Advertisements
Chapter 24 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   24 / 54

69K to 72K   out of 160.3K words

ya bamu ikon tabbatar da gaskiya, amma aikin mu yana da had'ari sosai, idan mutum yaso zai nemi lahira dashi, idan kuma yaso sai ya tara abun duniya dashi. Jabeer yace wannan haka yake, muje muyi sallah naji an fara kira.



***

Bayan da suka tashi Ra'eez yayi sallama da Jabeer, bakin motarsa ya tsaya yana jiran fitowar Alkali. Yana nan tsaye sai gashi ya fito shida Brr. Bajinta suna tafe suna magana sai dariya sukeyi.


Da wani irin kallo Ra'eez ya bishi yana jin wani zafi aranshi. K'arasowa sukayi Alkali yana fad'in Ra'eez yi hak'uri na tsayar da kai. Ra'eez yace ai bakomai.



Brr. Bajinta yace 'yallab'ai yau kana da babban bako kenan? Alkali yace wallahi kuwa, bara muje sai Allah ya kaimu. Brr. Bajinta yace Allah ya kaimu. Alkali yace Ra'eez bara na shiga gaba sai ka biyoni abaya ko.


***

Tunda suka shiga unguwar Surelere idanuwan Ra'eez suka canza kala, gaba d'aya jijiyoyin kansa suka tashi, shigowarsu unguwar sai ya tuna masa da rayuwar Iyayensa. Runtse ido yayi lokaci guda suka kawo ruwa.


Tunaninsa ya tsaya ne alokacin da yaga Alhaji Barau ya tsaya a k'ofar gidan da yake tunanin ya tab'a rayuwa acikinsa a shekarun baya, tabbas ko ba'a fad'a masa ba yasan wannan gidan Abbunsa ne daya gina da kud'insa wanda Abbu yayi masa wayau akan baya sonshi hakan yasa ya koma Apapa.


Tsayawa yayi har yaga motar Alhaji Barau ta shige ciki, tunani yayi ko dai ya tafi, dan bazai iya shiga gidan ba. Wata zuciyar ta bashi shawara daya daure yashiga, dole ya b'oye komai matuk'ar yana son gano gaskiya.


Cike da gamsuwa da shawarar da zuciyarsa ta bashi ya kutsa kan motar cikin gidan, yayin da yake kok'arin saita kanshi. Alhaji Barau ya fito yana jiran fitowar Ra'eez.


Sai da ya rufe motar kafin ya nufo wajen Alhaji Barau. Murmushi kwance a fuskarsa ya kalli Ra'eez yana fad'in bsimilla muje. Haka yabi bayansa yana kallon gefen gidan wanda Abbunsa yace b'angarensa ne zai gina idan yayi aure su zauna, tuni an gama gina wajen da alama b'angaren baki ne ko na yaransa maza. Girgiza kai Ra'eez yayi aranshi yana fad'in fenti kawai aka sake ma gidan amma komai nashi yana nan.


Tunaninsa ya dawo alokacin da Alhaji Barau yake gaisawa da mai aikin gidan. Risnawa Ra'eez yayi yana gaishe da mai aikin daya fito daga gidan.


Har ciki suka shiga bakinsa d'auke da sallama, sai dai babu kowa afalon sai TV da takeyi ita kad'ai. Kallonsa Alhaji Barau yayi yana fad'in zauna Ra'eez bara nayima mutanan gidan magana.


Zama yayi yana k'are ma gidan kallo. Da sauri yasa hannu ya goge kwallar data zubo masa, duk yanda yaso ya tsaidata kasawa yayi dole sai da suka zubo, hakan yasa yayi saurin goge su.


Motsin da yaji ne yasa shi kallon matattakalar benen, wata mata ce ya gani sun jero da Alhaji Barau sai murmushi take suna magana. Tana k'arasowa falon ta kalli Ra'eez tana fad'in lallai Alhaji yau muna da babban bako, ka kyauta daka kawo manishi, dan tunda ka bani labarin yanda ya tafiyar da shari'ar su Amina naji ya burgeni, sannu da zuwa Ra'eez.


Zamewa Ra'eez yayi yana gaisheta. Zama tayi tana amsawa. Alhaji Barau yace ai Ra'eez yana da kirki, jinsa nake tamkar d'ana. Hajiya Hauwa tace nima haka kawai naji ya kwanta mani, shiyasa nace maka naji dad'i daka kawo manashi.



Alhaji Barau yace ina *Raheenatu* take? Hajiya tace tana ciki, bara na kirata ta kawo masa abunsha. Ra'eez yace Hajiya kibarshi akoshe nake tafiya ma zanyi. Alhaji Barau yace ai ba haka mukayi da kai ba, dole kaci abinci ko kad'an ne.


Duk'ar da kai Ra'eez yayi bece komai ba. Wucewa Hajiya tayi tana fad'in ina ma za'ayi haka ai har abinci sai kaci. Bayan ta kira Raheena ta wuce kicin.


Suna zaune Raheena ta fito, tun kafin ta k'arasa shigowa falon k'amshin turarenta ya bud'e falon, a hankali Ra'eez ya d'ago kanshi domin yaga wanda yashigo da k'amshin.


Ido suka had'a da Raheena alokacin da ta fito sai kwarkwasa takeyi, wata doguwar rigace ajikinta mai kyan gaske, d'inkin yayi kyau domin tabi jikinta, kanta d'aure da d'ankwali fuskarta tasha kwalliya, sosai kayan suka matseta sai yanga takeyi tana taubar cingam ko mayafi babu.


Kicin ta wuce, ta jima kafin ta fito hannunta d'auke da faranti babba. Ra'eez kuwa tunda ya kalleta ya d'auke kai. Alhaji Barau ne ya tashi yana murmushi yace bara nashiga daga ciki ka saki jikinka kaci abinci nan ma gidan ku ne, yanzu zan fito, Raheena ki tayashi fira.


'Daga kai tayi tana murmushi. A tare da Hajiya Hauwa suka haura sama. Zama Raheena tayi tana fad'in barka da zuwa da fatan kazo lafiya? Ra'eez yace lafiya lau.


Lemu ta zuba masa ta mik'a masa tana fad'in bismillah. Amsa yayi yana fad'in nagode. Matsowa tayi kusa dashi tana fad'in naji labarin shari'ar daka gudanar gaskiya kayi kok'ari, sosai naji dad'i fa.



Ra'eez yace nagode. Shiru tayi ta tsura masa ido, tunda take arayuwarta bata tab'a ganin namiji mai kyansa ba, haka tunda Dadynta yace mata tayi kwalliya zai zo da bako take jin farin ciki, ashe wanda zai zo had'ad'd'an gaye ne, gaskiya dole ma Dady ya aura mata shi don ayanzu kad'ai jitake bazata iya rabuwa dashi ba, idan ko yaki amincewa da ita. zata iya shiga wani hali.


Gyaran murya Ra'eez yayi ganin irin kallon da take masa, da sauri ta d'auke idonta tana murmushi. Ra'eez yace zaki iya tafiya nagode. Raheena tace haba Yayana baka son na taya ka firar? Kauda kai yayi yana fad'in kaina yana mani ciwo ne.


Murmushi tayi tana fad'in bara na kawo maka magani. Kai ya girgiza yana fad'in bana shan maganin ciwon kai kawai surutu ne bana so. Tashi tayi tana fad'in nayi shiru bara na zauna acan, kallon ka ya fiye mani surutun ma.


Zama tayi a saman kujera tana binshi da kallo. Kauda kai yayi yana jan tsaki a zuciyarsa dan har itama haushinta yakeji gashi bata da kamun kai.


Fitowar Alhaji Barau ce tasa ya d'an saki fuska. Alhaji Barau yace Ra'eez har ka sha ruwan ko? Ra'eez yace nasha tafiya ma zanyi. Hajiya Hauwa da ta sauko take fad'in ga abinci fa zamuci.


Mik'ewa Ra'eez yayi yana fad'in nagode Hajiya ana jirana a gida ne. Da sauri Raheena tace kana da aure ne? Murmushi Alhaji Barau yayi yana fad'in beda aure kila dai abokinsa ne yake jiransa.


Ajiyar zuciya ta saki tana fad'in har naji dad'i Dady. Hajiya Hauwa tace Oh! ni Hauwa'u, wallahi Raheena baki da kunya. Alhaji Barau yace nagode Ra'eez, amma wata rana zaka zo muci abinci tare.



Ra'eez yace insha Allah. Sallama yayi masu sai godiya suke masa. Alhaji Barau ne ya kalli Raheena yana fad'in bazaki rakasa mota ba. Da sauri tayi gaba tana fad'in na d'auka kai zaka rakashi ai Dady. Hajiya Hauwa tace waye k'arami anan ai dole kece zaki rakashi.


Har bakin mota ta rakashi, bayan ya zauna zai rufe tayi saurin rik'e murfin, langwab'ar da kai tayi tana fad'in Yayana sai yaushe kuma? Kau da kai yayi yana fad'in nima ban sani ba.


Shagwab'e fuska tayi hada dira k'afa tace kai dan Allah Yayana! Murmushi yayi dan ta basi dariya. Kallonta yayi yana fad'in shikenan zan samu lokaci nazo. Murmushi ta saki tana fad'in nagode Allah ya kaimun kai gida lafiya.


Ra'eez yace amin nagode. Rufe masa k'ofar tayi. Sai da ya fita daga gidan kafin ta shige ciki. A mota Ra'eez sai jan tsaki yakeyi akan abinda Raheena takeyi, sai kace ba mace ba, wai nan har karatu tayi. Murmushi yayi yana shafa fuskarsa, a hankali ya furta Alhaji Barau zan bar maka tabo biyu kuwa.


***

Da tsalle tashiga gidan ta rungume Hajiya Hauwa tana dariya. Alhaji Barau yace ikon Allah lafiyar ki kuwa? Hajiya Hauwa tace da alama anyi nasara.


Alhaji Barau yace ai tunda na ganshi nayi ma Raheena sha'awarsa, domin nasan shine irin zab'inta. Hajiya Hauwa tace wallahi nima ya kwanta mani, yaro sai kace jinin larabawa, jikinsa na hutu ne, da gani kasan ya fito daga babban gida, dan ya tsumu a cikin daula.



Raheena tace wallahi Dady ina matuk'ar sonshi dan Allah ka aura mani shi zan iya shiga wani hali idan na rasashi. Saurin rufe mata baki Hajiya Hauwa tayi tana fad'in haba shalele, kima daina fad'ar haka, ke d'aya muke da ita mace, sannan kece ta gaban goshin mu, dole ma ki auresa. Sake rungumeta tayi tana fad'in nagode Momy nah.



Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:39 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*



2⃣3⃣


Da gudu Raheena tayi d'akin ta tana mai cike da farin ciki, da kyar tayi sallolinta abinci ma a d'aki taci ta kosa dare yayi sosai ta kira Ra'eez dan ta amshi lambarsa a wajen Dadynta.


**

Ra'eez bayan ya kammala abubuwan da yakeyi ya kakkab'e gadonsa ya kwanta, rungume filo yayi yana jin kewar Iyayensa, tun dawowarsa gidan da aka gyara komai ya koma d'akin Abbunsa da zama, domin yana matuk'ar son gadon Abbunsa, babu abinda aka canza hatta da filo da katifar duk sune na kusan shekaru takwas, zanin gadon kawai ya canza shima na Ummunsa ya d'auko yasa, duk lokacin daya kwanta a gadon yana mai jin dad'i, sai yake jin kamar yana tare da Abbunsa ne.


K'arar wayarsa ce ta dawo dashi daga tunanin da yakeyi, d'auka yayi yana bin wayar da kallo har ta tsinke, dan besan lambar da ya gani ba, sake kira akayi amma be d'auka ba, sai da aka kira sau ukku kafin ya d'auka.



Shiru yayi ba tare da yayi magana ba. Mak'e murya Raheena tayi cikin shagwab'a tana fad'in haba Yayana sai da na kira sau ukku sannan zaka d'auka.


Murmushi Ra'eez yayi dan ya fahimci mai magana. Raheena tace koda yake laifina ne da ban baka lambata d'azu ba, amma kuma ya kamata ace ka d'auka tun akira na biyu.


Gyara kwanciya yayi yana fad'in kin kira waya sai surutu kikeyi baki fad'i sunanki ba. Cikin shagwab'a tace kai Yayana nasan dai ai ka d'auki muryata? Ra'eez yace ai ni ko wata mukayi da mutum ba lallai bane na rik'e muryarsa ba.


Murmushi tayi tana fad'in Raheena ce fa. Ra'eez yace Raheena? Wace Raheena fa? Yanzu kam kukan shagwab'a tasa hada birgima asaman gado, duk yana jiyota sai ma murmushi da yayi.


Gyaran murya yayi yana fad'in Malama zan kwanta naga alamar bakida abun cewa. Cikin sauri tafe Raheena da kazo gidan mu d'azu a Surelere fa.


Tab'e baki yayi yana fad'in Allah sarki ashe kece? Nasan dai ban baki lambata ba shiyasa nayi mamaki. Raheena tace awajen Dady na amsa ai. Ra'eez yace to yayi kyau ya 'yan gidan ki gaishe mani da su.


'Dif ya kashe waya yana sakin murmushin mugunta. Raheena kuwa saurin cire wayar tayi tana binta da kallo, sake kira tayi amma a kashe. Wurgar da ita gefe tayi tana mai jin haushi, amma bakomai zata jure komai matuk'ar zai amince da ita, tasan ma yana da saukin kai zai amince da ita. Bargo ta jawo tana murmushi.


***

Washe gari wayar Raheena ce ta tashesa abacci, dan bayan yayi sallar asuba ya kunna wayar ya kwanta bacci ya d'aukeshi. Saurin tashi yayi yana kallon yanda gari yayi haske sosai, wayar ya kalla yaga lambar jiya ce dan beyi saving ba.


Hannu yasa ya d'auka akaro na biyu da ta sake k'ara. Gaishesa tayi tana fad'in Yayana ko bacci kakeyi ne? Murza ido yayi yana fad'in wallahi kuwa gashi har na kusa makara, gaskiya nagode maki.


Dad'i ne ya kamata ta sake kank'ame wayar tana fad'in naji dad'i kuma zan rik'a tada ka a koda yaushe dan bana so ka makara. Murmushi yayi yace nagode, bara nashiga wanka.


Da sauri tace da ina kusa dana had'a maka ruwan. Ra'eez yace hakan ma nagode. Kashe wayar yayi ya nufi band'aki.



Raheena kuwa fad'awa tayi saman gado tana murmushi, saurin tashi tayi ta jawo hijabinta domin tayi sallah, dan alokaci zatayi sallar asuba, ahakan ma saboda suyi waya da Ra'eez yasa ta tashi wajen k'arfe takwas, dan Raheena akwai sallah a makare, wani lokacin sai ta kai k'arfe tara batayi sallar asuba ba.



Tashi tayi tana fad'in dole nasa alarm ko dan narik'a tashinsa sallar asuba, da haka zan saye zuciyarsa, idan na tashesa nima zan daure nayi sallar sai na koma bacci kafin alarm d'in 7:30 yayi na sake tadasa yayi wanka. Murmushi tayi tana kabbara sallah.


***


Komai beci ba ya rufe gidan ya nufi gidan su Rumaisa dan ya saba saiya fara duba su kafin yawuce wajen aiki.


A tsakar gida ya iske su suna karyawa koko da kosai, Rumaisa kuma tana had'awa da shayi dan bata shan koko. Da sallama yashiga. Amsawa sukayi Mama tana fad'in yanzu nake fad'in Rumaisa ta kawo mani wayata na kiraka naga shiru baka shigo ba.


Zama yayi yana fad'in wallahi yau makara nayi Allah yaso ma Raheena ta tashe ni da... Kwarewar da Rumaisa tayi ne yasashi yin shiru yana kallonta.


Mama tace kiyi ahankali mana Rumaisa. Shayin ta d'auka tasha tana goge hawayen da suka taho mata wanda babu wanda ya gani sai Ra'eez.



Murmushi yayi dan ya fahimci dalilin kwarewarta. Juyawa yayi yana gaishe da Mama. Bayan sun gama gaiswa Rumaisa ta gaishe sa. Harara ya buga mata yana fad'in shine ko ki tashe ni ko? Duk'ar da kai tayi fuskarta a d'aure.



Mama tace Rumaisa kawo masa kofi ya karya kafin yawuce. Ra'eez yace Mama na kusa makara gara dai na tafi kawai. 'Daure fuska Mama tayi tana fad'in tashi ki kawo masa kofin.


Murmushi yayi dan yasan halin Mama bata son ya fita beci komai ba. Tashi Mama tayi ta koma ciki ta barsu a waje. Zuba masa tayi ta mik'a masa kular kosan.


Amsa yayi yana kallon yanda tayi kicin-kicin da fuska kamar zatayi kuka. Murmushi yayi yana girgiza kai yace K'anwata waya tab'a mani ke kuma? Zama tayi tana kok'arin maida hawayen idonta.


Kosan ya kai baki yana kallonta sai juya kosan hannunta takeyi. Murmushi yayi yana fad'in ke shayi zaki sha ni kuma kin had'ani da koko saboda son kai ko? Kauda kai tayi bata ce komai ba.


Ra'eez yace wai bazaki kulani ba ne yau? Turo baki tayi tana fad'in kaje Raheena ta baka. Dariya yayi yana fad'in lallai sunan yayi maki dad'i, daga fad'ar suna so d'aya shikenan har kin haddace, ko kina so na had'aku kawance ne? Tab'e baki tayi tana fad'in Allah ya kyauta.


Girgiza kai yayi yana fad'in kada ki sake kiranta da Raheena domin Yayarki ce. A zabure Rumaisa ta tashi tana dira k'afa tayi d'akinta.


Dariya yayi sosai yana girgiza kai, abincinsa yacigaba da ci aranshi yana jin wani sanyi yana ratsa masa zuciya ganin yanda Rumaisar sa take nuna kishinta akansa, yana matuk'ar sonta amma har yanzu ya kasa fad'a mata, yana jira ta kammala karatun ta kafin ya fad'a mata amma a yanzu baya jin zai iya jiranta, domin yana buk'atar mai kula dashi, dole ma ya fito mata da abinda yake zuciyarsa shekaru da yawa.



Bayan ya kammala yayi ma Mama sallama. Fitowa tayi tana masa addu'a, kud'i ya aje yana fad'in Mama yau sakwara nake son ci. Mama tace badamuwa za'ayi maka, kun gaisa da Madu ko? Ra'eez yace lokacin dana shigo yana band'aki sai dai idan na fita yanzu.


Mama tace to Allah ya tsare ya baka sa'a a duk abinda kasa gaba, Allah ya kareka daga sharrin masu sharri. Murmushi yayi cikin jin dad'i yace amin Mama.


Mama tace ina Rumaisar fa? Ra'eez yace tana d'aki kila wani abun takeyi. Mama tace to sai ka dawo. Fita yayi yana waiwayen d'akin Rumaisa. Sai da suka gaisa da Madu ya bashi kud'i yana ta masa addu'a kafin ya tafi.


Asibiti ya fara biyawa ya duba Ummunsa kafin yawuce wajen aiki, koda yaje ya iske har Alhaji Barau yazo, kai ya jinjina yana fad'in lallai yau na makara da yawa. Ciki yawuce yana gaisawa da mutanan da suke waje.


Lokacin daya shiga ofis d'in Alhaji Barau tare da bako ya iskeshi, risnawa yayi ya gaishe su. Alhaji Barau yace Ra'eez ko dai bakayi bacci jiya da dare bane? Murmushi yayi yana fad'in wallahi makara ce kawai nayi.


Alhaji Barau yace Mr. Kallah kaga sabon lauyen da nake fad'a maka. Da sauri Ra'eez ya kalli wanda aka kira da Mr. Kallah, domin duka sunayen wad'an da suka zalunci Abbunsa babu wanda bai rik'e ba.


Murmushi Mr. Kallah yayi yana fad'in lallai ankawo maka cigaba a ofis d'inka, domin samun lauyoyi masu hazak'a yana k'arama waje kima, sannu Ra'eez kacigaba da dagewa kaji.



Kai Ra'eez ya d'aga. Alhaji Barau yace ga wani file nan kaje ka dubashi yanzu aka kawoshi, bana son ka wahalar da kanka domin ba wata babbar shari'a bace kasan wasu mutanan basu da kwakkwarar sheda kawai saboda sun maida kotu wajen wasa komai su kawo k'ara.


Ra'eez yace zan duba. Kai Alhaji Barau ya jinjina yana fad'in zaka iya tafiya. Sallama yayi masu ya fita. Mr. Kallah yace gaskiya natsuwar Yaron nan tayi mani sosai, daga ganinsa d'an manyan mutane ne.



Alhaji Barau yace shiyasa nake son had'ashi

24 / 54