Advertisements
Chapter 24 Reading Bahagon Rayuwa by Zainab Idris Makawa Seenabu BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Bahagon Rayuwa by Zainab Idris Makawa Seenabu

Author :  Zainab Idris Makawa Seenabu Category :  Complete Novels

Chapter   24 / 87

69K to 72K   out of 258.3K words

a hannun shi ashe rogo
ke ciki mai zafi da zogala ya sayo min.
İnna zata karbi ledan yace a a barshi kayan safiya ne sai ya kwala min kira ina
daga dakin mu najib sai na fito.
Ya miko min ledan dake hannun nasa yace karbi jeki ki gyara ki ci inna na tsaye
har lokacin tana son tasan may a cikin ledan.
Na duka na karba a cikin ladabi nai mashi godiya sai naji inna na cewa wata
sabuwa ke nan kuma.
Ban dai kula ta ba na wuce dakin mu sai da nashiga na bude naga ashe rogo ne
daffafa da zogale.
Jikina rawa na shiga gyarawa sai da na gyara na kasa naba kowa na gidan mu ba
wanda ban ba na zauna na dan ciyen sauran na kora da ruwa.
Tun wanan ranan idan zai dawo gida yakan dan riko min dan abin kwadai irin cimar
kauye na gyara naci duk da ina ba kowa isan na gyara amma sai da hakan ya zama
tsegumi a wurin İnna.
Don da ta tayar da fitina ta kaca kaca taiwa baba ranan kan haka yace shi yana
sayo min ne don ya ga ina cikin lalura na ciki.
Gashi kuma ban da miji kusa yasa yake sawo min amma duk da haka bata yarda ba
tana ta faman fada.
Sai mama ne ta dakatar da ita tace haba haba wanan abin da kikeyi bai kawo kallo
ba wallahi abinda ba ita kadai take zama taci ba kowa sai ta ba gidan nan.
Shine kuma har ya zama abin fitina haka yarinyar nan koke kike dashi ai kina mata
basai malam yayi ba.
Nan ta juya kan mama da fitinar ta tana ce mata munafuka ai da ita ake kulla
komai da akeyi a gidan.
Bata kare fadan taba sai ga Yaya Sani ya shigo min da kade a leda yana kwala min
kira na fito in karba.
Mama tace ta kin gani yanzu kuma may zaki ce duk wanda ke da imani dole ne ya
tausayawa safiya halin da take ciki a gidan nan.
Tace ai bani na aike ta da ba ana yi muna rawan kai an tafi birni ba diyan mu
suna nan sai da dubu ya cika za a zo a zauna muna gida dan kudin da za a yo muna
cefane a kwashi ana sayo mata gaye dashi.
Mama tace dubu bai cika ba don iyayyen kirki duk basu rushe gidan yar su sai dai
su gina shi don haka ki natsu kisan may kike fadi idan da yar ki ne haka ya cika da
ita yaya zaki yi.
Tai wani iri shewa tace can dai gasu gada diyana basu ciki wallahi tace amma kin
zuga na wasu sun shiga ai.
Tace muka dai zuga tare karki debe kan ki ciki wayai ruwa yai tsaki cikin wanan
hadin , tunda kin sai tun ba a yi auren ba watsetse ne shi.
Mama tace sanin haka danayi yasa ai nake tausaya ma yarinyar don kar abin yai
min yawa.
Kuma sa bakin da nayi ayi bawai na sheri bane don a hada zumun ta ne nayi badon
wani abuba kedai kika yi don sheri kije kitayi ai.
Ummi tana jin su tace wanda duk ya cuci wani dai Allah yana ganin sa shine
Alkalin mu daku.
Baba ne ya sake shigowa gidan ya iske suna rigiman har lokacin ya ce wanan wani
irin rigima haka kuke yi.
Kun ishi mutane da hayaniya haka yaci gaba da fadin dame kuke son muji da tashin
hankalin ku koda halin da yariya ke ciki.
Yanzu ba lokacin hayaniya bane abinda ya faru ba za a canza shi ba ku barmu muji
da abinda zuka tanmu ke ciki mana.
Yarinyar nan tana bukatan kwanciyan hakali amma kun tsaya kuna tonon asiri irin
haka yarinyar nan fa ba ita ta saka kan ta ba.


ZAİNAB İDRİS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , ,



2️⃣
2️⃣


YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,
, , , , ,



Na tura kofan na shiga da sallama yana kwance saman dogon kujera daga shi sai
kajeren wanda ga taba rike a hannushi yana zukawa.
Daidai lokacin da Lilliya ta fito daga dakin tana waya gaisuwar da nai niyar
yimai ban samu yi ba na shige kitchen abina kai tsaye ina tsuki.
Shiko yana ganin na gani na sai ya dan zabura alaman rashin gaskiya a tare da
shi.
Ina fitowa da ledan da na hadawa Mujida kayan miyan da tarokeni ci ta gama wayan
ta juya gare shi tana cewa.
Ahmed kayi gagawan yi ma wana yarinyar waigi kaina, kai mata magana ka
tsawata mata don bazan lamunci batacin ta gare ni ba.
Wai kaima kamar ka, ke zama da wanan karamar yarinyar mara kunya banza zata shigo
tasamu mutane tana masu tsuki kamar wacce ta samu dabbobi, karamar mara kunya
kawai.
Har zan wuce banyi niyar kula suba jin tace dani mara kunya sai na juyo gare ta
na fasa fita daga gidan.
Nai mata wani irin kallo sama da kasa a wullakance nace kar ki dauki alhakin
dabba kici mai mutunci, don ko dabban ma ya fiki mutunci da daraja a idon jama a.
Don da dabba yana da baki aikai mai sallama da zai amsa sallaman kai tsaye kin ko
kaga ashe sunfiki darajja kenan daidai nan mujida ta shigo gidan ta tsaya tana
sauraren mu.
Nace ke dani yanzu waye mara kunya da zaki zo har cikin gidana duk da na kyale ki
ki nemi ki kirani wai mara kunya ni yar kice ko may ?
Mujida ne ta katse ni da cewa towai ita din waye nace ban san ko ita din waye ba
na dai dawo na same ta a cikin gida na tana shige da fice min a gida ai yanzu dai
muka shigo dake gidan ko ?
Na tambayi mujida ta amsa min da eh wallahi nima naji shiru baki fito ba shine
naji muryan ki na leko.
To ta tare ni da suratai tana fada dani amasifance ni kuma bansan da watake yi ba
ma, a gidan sai dai ko idan mahaukaciya ce ita din don in ba hauka ba ba yadda za
ayi ta shigo min gida ki tube haka zindir don daga ita sai breziya da gajeren wando
a jikinta.
Mujida ta kalli Lilliya ta sake kallo na taga ban da inda nake da hadi da ita na
kinga ina da hadi da ita ne mujida ?
Sai Mujida tace kai dis one na ashawo,
Wanan ai karuwan titi ne ta shigo maki gida taci maki miji ne , "na so dem dey
do ehhuu ashawo ta shiga mata ihu da sowa akai tana batun tara mata mutane.
Lokacin ya zabura zaune kamar zai yi magana Mujida ta juya gare shi tace Oga
barin fada maka gaskiya zama da irin wa yan nan shedanun yana jawowa mutum babban
asara a rayuwa.
Ka gansu nan guba ne irin su don a take sun nakasa wa mutum rayuwa ko ta jama
hasara babba.
Da mamaki suka tsaya suna kallon mujida don bata da alaman tsoro ko kadan irin
matan nan ne da suka san kan lagos ciki da bai dinta.
Fada ba nata ba ta saye zancen haka, wai ko ina Safiya take haduwa da irin
goggagun mata haka yan duniya dasu oho.
Itako Lilliya zuciyar ta ji take yi kamar zai fashe don bakin ci, kalaman da muke
fada mata sun mata muni sosai.
Shiko maigidan da mamaki a fuskan shi ya ke kallon mu yana son yai magana sai
dai bai iya cacan bakin mata ne dai kawai.
Zan sake yin magana sai ya daga min hannu da cewa dakata, min don Allah, shin
munyi dake cewa gidan kine ke kadai.
Yadda gidan nan yake gidan mijin ki, na fada maki itama gidan mijin ta ne, tana
da daman shigowa duk lokacin da take so.
Sai Lilliya ta karbe da ai wanan cin mutumtuci ne kamar wanan zan zauna gida daya
da ita tana min rashin kuya don bata da tarbiya, wanan yar kauyen da ita may ta
sani banda jarabar maza iri naka har da zuwa mata ciki don kwakwa.
Wanan ga kankanta ga jahilci Mujida ta cabe da cewa yi muna shiru munafuka masu
yawon kwantan mijin mutane kawai ashawon banza ai gara da ita an sheda daurin auren
ta kefa a bariki ne aka dauro naku.
Na ce kin taba ganin karuwa tayi aure ne ai sai zaman banza dai, sai na hada da
cewa karuwan titi anzo za a samu wurin fake wa.
A hasale ya dani ki iya bakin ki Safiya kiyi hankali dani wanan dakike gani, ni a
wurina tafiki tunda tasan mutinci da daraja a idota.
Don kana dan bariki irin ta ba muje ne ya tadda mutafi kai da ita duk ruwan bariki
na cinku kaga dole kasan ta fini, tafini iya shan giya da karuwanci ba.
Fayau fayau ya kwashe ni da mari biyu masu kyau a fuska na yace ba nace ki iya
bakin ki ba wanan da kike gani tashigo gidan nan ke nan bata sake fita ko ina.
Na dade a duke tare da dafe kumci na inda ya mare ni , inajin mujida na ta mai
ruwan balai akai ta hadu su ta zage tas yace shi ba zai mata komai ba ni dai dana
jawo ta gidan zaiyi wa.
Don haka in zaki zauna ki zauna in ba zaki iya zama da ita ba ga hanya nan ki
fice min gida na fada maki sai lokacin na samu baki magana.
Nace zan fice amma sai ka bani shedan ficewa karna je gida ace zaa sake dawowa
dani gidan ka kuma don da in dawo gidan nan gwama muta.
Yace abu mai sauki kenan wai takarda kike nufi komay nace dashi eh a hasale.
Mujida dajin haka ta fara fadin a, aa kada kayi mata haka mana, ga ciki
ajikinta ga kurciya kace zaka saketa don wanan ashawon matar ta nuna Lilliya a
wullakance.
Wallahi na fada ma wanan da kake gani poison ne sai ta halaka ka, har dukiya ka
da komai naka, daga karshe ta gudu ta barka da wahala.
Indan taga sakin yafi mata sauki ai a shirye nake da yin sakin kalman sun ban
mamaki wai a kan karuwa yake maganan sakina.
To ko na zauna may zan tsinta ga mutumin da ya furta hakan banda tarin takaici da
bakin ciki da sune na ke gani a koda yaushe na dago kai na kalli Lilliya wace ke
tsaye tana wani muzurai da ido don jin abin da ke wakana tsakanin mu.
Bata da wani abinda za a so daga gare ta haka take kamar kato yai shirin mata da
ita, sai farin na mai data shafa ke aiki jikin ta kawai.
Muryan Lilliya ne ke fadin dama ai karanbani ne da kwadayi ya shigo da ita ba
komai ba may zaka deba a jikin wanan yarinya nema wai.
Na ce ai shi yasan abinda yake diba gare ni kullun in ba kaddaraba may zai shigo
dani cikin fasikai irin ku.
Ta tafa hannu da min tsowa miji dai ya dawo hannun na dama nawane ba naki ba,
dama matsala aka samu ya aure ki dan wani dalili yanzu ya dawo hannuna kenan .
Lilliya ya ambaci sunan ta cikin tsawa ta bar maganan da take yi din yace kyale
ta ni ma nagaji da wannan yarinyar mara tarbiya haka.
Nace dashi kayya amma kai kan anyi hasarare baka ko jin kunyan kiran wanan a
matsayi matar ka.
Wallahi kaban mamaki wai da hankalin ka da ilimim ka namiji kamar ka, zaka kar
awanan matar titin fuska a kone yasha mai, ga kai kamar iccen kwakwa,
Abu haka a tsaye kamar kato, mace ba addini ba al,ada ba dabia na kwarai, mutum
irin ka maijin duniya da hayaki bai kamata ya buge a wannan abin banzan ba .
Dama wata mai surar kwarai ce sai kai min gadara a dajin kai a kanta dan wanan
dai kake cewa wai tafini tafini iya shedana ko.
Wallahi na tausaya maka yaya kayi hasara namijin duniya kamar ka ya kare a
dadiro da wannan abu da bata cikin tsarin mata.
Ai gara dani da kankantana da rashin ilimina ko ba komai ina da addinina kuma a
gaban iyayyena ka dauko ni ba bariki na biyo ba
In dai wanan matar ne gatanan ga ka ba zan zauna ku kashe ni da bakin hali irin
na kuba kai da ita , da yarinta na tsohuwar banza ta zo ta zauna min gida tsofai
tsofai da ita wai kuna dadiro dadiron na kuma na iya shege ne.
Banji tsoron su ba haka na tsaya gaban su nai masu tasa yana tsaye kamar wani
soko a buge yake har lokacin.
Ya kalle mu nida mujida rai bace yace ku fice ku bani gidana, sannan ki tatara yau
yau ki bar min gida na ki bar garin nan ki koma gida uban ki na sake ki saki daya.
Mujida zatai magana ya daka mata tsawa yace na fada maku kubar min gidana haka
na.
Nasan halin shi sarai don haka na dakatar da mujida nai mata godiya tare da bata
abinda ta bukata gareni, ta fice tana tausaya min.
Dakina na shiga wurin da nake boye kudi na daga na kwashi kudina da takarduna na
fito ba tare da na sake waigen su ba yana zaune yayi tagumi kamar wanda abin ya
dama.
Koda na fita waje tsayawa nayi ina tunanen inda zan nufa araina ko inje gidan
gwago na don kartace ban fada mata ba na wuce.
Sai kuma nace banzan tafi ba gidan anty zan nufa maman biyu sai na tare taxi na
tafi, ina tafe ina tunane idanuwa na suka yi jawur ina jin zuciyana yana min zafi
da wani irin kuna da zugi.
Ina tuno irin cin mutuncin da nai ta fuskanta a gida duk hakkurina sai da haka ta
kasan ce dani yanzu in naje gida a haka ko wani iri hukunci zan fuskan ta gun
mahaifina kuma.
Wasu hawaye suka zubo min ina jin tsanar shi ya kara shiga min rai na har na kai
gidan maman biyu ina tunane a zuciya na.
Na samu ta dawo aiki kenan tana zaune yaran ta sun zagaye ta suna mata hira sai
gani na shigo.
A yadda ta ganni ta fahinci ba lafiya yaran suka rugumay ni suna min oyoyo da
ganina tace oya ku shiga ku cire uniform a huta .
Duk suka shige suka barmu da ita sai a lokacin ta dago kai ta dibeni take cewa
Safiya nayi mamakin ganin ki yanzu da yamman nan .
Dukar da kai nayi bance da ita komai ba nace anty yuwa nake ji murmushi tayi tace
yunwan ne kike ji yasa ki kuka don ga alaman kuka nan tare da ke.
Ban samu cewa komai ba takira yar aikin ta tace ta kawo min abinci da zai isheni
wai yunwa nake ji kin san abu gamai ciki.
An kawo abinci sai dai ban iya ci ba tana lura dani tana waya sai ta katse waya
tace a, a Safiya bakici abincin ba mana ko baiyi maki dadin ci bane.
Maimakon in yi magana sai ga hawaye yana zubo min a idona nace a hankali anty gida
zan tafi yau.
Ta dago da sauri tace wani gidan dai kike magana zuwa nace garin mu.
Tace kina ko da hankali kuwa yau din nan kina haka kice zaki tafi arewa may zaki
tafi yi arewa kina cikin wanan condition din.
A hankali nace da ita ya sake ni ne zan koma garin mu ne.
Ya may kika ce ta fada a razane .
Na sake cewa anty ya sake ni akan wanan karuwan tashi yaban saki ya zabi zama da
ita sama da ni ne.
Innalillahi take maimaitawa da karfi a bakin ta tace Safiya da gaskiya kike ko
wasa wai?
Nan na fara bata labarin abinda ya faru a gidan tun fitana har dawowa na gidan da
nazo na samay a cikin gidan.
Tace yanzu abin nashi har yakai can ya sake ki da tsohon ciki a jikin ki babu ko
tausayi hakan .
Anya wanan mijin naki ko yana da imani ya bata maki kurciyan ki ga banza ya cuci
rayuwan ki.
Kin ga hakkuri zaki duk abinda ya samu bawa mukkadari na daga ubangiji bai cuciki
ba kanshi ya cuta da yardan ubangiji zai girbi abin sa.
Amma uwarshi ta sani kuwa na girgiza mata kai alaman aa na hada da cewa ban tafi
can ba nan nayo.
Tace ya kamata muje mu sanar da ita karta ce baki fada mata ba don mutum abin
tsoro ne yanzu balle tana gani itace makusanciyar ki a garin nan.
Nan dai ta yanke shawaran mu tafi mu sanar da ita ko banza dai gwago nace ita
din .
Mun tafi mun samay ta tana cika tana batsewa dakyat take karba muna gaisuwan da
muke mata, bayan mun zauna ne tace kun kai ga yadda kuke so kedashi.
Yanzu may kika zo yin mun sai da kuka bata abu zaki taso ki zo min may kike son
na aiwatar yanzu din.
Gidan shi ne shike da iko da abinshi ki kyale shi mana yayi yadda yake son da
gida shi kema ba kawo ki akayi ba acikin gidan.
Anty ne ta katse ta da cewa kai kai wanan magana taki baiyi ba a saki yarinya
sai kuma ki bita da wanan irin maganan .
Yanzu in yarki ce ta samu wanan matsalar abinda zaki ce da ita kenan, karuwa fa
zaman dadiro a cikin gidan ta haba hajiya kiyi tunane mana.
Tace haka zan fada mana

24 / 87