Advertisements
Chapter 37 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   37 / 54

108K to 111K   out of 160.3K words

yaga Raheena ce, duba agogo yayi yaga har sha biyu tayi, tsaki yaja yana fad'in bana son rashin hankali wallahi.


Murmushi Jabeer yayi yana fad'in bacci ta kasayi shiyasa ta kira ka. Kashe wayar yayi gaba d'aya yana fad'in sai tayi da wani kuma.


Jabeer yace Ra'eez na Raheena, wallahi kuna bani dariya, tun farko na fad'a maka ka rabu da ita gashinan tana baka ciwon kai. Tsaki Ra'eez yayi yana fad'in daga ita har Iyayen ta basu da kai, sufa a haukansu jiran yan gidan mu suke suje neman aure, har kayan d'aki fa sun siyo.


Gyara kwanciya Jabeer yayi yana fad'in ka bari da Allah? Ra'eez yace wallahi kuwa, ba na fad'a maka zasuje Dubai ba a week end d'in da naje Kano ba.



Jabeer yace haka ne. Ra'eez yace wallahi jiya take fad'a mun wai kayan suna hanya, nifa na fara tausaya mata ma. Jabeer yace da nace maka ina tausayinta meka fad'a mun? Nifa aganina bekamata kayi ramuwar gayya akanta ba, duk da an zalunceka amma bata da laifi, idan mukayi haka kamar Allah zai kama mu ko kuma ya hana mu samun wani abun da muke so.


Ajiyar zuciya Ra'eez ya saki yana fad'in b'acin rai ne yaso ya jefani cikin damuwa, tabbas Raheena bata cancanci nayi mata haka ba, amma insha Allahu a yanzu zan fad'a mata tayi hakuri kawai.


Jabeer yace baza'ayi haka ba, Raheena tana maka so mai yawa, idan ka fito fili ka fad'a mata abinda yake ranka zata iya fad'awa wani hali, ina ganin abi komai a hankali.


Ra'eez yace shikenan nasan abinda zan rubuta mata. Wayarsa ya jawo ya kunna ya fara rubutu. Jabeer da yake gefenshi yace kafin ka tura ka bani na gani. Ra'eez yace sa ido. Jabeer yace gaskiya dai. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in bara na gama to.



Mik'a masa wayar yayi yana fad'in bance kamun gyara ba. Amsa yayi yana fad'in sai dai idan baka kwafsaba, dan na lura da kai haushin Mahaifinta yasa ka tsani kowa.


Jinjina kai yayi yana fad'in ba laifi kayi amfani da kalamai masu ma'ana, sai muce Allah yasa mata dangana. Ra'eez yace amin.



Shuru sukayi gaba d'ayansu bayan sun tura sakon. Jabeer! Ra'eez ya kirashi a hankali, be amsa ba sai juyowa da yayi yana fuskantarshi.



Mai zai hana ka nemi auren Ra... Kada ma ka k'arasa, Jabeer ya fad'a. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in wallahi tausayinta nakeji.



To kayi ta biyu da ita mana. Jabeer yace yana harararshi. Dariya Ra'eez yayi yana fad'in haba abokina, yanzu da bakin ka kake fad'in nayima Pretty kishiya.


Jabeer yace ai naji kana wani kilibibin kana tausayin ta, idan har bazaka iya aurenta ba damme zaka lak'aba mani ita? Ra'eez yace saboda naga babu soyayyar kowa a zuciyar ka.


Tsaki Jabeer yayi yana fad'in to kama dena wannan maganar, babu abinda zanyi da ita, na fad'a maka bazan iya soyayya da wacce ta mutu akan wani ba, wanin ma kai, haka kawai idan na aureta data ganka sai tsohon tsumin soyayyarka ya tasar mata.


Dariya Ra'eez yasa yana fad'in kawai kace kishi kake malan, bakomai Allah zai bata wani. Jabeer yace hakan ma yafi, amma kada ka janye mata lokaci guda kamar yanda ka rubuta kaga baka fito fili kace mata baka sonta ba. Ra'eez yace kada ka damu.


*** ***


*Raheena ina so ki tsaida hankalin ki wajen karanta abinda na rubuta maki, bana so kiyi mani wata fassara, dalilin rubuta maki wannan sakon saboda naga kunyi nisa akan abinda zuciyar ku take tunani shiyasa naga ya dace nayi maki magana dan kada ku zurfafa, a tunanin ku ayi bikin ki nan da wani lokaci, domin naji kina fad'ar kunje siyayyar kayan d'aki, idan baki manta ba na fad'a maki ki jirani zanyi tunani akan soyayyar ki, kuma har yanzu ban gama yanke hukunci akai ba, domin ko Iyayena banyi maganar dasu ba, kuma ni gaskiya ba yanzu zanyi aure ba dan akwai abubuwa masu muhimmanci akaina, kuma bazan tab'a yin aure ba har sai na kammala su, shiyasa nace zan fad'a maki gaskiya dan naga kamar kina son yin aure da wuri, ina fatan zaki fahimce ni dan bana son a takura mani dan ban shirya aure yanzu ba, dan haka kudena maganar yin aure ayanzu. Nagode.*


Ta maimaita sakon yafi a kirga, zufa kawai take zubo mata, wasu zafafan hawaye ne suka zubo mata, hannu tasa ta goge tana fad'in me D yake nufi da wannan sakon? Gashi dai bece mani baya sona ba, *Dama can kuma be tab'a fad'a maki kalmar so ba.* wata zuciyar ta kwab'eta.



Gyara zama tayi tana zurfafa cikin tunani, tabbas sunyi gaggawa wajen aminta da maganar aurenta dashi, amma tunda yace akwai abinda yake gabansa zata mashi uzuri, kuma bazata fad'ama kowa wannan maganar ba, sai dai zata nuna masu abar maganar aurenta zuwa wani lokaci, idan ya kammala komai tasan zai dawo gareta.


Murmushi ta saki tana fad'in zan jiraka, bazan tab'a bari naji kunya a wajen k'awaye na ba, bara naje muyi magana da Momy.


Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:40 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*



3⃣6️⃣


Ban gane abar maganar auren ki sai zuwa gaba ba? Matsowa tayi tana fad'in Momy Ra'eez yace beyi magana da Iyayenshi ba saboda akwai wani aiki mai muhimmanci da yakeso ya kammala kuma baya so maganar aurenshi tasa yaki maida hankali akan aikin, kinga babban biki ne za'ayi dole yana buk'atar natsuwa, nima bana so ace za'ayi bikin mu kuma yana wani aikin sai kiga bikin beyi dad'i ba, kuma tunda yace aiki ne mai muhimmanci nasan ba k'aramun abu bane, kinsan kuma yanayin aikinsu dole yana buk'atar natsuwa da zurfafa tunani, shiyasa yace a bari harya kammala aikinsa kafin yazo ayi magana.


Murmushi Momy ta saki tana fad'in yanzu naji batu, ai na d'auka ko wata matsala kuka samu, haba dan wannan ai bakomai, kaya ne an riga ansiyo su, idan ma baki son su zuwa lokacin auren za'a iya siyar dasu aje asiyo maki wasu dan bancika son amfani da tsofaffin yayi ba.


Murmushi Raheena tayi tana fad'in yanzu Momy zaku iya sake mani wasu kayan? Momy tace to me zamuyi da kud'in? Ke d'aya muke da ita shiyasa muke so muyi maki abinda ko d'iyar shugaban k'asa iya abinda za'a mata kenan, dan haka idan har aikin ya jashi dogon lokaci dole asiyar da kayan idan lokacin bikin yayi asiyo maki wasu.


Raheena tace nagode Momy, sai kiyi ma Dady bayani. Babu wani bayani da za'a mun domin naji komai. Alhaji Barau ya fad'a yana sakkowa daga bene. Murmushi Momy tayi tana fad'in ashe har ka gama shiryawa? Zama yayi yana fad'in tunda kin gudu wajen d'iyar ki dole na shirya ni d'aya.


Tashi Raheena tayi tana fad'in Dady ayi hak'uri bazata sake ba. Dariya sukasa gaba d'aya. Alhaji Barau yace bakomai naji duk abinda kuka fad'a, tunda dai yana sonta ai babu damuwa, ni dama ban matsa sai Raheena tayi aure da wuri ba dan nima bangaji da ita ba, dan haka zamu jirashi ya kammala abinda yakeyi.


Momy tace kila ma kaine ka bashi aiki mai wahala ko? Alhaji Barau yace babu ruwana, kila dai a wani wajen zaiyi aiki amma ni bana bashi aiki mai wahala. Momy tace to Allah ya nuna mana lokacin. Yace amin.


**** ***


Bayan sun tashi daga aiki Jabeer yace zaije wajen Kawu akan maganar su. Ra'eez yace bakomai zan wuce wajen Kawu daga can na biya wajen Ummu. Jabeer yace ka gaishe su mu had'e gidan Mama. Ra'eez yace ka gaishe dasu Mamy.


****


Hannu Kawun Jabeer yasa a hankali ya zare glass d'in idonshi, ido ya kurama Jabeer jin abinda yazo dashi. Kauda kai yayi yana jinjina kai.



Shiru Jabeer yayi yana addu'ar Allah yasa Kawun ya amince ya taimaka masu. Gyaran murya Kawu yayi yana fad'in Allah mai iko, lallai duniya da girma take, wai akace d'an hakkin daka raina wata rana zai iya tsone maka ido.


Kallon Jabeer yayi yana fad'in wai kana nufin tare kuke aiki da Yaron marigayi Alhaji Maiwada? Jabeer yace kwarai kuwa Kawu, yanzu haka shine babban gwarzo a kotun mu.


Kawu yace naga alama daga labarin shari'ar da kace yayi, wannan shine ikon Allah, ashe dama irin wannan ranar zata zo? Ashe jinin Alhaji Maiwada ba zai zuba abanza ba? Ashe Malan Sani zai samu adalci? Ashe wad'an can azzaluman zasu fuskanci hukunci dai-dai dasu? Lallai Jabeer ka zo da magana mai matuk'ar amfani, ayanzu ne zanyi ramuwar abinda na gazayi ashekarun baya, ayanzu ne zan nuna masu Brr. Barau bakomai ne kud'i yake badawa ba, tabbas anzo wajen, dan haka kaje ka fad'ama Ra'eez, da Rafeek ina son ganin su ko zuwa dare ne.


Cike da farin ciki Jabeer yace angama Kawu. Kawu yace bana son wannan maganar ta fita, shiyasa daka fara fad'a mani nace maka muzo mota, inaso komai ya tafi yanda ya kamata, insha Allahu zan shirya yanda komai zai kasance, sai Alhaji Barau yaji kunyar da bai tab'a jinta ba, sai ya gwammace k'asa ta tsage ya shige ya huta, kaje ka fad'a masu.



Godiya Jabeer yayi ma Kawu ya tashi ya tafi cike da farin ciki, tun alokacin yayi masu waya ya fad'a masu sakon Kawu, sosai sukayi murna.


****


Rafeek ne ya fito daga ofishin 'yan sanda tare da wani d'an sanda, har bakin motarshi suka k'arasa. Hannu Rafeek ya bashi yana fad'in nagode *Usman* Allah ya bar zumunci.


Murmushi wanda aka kira da Usman yayi yana fad'in haba babu komai, ai wannan taimakon juna ne, duk da baka fad'a mani dalilin da yasa kake neman Alhaji Bello Kabeer ba.


Rafeek yace bakomai fa, akwai wani yaro da yake son shiga aikin d'an sanda shine nace masa zan taimaka masa, to da nayi bincike sai na gano a ofis d'in ku yayi aiki harya kai babban matsayin Kwamishina na 'yan sanda ayanzu, shine nace zan fara zuwa wajen ka na fara jin labarinshi kafin nasan ta yanda zanje mashi.


Usman yace indai zaka bud'e masa bakin aljihu baka da matsala dan 'Yallab'ai akwai son naira. Rafeek yace babu damuwa tunda dai kayi mani kwatancen gidanshi insha Allahu zan sameshi Allah yasa mudace.


Usman yace amin. Sallama sukayi yashiga mota. Tafiya yake yana tunanin ta yanda zai fara b'ulloma Alhaji Bello Kabir, amma tunda ya ganoshi zai shirya masu fira ta haka zai san yanda yayi ya tab'o mashi maganar wannan shari'ar.


Agogo ya duba sai yaga lokaci ya tafi, yaso ya biya asibitin da Dr. Aliyu Sani yayi aiki yaji ko yana wajen har yanzu ko kuma ya k'ara matsayi, ajiyar zuciya ya saki, dole ya bari sai gobe saboda neman da Kawu yake masu.


***

Daga wajen Ummunsa gidan Mama ya wuce, acan ya iske Jabeer suna ta fira da Mama. Bayan sun gaisa suka wuce masallaci, bayan sun idar da sallah suka zauna Rumaisa ta kawo masu abinci.


Kallon Jabeer yayi yana fad'in nifa jinake akoshe nake duk na k'osa muje wajen Kawu, ina son naji ana bani labarin Abbuna. Murmushi Jabeer yayi cike da tausayin Ra'eez.


Wayar Rafeek ce tashigo, yana d'auka ya fad'a mashi suna gidan Mama. Rafeek yace dama yanzu na fito bara na k'araso mugaisa da Mama. Ra'eez yace shikenan sai kazo.



Jabeer yace gaskiya Yaya yana da kirki. Ra'eez yace shiyasa nace maka tunda muka had'u naji ya kwanta mani, kasan bana saurin yarda da mutane amma akanshi naji na yarda dashi.


Jabeer yace wai jiya inaso na tambayeka ka d'auki bayanin Adnan kuwa? Dafe kai Ra'eez yayi yana fad'in wallahi na manta, kuma kasan nace maka daga yanzu duk wata sheda da zamu samu sai mun rik'a d'aukarta gudun yaudarar mutane.



Jabeer yace Allah yasa kada ya yaudare mu, duk da naga alamun gaskiya atare dashi amma kasan halin yau, zuciya bata da k'ashi babu ta yanda bazata iya canzawa ba, sai dai muyi fatan Allah yasa ya cika alk'awarinsa.


Ra'eez yace amin, amma da ya gama damu idan ya kasa zuwa ya bada shedar abinda ya sani. Jabeer yace kaga sai mu kiyaye. Wayar Ra'eez ce tayi k'ara, saurin tashi yayi ya fita yana fad'in Yaya ne.


Sosai Mama taji dad'in bayanin da Rafeek yayi masu akan gano Alhaji Bello Kabir wanda yake inspector a lokacin da akayi shari'ar su Malan Sani, godiya tashiga yimasa tana saka masa albarka.


Rafeek yace haba Mama babu komai, insha Allahu wannan karon mune da nasara. Mama tace Allah yasa. Abinci tasa akawo masa yace daga gida yake, kallonsu Jabeer yayi yace muje kada Kawu yajira mu. Sallama sukayi ma Mama suka fita.


**** ***


Ido Kawu ya tsurama Ra'eez, tabbas ga kamanninsa da Mahaifinsa a fuskarshi, amma sai wanda ya san Alhaji Maiwada zai iya sheda hakan, kuma sai ka k'arema Ra'eez kallo zaka gano kamannin su, lallai Alhaji Barau be yima Ra'eez kallon tsab ba da tuni ya gano kamannin Mahaifinsa.



Gyara zama yayi yana fad'in sannu kaji Ra'eez, tabbas kai d'in Kainuwa ne dashen Allah, domin Allah yasan dalilin da yasa ya bar su Alhaji Barau har yanzu araye, haka kuma ya barka kaida Malan Sani da Ummunka araye, domin ya tsara yanda ikonsa zai kasance, hakika Mahaifinka yayi mutuwar cutarwa, domin wad'an da suka kashe shi basu da imani ko kad'an, amma ayanzu zasu gane kuren su.


Kayi hak'uri na kasa tsayama Mahaifinka, duk da alokacin nasan su Alhaji Barau suna da sa hannu a kisanshi amma bani da ikon magana saboda bani da hujjar da zan nuna, ita kuma kotu hujja take so, amma ayanzu dana ganka sai naji gashi can mun cinye shari'ar, da izinin Allah zamu samo hujjar da zata ruguzasu gaba d'aya.


Hannu Ra'eez yasa ya goge hawayen da suka zubo mashi, duk'ar da kai yayi yana fad'in babu komai Kawu, Allah ya rubuta dole sai hakan ta kasance, ko ka bada hujjar baza tayi tasiri ba alokacin tunda Allah ya tsara haka, amma ayanzu zamu samota Kawu.


Jinjina kai yayi yana fad'in dole amaido da shari'ar baya, domin ita shari'a bata tsufa, koda ta kai shekaru hamsin za'a iya maidota, kuma awannan kotu za'a gabatar da ita, dan haka zan shirya yanda komai zai kasance, koda Alkali Barau yace bazai amshi shari'ar ba za'ayi masa magana kuma dole ya amsheta.


Rafeek yace mungode Kawu, kuma zamu k'arasa nemo sauran mutanan da suka tsaya a waccan shari'ar matuk'ar suna raye. Kawu yace gashi kusa mani lambar ku, daga yau inaso ku kasance ashirye, domin zaku fara aiki mai had'ari, dan mutanan da zaku kara dasu azzalumai ne, zasu iya komai saboda rufin asirin su.


Bayan sun saka mashi lambar sukayi masa sallama suna ta godiya suka tafi. A can suka rabu da Rafeek yayi gida suma suka wuce gida saboda dare yayi.


***


Ina jinka Lucky. Gyara tsayuwa Lucky yayi hannunshi nad'e a kirji yana fad'in 'Yallab'ai gobe ne za'a kawo kayan Alhaji Marusan, kuma nasa yarana su ankare baza'a samu matsala ba.


Ruwa Alhaji Barau yasha yana fad'in Lucky na sanka da son kud'i, bana so ka fad'ama Alhaji Marusa komai dan nasan zakayi tunanin zai iya k'ara maka kud'i idan ka fad'a masa, mu ba kud'in bane suka dame mu, yaudara da cin amanar da yayi mana muke so mu nuna masa iyakarsa, kasan dai daga ni har Mr. Kallah bamu da zalamar kud'i, wannan aikin idan har ka yishi yanda ya kamata kana da kaso mai tsoka, kaga dai yanzu ka manyanta, aiki da yawa sai dai kasa yaranka suyi, dan haka ina so wannan ya zama sirri, kamar yanda nace ku kwace kayan kuma ku kashe masu d'aukar kayan zakaga abinda zan saka maka dashi.



Murmushi Lucky yayi yana fad'in Alhaji baka da matsala, wannan harka mun dad'e muna yinta daku, kuma ka dena tunanin zan koma wajen Alhaji Marusa domin shi d'in ba mai alk'awari bane, kanshi kawai ya sani, kafin ku shi muka sani ni da abokina Peter, amma saboda cin amana da son kud'i irin na Alhaji Marusa daga abokina yayi masa kuskure d'aya yasa aka kashe shi, har yanzu ina da haushin wannan abun, dan haka zanyi maku aiki koda bazaku biya ni ba, domin nasan Alhaji Marusa ya zuba makudan kud'i a wannan harkar, matuk'ar ya rasa wad'an nan kayan zai shiga tashin hankali, sannan hukuncina na farko da zanyi mashi nasa babban yarona yaje cikin dare ya kona mani babban store d'inshi.



Dariya Alhaji Barau yasa yana fad'in Mr. Kallah kaji mutumin ka ko? Mr. Kallah yace lallai Lucky ka d'ebo da zafi, ayi masa hakuri yaji da wannan asarar ma. Alhaji Barau yace aifa kai har yanzu bazaka canza hali ba, kada kamanta amanar mu yaci, tare muke kashewa mu rufe amma yau saboda harkar k'aruwa tazo shine yaci amanar mu, dan haka ka bari shima anuna masa iyakarsa, ganin yana da kud'i yasa yake abinda yaga dama, idan ya fara

37 / 54