Advertisements
Chapter 23 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   23 / 54

66K to 69K   out of 160.3K words

sai da yayi ta maza ya rik'eta da k'arfi akayi mata allura kafin tayi shiru, har bacci ya d'auketa hannunta yana rik'e dana Ra'eez, a hankali aka cireshi daga jikinta. Ra'eez yana waigenta har suka fita daga d'akin suka wuce gida sai kuka yakeyi.



A ranar haka ya wuni da kyar Rumaisa tasa yaci abinci. Bayan kwana biyu aka gama mashi komai na tafiya Madu ya d'aukeshi domin ya kaishi inda zai hau jirgi. Daga Rumaisa har Halima sai da sukayi kuka da zai tafi, shima kukan yakeyi da kyar suka rabu.


*** ***

Lokacin daya sauka Alhaji Mansur hada Labiba sukaje d'aukoshi, Labiba sai murna takeyi abokin firarta ya dawo. Haka suka nufi gida.


***

Lokacin da hutunsu ya k'are haka Alhaji Mansur ya had'a masu komai, d'aki yaja Ra'eez ya fad'a masa kud'in mahaifinsa sun fito, kuma ya saka masa abankin da Alhaji Maiwada ya bud'e masa ya saya masa hannun jari domin arik'a juya kud'in. Ra'eez yace Abbah bana so kace bazaka tab'a kud'ina ba, kaga a waje zanyi karatu ina so nayi karatu da kud'in Abbu domin ina so nayi amfani da guminsa nayi karatun da zan kwato masa hakkinsa.


Murmushi Alhaji Mansur yayi yace Ra'eez kenan, ko sisi baza'a tab'a maka ba, nine nayi niyar sai kayi karatu a waje kuma zakayi shi komin tsadarsa. Ra'eez yace dan Allah Abbah. Alhaji Mansur yace naji yanzu dai muje kada muyi dare, kuma bana so kasa damuwa aranka idan ba haka ba baza kaje karatun aikin lauya ba kaji. Ra'eez yace zan dage.


Haka suka fito suka yima Maman su sallama suka tafi cike da kewar gida, Labiba sai haushi takeji an canza ma Ra'eez aji yanzu saiya rigata gamawa, itama taso amayar da ita ajinsu amma Alhaji Mansur yace bazai maida ta ba dole ta hak'ura.


***

Haka rayuwa tacigaba da tafiya, wasu suna jin dad'i wasu suna cikin wahala, tuni Halima ta fawwalama Allah al'amuranta, ta rungumi k'addararta da hannu biyu, cikin ikon Allah take tafiyar da rayuwarta babu abinda ta nema ta rasa, Madu yana kokari akansu sosai, ga Sister Hassana da mijinta.


Cikinta sai girma yakeyi tana zuwa awo ba tare da wata matsala ba, damuwarta d'aya idan taje ganin Malan Sani, ganin yanda take damuwa yasa Malan Sani yace ta dena zuwa kawai tacigaba da kulawa da kanta.


Su Brr. Barau kuwa rayuwa tayi masu dad'i, domin arzik'in yanzu ya wuce na baya, sun had'a hannu da Alhaji Marusa suna shigo da kaya wad'an da suke so, domin Adebayo shine aka ba kujerar Alhaji Maiwada dama kuma alk'awari aka masa matuk'ar komai yayi dai-dai shi za'a ba yayin da aka bama Umar matsayinsa. Wannan dalilin ne yasa suke cin karen su babu babbaka dan yanzu mutane suna kuka da yanda ake amsar masu kudi.


****

Lokacin da cikin Halima ya isa haihuwa safiyar juma'a ta tashi da nakuda, alokacin Rumaisa tayi shirin zuwa makaranta sai fasawa tayi, da gudu taje ta kira Sister Hassana, haka suka d'auketa suka nufi asibiti.


Cikin ikon Allah ta haifi d'anta namiji. Bayan an gama komai suka koma gida. Bayan da ta gama gyara jikinta Ladi tayima yaro wanka, kunu ta kawo mata da d'umamen tuwo, kasa ci tayi sai kuka takeyi.


Zama Ladi tayi tana fad'in haba Halima, godiya ya kamata kiyima Allah daya sauke ki lafiya, nasan kina tunanin rashin Malan Sani, ki sani bazaiji dad'i ba idan yaji kina cikin damuwa, kinsan yanzu ba'a son kina saka damuwa aranki, ki daure kici abinci dan Allah.


Hannu tasa ta goge idonta tana fad'in shikenan Ladi nagode. Amsar kunun tayi ta fara sha tana kwalla.


Da wayar shugaban ma'aikatan gidan yari tayi magana da Malan Sani, sosai yaji dad'i haka yayi ta lallashinta kuma yace mata zai zo insha Allahu. Bayan sun gama waya shugaban ma'aikatan yace masa zai kaishi yaje yayi ma yaron hud'u ba. Sosai Malan Sani yaji dad'i yayi ta masa godiya.


Sai da dare suka je, alokacin Rumaisa ma tayi bacci. Haka yayi ma yaron hud'uba da *Abdallah*, yaso yasa sunan Alhaji Hamza amma sai ya tuna da maganar Alhaji Hamza da yake fad'a masa.. *idan Ummun Ra'eez ta haihu idan mace ce zai saka sunan mahaifiyarsa, idan kuma namiji ne zaisa sunan mahaifinsa Abdallah, saboda beyi amfani da sunansa a jikin takardunsa ba, sai yayi amfani da sunan da ake kiransa dashi a cikin 'yan uwa wato MAIWADA, hakan yasa yake son yasa sunanshi na gaskiya*. Wannan dalilin ne yasa Malan Sani ya cika ma Alhaji Maiwada burinsa. Ya dad'e yana kallonshi, wajen Rumaisa yaje yayi mata addu'a, sai da yaci abinci shida shugaban sannan suka tafi yana ta yima Madu godiya.


***

Dubu hamsin Alhaji Mansur ya aiko mata asayi rago ayi siyayyar kayan yaro. Godiya tayi masa. Haka akayi hidimar suna cike da rufin asiri tamkar Malan Sani yana nan.


****

Bayan da Ra'eez ya zana jarabawarsa suka baro su Labiba amakaranta, satinsa biyu a Kano ya taho Lagos yayi hutu kafin jarabawarsu ta fito. Sosai Rumaisa da Halima sukaji dad'in zuwanshi.


**** ****


Bayan da jarabawarsu ta fito haka aka kammala masa komai, cikin sa'a ya samu gurbin shiga makarantar koyon aikin lauya da take Landon, cike da farin ciki yaje yayi ma Ummunsa sallama, sai dariya takeyi kamar tasan abinda yake fad'a. Haka yayi ma kowa sallama ya tafi cike da fatan nasara.


*** ***

*Bayan shekaru da dama*,


Abubuwa da yawa sun faru, aciki hada kaddamar da Brr. Barau a matsayin sabon Alkali na babbar kotu bayan da tsohon Alkali ya aje aiki, sosai yayi farin ciki da wannan al'amari dan ya dad'e yana jiran wannan rana.


Mr. Kallah ma ya dawo Lagos da zama saboda ya aje aiki, gaba d'ayansu girma ya kama su, sai dai naira ta hana aga tsufansu, har zuwa wannan lokaci Alhaji Marusa yana shigo da haramtattun kaya, sai dai yanzu abun nashi na zamani yakeyi dan an samu cigaba.


Ummun Ra'eez tana kan amsar magani, zuwa yanzu jikinta da sauki sosai, sai dai bata da yawan magana, idan ka ganta tamkar mai hankali amma bata magana, a koda yaushe maganarta d'aya Abbun Ra'eez sai kuma d'anta.


Su Alhaji Mansur suna yawan kawo masu ziyara, haka wajen Malan Sani suna zuwa wajensa. Komai yana tafiya yanda ya kamata.


A yanzu haka Rumaisa an girma tana aji ukku a babbar makaranta. Sosai kyanta ya k'ara fitowa, ga natsuwa ga kok'ari, sosai take maida hankali a karatun ta. Abdallah ma yashiga fimare, sosai suke waya da Ra'eez.


Labiba kuwa tuni ta kammala makarantar ta, inda tayi karatu a FCE kano har ta kammala dan shekara ukku ne, yanzu haka ana shirin bikinta.


****

Bayan da Ra'eez ya kammala karatunsa haka ya dawo gida cike da nasara dan ya fita da first class, sosai Alhaji Mansur yaji dad'in haka.


Bayan dawowarsa yaje yaga Ummunsa kafin ya dawo kano, haka Alhaji Mansur ya nema masa (Bar school) da take abuja. Sai da akayi bikin Labiba kafin ya tafi.


Shekara d'aya yayi kafin ya kammala, bayan ya dawo yayi service shekara d'aya, alokacin Rumaisa zata jana jarabawar fita daga makaranta.


Yana kammala service d'insa ya samu aiki a babbar kotu da take kano. Kasancewar Ra'eez mai natsuwa da hazaka, cikin lokaci kad'an ya saye zuciyar mutane, dan duk abinda yasa agaba sai yaga bayansa, haka duk shari'ar da zaiyi sai yayi nasara, danshi baya amsar shari'ar da yasan babu gaskiya a cikinta, shiyasa mutane suke masa lak'abi da Mai gaskiya.


Sai da yayi shekara d'aya a kano kafin Alhaji Mansur yayi nasara aka canza ma Ra'eez wajen aiki zuwa babbar kotu da take lagos. Ranar da takardarsa ta fito sosai sukaji dad'i, haka Alhaji Mansur yayi ta masa nasiha yana bashi shawarar yanda zai tafiyar da komai musamman da yasan cewar Brr. Barau shine Alkali a kotun da Ra'eez zaiyi aiki, kuma yaja kunnansa akan ya b'oye komai nashi, dan baya so kowa yasan yana da alak'a da Alhaji Maiwada har sai komai ya kammala.




Cike da d'oki ya shirya ya tafi Lagos yana mai farin cikin zai koma kusa da abun sonshi Rumaisa, dan ya girma ne da soyayyarta, sannan zai koma kusa da Mahaifiyarsa.


Sai da sukayi kwana ukku suna gyaren tsohon gidansu dan Alhaji Mansur yace ya zauna acan, alokacin tuni an sake maigadi kusan ukku bayan wancan, haka aka gyara komai kamar alokacin aka zuba su.


A d'akin Abbunsa yace zai zauna. Haka ya shirya komai nashi. Yaso Maman Rumaisa su dawo gidan amma tace yayi zamansa tafi son ta zauna acan, duk yanda yayi haka ya hak'ura dan sai da Alhaji Mansur ya shiga maganar sannan.



*Wannan shine asalin labarin Alhaji Hamza Maiwada*


Ajiyar zuciya Kawu yayi yana goge hawayen da suka zubo masa. Ra'eez kuwa kuka yake sosai kamar k'aramin yaro. Hannunsa Kawu ya kamo yana fad'in kada ka barsu Ra'eez, sun cutar dani sama da shekaru da dama, nayi kuka har na gaji, nayi dauriya har sai da hak'urina ya kusa k'arewa, sun lalata mani rayuwa, sun b'ata mani suna, sunci mutuncin Mahaifiyarka, ta kwashe shekaru tana cikin hali na rashin lafiya.


Girgiza kai Ra'eez yayi yana fad'in kada ka damu Kawu, na girma da shirin d'aukar fansa, zan b'ullo masu ata yanda basuyi zato ba, insha Allahu sai asirin su ya tonu, sai Allah ya kawo mani hujja gamshashshiya, kamar yanda sukayi amfani da kwakkwarar hujja suka kada ka nima sai Allah ya bani wannan damar, kacigaba da tayani addu'a Kawu.


Murmushi Malan Sani yayi yana fad'in ina kan yi Ra'eez, kaine keda nasara a wannan karon, sai sunyi nadamar abinda suka aikata. Allah yayi maka albarka.


Ra'eez yace amin Kawu, zan zo na koma ka k'ara hak'uri Kawu. Malan Sani yace yanzu kam acikin farin ciki nake, fatana Allah ya barni da raina domin nasha kallo. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in amin. Sallama yayi masa ya tafi cike da damuwa aransa.


Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:39 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*



2⃣2⃣


Yana kan hanyarsa ta komawa wajen aiki wayarsa tayi k'ara, yana dubawa yaga *Alkali ne*, saurin d'auka yayi, yana d'agawa ya fara tambayarsa ina yaje? Ra'eez yace na d'an fita na siyo magani ne ganinan dawowa. Kashe wayar akayi.


Tsaki Ra'eez yayi yana jin wani b'acin rai, sosai yake jin hushin Alkali Barau, tunda yasan irin muguntar da sukayi ma Abbunsa da Ummunsa ya k'ara tsanarsa. Gudun motar ya k'ara dan yayi sauri ya isa.



Inda ake aje motoci ya aje kafin ya fito, kai tsaye ofis d'in Alkali Barau yawuce, sai da ya fara kwankwasawa aka bashi zini kafin yashiga da sallama.


Kallonshi Alkali yayi yana fad'in baka jin dad'i ne? Kai Ra'eez ya d'aga yana fad'in kaina ne yake ciwo amma nasha magani yayi sauki.


Alkali yace ko dai ka tafi gida kila bacci ne. Ra'eez yace da sauki zan iya zama. Murmushi Alkali yayi yana fad'in shikenan, dama nace idan an tashi ko zaka bini gidana nasa ayi abinci da kai amatsayin ka na sabon ma'aikacina mai kwazo, ina so na gabatar da kai a wajen Iyalina.



Kau da kai Ra'eez yayi yana fad'in badamuwa nagode Allah ya kaimu atashi. Alkali yace amin, kuma naji dad'i, dan haka idan an tashi zan maka magana sai mutafi. Ra'eez yace to. Juyawa yayi ya fita.


Zaune yake a ofis suna fira shida Brr. Jabeer, sauran ma'aikatan ne suka iso suna ma Ra'eez sannu da zuwa. Da murmushi ya amsa yana basu hannu suna gaisawa.


Bayan sun gama Ra'eez ya kalli Jabeer yana fad'in gaskiya naji dad'in zuwa wannan kotun, domin mutanan cikinta suna da kirki musamman 'Yallab'ai.


Murmushi Jabeer yayi yana fad'in wai Alhaji Barau kake nufi? Ra'eez yace shi nake nufi. Murmushi Jabeer yayi yana fad'in kayi a hankali dai, domin kura ce rufe da fatar akuya.


Ra'eez yace bangane ba? Jabeer yace bakomai manta kawai. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in tunda nazo muka gaisa da kai sai nake jin kamar kaine kafi cancan ta nayi abota dashi a wajen nan duba da yanayin ka, sai gashi nazo kai kuma kana so ka b'oye mani wani abu, kyakkyawar alak'a ana kullata ne da kyakkyawar zuciya, amma kila ni d'in ne banyi maka da zama aboki ba.


Hannunsa Jabeer ya kamo yana fad'in wallahi ba haka bane, kasan ba'a son mutum yarik'a saurin fad'ar mugun abu ga wanda yazo waje amatsayinsa na sabon zuwa, ban sani ba kilama 'yallab'ai d'an uwanka ne haka kawai nayi sara akan gab'a.


Ra'eez yace amma na fad'a maka ba'anan nake ba, bani da kowa nan aiki ne ya kawo ni. Jinjina kai Jabeer yayi yana fad'in nima ai ban dad'e anan ba, kawai nasan labarinsa ne a wajen Kawuna, domin sunyi aiki tare dashi alokacin yana lauya, yanzu haka Kawuna yana Babbar Kotu da take garin Abuja, da tare suke anan, sai Kawu na yaje ya k'aro karatu, sukayi wani taro na k'asa da k'asa akan yanda za'a kawo cigaba akan shari'ar k'asarnan, Kawuna ya bada gudummuwa sosai, hakan yasa aka maidashi babbar camber da take abuja, kaji dalilin da yasa yabar wannan kotun domin yanzu yana saman Alhaji Barau.



Ra'eez yace lallai ashe dai gadon aikin shari'a kayi. Jabeer yace wallahi kuwa, domin acikin 'ya'yansa ma akwai lauya amma shi yana Jos acan yake aiki, a cikin dangin mu kusan mu biyar ne muke aiki a wannan fannin, da anan garin kake kila da ka san Kawuna, sunansa *Kamal S. Buzu*, alokacin da yake aiki tare da Alhaji Barau yasha wahala, domin bakinsu d'aya da manyan masu kud'i, gashi ya iya tsara magana, shiyasa duk yawancin shari'a shine yake nasara musamman ta masu kud'i, yasan yanda zai maida gaskiya ta koma k'arya, ta yanda babu wanda zai iya ganowa.


Ra'eez yace lallai kace yanzu sai ya raina kanshi tunda Kawun ka ne samansa. Jabeer yace ai yanzu yayi sauki sosai, kasan dama idan kaga mutum yana yanda yaso ba'a bashi shugabanci bane, ai tamkar ka d'auki ajiya ne ka bama b'arawo, kaga dole idan kazo amsa ya baka, shiyasa wasu suke ganin da zama da munafuki gara zama da b'arawo.



Dariya Ra'eez yayi yana fad'in wallahi Jabeer kana da abun dariya, gashi ka iya karin magana kamar wanda tsofaffi suka yaye, to ni dai ban fahimci abinda kake nufi ba.


Murmushi Jabeer yayi yana fad'in ina nufin yanzu shine shugaba, dole abinda lauyoyi suka fad'a shi zaibi, domin yanzu kotu ce take tafiyar dashi ba shine yake tafiyar da kotu ba, kasan duk abinda lauya ya fad'a dashi kotu take zama ta duba kafin ta yanke hukunci, shiyasa nace maka yanzu yayi sauki, dole yake yanke hukuncin gaskiya, shiyasa yanzu mutane suke sara masa, gani suke shid'in mai gaskiya ne, musamman koda yana lauya ba'a tab'a kamashi da laifin cin amanar aikinsa ba, shiyasa yanzu duk inda kaje zakaji ana fad'in Alkalin babbar kotu yafi kowa iya aiki, dan haka mutane suke son kawo k'ara a wannan kotu, damma ana soke wasu amaida su k'ananan kotu.



Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in lallai irin wad'an nan mutanan wahalar sha'ani garesu, domin sun riga sun gama saye zuk'atan mutane, duk yanda wani yaso ya fad'i wani aibunsu mutane bazasu yarda ba har sai an gabatar masu da babbar hujja akansu.



Jabeer yace shiyasa ka zuba masu ido yafi, domin fad'a da aljani ba kyau, ko kace zakayi ma kaine a k'asa, domin zaka sa mutane su tsaneka ne kawai, shiyasa duk da nasan shid'in ba mai gaskiya bane dole na had'iye abuna nake binsa a yanda kowa yake kallonsa kafin ranar da Allah zai kamashi, wata kila a duniya wata kila kuma sai anje can.


Ra'eez yace irin wad'an nan mutanan asirinsu ya tonu aduniya yafi dad'i, domin mutanan da suka basu gaskiya zasu ga komai da idanuwansu, sannan masu aikata makamancin laifinsu zasu hankalta, idan suna da rabon shiriya sai kaga sun shiryu, amma abarsu sai anje lahira ai sun bar baya da k'ura.



Jabeer yace kai da kasan haka kenan, addu'ata d'aya Allah ya bayyana gaskiya, domin Kawuna yasha fad'a mani wata shari'a da sukayi wacce har yanzu bata wuce a zuciyar Kawu ba, saboda tare sukayi ta kuma shine yayi nasara, saboda irin hujjar daya gabatar ma kotu dole ne ta yanke hukunci, kuma Kawu yace ba hujjar gaskiya bace, sai dai shima bai da ikon k'aryatawa, domin an gabatar da ita ne amatsayin ta gaskiya, sune kad'ai suka san cewar ba ta gaskiya bace.


Ra'eez yace shari'ar waye haka? Jabeer yace an dad'e fa, shari'ar wani marigayi daya rik'e shugaban Kwastam a garin nan, kaga na manta sunansa wallahi, amma dai naji Kawu na yana fad'in har yanzu direbansa da aka k'ullama sharrin yana nan a gidan yari, kai wallahi wata shari'ar sai alahira kaji, amma mutanan da suke zaune agidan yari masu gaskiya suna da yawa.


Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in Allah ya kyauta, mu kuma

23 / 54