Author : Marubuciyar Zamani Category : Complete Novels
shedar k'arya, wannan kotu ta soke lasisin aikinsa, sannan ta yanke masa hukuncin d'aurin wata biyar agidan yari tare da tarar naira million d'aya ga Malan Sani.
*Kwamishna Bello Kabir,* bisa kamashi da hannu dumudumu wajen taimakawa masu laifi, da kuma aikata laifi wajen sakama Malan Sani jaka a gidanshi, wannan kotu ta soke lasisin aikinsa, sannan ta yanke masa hukuncin d'aurin shekara biyu a gidan yari, sannan zai biya Malan Sani tarar naira million d'aya da rabi.
*Shugaban Kwastam Adebayo da Mataimakinsa Umar,* bisa kamasu da akayi wajen k'arba'r cin hanci, taimakama masu aikata laifi, da zaluncin da sukayi ma Alhaji Maiwada wannan kotu ta kwace lasisin aikinsu, sannan ta yanke masu hukuncin d'aurin shekara asirin agidan yari, sannan zasu bada tarar naira million ukku ga iyalan Alhaji Maiwada.
Sai hukunci na k'arshe akan mutuwar Naseer Sambo Jarmai da Alhaji Hamza Maiwada.
Mutane hud'u ne suka had'u wajen bada gudummuwa akan wannan kisa, dan haka kotu zata yanke masu hukunci.
*Alhaji Barau, Alhaji Muhammad Sanda, Alhaji Marusa da Mr. Kallah,* bisa kwararan shedu da aka gabatar ma wannan kotu, da kuma amincewar masu laifi akan laifinsu, kotu ta tabbatar da laifinsu, hakika sunci amanar aikin su, dan haka kotu ta yanke masu hukuncin d'aurin rai da rai agidan yari tare da horo mai tsanani, Alhaji Marusa zai biya diyar kashe Malan Hassan da yayi ga Iyalansa, sannan su duka zasu biya diyar Naseer da Alhaji Maiwada tare da tara mai yawa ga Malan Sani, domin sun zalunceshi.
Da wannan ne kotu ta kawo k'arshen wannan shari'a, kuma ta wanke Malan Sani daga zargin da ake masa, haka kuma tana buk'atar masu kula da hakkin d'an Adam da su tsaya wajen tabbatar da biyan duk wata tara da aka d'ora akan masu laifi, had'e da sauran jami'an tsaro, sannan za'a sake d'ora sabon Alkali zuwa wani lokaci. Kottt!!!.
Hayaniya ce ta kaure a kotun. 'Yan sanda ne sukayi kok'arin fitar dasu Alhaji Barau dan mutane sai jawosu sukeyi, da kyar aka fitar dasu. Malan Sani kuwa zubewa k'asa yayi yana sujada hawaye suna bin kuncinsa.
Alhaji Mansur ne yaje ya kamoshi, rungumeshi yayi yana kuka. Ra'eez ma sai da yayi sujadar godiya ga Allah, kuka kawai yakeyi domin yau itace ranar farin ciki agareshi domin ya cika burinsa. Rungumeshi Jabeer yayi suna murna, haka suka fito waje.
Suna fita suka tsaya suna kallon fad'a atsakanin su Alhaji Barau. Alhaji Marusa ne ya cakumo wuyan Alhaji Barau yana fad'in tsakani na daku Allah ya isa, shegu ashe dama kune kuka jefani cikin tashin hankali, duk amanar dana baku sai da kuka cuce ni.
Dokeshi Alhaji Barau yayi yana fad'in dalla can azzalumi kawai, waye ya cuce mu idan ba kai ba, mu dukan mu nan kaine silar shigarmu wannan halin ba dan kai ba babu abinda zaisa na aikata wannan abun kunyar, waye ya koya mana kisa.
Haka sukayi ta mayar da kalamai yayin da suka fara fad'a suna tona asirin juna, 'Yan sjarida kuwa sai d'aukarsu sukeyi. Da kyar 'yan sanda suka rabasu.
Takowa Ra'eez yayi har gaban Alhaji Barau yana murmushi. Ido kawai Alhaji barau ya tsura mashi yana sauke numfashi. Raheena da Momy suna gefe sai kuka sukeyi.
Kallonshi Ra'eez yayi yana fad'in ina taya ka murnar samun sabon waje na rayuwa, ina fatan yanzu ka gane komai akaina? Murmushi yayi yana fad'in yau kam zanyi bacci mai dad'i domin karatun da nayi yau ya k'are domin ya biya buk'ata, dama nayi shine saboda ku, tunda naga k'arshen azzalumai Alhamdulillah, Allah shine abun godiya.
Takawa yayi har gaban Raheena, ido kawai ya tsura mata yana kallon yanda take kuka ajikin Momy. Kauda kai yayi dan tausayinta ne ya kamashi. Matsowa su Jabeer dasu Nabeel sukayi wajen.
Momy ce cikin muryar kuka tace Ra'eez bani da bakin magana, ayanzu kam mun fahimci komai, sai dai laifin wani baya shafar wani, ina rokon ka da girman Allah ka yafe mana domin bamu da sa hannu a cikin mutuwar Mahaifinka.
Ra'eez yace bakuyi mani komai ba, dama kuma ban tab'a furta kalmar so ga Raheena ba, hannu yasa ya jawo Rumaisa yana fad'in wannan itace matar da zan aura d'iya ga Malan Sani wanda Mahaifin Raheena yayi sanadiyar zamanshi agidan Yari shekara goma sha biyu, ina fatan bazaku kullace ni ba.
Momy ta kalli Alhaji Barau cikin kuka take fad'in ka gani ko, tun kafin aje ko ina abinda bakin halin ka ya jawo mana, shikenan kaji dad'i zaka tafi ka barmu cikin tsangwama da tsana, domin babu wanda zaiso had'a zuri'a damu, ka cucemu, dan haka garin zamu bari ka bani takardar sakina domin kai yanzu gawa ne.
Hawayen bakin ciki ne suka zubo ma Alhaji Barau, sunkuyar da kai yayi yana jin tsananin nadama atare dashi, zeyi magana sukaga Nabeel yayi gefen su Momy da gudu, yana zuwa Raheena ta fad'a jikinsa a sume, dan tun zuwanshi wajen ya sauke ido akanta ya kasa d'aukewa, duk bidirin da akeyi besani ba dan hankalinsa yana kanta, hakan yasa da yaga alamun zata fad'i yayi wajenta.
Kanta sukayi gaba d'aya, cak Nabeel ya d'auketa Jabeer na gaba sukayi hanyar ofis d'insu da ita.
Ammi ce tasha gaban Alhaji M. Sanda idanuwanta jawur alamun taci kuka, hannu ta mik'a masa tana bashi mukullin gidanshi had'e da biro da takarda.
Kuka yasa yana girgiza mata kai. Daurewa tayi tana fad'in wallahi bazan tab'a yafe maka ba, ka rubuta mani saki na a hanya nake, Fawwaz kuwa ba laifinsa bane, naje wajensa tunda safe kuma naji dad'in yanda na ganshi, domin alamu sun nuna yayi watsi da shawararka, kai da kake kok'arin sama masa gata kaima zakaje ka iskeshi acan, kuma har na mutu zan cigaba dayi masa addu'a, dan haka ina jiran ka.
Zubewa k'asa yayi yana kuka ya riko hannunta yana fad'in kar kimun haka dan Allah, da wanne zanji, idan baki yafe mani ba zan shiga wani hali. Fizge hannunta tayi tana fad'in ina jiranka.
Kai ya jinjina yana fad'in bazan sake zaluntar ki ba, domin nasan yanzu banida amfani agareki, na datse igiyar auren mu, amma dan Allah... Wucewa tayi hakan yasa yayi shiru yana kuka.
Haka 'yan sanda suka tasa su sukayi gaba, jiyowa Alhaji Barau yayi yana fad'in Ra'eez kace ma Momyn Raheena na yanke igiyar auren mu nasan bazata sake zuwa waje na ba, ka dubi girman Allah ga Raheena nan aduba mani lafiyarta.
Kauda kai Ra'eez yayi yana sakin tsaki. Rafeek yace muje muga halin da Raheena take ciki Ra'eez. Goge hawayen idonshi yayi yabi bayan su Rafeek da Sameer hada Husnah da suka shiga wajen su Jabeer.
Mama ce ta rik'e Ummu suka nufi mota saboda yanda jikinta yake rawa, haka Alhaji Mansur yayi sallama dasu Alhaji Kamal akan zaije gidanshi anjima, saboda yanzu zai kai su Ummu gida, tare da Malan Sani suka nufi motar.
Da sauri wasu 'yan jarida suka sha gaban Malan Sani. 'Daya daga cikinsu yace Malan Sani wane irin farin ciki kake ciki akan wannan 'yanci daka samu yau?
Murmushi Malan Sani yayi yana fad'in yau kam bani da bakin magana sai hamdala awajen Allah, domin wannan nasara da muka samu Allah ne yasa muka sameta.
To me zakace akan wad'an nan azzalumai da suka jefaka cikin wanan tashin hankali? Babu abinda zance masu domin Allah ya fisu, kuma wannan zaman gidan Yari da nayi dama Allah ya rubutoshi acikin K'addarata, Alhamdulillahi nayi godiya ga Allah daya bani ikon cin wannan jarabawa, domin ba k'aramun alkhairi bane Allah ya jarabceka sannan ya baka ikon cin jarabawar, su kuma sai dai nace Allah shine zeyi maganin su.
Zasu sake tambayarsa Alhaji Mansur ya janyeshi yana fad'in sai mu kwana anan. Murmushi yayi ya shiga mota sukayi gida.
Sun dad'e suna zubama Raheena ruwa amma ko motsi batayi ba, cike da tashin Hankali Momy tasa kuka tana fad'in ku taimaka mani kada na rasata dan Allah, jikin Ra'eez ne yayi sanyi ganin halin da Raheena take ciki, da sauri Nabeel da Jabeer suka kai hannu domin d'aukarta, tuni Nabeel ya sureta suka nufo waje domin su kaita asibiti.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:41 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
5️⃣0⃣
*Last page*
Kusan mintuna ashirin suna tsaye babu labarin Raheena, Nabeel da Jabeer sun kasa zaune kowa ya tsaya bakin kofar d'akin kamar zai shiga. Ra'eez da yake gefe guda a zaune sai kallonsu yake, duk da shima yana cikin damuwar halin da take ciki amma k'asan ranshi dariyarsu yakeyi dan tuni ya gama harbo jirginsu.
Zama Rafeek yayi kusa dashi yana fad'in wad'an can Romeo's d'in fa? Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in Yaya kaima ka ganosu kenan? Rafeek yace dama can ai Jabeer yana son Raheena, shi kuwa Nabeel shigar sauri Sonta yayi masa.
Ra'eez yace ga Husnah kuma a gefe. Murmushi Rafeek yayi yana fad'in abun ai yazo da sauki sai wani yayi hakuri.
Wai Husnah lafiyarki kuwa naga duk baki cikin natsuwarki. Ajiyar zuciya ta sauke tare da d'auke idonta daga kan Jabeer, kallon Sameer tayi tana fad'in Yaya. Sai kuma tayi shiru.
Murmushi yayi yace Jabeer ko? Hannu tasa ta rufe fuskarta. Girgiza kai yayi yana fad'in ai na fahimceki tun jiya, kada ki damu matuk'ar kina sonshi zanyima Ra'eez magana, ke kuma sai kiyi amfani da dabarun ku na mata ki janyoshi. Murmushi tayi tana fad'in nagode Yayana.
Fitowar likita yasa gaba d'aya sukayo kanshi. Ofis ya nufa hakan yasa suka bishi banda Nabeel da yayi saurin shiga wajen Raheena.
Ku kwantar da hankalin ku kawai tashiga cikin damuwa ne shiyasa tayi doguwar suma, amma yanzu komai yayi dai-dai munyi mata allurar bacci saboda zuciyarta ta samu natsuwa.
Ajiyar zuciya Momy ta sauke tana fad'in mungode likita, idan ta farka zata warke ko? Kai ya d'aga yana murmushi, kallon su yayi yana fad'in sai dai tana buk'atar arik'a kwantar mata da hankali idan ba haka ba zata iya had'uwa da hawan jini saboda akwai damuwa a zuciyarta.
Rafeek yace insha Allahu za'a kula likita, yanzu me ake da buk'ata? Takarda ya mik'a masa yana fad'in abiya wad'an nan kud'in zasu bada magungunanta. Amsa yayi suka fita suna masa godiya.
A gefenta suka iske Nabeel ya zuba mata ido, komawa da baya Jabeer yayi ganin abinda yake faruwa. Ra'eez yace Momy zamu wuce sai zuwa anjima idan ta farka zamu dawo kila ma asallameta zuwa anjima.
Momy tace nagode sosai Ra'eez Allah ya baku abinda kuke nema. Gaba d'aya suka amsa da amin. Rafeek yace Alhaji Nabeel muje ko. Kai ya sosa yana fad'in kuje Yaya anjima zan tafi. Murmushi sukayi Sameer yace ai gara ka tsaya kayi jinya. Sallama sukayi masu suka fita.
Suna fitowa suka iske Jabeer saman mota yana latsa waya. Ra'eez ne ya matsa yana fad'in Jabeer ya naga ka fito kuma? Jabeer yace jiran ku nake mu wuce. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in Jabeer kada ka kwari kan ka fa.
Kallonshi yayi yana fad'in wai Raheena kake nufi? Kai ya d'aga masa. Saukowa yayi yana fad'in fatana ta samu wanda zai kula da ita idan ta rasaka, kuma Alhamdulillahi ta samu, sai fatan ta amince dashi, kuma nayi murna daya kasance shine.
Hannunsa Ra'eez ya kamo yana fad'in kaine ka santa kuma kaine ya kamata ka kasance da ita, ina maka sha'awar samunta domin nasan wacece Raheena.
Murmushi Jabeer yayi yana fad'in wallahi ko son da nake mata zai iya cutar dani gara ya cutar dani da dai na aureta, bare kuma ni tausayinta yafi yawa a zuciyata, koda ina sonta to kad'an ne, kuma ni bazan iya aurenta ba.
Ra'eez yace dalili? Ajiyar zuciya ya sauke yana fad'in kaine dalilin, da ace wani ne daban da ban sani ba Raheena take ma irin wannan son to zan iya aurenta kuma na mantar da ita komai na koya mata sona, amma bazan iya aurenta ba bayan tana maka irin wannan son, har bada zuciyata bazata tab'a natsuwa ba, domin koda yaushe muna tare da kai, zaka zo gidana itama zata je gidanka, koda ta mance da kai zuciyata zata cigaba da raya mani tana sonka, kaga kuma shed'an beda gwani zai iya d'arsa wani abu a zuciyata shiyasa kaji nace maka bazan iya aurenta ba, ganin yanda Nabeel ya rikice daya ganta nasan cewar Allah ya kawo mata sauyi, dan haka ina so ka bar wannan maganar anan bana so Nabeel yaji kada wani abu ya tsarga zuciyarsa.
Rungumeshi Ra'eez yayi yana fad'in na fahimceka sosai abokina, kuma ko nine haka zanyi, idan ka amince dani zan iya baka mata? Saurin kallonshi Jabeer yayi. Jinjina masa kai Ra'eez yayi.
Murmushi Jabeer yayi yana fad'in na amince. Sakinsa Ra'eez yayi yasa hannu ya juya fuskarshi zuwa wajen dasu Sameer suke tsaye shida Rafeek, saitin da Husnah take ta zuba mashi ido ya aje fuskarshi.
Murmushi Jabeer ya saki har hak'oransa suka fito, shiru yayi suna kallon juna shida Husnah. Hannu Ra'eez yasa ya kamo hannun Jabeer yana fad'in na baka ita amatsayina na Yayanta.
Dariya Jabeer yasa ya tureshi. Wucewa Ra'eez yayi yana fad'in Yaya muje. K'arasowa sukayi Rafeek yace an gama Maths d'in ko? Kai Ra'eez ya d'aga yana fad'in sauran English. Dariya sukasa gaba d'aya.
*** ***
Lokacin da aka shigar dasu Alhaji Barau wajen da sauran fursunonin suke bayan an basu kayan gidan yari sun saka gaba d'aya mutanan wajen sukayo kansu suka sasu tsakiya.
Yanda kasan zasu rufesu da duka haka suka matse su kowa da abinda yake fad'i yayin da wasu suke masu dariya suna nuna su. Kunya da tsoro ne ya kamasu Alhaji Barau sai b'oye fuskarsu sukeyi.
Wani daga cikin mutanan wanda da ka ganshi kaga rik'ekken marar ji, shine ya matso tsakiya yana fad'in ansutu jama'a. Kowa yayi shiru suna kallonshi.
Takowa yayi kusa dasu Alhaji Barau yana tafa hannu, kallonsu yayi yana fad'in *da d'ina da gobe?*.. Mutane suka amsa gaba d'ayansu da *saurin zuwa.* Murmushi yayi yace *Alhaki?* suka amsa da *Kuikuiyo.*.... *Komin nisan jifa?*... *K'asa zata dawo*... *Idan zaka gina ramin mugunta*?... *Ginashi dai-dai tsawonka*... *NASHIGA BAN 'DAUKA BA?*... *BATA FIDDA 'BARAWO.*
Gaba d'ayansu suka d'auki ihu suna dariya. Hannu ya d'aga hakan yasa akayi shiru. Kallonsu yayi yana fad'in barkan ku da shigowa duniyar mu, gashi dai kun turo mu cikinta ashe dama zaku zo ku iske mu, dan haka ku sani kunzo wajen da za'a mulke ku, domin wannan gida Masarauta ta ce, Mazaje kuna ji? Gaba d'aya suka amsa da E muna ji.
Kallonsu ya sakeyi yana fad'in yau dai Allah ya fidda Baba Sani daga gidan nan yayin da ya maido azzalumai a cikin gidan, saboda haka bana so kowa ya d'aga masu k'afa domin da yawa wannan tsohon macucin Alkalin shine ya kawo mu nan, sai wannan guntun Lauyan wato Barau shine yayi silar aka yanke mana hukunci, daga yau babu sani babu sabo tsakanin mu dasu, dole cikin kwana biyu su gane shayi ruwa ne, domin hukuncinsu horo ne mai tsanani.
Dariya sukasa gaba d'aya yayin da suka sungumesu sama sukayi cikin gidan dasu sai ihu sukeyi. Masu gadi kuwa gefe suka koma suna shan dariya dan sun san basuda yanda zasuyi da su domin Allah ne ya kawo masu azzalumai har gida, hakan yasa kowa ya nufi wajen aikinsa.
Fawwaz da yake gefe guda yana kallon abinda yake faruwa hawaye ne kawai suke zubo masa na takaici, tunda Amminsa tazo masa da labarin d'azu da safe yake cikin damuwa, da kunya ace shida mahaifinsa suna zaune waje guda, dole ma ya rik'a nisantarsa dan ba zai iya zama kusa dashi ba, gara kowa yayi hanyarsa danshi ayanzu ilimin addini yasa agaba domin nasihar Amminsa ta shigeshi.
Ajiyar zuciya ya sauke lokacin da yaji an dafashi. Juyowa yayi sai yaga abokinsa ne wanda yake d'aukar karatu a wajensa. Zama yayi yana fad'in Fawwaz na fad'a maka sai kasa jarumta aranka idan ba haka ba ciwon zuciya zai iya kama ka, nasan da ciwo amma haka Allah ya k'addaro maka kayi hakuri kawai. Jinjina kai Fawwaz yayi yana fad'in nagode.
**** ****
Zaune suke afalo bayan da Malan Sani yayi wanka dama yayo aski, kaya sababbi Alhaji Mansur ya bashi ya saka, sosai ya fito yayi kyau duk da alamun tsufa da wahala sun fito masa amma ya canza.
Abdallah yana zaune saman cinyarsa sai shafa kanshi yake yana murmushi, abinci Mama ta zuba masu sai murmushi take kamar amarya.
Gyaran murya Alhaji Mansur yayi yana fad'in muna k'ara mik'a godiya ga Allah daya nuna mana wannan rana, hakika Allah shine mai iko mai juya al'amura yanda yaso.
Kallon Ra'eez yayi yana fad'in sannu da kok'ari Ra'eez, hakika kayi kok'ari kuma ka bada gudummuwa sosai, duk da ka fad'a mani duk ranar daka sauke wannan nauyi zaka aje aikin ka amma ban sani ba ko kana da sha'awar cigaba da aikin.
Saurin girgiza kai Ra'eez yayi yana fad'in wallahi Abbah aikin shari'a ya fitar mun rai, nikam daga yau nagama tsayuwa domin na kare wani, dama saboda haka nayi karatun kuma Alhamdulillahi