Advertisements
Chapter 10 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   10 / 54

27K to 30K   out of 160.3K words

ne.


Alhaji yace indai Rumaisa ce zakisha mamaki, wayonta har ya wuce shekarunta. Dariya sukasa Malan Sani yace ai Hajiya Lagos abun tsoro ce, addu'a kad'ai zamu rik'e. Ummu tace haka ne. Mik'ama Halima ledar tayi tana fad'in ga tsarabar kanawa. Amsa tayi tana fad'in mungode sosai. Ummu tace haba bakomai, munci abinci yayi dad'i angode.



Haka suka rakasu har bakin mota, sai da suka tafi sannan suka dawo. Ra'eez sai fushi yakeyi. Kamoshi Ummu tayi tana fad'in haba Ra'eez ai zaka rik'a ganinta tunda gari d'aya kuke. Alhaji yace ka bari zan kai ka wuni acan kaji.


Ummu tace wallahi dama su dawo wancan b'agaren na waje. Murmushi Alhaji yayi yana fad'in nayi tunanin haka tun farkon da aka fara zanen gidan, amma abinda nayi tunani ya hanani aikata hakan, akoda yaushe idan zaka taimaki mutum to kayi kok'arin d'orashi a hanyar da zai samu ba hanyar da zaka rik'a bashi ba, hakan yana kashe zuciya, hausawa suna fad'in daka d'auki abinci kaba mutum gara ka nuna masa hanyar gona, koba komai zai dogara da kanshi kuma zaifi tattala abinda ya samu, na duba naga gara na canza masa unguwa na cika masa ya sayi gida akan na kawoshi gidana ya zauna, domin kawoshi gidana da zama zai kashe masa zuciya ya kasa mallakar nasa, kuma zumuncin mu zaifi kwari idan akace muna nesa da juna, kinji dalilin da yasa ban maidosu nan ba.


Ummu tace kana da gaskiya kuma, shikenan Allah ya karemu daga sharrin mahassada kuma ya bamu zama lafiya. Alhaji yace amin. Ra'eez yace Abbu a wace islamiyar za'a sani? Abbu yace Ra'eez zamanka Lagos ba mai dad'ewa bane, bana son ma ka saba da ita har sai bayan ka mallaki hankalin kan ka, dan haka babu makarantar da zan saka, jarabawarku tana fitowa zaka tafi Kano, ko hutu akayi sati biyu kawai zaka zo kayi ka koma saboda islamiya, nafi buk'atar kayi ilimi mai zurfi dana zauna da kai anan, duk lokacin daka kammala karatun ka sai kazo mu zauna tare, domin wancan filin dana bari gidan ka ne za'a gina idan kayi aure ka zauna da matar ka.


Hannu Ra'eez yasa ya rufe fuskarsa ya bar wajen da gudu. Dariya sukayi Ummu tace Yarona fa akwai kunya. Alhaji yace ashe Yaron ki, Yarona dai. Murmushi Ummu tayi tace Yaron mu dai. Alhaji yace idan kina son naki to ki haifo Mamana. Murmushi tayi tana fad'in Allah ya kawo masu albarka, yace amin Ummun Ra'eez.


**** ***


Tunda suka dawo Lagos Alhaji ya k'ara samun natsuwa, aikinsa yake sosai, yayin da Ummu suke zumunci da Maman Rumaisa sosai, Ra'eez yana zuwa gidan su yayita koya mata karatu, itama ana kawota idan ba makaranta, sai dai babu wanda yake kwana gidan kowa, Malan Sani shine yake kaita kuma ya d'aukota koda tayi bacci, haka ma Ra'eez shine yake maidashi.


A wajen aikin su Alhaji Maiwada babu wanda yasan yana da 'Da, domin babu wanda ya fad'ama ya maido iyalinsa, ko walimar shiga sabon gida beyi ba, yayi addu'a kamar yanda addini ya koyar, shiyasa babu wanda yasan ya tare a sabon gida, asalima babu wanda yasan yana gini, dan Alhaji mutum ne mai son sirri, duk yanda kuke dashi baya bari ka sameshi agida musamman akan maganar data shafi wajen aiki.

***

Zuwa yanzu Boda d'insu ta samu lafiya, domin aiki ake sosai, duk wanda aka kama da laifi nan take ake yanke masa hukunci, shiyasa kowa yake kaffa-kaffa da aikinsa. Manyan masu kud'i wad'an da suke kasuwancin shigo da kaya sam basa son Alhaji Maiwada, sunyi-sunyi a canza shi sai dai abun yaki tasiri, domin har yanzu ba'a canzashi ba, ganin haka yasa suka fara shirya masa mugunta, sai dai har yanzu basuci galaba akansa ba.


*****

Jarabawar su Ra'eez ta fito kuma ya samu makarantar kwana shida Labiba, inda suka samu *FGC DAURA*, yayin da aka canza masu islamiya mai kyau idan suka dawo hutu surik'ayi. Sosai yayi farin ciki da samun makarantar kwana, saboda yana son makarantar kwana.



Haka aka kammala masa komai, lokacin da zai tafi hada kukan rabuwa da Rumaisa, Ummu tace tare da ita zata tafi domin tayi masa rakiya. Haka suka shirya kasancewar ta jirgi zasu bi hakan yasa basu tafi dasu Malan Sani ba.



Kwanansu biyu sai da suka kaisu har makaranta kafin suka koma Lagos. Rumaisa sai kuka take Ummu tana lallashinta.



Bayan komawarsu ne Ummu tace gidan yayi mata shiru tana son ta samu mai aiki. Alhaji yace ina tsoron mutanan garin nan, wane aiki ne agidan da sai kin samu mai aiki? Ummu tace kawai ina so na samu abokiyar fira ne, kaga idan ka tafi baka dawowa sai dare, wani lokacin ma har sai nayi bacci kake shigowa, bazan iya zama ni d'aya ba.



Alhaji yace ga Madu nan ai babu abinda zai sameki, wallahi ina tsoron mu kawo abinda zai halaka mu. Marairaice fuska tayi tana fad'i kayi magana da Malan Sani kila ya samo mana tagari. Jinjina kai Alhaji yayi yana fad'in shikenan, tunda kince Malan Sani nasan bazai tab'a kawo mana abinda zai cutar damu ba.


***

Koda ya samu Malan Sani da maganar sai yace akwai wata mata mai suna *Ladi*, makwabtansu ne acan tsohuwar anguwarsu, ta iya aiki dan tayi aiki sosai agidajen mutane, yawanci abinda yake sa tana barin gidan aikinta wulakancin mutane, wasu kuma idan taga ana aikata wani abu marar kyau bakinta baya iya shiru sai tayi magana, wannan ne yake sa a koreta, ko kuma idan aka so had'a baki da ita ayi cuta sai taki yarda to sai su rabu, aikin da tayi na k'arshe wanda dagashi tace ta daina aikatau, dalilin barinta gidan aikinta shine, matar gidan tasa ta zuba ma kishiyarta guba a abinci, data ki amincewa sai matar taso taja mata sharri ta zuba abincin a b'oye kuma ta kai maganin cikin kayanta, gashi dama itace take dafa masu abinci, sai akaci sa'a matar bata ci ba, ta zuba zataci ta tashi ta shiga d'aki, da yake suna da mage sai tazo ta saci nama taci, tana gamaci ta fara shure-shure sai gawarta aka iske ga kumfa abakinta.


Tunda aka ga haka akace guba ce a abinda taci, da aka duba sai akaga abincin matar ne taci, nan aka fara bincike sai ga magani an samu akayan Ladi, da yake Allah yana tare da mai gaskiya sai tayi sa'a mai gidan ya yarda da rantsuwar ta ya sallame ta da kud'i yace ta bar aikin. Mutuncin da Mai gidan yayi mata yasa ta sameshi ab'oye ta fad'a masa gaskiya, kuma ya yarda domin yasan halin matarsa. Tun daga lokacin ta dawo gidanta tace bazata sake aiki ba, domin wata rana za'a jawo mata d'auri, a bayan gidan mu take, ita kad'ai take zama a k'aramin gidanta mai d'aki d'aya, na mijinta ne daya mutu taci gado, da ba anan suke ba cirani ya kawo su har ya samu ya gina gida suke zaune shekara da shekaru, da ya rasu sai ta cigaba da zama dan tace bata da kowa, hakan yasa take aikatau. To yanzu sana'ar k'osai takeyi.


Jinjina kai Alhaji yayi cike da gamsuwa yace Malan Sani abun mamaki baya k'arewa a duniya, gaskiya naji tausayinta, kuma tunda ka yabeta nasan tana da hali mai kyau, dan haka kayi mata magana sai muji yanda kukayi. Malan Sani yace insha Allahu bazaku samu matsala da ita ba. Alhaji yace amma ka fad'a mata gidan mu zata dawo da zama, idan yaso sai ta bada hayar nata. Malan Sani yace angama.


****


Cikin sa'a Malan Sani ya samu Ladi da maganar, kasancewar Ladi tasan Malan Sani sosai, kuma taji shima a gidan yake aiki hakan yasa ta amince. Sosai tayi farin cikin samun wannan aikin, domin sana'ar babu kasuwa yanzu, hakan yasa ta fara addu'ar samun aiki sai gashi Allah ya kawo mata. Babu b'ata lokaci ta amince tace zuwa jibi yazo suje gidan kafin ta samu wanda zai tsare mata gidan kafin a samu mai haya.


Malan Sani yace Ladi haya a Lagos ai bata wahala, ayau idan aka tallata gidan zaki samu wanda zai kama. Ladi tace yauwa dan Allah ka taya ni tallata gidan. Malan Sani yace insha Allahu, abinda nake so da ke ki k'ara kok'ari akan wanda na sanki dashi, domin nasan kina da Amana da gaskiya. Ladi tace insha Allahu zan kiyaye. Sallama yayi mata yana fad'in sai nazo jibin, idan kuma na samu wanda zai kama gidan zaki ganni. Ladi tace nagode sosai Malan Sani.


Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:38 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, MTN Card ta wannan lambar... 08147669770, kayi screen shoot ka tura ta whatsapp a lambar k'asa, idan kuma bank transfer zakayi ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*



0⃣9⃣


Cikin kankanin lokaci Ladi ta fara aiki agidan su Ra'eez, d'aki guda mai had'e da band'aki aka bata wanda yake a k'asa kusa da kicin, basu dade ba suka saba da Ummun Ra'eez saboda Ladi mace ce mai tsafta, kirki da natsuwa, rayuwar Lagos ta ratsata shiyasa take a waye, idan ka ganta sai kace bata manyanta ba, domin sam jikinta baya nuna shekarunta, yanda kasan tayi boko haka take, gata da ilimin addini.


Itace take shara, guga da wanke-wanke, sannan tana yima Ummun Ra'eez wanki da guga, duk da a injin wanki ne takeyi, abinci kuma Ummun Ra'eez ce takeyi duk da Ladi tana tayata wani abun, haka idan tana da sako a kasuwa itace take zuwar mata saboda tasan ta kan kasuwa sosai. Ummun Ra'eez tana jin dad'in zama da Ladi sosai, sam bata jin kad'aici yanzu.


**** ***

Adebayo ne da Umar zaune a ofis d'in Alhaji Marusa, bayan sun gama gaisawa Alhaji Marusa yace Adebayo maganar gaskiya hak'urina ya k'are, jiya mukayi magana da Brr. Barau akan wannan mutumin Alhaji Maiwada, duk wata dabara da zamuyi akan a d'aukeshi daga nan munyi amma abun yaki aiki, Mr. Kallah ya fad'a mani bazai yuwu a canzashi yanzu ba, da ace ba amatsayin shugaban kwastam aka kawoshi nan ba da tuni an canzashi, amma yanzu dole sai nan gaba kafin a canzashi.


Saboda haka jiya na yanke shawara ina ganin idan muka bita zamu samu mafita. Adebayo yace Alaji wace shawara ka yanke? Murmushi yayi yana fad'in mai zai hana idan kayana suka shigo musan yanda zamuyi a b'oye wasu idan yaso sai muce shine ya kwashe su.


Gyara zama Umar yayi yana fad'in Alhaji akwai abinda nake zargi a wajen Alhaji Maiwada, ina tunanin kamar ya samu wani canji mai tsoka, domin da alama ya maido Iyalinsa nan garin, ada nasan agidan haya yake zaune, domin lokacin da yazo aka nemi abashi gida yace baya so, to sai yaje ya kama haya, abinci ma direbanshi yake siyo masa alokacin na gane Iyalinsa basa nan, to a kwanan nan naga canji sosai, da alamu ya maido Iyalinsa nan, domin ina ganin Malan Sani yana kawo masa abinci da azahar tayi, kulolin da ake zubo abincin sun sha bamban da abinda yake kawo masa abinci da, sannan alamu sun nuna ya tashi daga tsohon gidanshi, domin shekaran jiya ina bayansu naga ba hanyar tsohon gidanshi suka bi ba, kuma alokacin ya tashi gida zaije.



Alhaji Marusa yace ko dai yayi sabon gini ne? Umar yace da alama, domin hanyar da naga yabi wajen Surelere ne. Jinjina kai Alhaji yayi yana fad'in kasa mashi ido, idan har zargin mu ya zama gaskiya ina mai tabbatar maku Alhaji Maiwada ya shigo hannu.


Murmushi Adebayo ya saki yana tambayar Umar abinda suka fad'a dan be fahimta duka ba. Bayani Umar yayi masa. Saurin tashi yayi yana fad'in idan ya kasance gaskiya yayi gini Alaji kabarni dashi, zan kulla masa sharrin da zaiyi kuka. Dariya Alhaji Marusa yasa yana fad'in nasanka Adebayo baka da kyau, idan kana nan bani da sauran damuwa, dan haka na baka wuka da nama. Jinjina kai Adebayo yayi. Kud'i masu yawa Alhaji Marusa ya basu kafin suka tafi.



**** ***


Lab'e su Umar suke a wani waje suna kallo motar Alhaji Maiwada ta tsaya a bakin gate suna jira a bud'e masu. Mamaki ne ya kamasu ganin irin tsalelen gidan da zasu shiga. Basu gama mamaki ba sai da aka bud'e k'ofar gidan, k'ara matsowa sukayi domin su gane ma idanuwan su.


Bayan da suka shiga Madu ya rufe k'ofa. Umar yace Adebayo ka gani ko? Adebayo yace tunda naga sun shigo wannan unguwar nasan Sir ba k'aramin sata yayi ba, kalli yanda gidan yake kamar na shugaban k'asa. Umar yace ka bari yashiga dole muje wajen maigadin muji ko gidansa ne ko kuma haya yakeyi.



Suna nan sai ga Malan Sani ya fito daga gidan shi kad'ai suna sallama da Madu, dan anan yake barin motar yana hawa ta haya, duk da Alhaji yace yarik'a tafiya da ita amma Malan Sani yace nan yafi tsaro acan yana tsoron b'arayi.


Har suka gama sallama da Madu yazo ya wuce su be gansu ba. Bayan 'yan mintuna suka fito suka nufi gidan. Umar yace Adebayo ka tsaya anan, bana so maigadin yayi saurin gane mu, kaga idan ya fad'ama Alhaji akwai wanda baya jin hausa zai iya d'agowa, dan haka ka tsaya naje. Murmushi Adebayo yayi yace shikenan kaje.



Madu yana zaune yaji alamun sallama daga waje. Lek'awa yayi sai yaga Umar atsaye. Fitowa yayi ya bashi hannu suka gaisa. Umar yace sannu da aiki kayi hakuri na tadoka kana zaune. Madu yace haba ai bakomai, dama aikina ne na kula da k'ofar ai.


Umar yace ni bako ne, akwai gidan da akayi mani kwatance anan unguwar gashi nazo kuma wayata ta mutu bare nakira azo a d'auke ni kuma kwatancen ya b'ace mani shine nace bara nayi tambaya.



Madu yace ka kyauta kuwa, domin matambayi baya b'ata, ya sunan Maigidan da kazo wajenshi? Murmushi Umar yayi yace ina neman gidan Alhaji Hamza mai naira ne. Murmushi Madu ya saki yana fad'in duk da sabon zuwa ne ni nasan Alhaji Hamza, muma ba mufi wata biyar da muka dawo nan ba, maigidana ne ya gina wannan gidan shine muka dawo kasan shine shugaban kwastam.


Umar yace lallai kace agidan shugaban kwastam kake aiki, lallai kaja kaya abokina. Madu yace sosai kuwa, domin Alhaji ba ruwansa, yana da kirki sosai, yafi shekara biyu da rabi yana gina wannan gidan sai wannan shekarar muka dawo bayan ya d'auko Iyalinsa. Umar yace kaji dad'in ka, ina ne gidan Alhaji Hamzan?


Madu yace da ka shiga wancan layin zakaga gida mai babbar katanka fitilu sun haske layin, gidanshi yafi na kowa tsawo a layin zaka ga hada sojoji a k'ofar gidan. Umar yace nagode sosai. Madu yace bakomai agaida gida.



Har ya k'arasa wajen Adebayo yana mamakin irin kud'in da Alhaji Maiwada ya kashe a wannan gidan. Yana zuwa yaja Adebayo suka nufi wajen da suka aje motar su.


Sai da suka bar unguwar sannan Umar ya fad'a ma Adebayo komai. Hannu Adebayo ya tafa yana fad'in da kyau, anzo wajen, wallayi sai Sir, yasan yayi mana rashin mutunci, wannan gidan daya gina sai yayi danasani, ya hana mu jin dad'i ya tsare komai ashe kanshi yake tarama kud'i, kalli gidanshi kamar na babban d'an siyasa, Umar ka bani zuwa gobe zan nemo shawara. Dariya Umar yayi yace bana jinka Adebayo.


***

Tun da safe Malan Sani yazo domin yau da wuri zasu fita. Ummun Ra'eez ce ta fito daga kicin hannunta rik'e da kwandon abincin data zuba masa. Kallonta Alhaji yayi yana fad'in sannu Ummun Ra'eez.


Murmushi tayi tana fad'in sai kace nayi wani aiki babba. Alhaji yace aiki ne mana, yanda kike faranta mani Allah ya faranta maki kema. Murmushi tayi tace amin Abbun Ra'eez.


Amsa yayi yana fad'in yau zamu kai dare saboda wasu kaya za'a kawo kuma dole na tsaya a gama duba su domin kayan Alhaji Marusa ne kuma kinsan na fad'a maki yana shigo da kaya marasa kyau yanzu ne abun yayi sauki dana saka ido, amma duk da haka idan aka kawo kayan manyan mutane dole sai na tsaya na duba duk da yanzu komai yayi sauki.


Ummun Ra'eez tace to Allah ya tsare mun kai, ya kareka daga sharrin mahassada, domin wannan aikin naku akwai had'ari, domin mutane basa son gaskiya gashi kai mutum ne mai gaskiya. Murmushi Alhaji yayi yana fad'in kome zai faru dani bazan bari a aikata b'arna ba sai dai kawai addu'a.


Ummun Ra'eez tace to Allah ya tsare. Yace amin, yauwa na manta ban fad'a maki ba su Ra'eez zasuyi hutu amma nace ma Alhaji Mansur kada akawoshi ya zauna tunda sabuwar islamiya aka maidasu idan muka samu lokaci sai muje, wani hutun sai yazo ko sati daya yayi. Ummu tace bakomai nima nafison ya zauna yayi karatu ai.



Har bakin k'ofa ta rakoshi tana masa addu'a, sai da ya fita kafin ta koma ciki. Malan Sani yana ganin Alhaji ya fito yayi saurin tasowa ya amshi kwandon hannunsa yasa a mota. Bayan sun gaisa da Madu suka fita. A mota ma labarin kayan da za'a kawo Alhaji yake bama Malan Sani har suka isa ofis.


***

Yau

10 / 54