Author : Marubuciyar Zamani Category : Complete Novels
Adebayo yace ka bashi hak'uri kayansa suna nan babu abinda muka tab'a amma kada a koma kotu. Alhaji yace tashi kaje zamuyi magana dashi. Jiki a sanyaye Adebayo ya fita.
Bayan ya fita Alhaji ya d'auki waya ya kira Alhaji Usman domin ya samo lambarsa. Koda ya d'auki wayar ya gane har lokacin yana cikin damuwa. Bayan sun gaisa yayi masa bayanin kansa, cike da masifa Alhaji Usman ya fara magana, sai da ya gama Alhaji yace idan zaka yarda ina son ganinka amma agida, domin maganace akan kayanka dana gano, amma inaso kayi shiru kada ka fad'ama kowa. Cike da farin ciki Alhaji Usman yace kayi hakuri ban fahimceka daga farko ba, shikenan zaka iya zuwa anjima bayan sallar isha'i. Alhaji yace shikenan ka turo mani da kwatancen gidan ka. Sallama sukayi ya kashe wayar.
***
Bayan sallar la'asar su Umar da sauran mutane ukkun da Adebayo ya rubuta sunan su suka hallara ofis d'in Alhaji. Bayan ya gama masu bayani duk suka shiga bashi hak'uri. Alhaji yace bana magana biyu, kunci sa'a da na rage maku wata biyu, sannan zanyi kok'arin kare mutuncin aikin ku, amma daga yau idan na sake kama ku da aikata makamancin wannan abun to maganar sai taje sama.
Idan kunso zaku iya tona asirin ku, amma ni dai babu wanda zan fad'a mawa, kuma bazan dakatar da albashin ku ba domin daga banki yake zuwa, matuk'ar nace zanje adakatar dashi dole sai manya sun san da maganar, amma ni zan yanka ma kowa abinda zai bayar a bama Alhaji Usman amatsayin tara, domin wannan shine adalci, kuma baza ku zo aiki ba har sai nan da wata d'aya, sannan kowa acikin ku zai bayar da dubu hamsin ga Alhaji Usman domin kun jawo masa asara, ko ya amshi kayanshi wasu kud'in bazasu dawo ba, idan kuma kuna ganin wannan abun beyi maku ba, shikenan sai muje kotu ta yanke maku hukunci.
Gaba d'aya suka had'a baki wajen fad'in sun amince. Murmushi Alhaji yayi yana fad'in da kyau, daga yau ba sai kun sake zuwa aiki ba, kowa yaje ya huta. Adebayo yace Sir, ka barmu muzo aiki wasu zasu iya gano wani abu. Umar yace dan Allah Alhaji ka rufa mana asiri abarmu muyi aiki sannan zamu bayar da kud'in.
Jinjina kai Alhaji yayi yana fad'in shikenan, tunda wannan shine karo na farko dana fara kama ku da laifi zanyi maku uzuri, amma akan biyan kud'i babu uzuri, sannan zan rubuta na ba kowa yasa hannu akan duk lokacin da aka sake kamaku da irin haka babu sauran uzuri. Gaba d'ayansu suka amsa da sun amince.
Bayan da suka gama sa hannu akan kowa zai bayar da kud'in kuma sun amince da lifin da aka kamasu dashi. Haka kowa ya fita jiki a sanyaye. Adebayo da Umar waje suka samu kowa da abinda yake fad'a. Adebayo yace Omar wannan mutumin sai yasan yayi mana haka, Brr. Barau zan kira na fad'a masa komai.
Umar yace kada ka fad'a masa, kasan Brr. Barau da surutu zai iya fitar da maganar, tunda dai Allah yaso Alhaji zai rufa mana asiri to mu bar maganar. Adebayo yace shikenan, amma wallayi sai na rama kasanni ai. Umar yace ba yanzu ba, dole mu kwantar da kai har zuwa wani lokaci. Adebayo yace shikenan.
***
Bayan da akayi sallar isha'i Alhaji ya tashi domin yana son zuwa wajen Alhaji Usman. Haka suka nufi gidanshi suna bin kwatancen da ya turo masa. Malan Sani yayi mamakin abinda Alhaji ya fad'a masa, kuma ya jinjina adalcin da Alhaji yayi masu.
Zaune suke a cikin rumfar da take a harabar gidan. Bayan sun gama gaisawa Alhaji ya sake bama Alhaji Usman hak'uri akan rashin adalcin da akayi masa. Alhaji Usman yace bakomai, nima ina baka hak'uri akan abinda nayi maka awaya, duk da nasan kai d'in sabon zuwa ne amma nayi tunanin kaima irin halin tsohon shugaba gare ka, domin daga zuwanka har na fara asarar kaya.
Alhaji yace bakomai, domin ni bansan da maganar ba sai da Brr. Barau yazo mani da maganar, alokacin bani da abinda zanyi hakan yasa nayi shiru da niyar nayi bincike bayan an gama komai. Alhamdulillahi kayan ka suna nan babu wanda ya b'ace, kuma na gano wad'an da suka aikata hakan.
Alhaji Usman yace acikin su akwai Adebayo. Murmushi Alhaji yayi yana fad'in kaima kasan halinsa kenan? Alhaji Usman yace waye besan Adebayo ba, dashi da Mr. John halinsu d'aya, shegu arnan banza, babu Allah aransu sai cuta.
Alhaji yace nazo neman wata alfarma awajenka ne Alhaji, nasan zeyi wuya kayi mani ita, amma ina rokon ka da ka dubi girman Allah ka amince da abinda zan fad'a maka.
Alhaji Usman yace babu abinda zaka nema awajena banyi maka shi ba, domin kayi mani abinda Kotu ta kasa tayi mani, dan haka kayi maganar ka kawai.....
Bayanin abinda yake so yayi masa. Shiru Alhaji Usman yayi kafin can yayi murmushi yace saboda kai zanyi masu wannan alfarmar, domin ko alahira wani yana cin arzik'in wani, bakomai, ka d'auka baka fad'a mani komai ba, nayi maka alk'awarin babu wanda zaisan da faruwar haka, zan nuna cewar wasu kayan ne sukazo.
Murmushi Alhaji yayi yana fad'in nagode sosai Alhaji Usman Allah ya k'ara girma. Alhaji Usman yace amin nagode, kuma acikin kud'in da zasu had'a dubu d'ari biyu da hamsin ka d'auki dubu d'ari na baka kyauta.
Girgiza kai Alhaji yayi yana fad'in hakkina ne nayi maka hakan, bana buk'atar komai. Alhaji Usman yace nima kyauta ce nayi maka ai. Alhaji yace Allah bazan amsa ba. Alhaji Usman yace shikenan na bama direban ka, domin nasan irin halinka gareshi. Alhaji yace to mungode sosai, anjima kad'an kayanka zasu iso. Alhaji Usman yace nagode.
****
Tun daga wannan rana Alhaji Maiwada yake aikinsa hankali kwance, kowa yashiga hankalinsa domin sun san Alhaji Maiwada ba wasa. Adebayo da Umar sun natsu tamkar babu su a wajen, su kad'ai sukasan abinda suke kullawa.
A yanzu duk wani wanda yake samun matsala da ma'aikatan kwastam na wajen su Adebayo yanzu hankalinsa akwance yake, domin idan kaya suka iso cikin lokaci k'ank'ani za'a duba a cike komai bisa tsari a sakar maka kayanka idan babu haramtattun kaya aciki.
Duk wanda aka kama da haramtattun kaya aciki babu batun ya bada cin hanci asakar masa, idan aka kama shikenan baza'a badasu ba. Alhaji Marusa yanzu ya dakatar da shigo da kayan da yake shigowa dasu, domin sun tattauna akan Alhaji Maiwada, sun yanke shawarar su d'aga masa k'afa zuwa wani lokaci ya gama zafin kanshi.
Kafin wani lokaci Alhaji Maiwada yayi suna a Lagos musamman a wajen wad'an da suke jin dad'in zuwansa.
Duk bayan wata yake zuwa Kano ganin iyalinsa. Alokacin Ra'eez yana aji ukku a primary, Alhaji yace zai maidasu Lagos saboda ya kusa kammala gininsa.
Nan Ummun Ra'eez ta nuna ya bari Ra'eez ya kammala firmare kada a lalata masa karatu. Alhaji yace shikenan Allah ya kaimu, kafin lokacin ma na kammala gini na, bara naje muyi maganar da Alhaji Mansur kada yaji maganar daga sama.
Lokacin daya fad'ama Alhaji Mansur yana so ya mai da Iyalinsa Lagos sai Alhaji Mansur yace wannan yana da kyau, bazai yuwu kayi ta zama babu mata akusa da kai ba, kasan yanda zuciya take, duk yanda muka kai da sabawa dole muyi hak'uri, amma kuma zumuncin mu yana nan, amma nafi so Ra'eez yayi makarantar kwana anan Kano, haka kawai bana so yaje yashiga cikin arnan nan, kaga anan akwai karatun addini a makarantar da nakeso na samar masu shida Labiba.
Murmushi Alhaji yayi yana fad'in wannan ai bakomai, Ra'eez 'Danka ne, duk abinda ka yanke akanshi yayi, nima ina masa kwad'ayin samun ilimin addini mai zurfi domin Kano dabance a wajen ilimin addini. Alhaji Mansur yace to nagode.
**** ***
Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah Alhaji ya kammala gininshi, yayin da yasa Malan Sani ya sayar da gidanshi ya cika masa ya sayi wani gidan ya canza unguwa, yaso ya sama masa gida a unguwar da yayi gini amma babu gida mai k'aramin kud'i, hakan yasa ya saya masa a unguwa dai-dai kud'insa, sai dai tafi waccan unguwar da suke.
Sosai Malan Sani yaji dad'in abinda Alhaji yayi masa. Matarsa Halima tafishi jin dad'i, domin tunda taga Rumaisa tayi wayau kyanta sai fitowa yake ta fara tsorata da unguwarsu, domin unguwace ta marasa tarbiya, shiyasa har lokacin shigarta makaranta yayi Halima bata yarda ansata ba, lokacin da taji zasu tashi hada kukan farin ciki tayi, duk da zata rabu da makwabciyarta mai kirki.
Yanzu tsakanin Malan Sani da Alhaji yanda kasan 'yan uwa, d'aya baya zartar da abu ba tare da shawarar d'aya ba, akwai girmamawa sosai atsakaninsu, Malan Sani bai tab'a tsallake maganar Alhaji ba amatsayinsa na direbanshi, duk da Alhaji ya sakar masa komai amma baya masa almubazzaranci. Haka Alhaji da kanshi ya saka Rumaisa makarantar kud'i mai sauki, kuma shine ya d'auki nauyin karatun ta.
A wajen aikinsa kuwa yana kokarin adalci ga na k'asa dashi, sai dai yana samun damuwa daga na sama dashi, yasha kama kaya amma ya samu sako akan ya sake su, wani lokacin kuma a hanashi ya duba kayan, sosai wannan abun yake damunsa.
***
Bayan shekaru biyu Ra'eez ya kammala makaranta, haka Alhaji yaje akayi taron yayesu. Bayan kwana biyu sukayi sallama dasu Alhaji Mansur zasu tafi hada Ra'eez kafin jarabawarsu ta fito. Ummun Ra'eez da Matar Alhaji Mansur hada kukan rabuwa.
Haka suka d'aga zuwa Lagos cike da kewar babbar aminiyarta.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋[3/10, 8:38 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kudi ne, naira 200 kacal, MTN Card ta wannan lambar... 08147669770, kayi screen shoot ka tura ta whatsapp a lambar k'asa, idan kuma bank transfer zakayi ka tuntube ni a whatsapp ta wannan lambar. 08028525263.*
0⃣8⃣
*SURELERE* itace unguwar da suka koma, gida ne mai kyan gaske, domin Alhaji ya dad'e yana ginashi ta yanda zaiji dad'in rayuwa da Iyalinsa, acewarsa beda wasu dangi da suka wuce Iyalinsa, shiyasa ya tsara gida mai kyau saboda suji dad'in rayuwa aciki.
Tunda Ummun Ra'eez taga gidan taji ya burgeta, sosai tayi farin ciki da wannan gida. Ra'eez sai murna yake sun dawo gida mai kyau. 'Dakinshi daban babu abinda ba'asa mashi ba. Haka d'akin Ummunsa komai akwai aciki, jitake kamar wata sabuwar amarya, saboda farin ciki rungume Alhaji tayi hada kukan farin ciki.
Murmushi yayi yana shafa bayanta yace haba Ummun Ra'eez, meyasa zaki rik'a kuka haka? Hannu tasa ta share hawayenta tana fad'in Abbun Ra'eez dole nayi kukan farin ciki, ban tab'a tunanin kasancewa a irin wannan gidan ba, duk da gidan ka na Kano yana da kyau amma wannan daban ne, ginin zamani ne had'e da kayan zamani aciki, unguwar kad'ai abun kallo ce, bansan da wane baki zan gode maka ba.
Rungumeta ya sakeyi yana fad'in bana buk'atar godiyar ki Bilkisu, addu'arki kad'ai nake buk'ata, domin kinsan halin irin aikina, addu'a kad'ai zaki bini da ita, Allah ya albarkaci Ra'eez ya kuma kawo wasu masu albarka a sabon gida.
Guduwa tayi d'akinta tana murmushi. Dariya yayi yana fad'in yau kuma an tuno da daren amarci ne? Tana jinshi ta shige tana dariya. Madu ne ya danna kararrawa hakan yasa Alhaji yaje ya bud'e.
Kwando ya gani mai d'auke da kuloli aciki sai babbar roba wadda aka cikata da zob'o. Kallonsa Alhaji yayi cike da mamaki yana fad'in Madu wannan kuma daga ina? Madu yace Malan Sani ne ya bani yace na kawo maku.
Murmushin jin dad'i Alhaji ya saki yana fad'in ikon Allah!, ina shi Malan Sanin yake? Madu yace yana bani ya tafi yace baya son a taso ka kana hutawa. Amsar kwandon Alhaji yayi yana fad'in gaskiya naji dad'i sosai, yanzu nake shirin na fito na aike ka ka samo mana abinda zamuci saboda Ummun Ra'eez ta gaji bazata iya girki ba, ashe Malan Sani yayi mana tanadi, Allah ya saka masa da alkhairi. Madu yace amin. Alhaji yace bara nashiga ciki sai na miko maka naka.
Ciki yashiga yana kiran Ummu, fitowa tayi tana amsawa. Alhaji yace kinga Malan Sani ya kawo mana abinci, matarsa ce ta dafa. Murmushi Ummu tayi tana fad'in kai amma naji dad'i sosai, wallahi dama yunwa nakeji ina tunanin abincin siyarwa.
Ra'eez ne ya fito yana fad'in Abbu nima zanci. Murmushi Alhaji yayi yana fad'in ashe dai kowa yunwa yakeji? Taho kaci Kawun ka ne ya kawo mana. Ra'eez yace Abbu anjima zamuje naga Rumaisa ko? Dariya sukasa Ummu tace daga yau dai andena baka labarin Rumaisa zaka rik'a ganinta tunda mun dawo garin su. Alhaji yace anjima muna hutawa zamuje ka ganta. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in yauwa nagode Abbu.
***
Bayan sallar la'asar suna shirin zuwa gidan Malan Sani sai k'arar kararrawa sukaji, Alhaji ne yaje ya duba, saurin bud'ewa yayi yana fad'in ikon Allah, Malan Sani kune haka? Yanzu muke shirin zuwa Ra'eez ya matsa mana sai munje yaga Rumaisa.
Matsawa yayi yana fad'in kushigo, kamo hannun Rumaisa yayi yana fad'in kema kinzo ganin Ra'eez ko? Kai ta d'aga tana murmushi. Malan Sani yace ai mune ya kamata muzo muyi maku sannu da zuwa. Ciki suka shiga Alhaji yashiga kiran Ummu.
Kallon Malan Sani Halima tayi tana fad'in lallai Malan idan kana raye zakasha kallo, ashe haka gidan nan yayi kyau? Ai baka fad'a mani komai ba. Malan Sani yace dama ai gani da ido ya kori ji, duk yanda zan baki labarin gidan be kai yanda kika ganshi yanzu ba.
Rumaisa tace Baba ni dai anan zan kwana yau. Malan Sani ya d'aure fuska yana fad'in idan na sake jin wannan maganar abakin ki saina zaneki kina ji na? Kai ta d'aga cike da tsoro. Halima tace nima zaneki zanyi idan kika sake fad'ar haka, idan ma ance kizauna bance ki amince ba, nasha fad'a maki duk abinda zakiyi arayuwa kada ki hangi na wani, ban tab'a duba da k'arancin shekarun ki ba kullum nake fad'a maki haka saboda ya zauna a kanki, kwad'ayi bashi da amfani kinji Rumaisa? Kai ta d'aga tana fad'in bazan sake ba.
Murmushi Malan Sani yayi ya jawota yana shafa mata kai yace yauwa Rumaisar Baban ta, haka akeson yaron kirki ya kasance. Sallamar su Ummu sukaji hakan yasa suka maida hankalinsu wajen su suna amsawa.
Zama sukayi nan suka shiga gaisawa. Ummu tace Maman Rumaisa yau dai Allah yayi mun had'u, koda yaushe sai dai muyi waya yau gashi mun dawo garin ku. Halima tace wallahi kuwa, tunda Alhaji yace zaku dawo nake cike da farin ciki, Allah ya kare ki daga sharrin mahassada.
Ummu tace amin. Hannu ta mik'a ta kamo Rumaisa tana fad'in zonan 'Diyata. Duk'awa Rumaisa tayi har k'asa tana gaishe da ita. Dariya Ummu ta saki don sosai Rumaisa ta burgeta, gaba d'aya shekarunta bazasu wuce biyar ba amma tana da tarbiya.
Shafa kanta tayi tana fad'in lafiya lau Rumaisa ya karatu ana zuwa ko? Kai ta d'aga tana fad'in duka biyu duk ina zuwa. Ummu tace da kyau, ki dage kiyi karatu kinji? Kai ta d'aga tana murmushi.
Ra'eez ne ya sauko daga sama sai sauri yakeyi dan lokacin da suka zo yana band'aki. Yana isowa falon ya dai-daita tafiyarsa, dan Ra'eez akwai natsuwa, ya samu tarbiya mai kyau. Da sallama ya shigo, gaba d'ayansu suka amsa suna murmushi.
Har k'asa ya duk'a ya gaishe da su. Malan Sani yace matsonan mugaisa abokina. K'arasawa yayi ya bashi hannu yana mai masa sallama. Dariya sukasa Malan Sani yace lallai Malaman Kano sun karantar da kai da kyau, to ya hanya, kazo lafiya ko? Ra'eez yace lafiya lau Kawu.
Sosai Malan Sani yaji dad'in yanda Ra'eez ya kirashi da Kawu. Halima tace Ra'eez ya karatu ka gama firamare sai ta gaba ko? Ra'eez yace na gama. Matsawa yayi ya kamo hannun Rumaisa yana murmushi yace yau baza kiyi mani magana ba bayan a waya muna gaisawa? Dariya tasa tana fad'in sannu da zuwa Yaya.
Gaba d'aya sai da sukayi dariya. Ummu tace ta waya ta k'are ai tunda ka dawo garin su, sai karik'a koya mata karatu. Ra'eez yace to Ummu kice ma Kawu ya barta nan. Kafin Ummu tayi magana Rumaisa ta kwace hannunta tana fad'in ni dai wajen Mama zan zauna.
Dariya sukasa Ummu tace nima ai Mamanki ce. Rumaisa tace ni dai gidan mu zan kwana. Alhaji yace nan ma gidan ku ne ai. Kafad'a ta mak'ale tana kwanciya saman cinyar Mamanta.
Ra'eez yace Ummu kinji abinda tace wai. Ummu tace kada ka damu zata rik'a zuwa, kaga itama ita kad'aice a wajen Mamanta, idan ta dawo nan za'a bar Mama ita kad'ai.
Jinjina kai yayi yana fad'in to nima zan rik'a zuwa gidansu. Dariya suka sa. Tashi Malan Sani yayi yana fad'in bari mu koma yamma tayi kada mu hana ku aiki. Alhaji yace ba wani aiki da mukeyi kuyi zaman ku. Malan Sani yace zamu dawo wani lokacin akwai gajiya ai.
Tashi Ummu tayi tana fad'in ina zuwa. Tsarabar data kawo masu ta d'auko tana fad'in Rumaisa ga tsarabar ki. Kin amsa Rumaisa tayi tana nok'e kafad'a. Murmushi Ummu tayi tana fad'in Rumaisa da wayau kike, gaskiya Maman Rumaisa kin bata tarbiya me kyau, a garin nan dama idan yaronka be samu tarbiya mai kyau ba abun tsoro