Advertisements
Chapter 51 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   51 / 54

150K to 153K   out of 160.3K words

nasan da wannan abun bazan zo aiki yau ba, gashi aiki ya rik'emu mun kai har dare kada mu fita akama mu, da ace ina da mai a motata daga nan hanyar garin mu zan nemo gara na kwana a ahanya tunda ATM d'ina yana mota bani da matsala, to yanzu idan na tafi an kulle gidan Mai sai na masu jarka kuma ina tsoron na siya da yawa ya bani matsala.


Umar yace kasan abinda za'ayi? Tunda sai gobe k'arfe goma za'a shiga kotu kuma sai an fara shari'a sannan bincike yazo kanmu kawai yau mu kwana cikin shiri, gobe tunda asuba kowa ya kama gabanshi, lokacin da za'a neme mu nasan munyi nisa, dan haka kawai mu tafi. Adebayo yace haka za'ayi Umar kulle ofis d'in mu tafi.


Cak suka tsaya ganin 'yan sanda a gabansu. Tsoro ne ya kamasu gaba d'aya, babu b'ata lokaci suka kamasu suka tafi, motarsu ma sai wasu 'yan sandan ne suka tukasu.


*** ***


Kafin gari ya waye sai da su Hamza suka had'a kan duk wasu masu laifi, sai dai kowa da wajenshi babu wanda yasan an kamo wani sai wad'an da aka nuna a tv, hatta dasu Kwamishna da Dr Aliyu Sani duk an kamasu, sai dai shi kwamishna basu kawoshi ofishinsu ba wani waje suka ajeshi saboda girmamawa.


**** ****

*Tuesday 19/12/2019*

*High court Lagos*


Fad'in cikar da kotun tayi ba abu bane me yuwuwa, domin duk wanda yasan labarin wannan shari'a yasan dole tayi mutane, ko yawan masu d'aukar rahoto ya isa ya cika rabin kotun.


Gaba d'aya ma'aikatan kotun k'arfe bakwai suka halarci kotu saboda dole akwai tsare-tsare, manyan jami'an tsaro ne a harabar kotun su duka suna d'auke da manyan makamai, duk wanda zai shiga kotun dole sai an bincikeshi da abun duba mutane, hanyar maza daban ta mata da ban, sosai abun ya k'ayatar domin sun shirya ma shari'ar saboda sun san ana iya samun wani tashin hankali musamman da shari'ar ta kasance ta manyan mutane.


Lokacin da kotun ta cika dole sai hakuri sauran mutanan sukayi domin jami'an tsaro sun tare hanyar shiga sai dai masu son jin kwakwaf suka tsaya a harabar kotun.


Masu laifi dama da wuri aka kawosu kotun kowa da inda aka ajeshi, kana shiga cikin kotun zaka iske Alkalai ukku zaune asama sai b'angare guda na manyan mutane, yayin da d'ayan b'angaren lauyoyi suke zaune, sai wajen da su Magatakarda suke a zaune, daga wajen zaman mutane kuma duk akwai jami'ai ko wace hanya suna tsaro.


Tsit kake jin kotun dan kowa yasan yau babu wasa, iya mutanan da suke zaune agaba kad'ai ya isa yasa mutum ya natsu, ga kuma jami'ai suna zagaye da bindigu.


Bayan da kowa ya natsu aka umarci da ashigo dasu Alhaji Barau. Idanuwa kawai mutane suka zuba dan gangar jikinsu ta kasa motsi bare ta jawo hayaniya gudun kada suma suyi laifi.


Gaba d'ayansu kawunansu a k'asa suka shigo kotun, Alhaji Barau da aka kamashi yana sanye da kayan aiki zuwa yanzu babu su ajikinshi dan an bashi wata jallabiya yasaka. Haka suka jeru a gefe suna sunnar da kai.


Tashi Magatakarda yayi domin ya karanto shari'ar....


*A yau talata 19/12/2019 wannan kotu mai albarka zata cigaba da sauraron shari'ar da aka fara jiya litinin 18/12/2019, an tsaya a inda Brr. Ra'eez ya gabatar da shedar data tabbatar da wad'an da suka had'a baki wajen kashe Naseer Sambo Jarmai.*


*Sai shari'a ta biyu itace ta Iyalan Malan Sani, inda suke rokon wannan kotu data sake shari'ar da aka gabatar shekaru sha biyu da suka wuce akan mutuwar tsohon shugaban kwastam Alhaji Hamza Maiwada a wannan kotun domin an samu wasu manyan shedu da zasu tabbatar ma kotu ba Malan Sani bane ya aikata laifin da aka yanke masa hukunci akai.*


Risnawa yayi ya mik'ama d'aya daga cikin Alkalan da suke zaune. Bayan da ya gama dubawa ya mik'ama sauran. Na tsakiyar daya kasance shugaba shine ya bama Ra'eez izinin ya cigaba da gabatar da shari'a a inda ya tsaya jiya.



Tashi Ra'eez yayi yana risnawa, ganin bakin fuska yasa ya fara da gabatar da kanshi. Gyara riga yayi yana fad'in ya Mai shari'a ni sunana *BARRISTER RA'EEZ HAMZA MAIWADA, 'DAH GA MARIGAYI SHUGABAN KWASTAM NA LAGOS WATO ALHAJI HAMZA MAIWADA.*



Nine wanda yake kare wad'an da suke k'arar shari'a ta farko data biyu.


Gaba d'ayansu suka d'ago cikin firgici suna kallon Ra'eez, Alhaji Barau yafi kowa girgiza da abinda kunnuwanshi sukaji, tabbas sai yanzu ya gama gano dawa Ra'eez yake kama. Runtse ido yayi yana jin wani irin tashin hankali.


Mutane kuwa duk yanda suka natsu jin abinda Ra'eez ya fad'a dole tasa aka fara kus-kus, domin abun ya basu mamaki.


Raheena da Momy kuwa suman zaune sukayi. Runtse ido Raheena tayi hawaye suna zubo mata, ayanzu kam tasan Ra'eez ya girmema tunanin ta, dama fansa yazo d'auka kenan. Saman cinyar Momy ta kwanta tana kuka. Bubbuga teburin da akayi ne yasa kowa ya shiga hankalinsa.


Gyara tsayuwa Ra'eez yayi yana fad'in, kamar yanda aka gabatar da shedar vedion da aka shirya yanda za'a kashe Naseer a jiya nasan wannan shedar ta tabbatar da wad'an da suka shirya kashe Naseer domin fuskokinsu sun fito yayin da akaji muryoyinsu suna ambatar sunan juna.


Ina so kotu ta bani dama domin na yima mutanan da suke gabanta tambayoyi.... Kotu ta baka dama.


Matsowa yayi kusa da masu laifin yana sakin murmushi.


Alhaji M. Sanda zan fara ta kan ka, duk da fuskar ka bata bayyana a cikin vedion ba amma muryarka ta sheda kai ne, sannan mutane biyu sun tabbatar da cewar kai ne ka bada umarnin aka kashe Naseer, domin duk sauran goya maka baya kawai sukayi, kotu zataso taji daga bakin ka yanda komai ya kasance.


Alhaji M. Sanda... Kanshi a k'asa yace maganar gaskiya duk abinda akaji a ciki haka yake, sai dai kuma mun fad'a ne kawai amma ba mune muka aikata ba, domin mun aje akan zamusa ayi sai kuma aka samu wani ya rigamu aikatawa, dan haka ni bansa a kashe kowa ba.


Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in Alhaji Barau me zaka iya cewa agame da wannan vedion?


Alhaji Barau... Haka maganar take, kamar yanda Alhaji M. Sanda ya fad'a tabbas mun shirya yanda za'a kashe Naseer saboda a b'oye abinda Fawwaz ya aikata sai kuma wani ya riga mu.


Murmushi Ra'eez yayi kafin ya matsa gaba ya tambayi Alhaji Marusa da Mr. Kallah, sai dai duk amsar d'ayace. Murmushi yayi dama yasan za'ayi haka shi kuma yafiso su k'aryata kafin ya tabbatar masu.


Juyowa yayi yana fad'in ya mai shari'a inaso kotu ta bani dama domin na kira mutumin da akayi hayarshi ya gabatar da wannan kisa.... Kotu ta baka dama.


Kallon k'ofa kawai suke yayin da zufa ta fara keto masu, ji suke kamar su nutse, duk da basu san wanda zai shigo ba amma sun tsorata da murmushin kan fuskar Ra'eez.


Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:41 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*



4⃣9⃣



Hannu Mr. Kallah ya d'ora akai ganin anshigo da Lucky, bayansa kuma Dr. Aliyu Sani ne sai Kwamishna Bello kabir wanda duk kunya ta hanashi kallon kowa. Mamaki ne ya cika mutane ganin Kwamishnan 'yan sanda a jerin masu laifi, sai wad'an da suka san Dr. Aliyu suma sunyi mamakin ganinshi.


Lucky ne ya fara fitowa zuwa wajen da ake tsayawa. Matsowa Ra'eez yayi yana fad'in kotu zata so taji sunanka da kuma san'ar ka.


Sunana Adekulle Isnewa, amma anfi kirana da Lucky, sana'ata itace sata sai kuma ana d'aukata nayi aiki a biyani.


Ra'eez... Kamar wane irin aiki kenan?


Lucky... Kamar idan wani yana son ajama wani kunne ko kuma a shekeshi to ina irin wannan aikin a biya ni.


Ra'eez... Shin Lucky ko kasan wad'an nan mutanan?


Lucky... Kallonsu yayi yana sakin murmushi, juyowa yayi yana fad'in sosai kuwa, domin tunda nake harka da mutane ban tab'a harkar da nake jin dad'inta ba kamar harka dasu, zan iya cewa sune Ubayen gidana domin mun dad'e atare musamman Alhaji Marusa dan shine ya nuna masu ni.


Ra'eez... Ko zaka iya fad'ama kotu irin aiyukan da suka saka kayi masu.


Lucky... Gaskiya sun sani aiyuka da yawa, wasu zan iya tunawa wasu kuma bazan iya tunawa ba, dansu basa jin tsoron a kashe kowa matuk'ar zasu samu biyan buk'ata, hatta da junansu ma basu bari ba, domin ko kwanakin baya Alhaji Barau da Mr. Kallah sun sani nayi masu wani aiki akan Alhaji Marusa, duk da shi na sani amma silar kashe mun aboki da yayi yasa na amshi aikinsu.


Ba wani aiki bane sun sakani na kwace kayanshi da yayi odar su masu matuk'ar tsada, sannan na kashe matuk'an motar, ni kuma aikin da nayi mashi na cinna ma babban ma'ajiyarsa wuta kuma duk sun san da haka, wanda silar haka har ya kamu da ciwo.

Dalilin da yasa na fara baka wannan labarin saboda kasan cewar suma zaluntar junansu sukeyi, sai kuma kashe yarana da aka kama wancan satin da nayi a ofishin 'yan sanda kuma na fad'a masu duk sun san da haka.


Wani irin kallon Mamaki Alhaji Marusa yake bin Alhaji Barau da Mr. Kallah dashi, gaba d'aya takaicinsu ya rufeshi, jiyayi beda sauran wata dabara garama ya amsa laifinsa kowa ya rasa.


Ra'eez... To Lucky kotu tana sauraron ka.


Lucky... Acikin aikin da suka saka ni wanda bazan manta ba shine kashe tsohon shugaban Kwastam, sai kuma Naseer wanda ake magana amma shi ba nine na kashe shi ba abokina Peter ne ya kashe shi domin aranar aiki biyu mukayi, mune mukaje har gidan Alhaji Maiwada muka bugi matarsa yayin da muka shak'ama direbansa abun kauda hankali sannan muka saka hannun Matar Alhaji ta yakushi wuyanshi, bayan daya koma gidansa nine na kaima Inspector Bello wato Kwamishnan 'yansan na yanzu jakar da aka samu a gidan Malan Sani had'e da allurar da mukayi ma Alhaji, shine ya sakata a d'akin Malan Sani, sannan Dr. Aliyu shine aka had'a baki dashi wajen tabbatar da Malan Sani akan zargin da ake masa.


Ra'eez... Hannu yasa a aljihu ya ciro kyalle ya goge kwallar data zubo masa, gyara glass d'inshi yayi yana fad'in bayan wannan sai wane aiki kayi masu?


Lucky.... Labarin yanda suka saka kayan Alhaji Marusa a gidan Alhaji Maiwada ya basu wanda akayi shari'a har kotu tasa ya biya Alhaji Marusa makudan kud'i wanda silar haka ya siyar da gidanshi, duk abubuwan dasu Alhaji Marusa suka k'ulla sai da Lucky ya fad'a.


Gaba d'aya kotun tayi shiru ana sauraronshi har ya kammala bada labarin.


Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in zaka iya tafiya. Inaso kotu ta bani dama domin nayima Kwamishna da Dr. Aliyu tambaya... Kotu ta baka dama.


Dr. Aliyu kaji bayanin da Lucky yayi, shin ko kana da ja akan abinda ya fad'a? Duk'ar da kai Dr yayi dan beda ta cewa, a hankali ya d'ago kai yana fad'in wallahi tsautsayi ne yasa na amshi tayinsu ba halina bane.


Kallon Kwamishna Ra'eez yayi yana fad'in 'Yallab'ai akwai abinda Lucky ya fad'a wanda ba haka yake ba? Sunkuyar da kai yayi yana goge zufar data zubo masa.


Hannu Ra'eez ya tafa yana fad'in ya mai shari'a inaso kotu ta bani dama domin na gabatar da wasu shedu... Kotu ta baka dama.


Flash d'in da suka samu a d'akin Abbu yasa Jabeer ya kunna.... Anan kowa yaga yanda su Alhaji Marusa suka shirya duk wani tuggu akan Alhaji Maiwada, da yanda ake shigo da haramtattun kaya da yanda su Adebayo da Umar suke kulla nasu sharrin har zuwa lokacin da aka cire abinda Malan Hassan yasa a gidan Alhaji Marusa.


Kashewa yayi yana fad'in inaso abani dama domin nayima d'aya daga cikin mutanan da sukayi wannan aikin.... Kotu ta baka dama.


Cike da mamaki suke kallon Abubukar wanda ya zama babban mutum, haka ya tako har gaban kotu.


Ra'eez... Kotu zataso taji sunanka da kuma alak'ar ka da shugaban Kwastam.


Sunana Abubakar Sani, kuma ina d'aya daga cikin ma'aikatan da sukayi aiki tare da Marigayi Alhaji Maiwada, hakika shi mutum ne mai son rike gaskiya da amana, be yarda da cin hanci ko zalunci ba, zuwansa garin nan mun samu cigaba, sai dai wannan gaskiyar tashi itace ta jawo ajalinsa, domin duk abinda aka gani ayanzu haka yake, wasuma ba'a d'aukesu ba, amma tabbas Alhaji Marusa shine yasa aka kashe Malan Hassan tsohon maigadinsa kuma yasa aka rufeshi ba tare da iyalinsa sun sani ba, haka yasa aka wahalar damu nida abokin aikina shima ya mutu Moses saboda muna bayan gaskiya, sannan Mr. Kallah yayi mana canjin wajen aiki kuma suka tsorata mu da kada mu sake dawowa garin nan.


Tunda na bar garin nan ban sake dawowa ba, sai dai mutuwar Malan Hassan ta tsaya mani arai, domin mune silar jefashi cikin halin daya shiga, hakan yasa na kasa daurewa domin anbar Iyalinsa cikin tashin hankali saboda basu san halin da yake ciki ba, haka na dawo garin nan na fad'a masu abinda ya faru.


Sanin bazasu iya komai ba yasa suka sai da d'an gidan da suke ciki suka tattara suka koma garinsu. Tun daga lokacin bansake zuwa garin nan ba, bayan wani lokaci naji aikin kwastam ya faitar mun shine na ajeshi.


Ra'eez... Jinjina kai yayi yana fad'in mungode Alhaji zaka iya tafiya. Inaso kotu ta bani dama domin na gabatar da Matar Alhaji Maiwada... Kotu ta baka dama.


Fitowa Ummu tayi tana share hawayen da suke fuskarta, tabbas yau mutuwar Abbu ta dawo mata sabuwa. Da kallo su Alhaji Barau suka bita kowa jikinsa yana k'ara sanyi.


Ra'eez... Kotu zata so taji sunanki da kuma abinda kika sani akan sharrin da akayima Malan Sani.


Sunana Bilkisu kuma nice matar Alhaji Maiwada, tabbas abinda akace Malan Sani ya aikata k'arya ne, domin aranar yashigo yana kuka, bayan na tambayesa abinda ya faru shine kafin ya fad'a mutanan suka shigo, nice nayi yunkurin bugama wani flask sai shi kuma ya kwad'a mani sanda anan na zube, amma tabbas Malan Sani be aikata abinda aka fad'a ba.


Girgiza kai Ra'eez yayi, duk yanda yaso b'oye hawayenshi sai da suka zubo, gogewa yayi yana fad'in zaki iya tafiya.

Cikin d'aga murya Alhaji Marusa yace ya mai shari'a duk abinda aka gabatar agaban kotu gaskiya ne, gaba d'ayan mu muna dasa hannu a duka laifukan. Shiru yayi yana harararsu Alhaji Barau, dan gara ya fad'i gaskiya kowama akamashi.


Ra'eez kuwa shiru yayi har sai da zuciyarsa tayi dai-dai kafin ya kalli Alkali yana fad'in ya mai shari'a anan na kawo k'arshen duk wata sheda da zata tabbatar da wad'an da suke da hannu akan mutuwar Naseer da Alhaji Maiwada, ina rokon wannan kotu data hukunta masu laifi sannan ta bima Malan Sani hakkinsa na d'aureshi da akayi shekara da shekaru bisa zalunci wanda Alhaji Muhammad Sanda tsohon Alkalin kotun nan ne ya yanke wannan hukunci kuma akan sani ya yanke domin dashi ne aka aiwatar da komai, sannan ta hukunta Kwamishna domin ya bada gudummuwa wajen jama Malan Sani sharri akan saka masa jaka a d'akinsa da yayi, haka zalika ta hukunta Dr. Aliyu domin ya bada sakamakon k'arya wanda biyanshi akayi domin yayi hakan, sai Shugaban Kwastam na yanzu Adebayo da mataimakinsa, suma suna cikin wannan b'arna da akayi. Ina fata wannan kotu mai albarka zata bima Mahaifina hakkinsa bisa kisan zaluncin da akayi masa, kuma... Kasa k'arasawa yayi saboda kukan da yaci k'arfinsa.


Tashi Jabeer yayi ya kamoshi suka zauna dan shima hawaye yakeyi. Gaba d'aya kotun tayi shiru mutane da yawa sai da suka zubarma da Ra'eez hawaye saboda tausayi.


Bayan mintuna Alkalai suka gama duba shedun da aka gabatar, babban cikinsu ne yayi gyaran murya yana fad'in abisa manyan shedun da aka gabatar ma wannan kotu, kotu tayi dogon nazari wanda ta tabbatar da ingancin wad'an nan shedu, dan haka kotu zata yanke hukunci.


Da farko ina mai bakin cikin faruwar wannan al'amari, domin an samu manyan mutane wad'an da mutane suka yarda dasu, suka basu amana da hannu dumumu wajen aikata miyagun laifuka. *Tsohon shugaban Kwastam na k'asa, tsohon Alkalin babbar kotu ta lagos, Alkalin babbar kotu na yanzu, Kwamishnan 'yan sanda na Lagos, babban likita, shugaban Kwastam na yansu alagos da mataimakinsa.*


Wad'an nan mutane dana lissafo gaba d'ayansu manyan mutane ne wad'an da suke kula da dubban mutane a k'asan su, sai dai sunci amanar k'asa, sunci amanar aikinsu, sun had'a kai wajen dakusar da gaskiya, da kunya ace mutumin da yake kwatoma wasu hakkinsu yau shine aka kama da wad'an nan miyagun aiyukan, shigo da miyagun kaya, kisan kai, gaskiya ina mai tsananin jin kunyar wannan al'amari daya faru a k'asata, amma shari'a bazata barsu ba, domin duk matsayin ka bakafi k'arfin hukunci ba, dan haka kotu zata fara zartar da hukunci daga k'asa.


*Adekulle Lucky*... Bisa shedun da suka tabbatar cewar shine yake wannan kisa, da kuma amincewarsa akan laifukansa, bisa kundin tsarin mulki na k'asa k'ark'ashin Penal code shashin kisa, wannan kotu ta yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya har sai ya mutu.


*Dr. Aliyu Sani*... Abisa hujjar da kotu ta samu da kuma amincewarsa bisa laifin bada

51 / 54