Advertisements
Chapter 11 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   11 / 54

30K to 33K   out of 160.3K words

har karfe biyun dare Alhaji yana ofis ana duba kaya, aciki kuma sai da aka samu abinda aka fitar kafin yasa hannu suka gama biyan komai ya sallame su, sauran kayan kuma yace sai zuwa gobe za'a duba, acikinsu akwai sauran na Alhaji Marusa aciki. Haka sukayi sallama suka tafi hadasu Adebayo.


Aranar dole Alhaji yasa Malan Sani ya tafi da mota saboda dare yayi. Bayan ya ajeshi yashiga ciki shi kuma ya wuce. Gaiswa sukayi da Madu wanda har yayi bacci, bayan ya shiga ya rufe k'ofar shima yashiga d'akinsa domin Alhaji yace yarika shiga d'aki yana baccinsa idan ya dawo Allah ne mai tsarewa tunda suna addu'a. Hakan yasa da Alhaji ya dawo Madu yake kulle k'ofa yashiga ciki.


***


Washe gari kasancewar asabar ce yasa Alhaji bai fita da wuri ba, duk da yasan yana da aiki akwai kayan da zaije ya duba yasa hannu kafin a d'auka amma ya kwanta domin jiya agajiye ya dawo yace sai zuwa goma sai ya fita. Tunda ya tashi kawai yake jin kasala da fad'uwar gaba, wanka yayi sai yayi nafila ya zauna yana karatun kur'ani.


Sai k'arfe tara da rabi ya fito domin ya karya. Zaune suke yana cin abinci, kallonshi Ummun Ra'eez tayi tana fad'in Abbun Ra'eez yau sai naga kamar kana cikin damuwa ko? Murmushi yayi yace kawai na tashi da mutuwar jiki da fad'uwar gaba ne.


Hannunshi ta kamo tana fad'in kacigaba da addu'a nima ina taya ka, insha Allahu babu abinda zai faru da kai, Allah yana tare da kai domin kana rike da gaskiyar ka. Alhaji yace nagode kicigaba da yi mani addu'a kinsan aikin mu. Murmushi tayi tana mika masa abinci abaki. Amsa yayi yana sakar mata murmushi, da haka tacigaba da bashi abaki tana masa fira har yaji damuwar ta tafi.


Bayan ya gama Malan Sani yazo ta rakashi tana ta masa addu'a suka tafi.

Bayan da sukaje ofis suka kammala duba sauran kayan yasa hannu kafin aka d'auka. Aranar haka ya wuni baya jin dad'i, ko la'asar beyi ba ya tashi suka dawo gida.


****

Washe gari tunda safe wayar Mr. Kallah ta tadashi, yana ganin sunan sai da gabanshi ya faad'i, d'auka yayi tare da yin sallama. Bayan sun gaisa Mr. Kallah yace Alhaji jiya na samu waya daga Alhaji Marusa wai kayansa sunzo amma babu rabi acikin kayan kuma masu tsadar ne aka cire masa, ya fad'a mani abubuwan da babu kuma naji babu abinda ya sab'a doka bare ace an ciresu.


Ajiyar zuciya Alhaji ya saki yana fad'in Alhaji gaskiya babu wasu kaya da aka cire na Alhaji Marusa, wani kwali guda biyu ne kawai aka cire acikin kayansa domin akwai abinda ya karya doka, kuma agabana aka gama komai nasa hannu aka d'auki kayan kafin nabar wajen.


Mr. Kallah yace Alhaji Marusa yace bazaiyi asara ba dole a nemo masa kayansa ko kuma yashigar da k'ara domin yana da hoton komai kuma an kawo masa kaya babu wasu aciki, shiyasa nace bara na kira ka domin kayi bincike kafin yashigar da k'ara. Alhaji yace shikenan zan bincika tunda kace ayi haka. Sallama sukayi ya kashe wayar.


Kai Alhaji ya dafe yana fad'in innalillahi wa inna ilaihirraji'un. Da sauri Ummun Ra'eez ta tashi dan tunda aka kirashi ta farka. Dafashi tayi tana fad'in lafiya Alhaji? Labarin abinda ya faru ya bata. Jinjina kai tayi tana fad'in kayi binciken kamar yanda ya fad'a, gaskiya Mr. Kallah yana sonka da har ya iya kiranka ya fad'a maka, kila dai bayan daka gama duba kayan aka samu matsala bayan ka bar wajen.


Alhaji yace Ummun Ra'eez matuk'ar ba'a gano inda kayan suke ba akwai matsala, domin kayan da suka b'ace na miliyoyin kud'i ne, dole Alhaji Marusa bazai kyale ba domin hakan zai jawo masa babbar asara, dole ma yashigar da k'ara saboda kayan suna da tsada.


Ummun Ra'eez tace yanzu idan ba'a gano inda suke ba mai zai faru kuma? Alhaji yace Allah kad'ai ya sani, domin sai abun ya shafemu duk wani wanda yake wajen alokacin da aka duba kayan. Ajiyar zuciya ta saki tana fad'in insha Allahu haka bazata faru ba.


Tashi yayi yana fad'in bara nayi wanka na fita. Ummun Ra'eez tace yau fa lahadi taya zaka fita da wuri haka. Alhaji yace dole na fita domin wannan babbar matsala ce. Waya ya d'auka ya latso Adebayo.


Bayan ya d'auka ya fad'a masa su had'u ofis ya kira sauran wad'an da sukayi aiki ajiya da shekaran jiya. Adebayo yace Sir, zanje coci anjima sai dai idan mun dawo. Alhaji yace na manta, shikenan zan jira ku a ofis. Kashe wayar yayi ya kira Umar, yana dauka yace su had'u a ofis. Kashe wayar yayi yashige band'aki.



****

Zaune suke a d'akin taro kowa yayi shiru yana jimamin abinda ya faru. Alhaji ya rasa abinda yake masa dad'i, tun d'azu da yazo yake bincike amma be samo komai ba, har sauran ma'aikatan sukazo aka cigaba da bincike. Adebayo yashiga damuwa yanda kasan kayanshi ne. Sallah kad'ai take fitar dasu.


Har yamma suna bincike amma basu gano komai ba, sun duba komai gashinan kayan sunzo, kuma an duba su amma gashi ba'a kaisu ba, hatta da wad'an da suka d'auki kayan sun tabbatar iya abinda suka kai sune abinda aka basu. Sosai abun ya d'aure ma kowa kai, haka suka gaji kowa ya tafi.



Alhaji kuwa wajen Mr. Kallah ya wuce, alokacin suna tare da Alhaji Marusa, acan ma maganar d'aya ce Alhaji Marusa yace k'ara zai shigar, gaba d'aya ya tashi hankalinsa saboda kaya ne na makudan kud'i suka b'ace. Mr. Kallah sai hakuri yake bashi amma yaki hakura, yaki bari ma a cigaba da binciken yace yayi magana da lauyenshi gobe za'a shigar da k'ara.


Ganin Alhaji ya damu yasa Mr. Kallah yace ya kwantar da hankalinsa gara aje kotu za'afi saurin gano wanda ya d'auki kayan domin hukuma zata shigo ciki. Jin haka yasa Alhaji yaji hankalinsa ya kwanta domin shima yafi buk'atar hukuma tashigo ciki. Haka sukayi sallama ya tafi.



Yana barin wajen suka kwashe da dariya. Alhaji Marusa yace ai na fad'a maka, bani da kyau Mr. Kallah, dama can kyaleshi nayi amma yanzu yashigo hannu na, sai na sashi yayi dana sanin zuwanshi Lagos, haka kawai muna zaune lafiya wani yazo ya nemi tada mana hankali, wallahi rabon dana shiga damuwa har na manta sai zuwan wannan mutumin.


Mr. Kallah yace baka da kyau mutumina, wallahi banji tausayinsa ba, domin tun farko naso na d'orashi a hanya ya nuna mani shi mai gaskiya ne, yo yanzu waye yake wani aiki da gaskiya, ai yanda kazo kaga kowa da bindi kaima nemi ko tsumma ne ka d'aura domin agudu tare a tsira tare, wannan matsayin fa ba daga gidanku kazo dashi ba, anan ka sameshi kuma nan zaka barshi, ka bari kaci wasu ma suci amma ya tsaya yana nuna mana shi mai gaskiya ne, zaiga gaskiya kuwa Allah ya kaimu aje kotu gobe zai gane baida wayau.


Alhaji Marusa yace baka ga gidan daya gina bane, yasan beda gaskiya shiyasa ko walimar tarewa beyi ba. Mr. Kallah yace ai tunda kace mani a surelere yayi gidan nasan akwai wata ak'asa. Alhaji Marusa yace ka barshi da gidan zamu kamashi ai, yau da dare su *Peter* zasuyi aikinsu. Mr. Kallah yace kai dan Allah? Alhaji Marusa yace wallahi kuwa, ai kaidai kasa ido kayi kallo. Dariya suka kwashe da ita.



Ur's.
Nabeelert Lady[3/10, 8:38 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, MTN Card ta wannan lambar... 08147669770, kayi screen shoot ka tura ta whatsapp a lambar k'asa, idan kuma bank transfer zakayi ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*



1⃣0⃣


A daren ranar Alhaji Maiwada kasa runtsawa yayi, Ummun Ra'eez ce take kwantar masa da hankali, sosai hankalinsa ya tashi domin jikinsa yayi sanyi, yana ji aransa kamar wani mugun abu ne zai faru, yayi mamaki da akace wai masu d'aukar kaya basu dauka duka ba, bayan yasan sai da aka gama komai suka tafi kafin ya bar wajen.


Haka yayo alwala ya fara nafila yana neman tsarin Allah daga kowane sharri da yake tunkaroshi. Bayan ya idar ya bud'e kur'ani ya fara karatu har sai da aka kira sallar farko kafin ya tashi ya yo alwala yayi nafila sannan ya fita zuwa masallaci.


Beshigo gida ba sai da gari yayi haske, yana shigowa wanka kawai yayi ya kwanta anan bacci ya d'aukeshi saboda gajiya. Sai k'arfe takwas ya farka dalilin wayarsa da aka kira. Sunan Adebayo ya gani, yana d'auka bayan sun gaisa Adebayo ya fad'a masa an aiko da takardar sammaci daga kotu k'arfe goma za'a shiga. Alhaji yace shikenan sai na fito.


Band'aki yashi bayan ya fito ya shirya sannan ya fito falo. Bayan sun gaisa da Ladi ta shige ciki yayin da Ummu ta zuba masa abinci. Ruwan shayi kawai ya sha yace ya koshi. Zama Ummu tayi tana fad'in haba Abbun Ra'eez, ka sani damuwa bata haifar da komai sai ciwo, ka yi addu'a Allah bazai barka haka ba, idan kuma kaga wani abu ya faru da kai kada kace addu'ar ka bata karb'u ba, kasa aranka Allah yana so ya jarabceka ne kawai, kuma kasan muhimmancin yadda da k'addara.


Ajiyar zuciya ya saki yana fad'in naji dad'in maganarki, kuma tasa zuciyata tayi sanyi haka kuma kin k'ara mani kwarin guiwa, bakomai, duk abinda ya faru zan d'aukeshi amatsayin k'addarata, domin bawa baya zama haka dole sai da jarabawa.


Murmushi Ummu tayi ta zuba masa abinci ta fara bashi abaki tana kwantar masa da hankali, a haka yarika amsa har yaci sosai, yaji dad'in yanda Ummu tayi masa, shiyasa akoda yaushe yake k'ara sonta domin tasan yanda ake kula da miji.


Bayan ya gama ta rakashi har k'ofar gida inda suka gaisa da Malan Sani kafin tayi masa fatan alkhairi ta koma ciki. Amsar jakarsa Malan Sani yayi yana fad'in Alhaji yau ka makara. Murmushi yayi ya shiga mota bece komai ba.


Bayan sun fita ya kalli Malan Sani yana fad'in babbar kotu zamuje. Da sauri Malan Sani ya kalleshi yana fad'in maganar ta tabbata kenan?........ ....... Labarin abinda ya faru Alhaji ya bashi. Malan Sani yace ikon Allah, Alhaji wannan abu akwai alamar tambaya fa.


Alhaji yace Malan Sani kawai mu barma Allah komai, jikina yana bani akwai abinda suka shirya, dan haka zan d'auki duk wani abu da zai taso. Tausayin Alhaji ne ya kama Malan Sani, yasan wani kullin ne suke so suyi mashi. Malan Sani yace Allah ya saukaka koma menene. Alhaji yace amin.


****

Bayan sun isa kotu da Mr. Kallah ya fara had'uwa, wucewa yayi wajensa suka gaisa kafin ya jashi suka nufi wajen motarsa. Kallon Alhaji yayi yana fad'in kayi hak'uri da duk abinda zai faru, nayi magana da kwamishinan 'yan sanda yace zasuyi bincike dole a gano inda aka b'oye kayan, dan haka zasuzo suyi bincike duk inda ya kamata, Adebayo ya bani sunayen mutanan da suka tsaya akan kaya tun daga kanka har k'asa, kuma kowa za'a bincikesa, dan haka kada ka damu idan suka zo bincike, hakan ne kawai zaisa a gano gaskiya.


Jinjina kai Alhaji yayi yana fad'in babu damuwa, suzo zan basu damar yin bincike duk inda suke so, nima nafison hukuma suyi bincike domin na kasa gano komai.


Ganin motar Alkali yasa sukayi saurin nufar cikin kotun. Haka kowa yashiga ciki ya samu waje ya zauna suna jiran shigowar Alkali.



Brr. Barau ne yashigo bayansa Alhaji Marusa yana bayansa suna magana a hankali, wajen zamansa ya wuce Alhaji Marusa ya zauna gefen Mr. Kallah. Alkali yana shigowa kowa ya tashi, bayan ya zauna kowa ya zauna.


Gaba d'aya kotun tayi shiru ana jiran a fara. Magatakarda ne ya tashi ya fara karanto k'ara kamar haka.... *Yau sha biyu ga watan janairu shekara ta dubu biyu, (12/1/2000), wannan kotu zata saurari k'arar da Alhaji Marusa ya shigar akan tuhumar hukumar Kwastam da salwantar masa da kayansa na mukudan kud'i bayan sun iso a jirgin ruwa, wanda aka rik'esu har tsawon kwana d'aya da yini guda kafin aka sake su, sai dai aciki babu wasu daga cikin kayan da suka iso wanda ya tabbatar da zuwan su kuma an dubasu kafin a kaisu wajenshi aka cire wasu daga ciki. Alhaji Marusa yana rokon wannan kotu mai alfarma data kwato masa hakkinsa a wajen hukumar kwastam*.



Risnawa yayi ya mik'a takardar wajen Alkali. Bayan daya gama dubawa yace lauyoyin da zasu gabatar da shari'ar su fara.


Brr. Barau ne ya tashi yana fad'in sunana Brr. Nuhu Barau, nine lauyen da yake kare wanda yake k'ara. Alkali yace ina lauyen da zai kare wad'an da ake k'ara? Tashi Alhaji Maiwada yayi yana fad'in bamu d'auki lauya ba domin yau da safe takardar sammacin ta same mu, nine zan kare hukumar mu.


Jinjina kai Alkali yayi yana fad'in Brr. Barau zaka iya farawa. Risnawa yayi kafin ya fito yana fad'in ina so nayima shugaban kwanstam wasu tambayoyi. Alkali yace an baka dama.


Bayan Alhaji ya fito Brr. Barau yace kotu zata so taji sunanka da kuma matsayin ka.


Sunana Alhaji Hamza Maiwada, nine shugaban kwastam.


Brr. Barau yace kaji bayanin da aka karanta yanzu, shin ko zaka iya yima kotu k'arin haske akan abinda ake tuhumar hukumar ku dashi? Gyara tsayuwa Alhaji yayi yana fad'in tabbas nine wanda ya duba kayan Alhaji Marusa, kuma sai da na tabbatar da komai lafiya kafin nasa hannu aka gama komai sannan muka sakar masu kayan suka d'auka, agaban mu suka d'auki kayan babu abinda aka rage kafin muka bar wajen.


Brr. Barau.. Amma Alhaji Marusa yace kafitar da kwalaye biyu acikin kayansa kace sun sab'a doka, kuma gashi kai kace ba'afitar da komai ba? Alhaji yace ina nufin acikin kayansa da aka duba wanda nasa hannu babu abinda aka rage, wad'an da aka fitar kuma dama bandasu acikin wad'an da nasa hannu, haka ne nasa acire kwalaye biyu acikin kayansa domin sun sab'a doka.


Murmushi Brr. Barau yayi yana fad'in tun bayan zuwanka garin nan Alhaji Marusa ya fara fuskantar matsala da hukumar ku, kuma kowa yasan irin dad'ewar da yayi yana kasuwanci a k'ashashen waje, akwanakin baya ma sai da kayansa suka samu matsala, shin ko akwai wata matsala da take tsakanin ku ne? Girgiza kai Alhaji yayi yana fad'in nifa ma'aikacin al'umma ne, su nake ma aiki tare da k'asata, bani da wata matsala tsakanina da Alhaji Marusa, kamar yanda kowa yake shigo da kaya muke dubawa shima haka muke duba nashi, sai dai kawai kasan kowa da tsarin aikinsa, to nima haka nawa tsarin yake, matuk'ar kaya suka iso dole sai mun tabbatar da ingancin su kafin musa hannu a sake su, matuk'ar muka kama kayan da suka sab'a k'a'ida dole ne mu ciresu, bayan wannan ni banida wata matsala da kowa.



Brr. Barau... Amma yace kayan kwannasu d'aya da yini guda, baka tunanin kafin ku kammala duba kayan aka samu wani ya d'auke wad'an da suka b'ace? Alhaji yace babu wanda ya tsaya akan kayan, bayan da muka duba na farko haka kowa ya tafi sai washe gari aka k'arasa duba sauran, sai dai kasan zuciya bata da k'ashi, Allah ne kad'ai yasan gaskiya, tun bayan da aka fad'a mani wannan matsalar na tara duk wad'an da sukayi aiki aranar muka tattauna, sai dai maganar d'aya ce, babu wanda yasan inda suke, dan haka ina rokon wannan kotu mai albarka data bada izini hukuma tayi bincike akan wannan matsalar hakan zaifi mana sauki.


Jinjina kai Brr. Barau yayi ya juya yana fad'in ya mai shari'a, ina rokon wannna kotu mai albakar, kamar yanda Alhaji Maiwada ya nemi alfarma a d'aga wannan shari'a domin hukuma ta samu damar yin bincike hakan zaisa a samu cikakkar sheda. Nagode.


Bayan da Alkali ya gama rubutu ya d'ago yana fad'in wannan kotu ta bama hukumar 'yan sanda dama da su tsananta bincike zuwa nan da kwana biyu za'a dawo kotu domin acigaba da gabatar da wannan shari'a. Tebur ya buga gaba d'aya akace kottttt .


Gaba d'aya kowa ya fita yana jajanta abinda ya faru, yayin da wasu suke tausayin Alhaji Maiwada domin sun san halinsa.


Bayan da suka fito Mr. Kallah yaja Alhaji Maiwada suka nufi wajen motar kwamishinan 'yan sanda wanda be dad'e da zuwa ba saboda wayar da sukayi da Mr. Kallah.


Bayan sun gama gaisawa Mr. Kallah yayi masa bayanin halin da ake ciki akan abinda Alkali yace. Kwamishina yace kada ka damu Alhaji zansa yarana suyi bincike, ina so ku bamu had'in kai ta haka ne zamu ji dad'in yin aikin. Alhaji yace insha Allahu bazaka samu matsala da mu ba.


Haka suka gama tattaunawa kafin sukayi sallama ya shiga mota suka nufi ofis. A hanya Malan Sani sai kwantar ma Alhaji da hankaki yakeyi har suka isa.


***


A can ofis kuwa hankalinsa atashe yake, Adebayo da Umar ne kawai hankalinsu yake kwance domin sun san bakin zaren, Alhaji ya sake tara kowa ya rokesu akan idan akwai wanda yake dasa hannu akan wannan abun ya taimaki mutane ya fito da kanshi kafin hukuma ta ganoshi, domin duk wanda aka gano shi kad'ai za'a kama.


Nan kowa yace beda masaniya akan abun. Haka dai taron ya tashi babu wani labari. Haka Alhaji ya wuce ofis jiki a sanyaye. Yinin ranar haka yayishi jiki babu kwari.


Bayan anyi sallar azahar sai ga

11 / 54