Advertisements
Chapter 31 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   31 / 54

90K to 93K   out of 160.3K words

hakan yasa na fad'a masa komai, nan take yace kada na damu na bari muji asibitin da za'a kaita.


Muna nan Gayen ya kirani ya sheda mani yaga Mahaifinta ya samo mota sun nufi asibitin Dr. Kaseem, mamaki ne ya kamani nasan talakawa ne amma suka nufi asibitin kud'i, Dady yace kila baya son ya kaita babban asibiti atsaya b'ata masu lokaci wajen kiran 'yan sanda shiyasa ya kaita can.


Nan take Dady yakira Dr. Kaseem ya fad'a masa halin da ake ciki, kuma yace kada a karb'i kud'in su. A lokacin ya fita amma yace zaiyi sauri ya koma asibitin kuma zai rufe komai.



Wannan dalilin ne yasa Dr. Kaseem ya kori sister Asabe ya duba Halima kuma ya rubuta bayanin k'arya, domin yace har d'inki yayi mata.



Bayan kwana biyu da faruwar haka sai muka samu labarin an kaini kotu, hankalina yayi matuk'ar tashi, kuka nasa Dady yace kada na damu babu abinda zai faru, nan take yakira Dr. Sa'eed ya fad'a masa abinda yake so, babu b'ata lokaci ya shirya sakamakon k'arya akan rashin lafiyata, har gida ya kawo ma Dady suka tattauna yanda komai zai kasance, haka ya cika masa jaka da kud'i ya tafi.


Wallahi tun daga lokacin da haka ta faru ban sake samun natsuwa ba, hakan yasa a yanzu naga ya dace na fad'i gaskiya, kuma zan amshi ko wane hukunci aka yanke mun.


Shiru kotun tayi ana sauraren kukan Sameer. Dadynsa kuwa zama yayi jiki a sanyaye yana goge zufa, gashi d'an siyasa yana tsoron hakan ya tab'a masa mutuncinsa.



Jiki a sanyaye Alkali ya gama rubutu, gaba d'aya kunyar kallon Mahaifin Sameer yakeyi, babu yanda ya iya, Allah ma yaso Sameer ne ya tona komai yasan bazasu zargeshi ba.



Bayan ya kammala rubutu ya d'ago yana kallon Sameer...... Bisa hujjojin da aka gabatar ma wannan kotu da kuma samun babbar sheda daga bakin wanda ya aikata laifi cewar ya amince shine ya aikata wannan laifi, wannan kotu mai adalci ta yanke ma Sameer hukuncin daurin wata biyar agidan yari ko kuma tarar naira dubu d'ari biyar, sannan zai biya Halima tarar naira million talatin domin keta mata haddi da yayi, haka kuma zai cigaba da kula da lafiyarta har ta samu sauki, sannan idan rabo yashiga tsakanin su zai kula da ita har ta haihu da bayan ta haihu har zuwa lokacin da zata yaye abinda ta haifa ta bashi abunshi, idan kuma zata rik'e masa to shine yake da alhakin kula dasu.



Dr. Kaseem da Dr. Sa'eed zasu biya tarar dubu hamsin-hamsin bisa kamasu da akayi da kawo ma kotu shedar k'arya, idan aka sake kamasu da makamancin irin wannan laifin kotu zata soke lasisin su.


Kallon mutane yayi yana fad'in ina fatan wannan hukunci zai zama izna ga sauran mutane. Saurin tashi Brr. Bajinta yayi yana fad'in ina neman alfarmar wannan kotu data k'ara ma Sameer tarar da zai biya Halima saboda ya keta mata haddi, ya rabata da abinda yafi komai muhimmanci agareta. Nagode ya mai shari'a.


Jin jina kai Alkali yayi yana fad'in bisa duba da k'orafin lauya mai kare Halima wannan kotu ta amshi rokon ka, dan haka Sameer zai biya Halima tarar naira million hamsin, kuma dole ne ya biyasu akan lokaci... Kotttt.!!!!!


Gaba d'aya kowa ya tashi ana jinjina ma Alkali bisa hukuncin adalcin da ya yanke, haka kowa yarik'a masa jinjinar ban girma, wannan adalci da kowa yake samu yasa suke k'ara son Alkalin su.



Hannu Brr. Bajinta ya bama Ra'eez yana fad'in a wannan shari'ar dai na kada ka, amma duk da haka kayi kok'ari, nan gaba sai kayi kok'arin kada ni.


Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in na tayaka murna, amma nan gaba ka rik'a kok'arin tsayawa akan aikin ka kadena kok'arin juya akalar kariyar ka zuwa ga wani daban, sannan karika aikata abinda ya dace ba sai an fad'a maka ba.


Cira idanu ya fara yana yaken dole dan ya tuna d'azu da Ra'eez ya duko yana fad'a masa yayi sauri yatashi ya nemi a k'ara ma Halima kud'i hakan zaisa ya wanke kansa wajen mutane, hannunsa ya cire yana fad'in haka ne, kuma nagode.


Jabeer ne yaja Ra'eez suka bar wajen. Kusa da Sameer suka je wanda yake rungume jikin Mahaifiyarsa dan Dadynsa ana gamawa ya sulale ya bar wajen.



Dafa Sameer Ra'eez yayi yana fad'in kayi abun kirki, kuma har abada baza kayi danasanin abinda kayi ba, kaci sa'a ba kotun musulunci bace da sai kasha bulala, amma yanzu kana da damar biyan dubu d'ari biyar idan baka son zaman gidan yari.


Da sauri Mamansa tace kud'in zamu biya, mungode sosai lauya, idan bazaka damu ba ina son ganin ka idan kana da lokaci. Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in ayanzu Alhaji ya d'auki zafi, amma zanzo idan na samu lokaci.


Haka suka fito ita da Sameer suka wuce gida 'yan jarida sai d'aukarsu hoto sukeyi. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in wannan itace shari'ar ban dariya.


Jabeer yace wallahi yanda kasan a film, ban tab'a ganin irin wannan shari'ar ba, daga kai har Brr. Bajinta kun bani dariya. Ra'eez yace ai shiyasa na barshi ya fara, da yake be iya wasan ba ai kaga kowa ya ganoshi.


Jabeer yace amma nayi mamakin yanda Sameer yayi saurin amsa laifinsa. Ra'eez yace kila hakan yafi masa sauki. Kallonsa Jabeer yayi yana fad'in ban yarda da kai ba, anya babu sa hannunka? Dariya Ra'eez yasa yana fad'in muje ofis.


Iyayen Halima basu tsaya jiran Ra'eez ba dan ya fad'a masu ana gamawa su wuce gida baya son agansu atare. Duk da sunji haushin Brr. Bajinta amma abinda yayi daga k'arshe yasa sukaji dad'i, hakan yasa sukaje sukayi masa godiya.



Murmushi yayi yace haba babu komai, ai dama nace maku mune zamuyi nasara. Malan Haruna yace nawa ne kud'in ka? Brr. Bajinta yace haba kyauta nayi maku. Sosai sukayi masa godiya suka wuce cike da farin ciki.



Zagaye kawai Alhaji Barau yake a ofis d'insa, ya rasa taya zai kalli abinda Ra'eez yayi masa, ya akayi ya canza komai beyi amfani da abinda suka bashi ba? Dole ya turkeshi sai ya fad'a masa abinda yake nufi. Waya ya d'auko yana niyar kiransa.


K'ofa aka bud'e hakan yasa ya aje wayar. Alhaji Marusa ne yashigo fuskarsa d'auke da murmushi. Bayan ya zauna Alhaji Barau ya mik'a masa hannu suka gaisa dan shima haushinsa yakeji akan abinda yayi masu.


Daurewa yayi dan baya so ya gano ya san komai. Alhaji Marusa yace Babban Alkali da girman kujerar ka. Alhaji Barau yace zaka fara ko.


Dariya Alhaji Marusa yasa yana fad'in alokacin da nace kada ka bama Ra'eez shari'ar me kace? Na fad'a maku nifa jikina be yarda dashi ba, yaron da yazo a ranar farko ya cinye babbar shari'ar da aka sha wahala akanta taya kake tunanin zai amshi tayin rashin gaskiya? Tun farko na fad'a maku amma bakuji ba, sai kace wai zasu iya d'aukarshi, to ko sun d'aukeshi ba sai yana da hujjar nunawa ba, haba Alhaji Barau ya kake so kabar tsohuwar basirar ka ta gushe ne.


Ajiyar zuciya Alhaji Barau ya saki yana fad'in kai dai ka bari kawai Alhaji Marusa, kwanan nan na rasa abinda yake damuna, ganin yana neman yarinyar wajena yasa nayi tunanin zaiyi duk abinda na sashi sai gashi ya watsa mani k'asa a ido, wallahi yanzu daka shigo kiranshi nayi niyar yi naji dalilin da yasa zaiyi mani haka.


Dariya Alhaji Marusa yasa yana fad'in shiyasa nace basirar ka ta tsufa, taya kana Alkali zaka kira lauyenka ka titse shi akan shari'ar da yayi bayan kasan gaskiya ce, ai Brr. Bajinta ne kawai ze maka haka ka titse shi a zauna lafiya.



Abinda nake so da kai ka nuna baka damu ba, kuma kayi masa jinjinar ban girma ka gode masa akan abinda yayi, kuma ka fad'a masa baka san haka abun yake ba amma kace ka gode da yaje ya sake bincike, ina tabbatar maka idan ka fad'a masa haka zai yarda da kai, gashi ka yanke hukunci yanda ya kamata, domin ko wannan kud'i da za'a bata zai inganta mata rayuwar ta, kaga zaka fita daga zarginsa.


Jinjina kai Alhaji Barau yayi yana fad'in nagode da zuwanka Alhaji Marusa da na kwafsa, damuwa ce tamun yawa hakan yasa na kusa rasa dabarata, amma zanyi yanda kace.


Tashi Alhaji Marusa yayi yana fad'in zanje na rarrashi Alhaji, ya godema Allah da ba kisa yaron yayi ba, gashima har ka bada zab'i biyu, kuma nasan bazasu barshi ya shiga gidan yari ba.


Alhaji Barau yace ka gaishe shi kuma ka bashi hak'uri nagode. Alhaji Marusa yace zaiji.


***


Ina jinka Ra'eez, Jabeer ya fad'a yana sunno kanshi a fuskar Ra'eez. Dariya yayi ya tureshi yana fad'in kaga Malan kada ka dameni, taya zaka zo a wajen aiki ka ishe ni na baka labari idan wani yaji fa, kawai ka bari idan muka fita na fad'a maka.



Jabeer yace ai gashi can ana kiran sallah muje muyi idan muka fito sai ka bani. Ra'eez yace muna fitowa na tashi dan wallahi na gaji, kasan dama idan nayi shari'a bana son nayi zaman aiki. Jabeer yace aiko sai dai mutafi tare dan bazanji dad'in zama wajen nan baka nan ba.


Ra'eez yace idan kuma na bar kotun fa? Da sauri Jabeer ya kalleshi yana fad'in ban gane ba? Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in ina nufin idan aka mana canjin wajen aiki. Jabeer yace insha Allahu hakan bazata faru ba. Ra'eez yace Allah yasa.


***

Bayan sun gama sallah yashiga domin ya fad'ama Alhaji Barau zai wuce gida.


Cike da jin nauyi Alhaji Barau ya kalleshi yana fad'in Ra'eez na rasa bakin da zan maka godiya, hakika zuwanka wannan kotun alkhairi ne a wajena, so biyu kana ceto ni daga yanke hukuncin danasani, bazan iya biyanka da komai ba wallahi, nagode sosai, sam banyi tunanin haka abun yake ba, shiyasa wanda nasa yaje yayi mani binciken yana kawowa ban tsaya dubawa ba na baka saboda nasan na yarda da kai, ashe abubuwan da suke ciki ba gaskiya bane, nagode sosai da ka sake bincike, duk da kayi kok'ari baka fito fili ka nuna kasan gaskiya ba, amma kayi aikin da yakamata ace Brr. Bajinta ne yayi, tabbas nasan wannan shari'ar ta yau ta juya ma mutane kai, domin ku duka lauyoyin an rasa gane a wane b'angare kuke, gaskiya nagode sosai, shima Brr. Bajinta ya taimaka daya gyara kuskuren da ya kusayi.


Murmushi Ra'eez yayi yace ai bakomai duk taimakon kaine, nima nasan bazaka bani abinda za'ayi rashin gaskiya aciki ba, hakan yasa dana duba shedar nasan baka duba ba, shiyasa banyi maka magana ba naje na sake sabon bincike.


Alhaji Barau yace naji dad'i sosai tunda kasa bamuji kunya ba. Ra'eez yace ina son zanje gida kaina yamun nauyi ne. Murmushi Alhaji Barau yayi yace haba bakomai kaje kawai nima yau da wuri zan tashi nagaji.


Tashi yayi yana masa sallama, da sauri Alhaji Barau yace zaka lek'a wajen mutuniyar ko? Murmushi ne ya kwace ma Ra'eez babu shiri, duk'ar da kai yayi alamun kunya yayi waje da sauri.


Dariya Alhaji Barau yasa yana fad'in Allah nagode maka daka zab'a mani suriki nagari, gaskiya Raheena tayi dace, Allah nagode maka da banyi saurin sata ta fiddo da miji ba ashe yana zuwa.



Da k'yar Jabeer ya bar Ra'eez dan yace sai ya tsaya ya bashi labarin yanda akayi, shi kuma Ra'eez yace ya gaji sai dai suyi waya anjima. Babu yanda ya iya dole ya kyaleshi ya tafi.



Bayan sunyi sallama da Jabeer yana kok'arin shiga mota yaji anyi masa sallama. Juyowa yayi tare da amsawa. Murmushi ya saki ganin kamar yasan fuskar wanda yake tsaye.


Hannu ya mik'a masa yana fad'in barka da kok'ari Brr. Ra'eez ina tayaka murna akan wannan nasara da kayi a wannan shari'a.


Hannu Ra'eez ya bashi yana fad'in nagode, amma kamar nasan fuskar nan? Murmushi yayi yana fad'in *Rafeek Labaran Zaki*, Ma'aikacin gidan redion *Liberty*.


Jinjina kai Ra'eez yayi yana murmushi yace yanzu kam na tuna, nagode Rafeek amma ai ba nine nayi nasara ba.


Murmushi Rafeek yayi yana fad'in wanda ka kare dai ya faad'i amma ai kaine hasken shari'ar, gaskiya kayi matuk'ar burge ni, na saurari shari'ar ka ta farko a wannan kotun, duk da alokacin ana gamawa na tafi saboda saurin da nakeyi, naso mu had'u amma wani aiki yasha kaina ga tafiye-tafiye, sai a wannan karon naji labarin wannan shari'ar shine nazo domin naji yanda zata kasance, sai gashi nazo nasha mamaki, gaskiya kai d'in na daban ne.


Ra'eez yace nagode. Rafeek yace gaskiya ina so mu kulla abota idan bazaka damu ba, yanzu naga kana sauri amma zan amshi lambarka duk lokacin da kake da lokaci zan iya kawo maka ziyara.


Kallonshi Ra'eez yayi, yasan dai ya girme mashi sosai, sai yaji kunya da yace zasu kulla abota. Kamar Rafeek yasan abinda yake tunani yayi saurin fad'in nayi maka tsufa ko? Dariya Ra'eez yasa yana girgiza kai.


Rafeek yace ita abota ai ba'a duba girma, idan na yarda da hankalin mutum ina abota dashi koda na haifeshi bare kuma nasan ban haife ka ba, dan haka kada ka damu kawai naji ka kwanta mani ne.


Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in nagode Yayana, kada ka hanani kiranka da haka domin nima naji inaso na kiraka da hakan domin ina buk'atar hakan.


Murmushi Rafeek yayi yana fad'in nima ina buk'atar samun K'ani domin na rasa nawa shekaru da yawa, amma tunda na samu wani nafi kowa farin ciki.


Wayarsa ya mik'a mashi, amsa yayi yasa masa lambarsa ya kirashi yana fad'in ga tawa nan, sai munyi waya nagode. Ra'eez yace nima nagode.


Mota yashiga yana kok'arin kunnawa wayarsa tayi k'ara, yana dubawa yaga lamba ce, yana d'auka yaji muryar Sameer da alamun kuka.


Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in lafiya Sameer? Cikin sanyin murya Sameer yace ina so mu had'u ne ko zaka mun kwatancen gidan ka? Ra'eez yace kada ka damu bara nazo Mamanka ma tace tana son gani na.


Sameer yace nagode sai kazo. Kashe wayar yayi yana murmushi, yaso yaje gida ya huta anjima yaje wajen Ummunsa amma dole yaje yaji dalilin kiran.....


Ur's.
Nabeelert Lady🖋[3/10, 8:39 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*



3⃣0⃣


Cikin kuka Sameer ya rungume Ra'eez yana fad'in nagode sosai Ra'eez da abinda kamun, wallahi yanzu ina jin sanyi araina, gashi dai na girma amma na kasa gane hakan, abinda nake so yanzu naje na nemi yafiyar Halimatu, da zata amince dani wallahi zan aureta ma.


Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in bakomai kadena kuka, tunda dai har kayi nadama Allah zai yafe maka, sai dai kaje ka nemi yafiyar Halima, idan da hali zaka iya tuna sauran matan da ka lalata ma rayuwa suma kaje ka basu hak'uri sannan kayi masu alkhairi hakan zaisa ka sake samun nutsuwar zuciya sosai.


Zama Sameer yayi yana fad'in zanje, wallahi zanje Ra'eez, duk da nasan ba lallai bane na iya samun wasu amma duk matan da nayi harka dasu nasan su, nagode Allah da basu da yawa kuma zanje na nemi yafiyarsu, amma ni ina son kashige mun gaba muje gidan su Halima.


Ra'eez yace kada kadamu zan zo muje, amma shawarar da zan baka ka ajiye kudirin ka na son aurenta a gefe, ina mai tabbatar maka Halima bazata amince da kai ba, duk da hakan taimako ne agareta amma baza ta amince ba, gara ka bata hak'uri idan akwai taimakon da zaka sake mata kayi mata kaje ka cigaba da istigfari ka samu wata mata can daban ka aura hakan zai fi maka kwanciyar hankali.


Jinjina kai Sameer yayi yana fad'in shikenan, dama tausayinta ne yasa nace zan aureta badan soyayya ba, saboda dama sha'awarta kawai nakeyi amma zanyi yanda kace.


Ra'eez yace kaga tunda baka sonta gara ka hakura, domin shi aure soyayya ce jigonshi, Allah ya k'ara tsare gaba.


Sameer yace amin, amma dan Allah a ina ka samu hoto na? Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in tunda komai yawuce ai shikenan ba sai kaji ba.


Sameer yace shikenan, ai nasan sirrin ku ne na lauyoyi na barshi. Maman Sameer ce tashigo bakinta d'auke da sallama.


Bayan sun gaisa ta kalli Ra'eez tana fad'in nagode sosai, dama godiya nake so nayi maka domin ka taimake mu, sam banyi danasanin fad'uwar mu ba, domin gata kayima Sameer, gara mutum yaji kunyar duniya akan ta lahira, gashi ta silarka Sameer ya natsu, shima Alhaji da yayi fushi na sameshi nayi masa bayani kuma ya fahimce ni yace ayi maka godiya yana jin kunyar ka ba zai iya fitowa ba.


Ra'eez yace haba babu komai Allah ya tsare gaba. Sukace amin. Kallon Sameer tayi tana fad'in Alhaji ya tura maka duka kud'in da za'a kai kotu, sai ka shirya gobe kaje Ra'eez yayi maka jagora ka kai kud'in a aika ma su Halimar.


Sameer yace nagode Mamy, kuma Ra'eez yace zai rakani wajen Halimatu na bata hak'uri. Mamy tace angode sosai Ra'eez.


Tashi Ra'eez

31 / 54