da
yarinya ana mata wullakancin da aka ga dama amma kamar bakai ka haifeta ba.
Sai ga yan uwan shi sun shigo maza da mata nan suka taru sukai mai tas a kan mu
suka ce sai sunyi karan shi ga hukuma idan ya kore mu ni da ummi gidan nan ai ba
kaina aka fara aure ya mutu ba.
Nan ya fice gidab yana banbami kowa na mai tirda halin shi itako ummi ta hada
kaya wai zata bargidan aka taru har gwagon ta da ta shigo akace ina zata tabar yar
ta da tsohon ciki haka ?
İna waje tsugune a ina kuka mama ta fito tace a hasale tashi ki shiga ciki kin
zauna waje kina kuka ba inda zaki tafi.
İnna sai wani kallon banza take min ita da diyan ta don ba haka suka so ba sun so
baba ya kora mu ne yadda yai niya.
Muna sauraren dawo wan baba muji may zaice sai muka ga ya dawo bai ce komai ba
ashe maigari ya samu labari ne yai mashi tas gwagon ummina ta kai karan shi wurin
shi.
Sai dai bana fitowa waje in kuma gari ya waye na gaida shi da kwana baya amsa min
sai ya kawar da kanshi yaki kulani wanan abin ya matukar tayar min da hankali a
gida.
İnna ta shiga sake maganganu a gidan wai sai bakin ciki na ya kashe masu miji
inda basuyi hankali ba.
Sai yarta ta karbe da cewa wallahi sai dai ta kashe uwarta ba mahaifin mu ba ita
da ta hana ta zaman aure, ai da har wani jin kai ake muna an auri dan birni za a
tafi birni.
Ban saurare su ba don ina sharan kofan mune mama ce tace sai ko makiyin Allah bai
fadin haka ga Rabi.
Don kowa yasan yadda ta nuna kin ta ga auren nan abu dai ne in an fi karfin ka
baka da yadda zakayi sai hakkuri amma zancen ta wa mutane hawan kai karya ne.
Nan dai fada ya kaure a tsakanin su koma sai da suka dauki lokaci suna yi suka
dakatar don kan su.
********* ********* *********
Tunda hakan ya faru na samu dan sa ida a gidan sai dai ba wani dadi ga zaman
gidan yayana nan a yadda yake baya komai ya lafa ne na kwaso kaya dake gidan gwagon
ummi.
Wanda maman biyu ta hada min kan kudi na taimin kari ta saro min kaya dasu wai na
juya kar nai zaman banza haka na.
Sai lokacin su inna yan sin banza suka dan sake min fuska don ana son banza nadai
basu wanda na yo tsara a kyauta sauran kuma na shiga lodawa kanne na suna fita min
da su.
Kafin wani lokaci mutuwan aure na ya ba gari mu kowa ya sani ana tir da halun
baba kowa sai cewa yake yaci kudin su ne in ba kudin su yaci ba may ya kawo haka
gare shi.
Ana dukan yar ka a wullakanta ta har tazo ma gidan da rauni kace wai sai ta koma
gidan mijin nan da zama.
Wurin yanne na maza nake samun gata sosai don zasu sayo min abin kwalama da yan
abubuwa idan sun fita.
İtako ummi har lokacin ba dadi tsakanin ta da baba zaman dai akeyi amma kullun
sai masifa a tsakanin su.
Gashi shiru tunda na zo baba baiji wani labari daga wurin su gwago ba ita bata
zo ba dan ta bai zo ba sai jikin baba ya fara sanyi .
Gashi yai masu aike yafi a kirga amma sun ki bashi amsa balle ya san abinda yake
ciki din yana a kan bakan shi sai na koma gidan dole.
Ranan kwatsam sai ga yaya Saadu ya dira gari wai sun shigo arewa ne yace zai
karaso ya dubani.
Yana zaune dakin mama naje gaishe shi da zuwa sai ga baba yazo shima anyi sa a
yana gida bai fita ba bsyan sun gaisa sai ya dube ni yace ke kuma ashe haka abin
yakai.
Baba sai dai kai hakkuri don maman mu da dan uwana basu rike amana ba ba gwama
ma da auren na ya mutu tun baika ga kasheta ba a rasata.
Akai tsit ana sauraren shi ya shiga lissafo masu irin rayuwan da nayi a can harda
wanda ban fada ba na yunwa da irin zagin da yake min na cin fuska.
Yace baba wallahi Ahmed da wuya ya sauya halin shi don yayi nisa da duniya
yaudaran ku dai mummy mu tayi bata fada maku halinshi ba na gaskiya.
Amma baba yarinyar nan tasha matukar wuya a han shi yai amai ta kwashe ya shawo
giya yazo yai mats dukan tsiya a gidan sai ya barta kwance.
Ya kwaso mata tana zaune suna cin abu ya hana mata ga ciki a jikin ta, kai abin
ma baya faduwa wallahi sai dai Allah ya saka mata ka wai za a ce.
Jikin baba ne yai sanyi ga bayanin da yake masu nauyi da kunya suka rufe shi don
har su yaya Sani suna a tsaye wurin suna sauraren baiyanin shi.
Zai tafi ya kawo kudi yaba baba yaba su mama da yaran gida ni kuma ya rubuta
lanba ya bani ya bani karamar wayan shi yace inda wani abu a kirashi insha Allah
zai taimaka ya kawo kyautan kudi masu yawa ya bani.
Yace idan aiki ya sake kawo shi arewa zai dawo ya duba mu lokacin yasan na haihu
yace kiyi hakkuri Safiya tun yazu Allah ya fara saka maki ai don ya fara ganun
abinshi.
Nai murmushi nace yaya banda abinda zance sai godiya gare ka don ka fitar dani
zargi a gurin baba.
Don ni na kasa mai bayani yadda kai masu saboda ina jin kunya fadi amma yanzu
sunji nagode maka da Allah ya kawo ka zo kai masu bayani.
Ya tafi yabar zukata da magana da kiyastawa na abubuwan da ya fada baba kan nauyi
da kunya sun hana shi shakat a rayuwan shi.
Mahaifina ya dan sasauta min don tun da yaya Saadu yazo yana amsa min gaisuwa
indan na gaida shi sabanin da da yake kyale ni.
Ranan wata jumma,a ya dawo daga kasuwa ya shigo da leda