Author : Marubuciyar Zamani Category : Complete Novels
DPO da yaranshi sun iso. Haka suka fara nasu binciken cikin kwanciyar hankali. Duk ma'aikatan da sukayi aiki aranar sai da aka d'auki komai nasu tun daga kwatancen gidansu da bayanin bankinsu. Bayan da suka gama sukayi sallama da Alhaji sukace akowane lokaci za'a iya ganinsu a gidan mutum. Godiya Alhaji yayi masu suka tafi.
Sunayin la'asar ya tafi gida domin baya jin dad'in jikinsa. Malan Sani bayan ya ajeshi yace zaisa Malamin unguwarsu ayi addu'a. Alhaji yace nagode sosai Malan Sani, bara na baka kudin da za'a basu sadaka. Malan Sani yace wallahi bazan amshi ko sisi ba, nine nayi niya dan haka ka barni kawai. Murmushi Alhaji yayi yace nagode agaishe da Rumaisa.
****
Ana gobe za'a koma kotu da misalin k'arfe bakwai bayan anyi sallar magriba Alhaji yana zaune a tsakar gida shida Malan Sani da Madu suna fira kawai sukaji k'ararrawa. Da sauri Madu ya tashi ya nufi k'ofa, sai da ya lek'a kafin yayi saurin bud'ewa.
Tashi Alhaji yayi tsaye ganin 'yan sanda, lokaci guda yaji gabanshi ya faad'i, duk da yasan suna zuwa gidaje suna bincike amma haka kawai yaji gabansa ya faad'i.
Bayan sun gama gaisawa DPO yace Alhaji sai dai kayi hak'uri yau gamu munzo bincike yazo kan ka. Murmushi Alhaji yayi yana fad'in haba ai bakomai, ai haka mukeso domin ta haka ne za'a gano gaskiya. Bismilla ku shigo, bara nayima Iyalina magana. DPO yace bakomai kayi masu magana.
Suna tsaye suna k'arema gidan Alhaji kallo ya fito yana fad'a masu su shigo. Suna shiga suka iske Ummu da Ladi a falo sanye da hijabi suna zaune. Gaishe dasu sukayi Alhaji ya samu waje ya zauna yana fad'in DPO kushiga ko ina abud'e yake. Jinjina kai yayi kafin yasa yaranshi suka fara bincike.
Tunda suka haura sama Ummu tasa kuka, rungumeta Alhaji yayi yana fad'in kidena kuka, ina da gaskiya ta dan haka su shiga duk inda suke so. Ummu tace yanzu har d'akin kwanan mu sai sun bincika mana? Alhaji yace daga binciken fa shikenan, bana so kisa damuwa aranki.
Suna nan zaune kusan mintuna goma sai gasu sun sauko, DPO yace zamu shiga kicin Alhaji. Jinjina kai yayi ya nuna masu hanyar kicin d'in. Bayan sun gama duba komai suka fito. DPO yace Alhaji babu abinda muka samu acikin gidan ka, sai dai zamu duba can waje zuwa bayan gidan ka dan kamar naga akwai ginin da kakeyi acan baya wanda ba'a kammala ba.
Alhaji yace akwaishi muje ku duba. Cire Ummu yayi ajikinshi yabi bayansu. Suna fita Malan Sani yace Alhaji mujirasu anan kada suga kamar muna binsu. Kai Alhaji ya jinjina ya samu waje ya zauna.
Kusan mintuna ashirin sai ga wani d'an sanda ya fito da gudu, Alhaji yana ganinshi yayi saurin tashi tsaye. Yana zuwa yace Alhaji Oga yana son ganinka. Jiki a sanyaye Alhaji da Malan Sani hada Madu suka bi bayan shi.
Tun kafin su k'arasa suke hango kaya daga cikin wani d'aki da aka bud'e. Da sassarfa Alhaji ya k'arasa wajen. Turus ya tsaya yana kallon DPO. Girgiza kai DPO yayi yana fad'in meyasa haka Alhaji? Meyasa ka zab'i ka bamu wahala bayan kasan komai? Salati kawai Alhaji yakeyi jikinsa yana rawa, idan ba gizo idanuwansa suke masa ba kaya yake gani a cikin d'akin da yake gabanshi kuma kayan da ake tuhumarsu akansu, sai dai kayan da suke wajen basu kai rabin wanda akace sun b'ace ba, da alamu ba duka bane a d'akin.
Da sauri Malan Sani ya rik'e Alhaji yana fad'in wallahi Yallab'ai bamu da masaniya akan wannan kayan, sai dai idan wani ne ya shigo dasu.
Murmushi DPO yayi yana fad'in meye matsayinka awajen Alhaji? Malan Sani yace direbansa ne. Dafashi DPO yayi yana fad'in Malan Direba ka tsaya amatsayinka, wannan mune muke da ikon yin bincike, dan haka kaja bakinka kayi shiru domin duk abinda zaka fad'a zai iya zama hujja akan ka.
Kallon Alhaji yayi yana fad'in bincike ya k'are Alhaji, dan haka zamu tafi da kai kafin gobe akoma kotu, sai dai na lura kamar kayi amfani da wasu kayan saboda yanda na samu labari kayan sunfi haka yawa, amma dai koma meye zamuji daga bakin ka gobe. Shiru Alhaji yayi ya kasa magana. DPO yasa mai d'aukar hoto ya d'auki komai kafin su tafi.
Kallon yaransa yayi yana fad'in ku taho dashi. Alhaji yace zan iya sallama da Iyali na? Wani d'an sanda yace babu inda zakaje. DPO yace barshi ka rakashi yaje yayi magana dasu. Bayansa Malan Sani yabi suka wuce jiki a sanyaye.
Tunda Ummun Ra'eez taga Alhaji taji gabanta ya faad'i, saurin k'arasowa tayi tana kuka. Rungumeta Alhaji yayi shima ya saki kuka. Sun dad'e ahaka kafin ya goge idonshi yana fad'in kiyi mani addu'a Ummun Ra'eez, abinda nake tsoro ya tabbata, Allah ne kad'ai zai fitar dani, sun samu kayan a ginin Ra'eez wanda bansan da suba.
Hannu tasa ta goge masa fuskarsa tana fad'in wallahi nasan k'arya ne, nafi kowa saninka, baka tab'a ciyar damu da haram ba, kuma Allah zai fitar da kai. Gyaran murya d'an sandan yayi yana fad'in Alhaji kana b'ata mana lokaci.
Cireta yayi daga jikinsa yana fad'in kada kiyi kuka, kiyi mani addu'a gobe zan dawo. Kai ta jinjina tana hawaye tace Allah ya tsare mani kai. Ladi ma kuka takeyi tana masa addu'a. Haka suka tasa keyarsa Malan Sani da Madu sai kuka sukeyi. Suna kallo suka tafi dashi yayin da aka sa kayan amota aka tafi dasu.
****
*Washe gari a kotu.*
Ur's.
Nabeelert Lady
[3/10, 8:38 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, MTN Card ta wannan lambar... 08147669770, kayi screen shoot ka tura ta whatsapp a lambar k'asa, idan kuma bank transfer zakayi ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
1⃣1⃣
Zaune Alhaji Marusa da Mr. Kallah suke a ofis d'in Brr. Barau. Dariya Alhaji Marusa yayi yana fad'in Mr. Kallah ai na fad'a maka bani da kyau, yanzu Alhaji Maiwada zai san ya ja dani, babu wanda ya isa yazo ya kawo mani matsala akan kasuwancina, domin bana had'a kud'i da komai, saboda ina samun had'in kai da ma'aikatan Lagos yasa ban damu da shigo da kaya ta bodar portcourt ba, amma saboda shi sai da na koma ina shigo da wasu kayan ta can saboda ya kasa ya tsare, duk da ba huruminsa bane diba kaya amma sai yayi hakan, ya tsaya ofis yayi aikinsa bazeyi ba ya koma shine yake duba duk kayan da aka shigo dasu, wanda yake kula da b'angaren duba kaya ya zama hoto, kuma saboda raini yafi tsayawa ya duba kayana fiye dana kowa, amma ai yanzu nayi maganinsa, Mr. Kallah kayi mana wannan taimakon a saukeshi daga wannan matsayin, naji dad'i da ya kasance kana hutu abun ya faru, tunda litinin zaka koma Abuja idan kaje ofis inaso a aiko masa da takardar rage matsayi saboda an kamasa da babban laifi.
Murmushi Mr. Kallah yayi yana fad'in Alhaji Marusa baka da kyau, kasan nine shugaban kwastam na k'asa baki d'aya, duk da ina goyon bayanka dole wani abun sai an duba saboda idanuwan mutane, ba kai kad'ai ba, manya da yawa nine nake tsaya masu saboda nidai inason kud'i, duk wanda zai yaga mani dole na bashi goyon baya, amma duk da haka muna kimantawa saboda mu kauda hankulan mutane, hutun dana d'auka litinin yake k'arewa, tunda yau za'a yanke hukunci bayan na koma zamu tattauna akan abinda yayi.
Brr. Barau yace rankaidad'e ai ko da abinda kotu zata yanka masa aka barshi ya isheshi ya tsani aikin kwastam, domin miliyoyin kud'i zai biya, inaji ma kila ya saida gidanshi saboda Kwamishna yace da suka binciki bankinsa babu wasu kud'i da yawa aciki duk ya zuba su a gini, domin wannan binciken sai da suka had'a da EFCC saboda babban abu ne, kaga kuwa dole ya sayar da wannan makeken gidan ya biya kud'in da kotu zata yanka masa.
Murmushi Alhaji Marusa yayi yana fad'in kuma nine nan zan sayi gidan, sai dai banzan bari yasan haka ba, zan aika wani yaje ya siya mani shi. Dariya sukasa gaba d'aya. Brr. Barau yace ina ganin lokacin shiga yayi. Mr. Kallah yace bara na fara fita kada azargi wani abu.
***
Duk girman kotun sai da ta cika da jama'a, domin tun jiya ake fad'ar an kama shugaban kwastam na Lagos da laifin satar kayan Alhaji Marusa, wannan dalilin ne yaja hankulan mutane da yawa suka kawo ziyara a kotun, hada manyan mutane sai da suka ziyarci kotun saboda suji abinda za'ayi, 'yan jarida kuwa sun cika kotun kowa yana jira ya samu abun k'araswa.
Bayan da Alkali yashigo kowa ya natsu. 'Yan sanda ne suka shigo da Alhaji Maiwada, kowa kallonsa yakeyi yayin da Alhaji Maiwada yake ta addu'a, gaba d'aya jikinsa rawa yake masa, idanuwansa a k'asa ko kallon mutanan bayayi.
Ummun Ra'eez kasa zuwa kotun tayi, domin bazata iya ganin ana cima mijinta mutunci ba. Malan Sani da Madu sai Alhaji Mansur kawai suka zo kotun, shima a safiyar yau ya biyo jirgi saboda tun a jiya Ummun Ra'eez tayi masa waya. Maman Rumaisa da Ladi sune suke ta bama Ummun Ra'eez hakuri.
Ma'aikatan ofis d'insu Alhaji Maiwada da yawa sun zubar masa da kwallah musamnan wad'an da suke jin dad'insa. Adebayo, Umar da sauran mabiyansu sunfi kowa murna, sai dai a fuskarsu suna nuna jimami.
Bayan da Magatakarda ya sake karanto k'arar Alkali yace a fara gabatar da shari'ar. Tashi Brr. Barau yayi yana fad'in inaso kotu ta bani izini na kira Alhaji Maiwada domin nayi masa wasu tambayoyi. Alkali yace kotu ta baka dama.
Bayan ya fito Brr. Barau ya k'arasa wajensa yana fad'in Alhaji inaso kayima kotu cikekken bayani akan yanda aka samu kayan Alhaji Marusa wanda ake tuhumar hukumar ku dasu a gidan ka.
Ajiyar zuciya Alhaji yayi yana fad'in tabbas an samu kayansa a gida na, amma maganar gaskiya bani da masaniyar zamansu agida na, sai dai idan saka mani akayi, domin duka kwali ukku ne aka samu a gidana.
Murmushi Brr. Barau yayi yana fad'in Alhaji kada ka bama kotu wahala, 'Yan sanda sun tabbatar mana a cikin d'akin da yake bayan gidanka aka samesu, kuma tambayar anan itace, Alhaji Marusa ya bamu iya yawan kayansa da suka b'ace hada kud'ad'en su, sai dai kuma kayan da aka samu a wajenka basu kai kwatar kud'insa ba, haka kuma ko rabin wad'an da suka b'ace basu kai ba, domin lokacin da aka duba gidanka an iske saura kad'an ka rage, shine muke so muji ina ka kai sauran? Idan kuma siyarwa kayi to ina kud'in suke, domin a binciken asusunka da akayi kud'in da suke ciki ba wasu masu yawa bane, shine muke so kayi mana bayani.
Wani lauya ne ya tashi yana fad'in ya Mai shari'a nine lauyen da nake kare wanda ake k'ara. Sunana Brr. *Kamal Auwal*. Kai Alkali ya jinjina yana fad'in Brr. Kamal akwai maganar da kake da ita ne? Risnawa yayi yana fad'in ya mai shari'a ya kamata lauyen da yake kare wanda yake k'ara ya sassauta maganarsa akan wanda ake k'ara, be kamata yarik'a masa wasu tambayoyin ba. Nagode.
Jinjina kai Alkali yayi yana fad'in wanda ake tuhuma ba zarginsa ake ba domin anga zahiri a gidanshi, dan haka dole ya amsa tambayar da akayi masa saboda shi kad'ai ne zai iya warware mana wannan matsalar.
Murmushi Brr. Barau yayi yana fad'in Alhaji kotu tana sauraron ka. Gyara tsayuwa Alhaji yayi yana fad'in kamar yanda nace bansan da zaman kayan Alhaji Marusa agidana ba, haka zalika bansan ina sauran suke ba, kuma ni ban siyar da komai ba saboda ban tab'a zaluntar kowa akan kayansa ba, iyakar abinda na sani kenan.
Juyowa Brr. Barau yayi yana fad'in ya mai shari'a inaso wannan kotu tayi duba da abubuwa guda biyu da zan gabatar mata yanzu, wanda sun isa su tabbatar ma kotu lallai Alhaji Maiwada shine ya d'auki wad'annan kaya.
Na farko Alhaji Maiwada ya gina katafaren gida na makudan kud'i, kuma babu wanda yasan lokacin daya fara ginin da lokacin da aka gama, sannan be gayyaci kowa ba alokacin da zai tare agidansa, haka zalika Alhaji Maiwada baya son kowa yasan inda gidansa yake acikin ma'aikatansa gaba d'aya, duk wanda yake son ganinsa sai dai su had'u a ofis, domin baya bari aje gidansa.
Abu na biyu alokacin da aka kawo kayan Alhaji Marusa bayan Alhaji da ma'aikatan da suke aiki aranar sun gama duba kayan aka barshi akan sai washe gari zasu k'arasa, bayan da kowa ya tafi Alhaji Maiwada shine wanda aka bari na k'arshen tafiya, wanda maigadi ya tabbatar mana da cewar ya dad'e kafin ya tafi, kuma kafin ya tafi sai da ya aikeshi ya d'auko masa wasu takardu wanda hakan ya d'aukeshi kusan mintuna ashirin kafin ya dawo, da wannan ne Alhaji Maiwada yayi amfani domin ya fitar da abinda yakeso wanda shine yasan ta yanda ya fitar da kayan a cikin lokaci k'ankani.
Da wannan nake rokon kotu data kwatoma Alhaji Marusa hakkinsa. Nagode.
Bayan Alkali ya gama rubutu yace lauyen da yake kare wanda ake k'ara ko kana da abinda zakace? Tashi Brr. Kamal yayi yana fad'in ina dashi ya mai shari'a, ina so zanyima Mai gadin da yayi aiki aranar da aka kawo kayan Alhaji Marusa tambaya. Kotu ta baka dama.
Matsowa yayi kusa da Maigadin bayan ya fito yana fad'in ko zaka iya fad'a ma kotu wajen da Alhaji ya aike ka d'auko takardun da kace? Maigadi yace a cikin ofis d'in da ake aje kaya ne inda suka zauna shine ya mantasu acan sai yace na d'auko masa.
Brr. Kamal... Idan na fahimceka Kenan shi Alhaji ya fito wajen motarsa, daya tuna yayi mantuwa shine ya aike ka?
Kai Maigadi ya jinjina yana fad'in yashiga mota ma sai ya aike ni, to kafin na d'auko masa na d'an jima saboda ban gansu a inda ya fad'a mani ba.
Jinjina kai Brr. Kamal yayi yana fad'in ya mai shari'a inaso kotu tayi duba da abinda Maigadi ya fad'a, Brr. Barau ya ce Maigadi ya fad'a masu Alhaji ya aikesa bayan kuma Alhaji yana cikin mota, hakan zai nuna mana cewar Alhaji baya cikin d'akin da kayan suke taya zai d'aukosu ya fita dasu bayan Maigadi yana cikin d'akin? Inaso wannan kotu mai albarka da tayi duba da wannan sheda da aka gabatar, duk da an samu kaya a gidan Alhaji ba shine yake nuna Alhaji ne ya d'aukesu ba, nagode.
Tashi Brr. Barau yayi yana fad'in ya mai shari'a wannan hujja da abokin aikina ya kawo bata isa ta kare wanda ake k'ara ba, domin kowa ya sheda an samu wad'an nan kaya agidan Alhaji, idan akace yana cikin mota ya aiki mai gadi mai yasa da Maigadin yashiga baiga takardun a inda Alhaji yayi masa kwatance ba? Dama yana da wata manufa shiyasa ya barosu kuma ya aiki Maigadi domin yasan kafin ya gansu ya gama abinda yakeyi.
Ina rokon wannan kotu data yi amfani da shedun da aka gabatar mata domin ta kwatoma Alhaji Marusa hakkinsa, domin ga kwararun hujjoji nan mun gabatar. Nagode.
Bayan da Alkali ya gama rubutu ya d'ago kai yana fad'in Alhaji Maiwada kana da ja akan abinda aka gabatar? Girgiza kai Alhaji yayi wasu hawayen bakin ciki suka zubo masa, hannu yasa ya goge idonshi yana fad'in iya gaskiyata na fad'a, bani da sauran ja akan abinda aka gabatar ma kotu Allah ne kad'ai yasan gaskiya.
Gaba d'aya kotun akayi shiru, mutane da yawa jikinsu yayi sanyi akan maganar Alhaji, su Malan Sani sai kuka sukeyi.
Bayan Alkali ya gama rubutu ya d'ago yana fad'in abisa kwararun shedu da aka gabatar ma kotu, kuma wanda ake tuhuma ya kasa kare kanshi a gaban kotu, wannan ya tabbatar mana cewar Alhaji Hamza Maiwada yana dasa hannu acikin b'acewar wad'annan kaya, inda wasu daga ciki suka salwanta.
Abisa adalci irin na wannan kotu Alhaji Maiwada zai biya Alhaji Marusa duk abinda ya kashe akan kayan da suka b'ace, tun daga siyosu, kud'in kawosu zuwa nan, sauran da suka rage kuma za'a mik'asu ga Alhaji Marusa, 'Yan sanda da hukumar bincike zaku tsaya a kammala komai, domin a tabbatar Alhaji Maiwada ya biya komai daya b'ace, hukumar kwastam sai ku d'auki mataki domin akiyaye sake faruwar irin wannan.
Tebur ya buga gaba d'aya akace kotttt!.
Duk'awa Alhaji yayi ya d'ora kanshi saman katakon da yake tsaye wasu zafafan hawaye suna zubo masa. Malan Sani da Madu sai Alhaji Mansur ne kad'ai suka k'araso wajenshi.
Kamoshi Alhaji Mansur yayi yana lallashinsa. Haka suka fito 'yan sanda suna binsu abaya. Mr. Kallah ne yayi magana da DPO tare da mai jagorantar cibiyar bincike akan su bar Alhaji ya koma gida zasuyi magana da Kwamishna dan ayi komai cikin hankali kwance tunda Alhaji babban mutum ne.
Haka Mr. Kallah ya samu su Alhaji Mansur yayi masu bayani, sosai sukaji dad'in abinda yayi masu, godiya sukayi mashi sannan suka k'arasa wajen Brr. Kamal sukayi masa godiya akan abinda yayi masu domin sun san basu d'aukeshi ba amma ya tashi domin ya kare Alhaji.
Brr. Kamal yace haba bakomai, wallahi naji tausayinsa hakan yasa na tashi domin na kareshi, rashin hujjoji yasa aka kadamu, amma bakomai Allah yana gani.
Godiya sukayi masa suka wuce gida. Duk yanda 'yan jarida suka