Advertisements
Chapter 49 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   49 / 54

144K to 147K   out of 160.3K words

a gidan, sai dai su daka yanke ma hukuncin har abada bazasu tab'a mance fuskar ka ba.


Murmushi Alhaji yayi yana fad'in bawan Allah duk wanda kagani agidan nan to abinda ya shuka ne yazo girba.


Malan Sani yace sosai kuwa, tunda gashi ma har an fara kawo 'Ya'yanku a gidan, da sannu sauran zasu biyo bayanshi, domin mutanan da sukayi suka agidan nan suna da yawa, lokaci kawai ake jira yayi domin akawo su su girbe shukar su, domin gidannan yana maraba da kowa, mai kud'i ko mulki ko sarauta babu wanda baya d'auka, kuma duk wanda yazo dole ya jeru da sauran mutane.


Ajiyar zuciya Alhaji ya sauke yana fad'in kaga Malan ni bansanka ba haka kawai kazo kana gasa mani magana, Fawwaz kaje ciki zanje wajen shugaban gidan nan.


Juyawa Fawwaz yayi yana goge idonshi, har Alhaji ya juya Malan Sani yace idan baka sanni ba ai kasan Tsohon shugaban kwastma marigayi Alhaji Maiwada, idan har ka tunashi dole ka tuna da direbanshi da ka yanke ma hukunci zuwa gidan nan.


Dammm!!! Gaban Alhaji ya fad'i, saurin jiyowa yayi yana kallon Malan Sani. Murmushi Malan Sani yayi yana fad'in da sannu zaku maye gurbina yayin da Allah zai d'aukeni naje nacigaba da rayuwa cikin Iyalina. Wucewa yayi yana murmushi.


Jiki a sanyaye Alhaji yaja k'afarsa zuwa ofishin shugaban gidan Yari, har ya isa yana maimaita maganar Malan Sani. A bakin k'ofar ofishin ya tsaya suna gaisawa da masinjan, magana yayi masa akan yana son ganin shugaban wajen.


Masinja yace ai baya gari Alhaji. Kallonshi yayi yana kallon motar mutumin, juyowa yayi yana fad'in amma ai ga motarsa can. Masinja yace ai yau yayi tafiyar bayan yazo nan ya ajeta suka tafi a motar abokinsa. Jinjina kai Alhaji yayi yana fad'in shikenan bani lambarsa.


Babu musu Masinja ya bashi, juyawa yayi ya tafi yana masa godiya. Tsaki Masinjan yayi yana fad'in munafukan Allah, a hankali asirin ku zai tonu, shekara nawa kana aiki baka tab'a zuwa gidan nan ba sai yau da aka kawo d'an ka, insha Allahu sai Allah ya toni asirin duk wasu masu zalunci, kun lalata Yara sai abinda sukaga dama sukeyi ba dole surik'a kisan kai ba.


Ciki ya shiga, yana shiga
yace 'Yallab'ai ya tafi. Tsaki 'Yallab'an yayi yana fad'in ai tunda naji yanda shari'ar ta kasance nasan dole sai yazo shiyasa na shirya masa hakan, su sauran da ake kawowa suna rayuwa ba mutane bane, a yanda hukuncinsa yazo aikin wahala zeyi sosai, kaga hakan zai zama darasi akanshi, kuma wallahi zan jama sauran ma'aikatan kunne duk wanda ya amshi cin hanci akan wannan yaron zai iya rasa aikinsa, domin ni ba tsohon shugaba bane babu maganar cin hanci, duk wanda yazo gidan nan dole yayi aiki, wasu ma basu da alifi amma haka suke aiki, sai kuma ace za'a kare masu laifi, koya kirani ba zai samu ba ma.


**** ****

Duk wani shirye-shiryen shiga kotu sun kammala shi, sosai Ummu ta sake a cikin su Mama da Umman Labiba, kuma jikinta yayi sauki sosai, sai damuwar rashin Abbu da take damunta.


Zaune suke a falon gidan su Sameer sunzo duba Adnan, jingina yayi dan jikinsa da sauki sosai. Nabeel yace abokina kajiyo k'amshin lahira fa. Murmushi Adnan yayi yana fad'in ai azabar kishi bata da dad'i, wallahi mutanan nan basu da Imani, wai shikenan an sake su? Rafeek yace taya za'a sake su, ai tunda Alkali yace acigaba da rik'esu har sai an kawo kwakkwarar sheda akansu dole a rikesu, Hamza ma yace suna nan suna shirya yanda zasu kama Ogansu.


Jabeer yace ai wannan Ogan nasu shine babban azzalumi, matuk'ar aka kamashi shikenan komai yazo k'arshe, dan yanda na fahimcesu bazasu tab'a tona asirin junan su ba.


Ra'eez yace Adnan baka da wata hanyar da za'a iya kamashi? Adnan yace gaskiya gidanshi ba cikin gari yake ba, domin wani lokacin idan suna waya ina jin yana fad'a masu su sameshi bayan ruwa, ina kyautata zaton kamar yafi zama acan.


Rafeek yace shikenan zanyi magana da Hamza saboda su san inda zasu farauceshi. Sameer yace wato a kullum ina k'ara godema Allah da yasa shiryata tazo mani tun ina da sauran kwana, hakika zalunci beyi ba, haka zalika aikata b'arna beda amfani, wallahi ayanxu ne nake jina cikekken mutum.


Rafeek yace sai ma kayi aure zaka k'arasa zama cikekken mutum. Dariya sukasa gaba d'aya. Sameer yace ai na kusa nayi auren nan, akwai Hindatu tana d'aya daga cikin matan da na b'atama rayuwa, sai dai ita ba ta hanyar da nakebi na bi da ita ba, anan bayan layin mu take, Iyayenta suna da rufin asiri haka yarinyar akwai natsuwa, tun farkon ganina da ita sai naji ta burgeni, hakan yasa na fara mata magana har muka fara gaisawa, a hankali sai ta fara sona, duk da bata fad'a mani ba amma na fahimci hakan, ni kuma kawai sha'awarta nakeyi, da haka na fara janta jikina, soyayyar da take mun yasa take bin umarni na, da haka har na samu na biya buk'ata ta da ita, tun daga lokacin na dena kulata, lokacin da Iyayenta suka gane abinda nayi mata tasha duka, inda Allah yaso bata d'auki ciki ba, mahaifinta yaso ya tada maganar sai mahaifiyarta tace ya rufa masu asiri yin hakan kamar tona masu asiri ne, dole haka ya hakura, tun Hindatu tana kirana bar na kulleta dole ta hakura dani, shiyasa a lokacin da nace zanbi wad'an da na b'atama rayuwa na basu hakuri naje har gidansu na bama Iyayenta hakuri itama na bata hakuri, cikin sa'a kuma ta yafe mani, tun daga lokacin kawai sai na fara tunaninta, daga baya na fara kiranta, maganar da nake maku yanzu haka soyayyarmu mukesha kuma za'ayi maganar bikin mu.


Tafi sukasa suna dariya. Rafeek yace gaskiya naji dad'in hakan, kuma nasan zaka kula da ita, dama kuma haka ake so, Allah ya baku zaman lafiya. Gaba d'aya suka amsa da amin.


Wayar Rafeek ce tayi k'ara, yana dubawa yaga Hamza ne, bayan sun gaisa ya fad'a masa mutuwar Yaran Lucky, Rafeek yace shikenan yanzu zan zo. Kashe wayar yayi ya fad'a masu abinda ya faru. Shiru sukayi suna jimamin abun.


Rafeek yace kada ku damu hakan bazai tab'a shedunmu ba, domin su kawai hanyar muce da zata sa mu gano inda Ogansu yake, kuma insha Allahu za'a kamashi. Suka ce Allah yasa.


**** ****


Wai Raheena me yake damunki ne kwana biyu bana ganin ki cikin walwala? Gyara zama tayi tana fad'in Momy haka kawai nakeji kamar bazan samu Ra'eez ba, ada nafi jin zan mallakesa, amma ayanzu zuciyata ta fara tsinkewa, kina gani yaushe rabon da yazo gidan nan, kowane irin aiki yakeyi tunda har muna gari d'aya ai ya kamata ko so d'aya ne ace yana zuwa wajena, idan bezo bama ai akwai waya, wallahi Momy jikina ya fara sanyi.


Hannu Momy tasa ta goge mata hawaye tana fad'in ki kwantar da hankalin ki, tunda har yace maki aiki yakeyi kiyi masa uzuri, kina ganin Alhaji ma yaushe rabon daya zauna muyi fira dashi, da alama wata shari'a zasuyi mai zafi, kinga duka shekaran jiya suka kammala shari'ar yaron gidan Alhaji M. Sanda, yanzu kuma gobe suna da wata shari'ar, shiyasa nima nayi ma Alhaji uzuri saboda nasan yanda aikinsu yake.


Murmushi Raheena tayi tana fad'in Momy kina ganin da sun kammala shari'ar nan zai dawo gare ni? Sosai kuwa, ai ina ganin suna gama wannan shari'ar za'asa maku rana, shima Alhaji lokacin hankalinsa ya kwanta kinga sai ashirya komai, wad'an nan kayan naki idan bakison su kawai zai siyar dasu.


Raheena tace a'a Momy abarsu tukunna. Momy tace shikenan tashi kije kici abinci.


**** ***

*Safiyar litinin a kotu.*



Ur's.
Nabeelert Lady🖋[3/10, 8:41 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*



4⃣7️⃣


*High court Lagos*


Cikar kotu ya bama ma'aikatan wajen mamaki, yanda kasan za'ayi wata shari'ar da bata wuce kwana biyu da faruwa ba, wanda yazo da wuri shi ya samu waje.


Bayan da aka gama shiga Alkali ya shigo, bayan ya zauna kowa ya samu waje ya zauna. Kallon mutanan kotun yake yana so yaga kosu Alhaji Kamal sun zo, aikuwa caraf suka had'a ido, mamakin da yayi yau sun k'ara yawa, hakan yasa jikinsa yayi sanyi, gashi su Alhaji Marusa basu zo ba.


Magatakarda ne ya tashi domin karanto shari'ar da za'a gabatar...... *Kamar yanda aka karanta wannan shari'ar a wancan lokacin kafin a shigo da wadda ta gabaceta, hakan yasa aka d'age wannan shari'ar zuwa yau litinin. A yau litinin 18/12/2019 wannan kotu mai albarka zata saurari k'ararraki guda biyu, ta farko itace wadda zuri'ar Alhaji Sambo Jarmai suka shigar akan mutuwar d'ansu mai suna Naseer Sambo Jarmai, wanda aka tsinci gawarsa a shekaru goma sha biyu da suka wuce a ranar wata juma'a da misalin k'arfe 9:00 na dare a bayan gari, hakan yasa Iyayensa suka shigar da k'ara domin suna buk'atar kotu ta bi masu hakkinsu.*


*Shari'a ta biyu itace wadda Iyalan Malan Sani suka shigar, shari'ace tsohuwa wadda akayita a wannan kotun a shekarar 10/5/2008, inda aka yanke ma Malan Sani hukuncin d'aurin rai da rai a gidan yari, shari'a ce data shafi tsohon ma'aikacin Kwastam Alhaji Hamza Maiwada, wanda ake zargin Malan Sani da kasheshi da kuma yunkurin haikema matarsa a matsayinsa na direbansa, Iyalan Malan Sani sun sake dawo da wannan shari'ar baya saboda suna so asake shari'ar dan basu gamsu da hukuncin da kotu ta yanke a shekarun baya ba.*


Mik'ama Alkali takardun yayi kafin ya koma ya zauna. gaba d'aya kotun ta d'auki hayaniya dan basu san da wata shari'ar ba bayan ta Naseer. Alkali kuwa tamkar wanda aka sama shokin, gaba d'aya jikinsa rawa yakeyi yayin da zufa ta fara keto masa, duk yanda yaso ya daure sai da zufar ta sauko masa afuska tamkar wanda aka zuba ma ruwa, kyalle yasa ya goge fuskarshi kafin ya shanye ruwa kofi d'aya.


Bubbuga tebur Alkali yayi hakan yasa akayi shiru. Jarumtarsa ya tattaro kafin yace lauyen da zai gabatar da shari'a bismilla.



Tashi Ra'eez yayi yana gyara zaman farin glass d'insa, sosai yau yayi kyau sai kace zeyi gasar lauyoyi, gaba d'aya mutanan suka bishi da kallo yanda haibarsa ta fito.


Risnawa yayi yana fad'in ya mai shari'a kamar yanda muka fara karanto k'arar Naseer Sambo Jarmai a wancan satin yanzu ma zamu cigaba, duk da yanzu shari'ar ta zama biyu kuma duk nine zan gabatar dasu, amma ayanzu zamu fara gabatar data Naseer.


Kamar yanda na fad'a an samu gawar Naseer a bayan gari, kuma na gabatar ma kotu da bayanin mutuwarsa da 'yan sanda suka rubuta, inda bincike ya nuna cewar ankashe Naseer ta hanyar shakeshi da akayi har ya mutu, kuma wannan kisa da akayi kisa ne da aka shiryashi domin a toshe wata kafa wacce ake zargin Naseer da kok'arin tona wani b'oyayyen sirri, hakan yasa aka kashe shi wajen b'oye wannan sirri.


A cikin sirrin da Naseer ya d'auka akwai wanda aka nuna anan ranar alhamis data wuce inda ya d'auki hoton Fawwaz alokacin da ya yanki Farouk da wuk'a, acikin abokan Fawwaz wani yaga lokacin da Naseer yake d'aukarsu, hakan yasa suka sanar da Mahaifin Fawwaz. Ina so kotu ta bani dama domin na kira Adnan d'aya daga manyana abokan Fawwaz domin yayi mana bayanin yanda komai ya faru...... Ajiyar zuciya mai k'arfi Alkali ya sauke kafin yace kotu ta baka dama.


Adnan ne ya fito yana takawa da kyar dan har yanzu jikinsa beyi kwari ba.


Ra'eez... Kotu zata so taji sunan ka da kuma alak'ar ka da Fawwaz.


Sunana Adnan kuma Fawwaz abokina ne, domin alokacin da mukayi secondary kowa yasan abotar mu saboda mu ukku ne muke tare, duk inda kaga Fawwaz to dole kagan mu nida marigayi Sufwan, abotar mu ta kai har Iyayen mu sun san mu atare.


Ra'eez... Kotu tana buk'atar kayi mata cikekken bayani akan abinda ka sani na kisan Farouk da kuma abinda ya shigo da Naseer cikin maganar.


Adnan.... E to, kamar yanda kowa ya gani a vedion da aka nuna Fawwaz ya kashe Farouk wanda ba kowa bane ya d'auki wannan vedio sai Naseer, kuma Naseer d'an ajin mu ne muna gaisawa dashi, alokacin da Fawwaz ya kashe Farouk bayan munzo muka iske ta'asar da yayi sai hankalin mu ya tashi, kasancewar mu abokai yasa mukayi kokarin rufama Fawwaz asiri, nine na d'auki wauk'ar na jefata a wani rami da ake tara bola, bayan da muka juyo zamu tafi sai na hangi Naseer yana d'aukar mu, sai dai muna jiyowa shi kuma ya bar wajen da gudu.


Bayan da mukaje muka sanar ma Dadyn Fawwaz sai yace kada mu damu, abinda yake so shine kada mu fad'ama kowa yasan yanda zaiji da komai.


Washe gari dana tambayi Fawwaz ya naji ance a bayan gari aka samu gawar Farouk, shine yake fad'a mani Mahaifinsa ya had'a baki da shugaban makarantar aka fitar da ita.


A ranar da za'a kashe Naseer munzo gidan su Fawwaz sai muka iske Dadynsa da bak'i a waje, bayan mun gaisa sai ya bukaci da mu fad'a masu kwatancen gidansu Naseer kuma mu tura masu hotonshi, haka muka bashi muka tura masu hotonshi.


Washe gari sai mutuwar Naseer naji, tabbas na girgiza da mutuwarshi, kuma har gobe ina ganin laifina, domin nine na fad'a cewar ya d'auki vedio, da ban fad'a ba babu yanda za'ayi asan shine, tun daga lokacin na fara janye masu Fawwaz har Allah yasa muka gama kowa ya kama gabansa, ina mai bama Iyayen Naseer hakuri abisa sakarcin da nayi.



Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in mungode Adnan zaka iya tafiya. Ya mai shari'a wannan shine Adnan abokin Fawwaz, kuma kowa yaji wanda yasa aka kashe Naseer saboda kawai a b'oye gaskiya ina....


Saurin tashi Brr. Bajinta yayi yana fad'in ya mai shari'a ai wannan shedar baki ce kawai Adnan ya bayar, kuma shi kad'ai ne ya bada sheda wanda kowa yasan cewar mutum d'aya baya sheda, domin za'a iya biyanshi yazo ya b'ata Alhaji M. Sanda.


Miyau Alkali ya had'iye dan ya riga daya sadakas, yasan Brr. Bajinta yana kokarin kare Alhaji M. Sanda ne kawai saboda ba komai ya sani ba. Ruwa yasha kafin yace Brr. Ra'eez kotu tana buk'atar cikakkar sheda domin bazata amshi wannan hujjar da aka bayar ba.


Risnawa Ra'eez yayi yana fad'in ya mai shari'a zan so kotu ta bani dama domin na nuna mata hujjata ta k'arshe wadda zata tabbatar da abinda Adnan ya fad'a gaskiya ne... Kotu ta baka dama.


Tashi Jabeer yayi ya had'a kayan da za'a kunna. Tunda Jabeer ya tashi Alkali yaji cikinsa ya kad'a, zufa kawai take keto masa ta ko ina, gaba d'aya kyallen dayake goge zufar ya jike. Mutane kuwa mamakin yanda hankalin Alkali ya tashi suke dan zuwa yanzu ya kasa b'oye tashin hankalinsa, zaman kanshi a d'osane yake.


Shiru kotun tayi yayin da fuskokin Alhaji Marusa dana Mr. Kallah suka bayyana, sai gefen fuskar Alhaji Barau saboda shi a gefe yake hakan yasa ba'a d'aukoshi duka ba, idan ba wanda yasanshi ba bazai iya shedashi ba, sai kuma bayan Alhaji M. Sanda danshi ya bama mai d'aukar baya.


Muryoyinsu ne suka fara cika kotun, muryar Alhaji Barau itace ta tonashi, domin yana magana wasu suka fahimci shine, sai kuma lokacin da aka fara ambatar sunanshi, haka suka cigaba da sauraron shirin da suke akan kashe Alhaji Maiwada da kuma yanda zasu sa akashe Naseer.


Babban abinda ya k'ara tabbatar da Alhaji Barau ne awajen alokacin da Alhaji M. Sanda yake fad'in *Brr. Barau idan har kayi mani wannan taimakon ina mai tabbatar maka kaine Alkalin gobe*. Zuwa lokacin mutanan kotun kasa jurewa sukayi dole wajen ya d'auki hayaniya, dama kuma d'aukar tazo k'arshe. Hannu Jabeer yasa ya kashe.


Jiyowar da Ra'eez zeyi sai dai yaga wayam a kujerar Alkali domin ya sulale ta kofar da take kusa dashi🤣. Ra'eez besan lokacin da dariya ta kwace masa ba, hannu yasa ya toshe bakinsa yana girgiza kai, ai da mutane suka fahimci abinda yake faruwa sai kotu ta hargitse da dariya tare da surutu.


Duk yanda aka so mutane suyi shiru abun ya faskara, dole sai Magatakarda ne ya hau sama ya buga tebur hakan yasa kowa yayi shiru ya juyo sun d'auka Alkali ne ya dawo. 'Daya daga cikin manyan ma'aikatan kotun ne ya mike yana fad'in an d'age wannan shari'a zuwa lokacin da za'a sanar.


Haka kowa ya fito daga kotun yana fad'ar yanda akayi, 'Yan jarida kuwa sun cika wajen kowa yana son yaji yanda za'ayi, kamar ance su kalli gefe sai ganin 'Yan sanda sukayi sun saka Alhaji Barau a tsakiya suna shirin barin kotun dashi, ai da gudu 'Yan Jarida sukayi wajen, sai dai kafin su kai sai kurar motar suka iske.


Abinda ya faru shine, tun alokacin da hankulan mutane suka raja'a wajen kallon abinda aka kunna hankalin Alkali ya tashi musamman da yaga an hasko hotonsu, tabbas ya tuna da

49 / 54