Author : Marubuciyar Zamani Category : Complete Novels
wannan vedion, domin irinshi ne suka kalla a wayar Naseer kuma anan suka konata, ganin beda wata mafita gashi su Mr. Kallah basa wajen hakan yasa ya fakaici idanuwan mutane ya sulale.
Sai dai yana fita su Inspector Hamza suka tareshi, domin sun shiryama hakan, gaba d'aya jikinsa ya d'auki rawa a lokacin da suka kamashi, rokonsu ya farayi akan su barshi ya tafi baya son yaji wannan kunyar, har zasu wuce dashi Hamza yace su jira mutane su fito dan yafison kowa yasan an kamashi. Hakan yasa suka tsaya har sai da aka fara fitowa sannan suka taho dashi.
Tsaye su Alhaji Kamal suke tare da sauran mutanan da yazo dasu. 'Daya daga cikinsu yace lallai Alhaji Kamal maganar ka gaskiya ce shiyasa kace muzo, wallahi na d'auka ba wata babbar shari'a bace, amma meyasa baka fad'a mana komai ba kafin muzo dan nasan kasan da wannan vedion?
Murmushi Alhaji Kamal yayi yana fad'in nafiso ku gani da idon ku. Mutumin yace fad'i gaskiya dai Babban Alkali, kawai kace kasan halin zuciya, kada ka nuna mana asamu wani ya sanar dasu Alhaji Barau kafin muzo.
Alhaji Kamal yace kunga laifi na? Gaba d'aya sukace a'a, ai ana son sirri, kuma hakan da kayi yayi dai-dai, dan haka sai asanar da manyan mu saboda wannan babban abu ne dole sai anyi zama.
Alhaji Kamal yace tun kafin muzo na sanar da Chief Judge, duk da bansanar dashi komai ba amma na fad'a masa ana zargin babban Alkalin kotun nan tare da wasu manya da aikata babban laifi, kuma na sanar dashi za'a gabatar da shari'ar a yau wanda acikinta ne za'a gano komai, kunsa dai mutum baya yanke ma kanshi hukunci, hakan yasa shima Alkalin ya gudu tun kafin a sauke shi, dan haka nasan zuwa yanzu sun kusa isowa dole muyi zama zuwa anjima dan bana so shari'ar nan ta wuce gobe.
***
Wallahi Ra'eez kai mugune, ashe dama ka iya dariyar mugunta, yanzu agaban mutane kasa dariya sai ka tona kan ka. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in ayanzu bana tsoron kowa yasan waye ni, domin komai yazo k'arshe, kuma tsakani da Allah bazan iya rike dariyata ba alokacin shiyasa nayi abuna domin Alhaji Barau yayi abun kunya Alkali da guduwa.
Dariya sukasa gaba d'ayansu. Jabeer yace Allah yaso Raheena da Momynta basa nan da Allah kad'ai yasan halin da zasu tsinci kansu. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in wallahi Jabeer kana son Raheena kawai dai kana b'oyewa ne saboda ni, kuma kasan dai ni ba aurenta zanyi ba.
Tsaki Jabeer yayi yana fad'in wai kai zuciyata kashiga da zaka rik'a fad'ar haka, nifa ba sonta nake ba kawai tausayinta nakeyi. Murmushi Rafeek yayi yana fad'in kai ma Ra'eez da sa ido kake, tun yaushe Jabeer yake fad'a maka ba sonta yake ba kawai tausayinta yakeyi abarshi ahaka.
Jinjina kai Ra'eez yayi yana dariya yace an barshi ahaka Yaya, Allah ya kawo masa mai sonshi. Tsaki Jabeer yayi yana fad'in d'ansa ido kawai.
Ra'eez zeyi magana wata matashiyar yarinya tayi masu sallama. Amsawa sukayi suna kallonta yayin da Jabeer ya juya baya yana waya. Gaishe su tayi tana fad'in dan Allah Yaya Sameer nake nema munyi waya yace yana kotu kuma nashigo wayarsa bata shiga.
Ra'eez yace wane Sameer fa? Tace Yayan Adnan wanda yazo bada sheda. Ra'eez yace oho, K'anwarsu ce ke? Kai ta d'aga tana murmushi. Ra'eez yace kuma bamu sanki ba ya sunan ki? *Husnah!* ta bashi amsa.
Ra'eez yace amma dai ba'a nan kike zaune ba ko? Murmushi tayi tace sati na d'aya dana dawo na kammala karatuna a A.b.u zariya. Ra'eez yace masha Allah, na tayaki murna, bara na kira maki shi yanzu na ganshi kila koya zagaya.
Kafin ya bar wajen saiga Sameer ya fito daga baya da alama band'aki yaje. Murmushi ya saki yana fad'in Husna ashe kin iso? Kai ta d'aga tana fad'in na kira ka bata shiga ba. Sameer yace kila network ne.
Juyowa Jabeer yayi yana maida wayar aljihu yace mu tafi idan ka gama surutun naka. Dariya Ra'eez yayi yana fad'in ai fa yau nashiga ukku, sai fushi kake kamar kaine Alhaji Barau.
Dariya sukasa gaba d'ayansu banda Husnah data shagala wajen kallon Jabeer😉. Rafeek yace wallahi Jabeer sai kayi da gaske dan Ra'eez yaga wajen baccin ka.
Harara ya buga ma Ra'eez yana fad'in ka barni dashi Yaya nasan tsiyar da zan masa. Kamoshi Ra'eez yayi yana fad'in haba d'an uwana na kaina, yi hakuri muje, kasan akwai sauran abubuwa agaban mu.
Sameer yace bara na aje Husna gida zanzo. Rafeek yace shikenan nima ofis zan wuce dan dole ayau mu saki wannan labarin, gidan Tv ma nasan zasu haska dan nasan dole akwai wad'an da suka d'auka kasan mutane ba'a iya masu ko yaya ne sai an samu cikin 'Yan jarida sun d'auka.
Sameer yace shikenan Husna muje. Jin shiru yasa suka juyo suna kallonta, ita ko hankalinta yana wajen Jabeer da yayi gaba zuwa wajen motarsu. Hannu Sameer yasa ya mintsinota da sauri ta juyo tana sosa kai.
Ra'eez yace K'anwarmu ki gaida gida ko. Murmushi tayi tana jinjina kai. Gaba Ra'eez yayi yana fad'in Yaya sai munyi waya. Murmushi Rafeek yayi yana fad'in tunda kana sauri kayi d'aukar magana ba.
Zama cikin motar yayi yana fad'in wai saurin me kake ko sallama dasu Husna bakayi ba bayan kuma kayi kasuwa. Harara ya wurga mashi yana fad'in wallahi Ra'eez kashiga hankalin ka dani, wacece kuma wata Husnah? Kafad'a Ra'eez ya d'age yana fad'in oho, lokacin da ka gama wayar wayace baka tsaida hankalin ka har ka ganta ba.
Murmushi Jabeer yayi yana girgiza kai yace naga alama yau ahaka zaka k'are wajen tsokana, ina su Ummu ko sun wuce? Ra'eez yace suna fitowa Abbah ya tafi dasu kasan kotun ta cika. Jabeer yace ina muka nufa? Ra'eez yace muyi gida dan nasan anjima Kawu Kamal zai nememu dan yace akwai zaman da zasuyi gara muje mu huta.
**** ****
Zaune suke a gidan Alhaji Marusa su ukku suna jiran tsammani, dan tunda sukasan an shiga kotu suka had'u a gidan Alhaji Marusa dan Alhaji M. Sanda ya fad'ama Alhaji Barau da zarar yaga za'a gabatar da shedar data tabbatar suna dasa hannu a kisan Naseer da Alhaji Maiwada yayi kokarin fitowa yazo su gudu tun kafin a kamasu. Sai dai basu san jiran gawar shanu suke ba.
Gyara zama Mr. Kallah yayi yana fad'in nifa hankalina ya kasa kwanciya, tun d'azu nake kiran Brr. Bajinta naji ko an gano wani abu amma wayarsa ma akashe take, da farko tana shiga be d'auka ba, nasan lokacin ko yana cikin kotun, amma yanzu a kashe ma take. (Abinda basu sani ba Brr. Bajinta ma yayi takanshi, dan tunda ya tabbatar da mugayen halinsu ya tsorata, danshi duk tarayyarsu dashi iyaka su sashi yayi shari'ar karya su biyashi amma betab'a sanin su d'in makisa bane, hakan yasa asiri yana tonuwa ya kashe wayarsa dan yace bazai fada masu ba kada su gudu, shiyasa ma ya sanar ma Hamza inda suke.)
Alhaji Marusa yace nima hankalina ya fara tashi, gashi na kira wayar Lucky itama akashe, da alama shima yayi takanshi, ina ganin fa lokaci yayi da kowa zai nemi hanyar tsira, kawai ku tashi mubar garin nan kafin komai ya kwab'e.
Mr. Kallah yace Alhaji Barau fa? Alhaji Marusa yace kai kasanshi, amma wallahi bazan sake mintuna goma awajen nan ba, idan kai zaka tsayashi to ni nayi nan.
Tashi Alhaj M. Sanda yayi yana fad'in jirani Alhaji Marusa. Dole Mr. Kallah ya mik'e jiki a sanyaye yabi bayansu. Suna fitowa suka iske 'yan sanda suna jiransu, ai gaba d'aya sai hankalinsu ya tashi, nan fa suka fara kokarin tserewa, da sauri aka cafkesu akasa mota yayin da 'Yan jaridan da Hamza ya taho dasu suke ta d'aukarsu.
Yayi haka ne domin a watsasu ayau saboda kowa yasan halin da ake ciki, haka suka tafi dasu sai zare ido suke a mota.
Ganin haka gaba d'aya ma'aikatan gidan Alhaji Marusa suka fito domin suyi takansu, sai dai kowa sai da ya kwashi rabonshi kafin yayi gaba.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:41 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
4⃣8️⃣
Gaba d'aya gari ya hargitse da labarin abinda ya faru, yayin da 'yan jarida suke ta kok'arin had'a kan labarin da zasu gabatar.
Da misalin k'arfe hud'u su Alhaji Kamal suka shiga taron gaggawa. Manya sun fusata akan wannan abun kunyar da aka jawo ma kungiyar su, dan wannan abun ba k'aramun tab'a Kadar su zeyi ba domin sun san dole sai duniya taji wannan abu. Haka suka gama tattaunawa yayin da suka tsaida wanda zaiyi shari'ar a gobe.
Haka Alhaji Kamal ya sake kunna masu vedion kowa ya gani, tabbas sunji kunyar wannan abu, babu abinda yafi ciwo irin na Malan Sani, shekaru da yawa an kulleshi ba akan hakkinsa ba. Da haka taron ya tashi.
*** ****
Rafeek agaskiya yanzu kam naji dad'in wannan shari'ar daka tado, koba komai silar shari'ar Naseer ta jawo za'a tona asirin mutane da yawa, kamar yanda mutane suka aminta da wannan kotu suna fad'in irin adalcinta ashe dama a cikin duhu muke, Allah ya k'ara tona asirin munafukai.
Rafeek yace amin Baffa, ai yau jinake kamar nayi kuka saboda farin ciki, hakika Allah yana son bayinsa, kuma shi maji rokone, insha Allahu zuwa gobe kowa zaisan matsayinsa.
Ummansu tace nikam ko ba'ayi komai ba zuciyata ta wanke, koba komai duniya tasan waye ya kashe mani Naseer, kuma sun kunyata sai fatan Allah ya kara tona asirinsu. Rafeek yace amin Umma, bara na wuce dama ina wajen aiki naga kiran ku. Baffa yace Allah ya tsare ka. Yace amin.
**** ****
Ya Allah wannan wace irin bak'ar rana ce haka, yanzu Alhaji ne 'yan sanda suka kama har wajen aikinsa saboda tozarci, ina zansa kaina yau, da wane ido zan kalli K'awayena da sauran mutane? Zubewa Raheena tayi jikinta tana kuka.
Dafata Momy tayi tana fad'in wallahi dole kiyi kuka Raheena, mu kam Alhaji ya gama cutar mu, taya zamu iya rayuwa cikin wannan tashin hankalin, ashe dama halin da yake aikatawa kenan ab'oye bamu sani ba? Duk tarin dukiyar nan daya tara mana ta hanyar haram ya tara ta? Kalli wannan uban gida da muke ciki, haba ashe shiyasa Alhaji Marusa ya sayar masa da gidan ashe duk jirgi d'aya ne ya d'ebosu, yanzu gashinan sun kaishi sun baro, meyafi wannan kunya ace kana zaune saman kujera kana shirin yankema wani hukunci sai kuma a nunoka kana cikin masu laifin.
Tashi Raheena tayi tana fad'in wallahi Momy nayi dana sanin shiga yanar gizo ayau, domin ina hawa nayi bakin gani, a group d'in da nake kawai naga an turo hoton Dady a kotu hada vedion shi lokacin daya sulale a kotun, dan bala'i hatta da shedar da aka kunna akotu wallahi an samu wad'an da suka d'auketa, ina hawa face book ma abinda nagani kenan, duk wata kafa ta yanar gizo idan kika shiga maganar su Dady akeyi.
Goge ido Momy tayi tana fad'in bamu da bakin magana kam, abinda nakeso da ke kawai ki kashe wayarki, idan da hali ma kawai ki kulle account d'inki sannan ki karya layin ki hakan zai fi maki kwanciyar hankali, idan yaso lambobin da kike so ki barsu akan wayar dan nima haka zanyi wallahi Raheena bazan iya wannan abun kunyar ba, dole mubar garin nan, gara na koma asalina dama nayi gini na a kano ina shirin zuba 'yan haya wallahi na fasa garin zamu bari.
Raheena tace ya zamuyi da wannan gidan kuma? Waro ido Momy tayi tana fad'in ke yanzu har maganar wata kadara ta Alhaji kikeyi, to ina tabbatar maki sai kotu ta kwace komai nashi dan sai ya biya diyar mutanan da ya kashe, kayan d'akin ki ma zansa azo goben nan a tafi dasu kano, kije ki fara had'a kaya ki da duk wasu abubuwa masu muhimmanci dan wallahi idan masu bincike sukazo bazasu bari mu d'auki komai ba.
Kuka Raheena tasa tana fad'in shikenan yanzu kam nasan Ra'eez yafi k'arfina, dan ko rana aka samana sai ya fasa dan yanzu Dady yayi mana bakin fenti. Momy tace ki kwantar da hankalin ki sai kiga kuma yaji tausayinki tunda yasan ba laifinki bane, dole muje kotu domin ayi komai agaban mu, tashi ki kunna mana Tv nasan yanzu zasu nuna komai.
Aikuwa Raheena tana kunnawa sai ga masu labarin k'arfe takwas na dare. Kowace tasha ka kunna ko gidan radio duk maganar d'aya ce, nuno su Alhaji Marusa ne ya k'ara d'aga masu hankali, shikenan yanzu an had'a kan masu laifi dole a yanke hukunci.
Daga k'arshen labaran aka tabbatar da gobe talata k'arfe goma na safe za'a zartar da hukunci a babbar kotu. Kashewa Momy tayi tana sakin kuka. Masu aikin gidan ne suka shigo jiki asanyaye suna masu jaje.
Tashi Momy tayi tana fad'in bazan bari a cuce ku ba, domin nasan gidan nan ya kusa haramta agaremu, dan haka zan sallame ku zuwa gobe kowa ya tafi ina rokon ku daku yafe mana, bara naje d'akin Alhaji dole nayi maku sallama mai tsoka.
Farin ciki suka kamayi jin abinda Momy tace. Fitowa tayi da wata k'atuwar jaka wadda kud'i ne kawai aciki, haka tasa suka d'auko bakar leda ta bama kowa kud'i masu yawa, kayan Alhaji ta d'auko duk ta raba ma mazan masu aikin, sannan ta d'ebo wasu daga cikin nata dana Raheena ta bama matan, haka sukayi ta godiya kowa ya nufi wajen kwanansa kafin gobe.
Ciki suka shiga suka fara had'a kaya yayin da tayima wani d'an uwanta waya da yake Lagos akan ya taho da motar d'aukar kaya tunda asubar fari zai kai mata kano kafin a kammala shari'ar sai su tafi.
**** ***
Hawaye ne kawai yake zubo ma Ammi bayan data gama kallon labarai, mai aikinta da take gefenta sai hakuri take bata. Ammi tace dole nayi kuka Inno, Alhaji ya gama zalunta ta, ya b'ata mani tarbiyar yarona, ya lalata mani mahaifa, gashi daga k'arshe ya sani jin kunyar duniya, na farko an yanke ma Fawwaz hukuncin kisa, na biyu an kama Alhaji shima nasan hukuncin kisa ne domin rayuka ya kashe, shikenan na tashi a babu, wannan gidan dole na barshi koda bazai shiga cikin diyar da zai biya ba wallahi bazan zauna aciki ba domin komai na ciki haram ne, sisinsa bazan d'auka ba, haka zan tafi garin mu gara idan naje Iyayena su siya mani sutura da kud'insu amma babu abinda zan iya cigaba da amfani dashi domin duk haramun ne.
Inno tace kiyi hakuri Hajiya ai bakisan haramun bane sai yanzu kinga duk abinda kike dashi ya halatta agareki sai idan ya sake baki wani abun ne.
Murmushin takaici Ammi tayi tana fad'in Inno bakinsa girman haram ba, matuk'ar ka kasance kana cin haram kuma kasan haram ne wallahi Allah bazai barka ba agobe kiyama, tabbas ada bansan bakin halin Alhaji ba, nasan dai ma'aikaci ne kuma albashinsa muke ci, amma zuwa yanzu na fahimci ya cakud'a kud'insa da haram domin harkar shigo da haramtattun kaya sukeyi, ban tab'a sanin haka ba sai jiya da nayi bincike a d'akinsa naga wasu takardu, kinga kuwa idan har nacigaba da amfani da kayanshi nima nashiga layin halaka, dan haka ki barni, idan kina son kayana gasu can kije ki had'a dan sallamarki zanyi, sauran kud'ina na banki ma asusun marayu zan kaisu, idan baki son kayan zan mik'asu gidan marayu sadaka.
Inno tace tunda sadaka kika bani ai ba haram bane zan d'ebi wasu sai akai sauran gidan marayu bazan had'e duka ba, gaskiya wannan abu beyi dad'i ba, amma ai zakije kotun gobe ko? Ammi tace badan inaso na mik'a mukullin gidan nan a gareshi ba kuma ya furta mani saki da babu abinda zai sa rana ta fito ta sameni a Lagos, amma dole naje nayi sallama da Fawwaz kuma na amshi sakina.
Inno tace gaskiya zanji babu dad'i, amma Allah yasa haka yafi alkhairi, yama sunan garin ku? Ammi tace Sokoto. Inno tace ikon Allah ashe fa kin tab'a fad'amin wallahi na manta, ai gaskiya garin ku akwai nisa, amma idan da rai wata rana zaki ganni. Ammi tace Allah yasa, kira mani masu gadi su duka.
*** ****
Umar yanzu ya zamuyi, ni wallahi na manta da wannan maganar, tunda na haye saman kujerar Oga shikenan na manta dashi da abubuwan da mukayi, sai cikin satin nan Alhaji Barau yake fad'a mani an fara bincike akan shari'ar da akayi shekarun baya.
Miyau Umar ya had'iye yana fad'in Adebayo wannan shi ake kira ga k'oshi ga kwanan yunwa, muna farin ciki shekaru sun ja an manta da komai ashe abu be wuce ba, kana kallon dai yanda aka kama Alkali a kotu, su Alhaji kuwa har gida aka bisu, taya kake tunanin abun bazai zo kan mu ba, koda ba'a kamma mu yanzu ba idan akaje shari'a gobe dole bincike yazo kan mu.
Adebayo yace wallahi tsoro nakeji, da