Advertisements
Chapter 28 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   28 / 54

81K to 84K   out of 160.3K words

Wani abu ya had'iye yana fad'in Halima kuka dai, shiyasa fa bana so kina zuwa domin kina raunana mani zuciya, bayan kin tafi kuma ina jinyar zuciyata, ina tsoron kada hakan ya fara tab'a lafiyata, idan bazaki rik'a dakewa ba gara ki zauna agida sai murik'a gaisawa ta waya.



Hannu tasa ta goge idonta tana fad'in na dena, gaishesa ta farayi. Murmushi yayi yana fad'in lafiya lau ya gidan? Bazan tambayi komai ba domin nasan ina da masu kula da ku, sannan idanuwana sun ga abinda nake son gani, kuma naji dad'i a zuciyata.



Ra'eez yace Kawu Abbah yace idan nazo zaku gaisa bara na kirashi. Malan Sani yace Allah sarki ya iyalan nashi? Ra'eez yace lafiya lau. Waya ya d'auka ya kira Abbah.



Bayan sun gaisa ya mik'ama Malan Sani. Gaisawa sukayi yana tambayarsa rayuwa. Malan Sani yace lafiya lau Alhaji, ai rayuwar gidan yari tabi jikina, nasa araina nan d'in Muhallina ne, domin ina son naga ranar da Allah zai kawo mani k'arshen zama acikinta, ina son nayi wata rayuwar hakan yasa nasa juriya araina dan gudun damuwa ta kassarani.



Alhaji Mansur yace wannan haka yake, kuma naji dad'i sosai, dama abinda nake son na fad'a maka kenan, domin acikin satin nan bani da tunani sai na yanda zamu maido da shari'ar ku baya, domin kwanakin baya na had'u da tsohon ma'aikacin Alhaji Abubakar, dan yanzu a Kano yake aiki shima ya zama babba, Allah ne yasa zamu had'u har labari ya kawo muka zo maganar Alhaji Maiwada, ya tabbatar mani a yanzu baya tsoron kowa, kuma duk lokacin da muke buk'atar taimakonsa ashirye yake, abokinsa da aka canza ma wajen aiki Moses shi ya mutu a had'arin mota, amma yace shi zai zo ya bada sheda.


Jinjina kai Malan Sani yayi yana fad'in wallahi nima kwanan nan mafarkin da nake yawanyi kenan, wai an sake shari'a kuma munyi nasara, ina nan ina fad'ama Allah nasan kuma zai shige mana gaba, ko ban fita a nan ba matuk'ar asirin azzalumancen zai tonu burina ya gama cika.



Alhaji Mansur yace zaka fita, matuk'ar asirin su ya tonu dole a wanke ka, dan haka kacigaba da daurewa komai zai zo k'arshe. Malan Sani yace insha Allah. Sallama sukayi ya kashe wayar.



Sai da yaci abincin da suka kawo masa suna ta fira, bayan ya gama Ra'eez ya bashi ledar da suka kawo masa mai d'auke da kayan bukata, kud'i ya bashi yana fad'in zamuje wajen Ummu.



Godiya Malan Sani yayi masa yana fad'in agaisheta. Tashi sukayi kowa jikinsa a sanyaye, duk dauriya irin ta Malan Sani sai da kwalla ta cika masa ido, azuwansu sai yaji damuwarsa ta yaye, yanaji kamar a gida suke zaune, amma yanzu da zasu tafi sai yaji duk babu dad'i.



Mama kuwa saurin fita tayi tana kuka, bayanta Rumaisa tabi itama kukan takeyi, kama Abdallah Madu yayi sukayi hanyar fita shima jikinsa a sanyaye. Kallon Malan Sani Abdallah yayi yana fad'in Baba sai yaushe zakazo gidan mu? Saurin juya baya Malan Sani yayi hawayen da yake b'oyewa suka zubo masa, yana jin muryar Abdallah amma ya kasa magana, ganin haka yasa Madu yayi saurin jansa sukayi waje.



Hannu Ra'eez yasa ya goge idonshi kafin ya dafa Malan Sani yana fad'in Kawu zamu tafi sai mun sake dawowa. Ajiyar zuciya ya saki yana fad'in Ra'eez kada ka sake kawo su, idan zaka zo kazo kai kad'ai dan Allah.


Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in insha Allah. Tare suka fito suka k'arasa wajen ma'aikacin. Kallonsu yayi cike da tausayi yana fad'in zaku koma? Ra'eez yace magriba ta kusa, mungode sosai.



Hannu yasa ya ciro kud'i ya mik'a masa yana sake masa godiya. Amsa yayi yana fad'i ai babu komai nima nagode. Sallama yayi masu Malan Sani ya d'auki kayanshi ko juyowa beyi ba yayi gaba yana kuka.



A mota gaba d'ayansu shiru sukayi kowa yana jimami, Abdallah kanshi da yake yaro shiru yayi ya kwanta jikin Rumaisa yana goge mata fuskarta, har suka isa asibiti babu mai magana.



Sai da Ra'eez yayi ma Dr. Sadeek waya, dan yanzu ya zama babba baya aiki a asibiti sai dai sune masu kula da wajen, hakan yasa ya damk'a Ummu a hannun babban likitan da yake wajen duk da idan yashigo yana kawo mata ziyara.



Bayan sun gama wayar suka fito suka nufi d'akin da Ummu take. A zaune suka isketa tana sanye da hijabi ta kurama tv ido wadda ake shirin addu'ar safe da marece, wata dattijuwa ce zaune a gefe da alama itace take kula da ita.



Idan kaga Ummu sai ka d'auka mai hankali ce, domin komai fess a jikinta, fuskarta ta nuna alamun manyanta kad'an saboda tana samun kulawa ga cima mai kyau sai fatar ta tayi kyau sosai, sam yanzu bata komai sai dai wani lokacin idan ta fara kuka tana kiran Abbun Ra'eez sai ta kai wani lokaci ta nayi, wani lokacin dole sai anyi mata allurar bacci kafin suke samun saukinta.



Wani lokacin kuma sai tayi sati bata nuna alamun hauka ba, magana ma batayi sai dai mai kula da ita ta rik'a kula da abinda take so tayi mata, dan yanzu kam ta zama shiru-shiru, idanuwanta duk sun canza kala sun rage girma saboda kuka.



Da sallama suka shiga d'akin, matar da take zaune tayi saurin amsawa ta mik'e tana masu sannu da zuwa. Har suka shigo Ummu bata kalli inda suke ba, yanda kasan bata cikin d'akin dan yau 'yan miskilancin take.



Bayan sun gaisa da matar ta basu waje tayi waje. Ido Ra'eez ya tsura ma Ummu kwalla tana cikowa a idonshi, kusa da ita ya matsa yana mai kamo hannunta.



Shiru tayi bata kulashi ba. Zama yayi ya jawota hawaye suna gangarowa a fuskarshi. Mama dasu Rumaisa duk sai sukaji wani sabon kuka, a hankali Ra'eez yace Ummu kiyi hak'uri aiki ne yamun yawa shiyasa banzo ba amma bazan sake ba.



Tamkar bada ita yayi magana ba haka ta kyaleshi idanuwanta suna kan Tv tamkar mai fahimtar abinda akeyi. Matsowa Mama tayi ta kamo Ra'eez tana fad'in kayi shiru mu bata lokaci zatayi magana idan ka tursasata kanta zai iya d'aukar zafi.



Zama sukayi kowa da abinda yake tunani, Ra'eez kam yana rik'e da hannun Ummu yaki sakinta. Can yayi saurin kallonta yana fad'in Ummu jiya fa nayi mafarkin Abbu ina kwance a kan gadonshi har... Zumbur tayi tana kallonshi, kamoshi tayi tana fad'in Abbun ka? Nima jiya yazo mun anan ma ya kwana, hannu tasa tana buga gadon da take zaune.


Murmushi sukayi dukansu, Ra'eez yace Ummu meyasa baki tsaidashi har nazo ba? Dariya tayi tana tafa hannu tace ai yau idan yazo igiya zansa na d'aureshi, jiya nace ya zauna tare dani shine yamun wayau ya gudu, amma ka barshi yau sai na d'aureshi kaga bazai sake barina ba ko.


Murmushi Ra'eez yayi ya gyara zama tare da d'ora kanshi saman cinyarta yana fad'in sosai ma Ummu, zan kawo maki igiya ki d'aure manashi kullum murik'a ganinshi.



Nan fa Ummu ta saki jiki da Ra'eez sukayi ta firar Abbu, haka ya biye mata yana taya ta shirme duk dan suyi labari, Mama da Madu kuka kawai sukeyi a b'oye ganin yanda Uwa da 'Danta suke fira ta marasa hankali.


Cikin firar sai dai Ra'eez yasa hannu ya goge hawayen da suke zubo masa saboda firar tana sakashi shiga cikin yanayi, ita ko Ummu dariya kawai takeyi suna firar Abbu.



Da haka Mama ta zuba mata abinci, amsa Ra'eez yayi suna fira yana bata abaki, itama haka tarik'a bashi, duk da akoshe yake haka yake amsa yanaci yana hawaye.



Bayan sun gama tacigaba da bashi labarin shirmenta. Har akayi sallah suka fita shida Madu da kyar ma ta yarda suka tafi. Bayan sun dawo ta jawo Ra'eez tana fad'in kaima yau anan zaka kwana idan Abbunka yazo sai muyi fira muci abinci gaba d'aya.



Murmushi Ra'eez yayi ya haye saman gadon yana fad'in tabbas anan zan kwana Ummu muga Abbu atare. Wayarsa ce tayi k'ara, yana dubawa yaga Alhaji Barau ne, tsaki yayi kafin ya d'auka.



Bayan sun gaisa ya fad'a masa idan anyi sallar isha'i yana nemansa muhummiyar magana ce. Ra'eez yace shikenan sai nazo, kashe wayar yayi yana tsaki.



Mama ce ta tambayeshi wanda ya kira? 'Bata fuska yayi yana fad'in Alhaji Barau ne wai yana... K'arar da Ummu tasa ne yasashi saurin yin shiru. Kular abincin da take kusa da ita tayi wurgi da ita tana fad'in sai na kashe shi, wallahi sai na kashe shi, Abbunka baya sonshi, ya takura ma Abbunka.



Saurin tashi Ra'eez yayi yana kok'arin rik'eta amma ya kasa, da sauri Madu ya fita domin kiran ma'aikatan, kafin suzo duk ta hargitse wajen tana ihu, hannun Ra'eez kuwa duk taji masa ciwo.



Allura akayi mata cikin mintuna biyu bacci ya d'auketa. Zama Ra'eez yayi tare da sakin wani irin kuka mai cin rai. Kamoshi Madu yayi yana lallashinsa.



Tashi Mama tayi tana fad'in mutafi tunda ta samu bacci, Ra'eez kada ka sake yin maganar wad'an nan azzaluman agabanta, nima mantawa nayi har na tambayeka.


Kai ya d'aga ya tashi yana mai sake kallon Ummunsa, sosai ya k'ara jin kiyayyar su Alhaji Barau. Haka yayi ma ma'aikatan alkhairi da wannan matar kafin suka tafi, a waya ya fad'ama Dr. Saddek halin da take ciki.


Dr.. Sadeek yace insha Allahu Ummunka ta kusa samun sauki, tunda har take jin haushin mutanan da take zargi tabbas alamun sauki sun fara bayyana, gobe zan shiga dan a d'auki hoton kwakwalwarta.


Godiya Ra'eez yayi mashi ya kashe wayar. Mama tace idan ka ajemu sai kaje kaji kiran da yake maka. Ra'eez yace bazanje ba sai dai mu had'u a ofis gobe. Mama tace a'a, idan bakaje ba zaiyi tunanin wani abu.


A fusace Ra'eez yace wallahi bazanje ba, saboda sunanshi kad'ai komai na Ummu ya hargitse, muna firar mu daga jin sunanshi komai ya tsaya, idan naje wallahi zan iya yin wani abu da zaisa na b'ata masa.


Jinjina kai Mama tayi tace shikenan ka fad'a masa wani uzuri to. Kai ya d'aga yana goge idonshi.


Bayan ya ajesu Mama tace yashigo yaci abincin dare. Ra'eez yace akoshe nake ai munci a asibiti gida zan tafi kaina yana mun ciwo. Mama tace idan kaje kasha magani, kuma bana so kasa wata damuwa aranka wani ciwon ya shige ka. Kai ya d'aga yana masu sai da safe.


Har yashiga mota Rumaisa ta fito, jiki a sanyaye ta k'arasa bakin motar. Idanuwa ya tsura mata ganin yanda take kuka. Fitowa yayi ya hard'e hannuwansa a kirji yana kallonta.



Kasa magana tayi sai kawai ta juya, da sauri ya kamo hannunta ya maidota baya, sakinta yayi kafin yace ta goge fuskarta.


Hannu tasa tana goge fuskarta wasu hawayen suna zubowa. Murmushin k'arfin hali yayi yana fad'in kina so na kasa bacci ne? Kai ta girgiza.



Ra'eez yace to bana son kukan ki, idan naje gida zan kiraki kimun fira mai dad'i da zata sakani bacci kinji? Kai ta d'aga tana murmushi.


Ra'eez yace da kyau Pretty nah, yanzu kishiga gida sai na kiraki, kuma kici abinci kinji? Kai tazo d'agawa yayi saurin fad'in magana zaki mun Malama.


Dariya tasa tana rufe fuskarta. Shima murmushi yayi yana jin sauki a zuciyarsa. Kallon shi tayi tana fad'in kayi tuki a hankali Yaya. Murmushi yayi yashige mota yana fad'in zanyi amma sai kince kina sona idan ba haka ba a 180 zanje gida.



Zaro ido tayi tana fad'in kai Yaya. Gira ya d'aga mata yana fad'in sosai kuwa. Murmushi tayi tace to ka rufe idonka zan fad'a. Ra'eez yace Allah beyini makaho ba kuma bazan rufe ba, idan bazaki fad'a mun ba zanje na saurari na wasu Mat... I love you!


Kafin ya kallota sai kurar gudunta ya iske tayi cikin gida. Besan lokacin daya saki wata dariya ba. Baki ya rik'e yana fad'in lallai ma Pretty, anya itace ma tayi maganar? Lumshe ido yayi yana mai-maita abinda ta fad'a.



Rufe motar yayi ya nufi gida, shi kad'ai sai murmushi yake saki, a hankali ya furta lallai soyayya tana da dad'i, kuma tana taimako sosai, kafin minti goma zuciyata zafi take ina cikin damuwa, amma cikin mintuna biyar na samu canji. Allah nagode maka da ka saka soyayya a zukatan mu.



K'aran wayarsa ce ta katse mashi abinda yakeyi, saurin d'auka yayi yana fad'in Abbah ina hanyar gida dana k'arasa zan kira ka. Abbah yace shikenan amma ka kirani fa. Kashe wayar yayi.



K'ara gudun motar yayi dan yasan tunda Abbah yace zeyi magana dashi to ba k'aramun abu bane, yaso ma tun d'azu ya kirashi a ofis to yasan Abbah baya son magana a waje shiyasa bai kirashi ba.



Ur's.
Nabeelert Lady🖋[3/10, 8:39 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*



2⃣7⃣


Cikin sauri ya kammala abubuwan da ya saba kafin ya kwanta, kallon agogo yayi yaga k'arfe 8:30, wayarsa ya jawo yayi kiran Abbah kirjinsa yana bugawa, tun lokacin da yaji yana son magana dashi yake jin fad'uwar gaba.


Bayan sun gaisa Alhaji Mansur yace Ra'eez ya Ummun taka da jiki? Ra'eez yace da sauki sosai Abbah, sai dai sunan Alhaji Barau da Mama ta ambata agabanta ya jefata cikin tashin hankali har sai da akayi mata allurar bacci kafin aka samu kanta.


Jinjina kai Abbah yayi yana fad'in da alamu sauki ya fara zuwa. Ra'eez yace haka Dr. Saddek ma ya fad'a, yace zai shigo asibitin gobe domin suyi mata awo.


Abbah yace to Allah yasa muji alkhairi. Ra'eez yace amin Abbah. Gyaran murya Abbah yayi yana fad'in Ra'eez ya kamata a birkito da abinda ya faru shekaru 11 da suka wuce.


Ajiyar zuciya Ra'eez ya saki jin abinda Abbah ya fad'a. Ya naji kayi shiru Ra'eez? Abbah ya fad'a jiki a sanyaye. Murmushin yake Ra'eez yayi yana fad'in bakomai Abbah, kawai maganar ce naji tazo mun daga sama.


Abbah yace ya kamata kasa wannan maganar aranka, ka tuna akowane lokaci zamu iya maidota domin bazamu tab'a barin jinin Alhaji ya tafi abanza ba, idan kaga haka ta faru to bamu da cikakkar hujjar da zamu gabatar ma kotu.



Ra'eez yace nima wannan abun yana damuna Abbah, wani lokacin ina ganin kamar bamu da shedar da zamu iya mik'a su Alhaji Barau kotu, duk wata hujja sune suke da ita, koda kotun duniya zamu kaisu sune zasuyi nasara akan mu.



Abbah yace kada kayi saurin sarewa Ra'eez, mai gaskiya Allah baya tab'ar dashi, ko alhakin Malan Sani ya isa yasa a wannan karon muyi nasara, domin zalunci baya d'orewa.


Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in insha Allahu muna kammala shari'ar da zamuyi ranar litinin zan fara shirya yanda tamu zata kasance, zanje na lalubo kundin shari'ar su Abbu domin na fara dubashi.


Abbah yace haka nake son ji Ra'eez, ai fad'uwar gaba asarar namiji, kasa aranka zamuyi nasara. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in insha Allahu Abbah.


Abbah yace sai kuma maganar waccan motar da take ajiye a gareji, badan kace kana sonta ba da ansayar da ita da ayita ajiyarta bata komai.


Ra'eez yace dan Allah Abbah abarta, inaso idan nazo Kano na kaita ayi mata seti dan ita nake son nacigaba da hawa. Murmushi Abbah yayi yana fad'in haba Ra'eez, ai zamaninta yawuce, idan aka ga kana hawanta sai arik'a maka kallon matsolo.


Dariya Ra'eez yasa yana fad'in Allah Abbah sai na hauta kona 'yan watanni ne, tun lokacin da Abbu ya siyeta nake cewa idan na girma zai koya mani ita, kuma yace zai ajeta har na girma a cikinta zai fara koya mani mota, kaga tunda ban fara koyo acikinta ba ai gara na hauta.


Abbah yace wannan haka yake, bakomai duk lokacin da kazo sai ka kaita a dubata, amma maganar shari'ar da zakuyi ina fatan babu wata matsala? Ra'eez yace akwai Abbah, amma insha Allahu komai zaizo da sauki, idan muka kammala zan baka labari. Abbah yace shikenan Allah ya bada sa'a. Ra'eez yace amin. Sallama yayi mashi ya kashe wayar.


Kwanciya yayi yana kallon saman d'akin, tunanin ta yanda zai nemo kundin shari'arsu Abbu kawai yakeyi, dole ya k'ulla alak'a da ma'aikacin d'akin ajiyar kundi.


K'arar wayarsa ce ta maido dashi daga tunanin da yakeyi. Raheena ya gani, d'an tsaki yayi kafin ya d'auki wayar.


Sallama tayi masa, bayan ya amsa ta gaishe shi tana tambayarsa gajiyar aiki. Ra'eez yace lafiya lau. Raheena tace d'azu Dady yake fad'amun zaka zo ina ta murna sai kuma yace wai wani uzuri ya hana ka zuwa duk banji dad'i ba ko abinci kasa ci nayi, ta fad'a cike da shagwab'a.


Murmushi yayi jin abinda ta fad'a. Raheena tace Allah baka san irin son da nake maka bane, saboda kai duk wasu abubuwa da nakeyi marasa kyau na dena, yanzu tsakanina da masu mana aiki sai alkhairi da girmamawa, abinci kuwa tuni na fara iyawa duk saboda kai.



Ra'eez yace haka akeso ai, kinga har abada bazaki tab'a mantawa dani ba, domin ta sila ta kin samu rayuwa mai kyau.



Murmushi tayi tana fad'in sosai kuwa, kaga nima zan zamo Uwa ta gari, zan

28 / 54