Author : Marubuciyar Zamani Category : Complete Novels
shikenan hakan za'ayi. Dariya suka sake sawa da haka suka bar zancen akan a bama Ra'eez case d'in, sai gashi kuma an bashi.
Shiru Ra'eez yayi yana kallon takardun da masinjan Alhaji Barau ya kawo masa. Sake dubasu yayi yana mamakin irin wannan abu, gashi dai an bashi takardar case, ina ruwanshi da aiko masa da shedu kuma? Ai wannan aikinsa ne yaje ya nemo komai da kanshi, kuma yana so ma ya gana da yaron da zai tsaya mawa.
Tsaki yayi yana fad'in bazan biye tasu ba, dole na gano lauyen da zai tsaya ma d'ayan b'angaren domin nasan irin shirin da zanyi, tunda yaga haka ajikinsa yasan abinda aka bashi babu gaskiya aciki, shi kuma yayi alk'awarin bazaiyi aikin rashin gaskiya ba.
Jabeer ne ya dafashi yana fad'in Ra'eez lafiya kuwa? Ajiyar zuciya yayi yana fad'in wallahi nashiga tunanin wani rainin hankali da akeso amun ne. Jabeer yace akan mefa? Takardar Ra'eez ya mik'a masa yana fad'in wani k'arfin hali nake gani yanzu, sai kace wanda yake aikin gata, ace ina lauya amma sheduma sai an nemo mani kawai zuwa zanyi na gabatar dasu.
Dariya Jabeer yayi yana fad'in da sannu dai zaka fara gano halin mutumin. Tsaki Ra'eez yayi yana fad'in ko kasan wanda zamu kara dashi? Jabeer yace yawuce Brr. Bajinta.
Saurin kallonshi Ra'eez yayi cike da alamun tambaya. Jabeer yace nasan dole hakan ne zata kasance, domin farkon zuwana da nayi wani case nayi nasara anyi mani irin haka, sai dai alokacin ban gama gogewa da kowa ba sai nayi yanda suka ce, kuma nida Brr. Bajinta muka kara, abun ya bani mamaki ganin yanda yake ma wanda yake karewa wata irin tambaya, sai ka kad'auka shine yake kare wanda nake karewa, gashi dai abinciken da suka bani nasan akwai alamun tambaya, bangama shan mamaki ba sai da shari'ar tazo k'arshe, ina ji ina gani aka yanke ma wanda Brr. Bajinta yake karewa hukunci, mutane sunyi mamakin yanda sabon zuwa kamata ya iya kada kwararren lauya, kuma a shari'ar da mukayi ya fini baki amma duk da haka nine nayi nasara.
Jinjina kai Ra'eez yayi yana sakin murmushi ta gefen baki, kallon Jabeer yayi yana had'a takardu yace ka barni dasu, zanyi wasa dasu, za'aga yanda ake shari'a a wajena domin bazan bari su sani aikata kuskure irin nasu ba.
Jabeer yace sai kayi da gaske kam. Ra'eez yace dole inaso na had'u da yaron domin bazan shiga shari'a da abinda suka bani ba. Jabeer yace kayi dai-dai, tashi muje sallah.
*** ***
Bayan sun tashi daga aiki kowa ya fito ya nufi motarshi, wani dattijo suka gani zaune a gefe ya buga tagumi ya lula tunani, har sun wuceshi sun kai wajen motarsu sukaji alamun motsi.
Dattijon suka gani yayo wajensu da d'an sassarfa. Tsayawa sukayi suna kallonshi. Bayan ya k'araso ya matsa kusa da Ra'eez fuskarsa d'auke da damuwa. Ra'eez ne ya fara gaisheshi yana fad'in lafiya dai Baba? Wanda aka kira da Baba yace ba lafiya ba Yaro.
Gyara tsayuwa Ra'eez yayi yana fad'in mecece damuwar ka Baba? Hannu Dattijon yasa ya goge kwallar data zubo masa yana fad'in nazo wajen nan dasa ran ganinka domin nasan zaka iya kwato mana hakkin mu, tun ranar dana fara kallon shari'ar ka da akayi ta farko na yaba da kwazon ka, duk da ban tab'a tunanin zan samu kaina a kotu na kawo k'ara ba amma tun a wancan lokacin nake aiyana koda shari'a zata had'oni a kotu tabbas kaine wanda zan nema, sai gashi lokaci yazo shari'a ta kawoni kotun ku, an zalunceni anci mutuncin Auta ta, nazo neman lauya sai na samu ance kaine wanda zai kare Yaron daya lalata rayuwar 'Yata, abun ya bani mamaki alokacin da Brr. Bajinta ya tarbeni kamar dama ni yake jira, kuma anan take yace shine zai tsaya mani, tunda ya fad'i haka jikina ya kasa amincewa dashi, domin nasan shi lauyan manyan mutane ne, narasa inda zansa raina hakan yasa nace dole sai na ganka naji da gaske kaine zaka tsayama wannan Yaron ko kuwa.
Ajiyar zuciya Ra'eez yayi cike da tausayin wannan Dattijo, tabbas su Brr. Bajinta sun shirya wani abu, tun daga jin bayanin Baba yasan akwai alamun tambaya.
Kallon Dattijon yayi yana fad'in Baba kayi hak'uri, insha Allahu kaine zakayi nasara, tabbas nine wanda 'Yallab'ai ya bama damar kare wanda kake k'ara, amma ina mai tabbatar maka kaine zakayi nasara.
Dattijo yace ta yaya Yaro? Nasan irin basirar ka baza'a iya kada ka ba, yanzu kam inaji na hak'ura da wannan shari'ar, cuta ce an cuci Auta ta, zan koma gida muyi hakuri da K'addarar da Allah ya aiko mana, shi kuma mun barsa da Allah, zai biyamu alokacin da beda kowa.
Jabeer ne yayi saurin fad'in Baba kada kace haka, tunda abokina yace kaine zakayi nasara to kasa aranka zakayi d'in, bazamu bari a danne maku hakkin ku ba, ka yarda damu.
Jinjina kai Dattijon yayi yana fad'in shikenan, na amince da ku, Allah ya bamu sa'a. Ra'eez yace amin Baba, yanzu kashiga mota ina so naje naga Autar taka dan bana so kowa ya gammu tare, kuma kada ka fad'ama kowa munyi magana da kai kawai kayi abinda Brr. Bajinta yace maka. Dattijo yace nagode sosai. Mota suka shiga Ra'eez yana fad'in na makara ma akwai inda zamuje, amma daga can sai na d'auko su Mama mu wuce kawai. Shima Jabeer yashiga tashi motar ya bisu abaya.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋*Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
2⃣6⃣
Idanuwan Ra'eez ne suka ciko da kwalla tun daga lokacin da yayi ido biyu da Yarinyar Baba wacce bazata wuce shekara 16 ba amma an lalata mata rayuwa. Hannu yasa ya goge idonshi yana kallon Mahaifiyar Yarinyar yana fad'in Mama kuyi hakuri, insha Allahu zakuyi nasara, duk da ba nine zan tsaya maku ba kusa aranku ku nake ma aiki.
Goge idonta tayi tana fad'in na yarda da abinda kace, mungode da wannan taimako. Ra'eez yace bakomai, ya sunanta ne? *Habiba* sunanta, ita kad'ai gare mu mace dama su ukku ne, biyu maza sai ita, babban cikinsu ya rasu yanzu su biyu ne, muna murnar ta kammala babbar makaranta Malan yana cewa za'a sama mata wata makarantar tunda burinta ne ta karanci aikin lafiya sai gashi an lalata mata rayuwa, duk da bamu da k'arfi mun yanke shawarar tsaya mata tayi ilimi domin ta cika burinta, hatta da Yayanda iya karsa babbar makarantar sakandire, ganin bamu da hali yasa bece zai wuce ba haka ya fara sana'a, sai gashi yanzu Allah ya d'aukakashi, ganin haka yace dole Habiba tayi karatu zai tsaya mata, amma yanzu an cutar da ita.
Ra'eez yace insha Allahu sai burinta ya cika. Habiba ina so kisa jarumta aranki, kada kiyi kallon an ruguza maki rayuwa ki hakura da karatun ki, da izinin Allah sai kin d'aukaka, kisa aranki zakiyi karatu, domin shi kad'ai zakiyi kijawoma kanki daraja a wajen kowa, idan kika zama wata babu wanda zaifi karfin ki, amma idan kika sare ma rayuwa haka zakiyi ta cikin kunci, saboda ko aure zakiyi babu wanda zai d'auke ki da daraja, amma idan da ilimin ki zakiga yanda za'a daraja ki.
Kai Habiba ta jinjina tana share hawayen idonta. Jabeer yace duk yanda za'a maki tambaya a kotu kada ki bari a saki fad'in abinda ba shikenan ba, ki tsaya akan gaskiyar ki kuma kada kiji tsoro, koda Brr. Bajinta ya zo yace ki fad'i abinda zai tsara maki kada kice bazaki amince ba, ki bari sai anje kotu sai ki canza abinda ya fad'a ki fad'i abinda kika sani.
Baba yace mungode sosai Allah ya saka maku da alkhairi. Gaba d'aya sukace amin. Amsar lambar wayar Baba Ra'eez yayi yasa masa tashi yana fad'in zamu rik'a magana a waya kafin litinin ashiga kotun.
Baba yace nagode sosai. Tashi sukayi Baba ya rakosu sai godiya yake masu. Bayan ya koma gida Ra'eez yace wallahi duniya babu gaskiya, ka duba fa acikin shedun da Alhaji ya bani hada rahoton likitan daya duba Habiba, saboda shima d'an rashawa ne har ya canza abinda ya gani, amma ka barni dashi dole zai zo kotu zamuji komai, nima zan caza masa kai.
Jabeer yace ai duniya babu gaskiya, da likita, da 'Yan sanda da Lauyoyi dama ana samun azzalumai, domin kowa kud'i yake so, shiyasa duk inda suke kansu a had'e yake. Ra'eez yace Allah ya kyauta, bara na wuce sai gobe ko.
Jabeer yace gobe juma'a bazan fito da wuri ba. Ra'eez yace kaji d'an gayu, dan Allah kazo da wuri bazanji dad'i ba idan bakanan. Dariya Jabeer yayi yana fad'in shikenan Allah ya kaimu.
Wayar Ra'eez ce tayi k'ara, yana dubawa yaga Raheena ce, d'agawa yayi. Sallamarta yaji tana mai kwantar da murya, yana amsawa ta fara gaisheshi. Murmushi yayi ya amsa aranshi yana fad'in lallai su Raheena an fara canzawa.
Daga can Raheena tace kira nayi naji yanda ka tashi daga aiki. Ra'eez yace lafiya lau gani zan tafi gida ma. 'Dan zaro ido tayi tana fad'in biyar fa ta kusa amma baka koma gida ba? Ra'eez yace naje wani waje ne yanzu zan tafi.
Murmushi tayi tana fad'in bara na barka idan kaje mayi waya, ina fatan dai kaci abinci? Ra'eez yace idan naje zanci dai. Raheena tace shikenan kaci dani, amma yaushe zaka zo? Tab'e baki yayi yana fad'in wani aiki zanyi kuma yana buk'atar natsuwa, bazan samu hutu ba har sai na kammalashi.
Raheena tace shikenan amma dan Allah ka rik'a kirana hakan zai mun dad'i naga kiranka awayata. Ra'eez yace shikenan. Sallama sukayi ya kashe wayar.
Har zaisa aljihu wayar ta sake k'ara. Murmushi ya saki yana mai tsinke kiran domin ya kira. Sakin baki Jabeer yayi yana kallonshi.
Pretty na kinga na dad'e ko? Murmushi tayi tana fad'in damuwata rashin cin abincin ka gashi yamma tayi. Ra'eez yace ni kuma damuwata na wuni banji muryaki ba kuma banga fuskarki ba, amma gani nan yanzu zanzo amun kwalliya mai kyau, da nazo na ganki naci abinci sai mu tafi.
Murmushi tayi tana fad'in sai kazo, kayi tuk'i a hankali. Ra'eez yace angama Pretty na, ki kula da kanki. Dariya Jabeer yasa yana fad'in dama haka kake? Ra'eez yace namafi haka, ka zauna nan ayi babu kai, wallahi abokina soyayya dad'i gareta, gaskiya an barka abaya.
Jabeer yace abinda bangane ba shine, yaushe ka fara soyayyar? Ra'eez yace lokacin kana bacci. Dariya Jabeer yasa yana fad'in Allah da gaske nake, nasan dai kace mun kana son Rumaisa kuma nasan baka fad'a mata ba, amma kuma gashi kuna waya kamar wad'an da suka dad'e suna soyayya.
Ra'eez yace kasan duk soyayyar da aka tara, aka jik'ata ta tsimu ba'a sanin lokacin da ake fara ta, idan kuma aka fara ba'a mata bakunta, to haka tamu take, ajiya muka bayyanata gashi kuma har tabi mana jiki.
Jinjina kai Jabeer yayi yana fad'in lallai kam, soyayya tayi kam, sai nace Allah ya bada sa'a, ga Raheena kuma a gefe. Ra'eez yace ba ruwanka kasa ido kawai kayi kallo.
Jabeer yace hada jiki ma duk zansa, ina jiran ranar da zansha kallon da kyau. Ra'eez yace E naji. Murmushi Jabeer yayi yana fad'in soyayya ko wahala. Ra'eez yace ga wanda bai samu ba ko. Tab'e baki Jabeer yayi yana fad'in kaga Malan sai da safe. Ra'eez yace ai gara katafi ka tsareni da surutu Pretty na jirana.
Murmushi Jabeer yayi yana fad'in agaishe da Pretty to. Ra'eez yace wannan sunan ya fita abakin ka wallahi. Baki Jabeer ya kama yana fad'in yanzu kuwa. Dariya sukasa sukayi sallama kowa ya nufi gida.
****
Ganin yanda Rumaisa tayi kwalliya sai gyare-gyare takeyi yasa Mama ta koma d'aki tana mata dariya dan tasan Ra'eez yakusa dawowa. Abincinsa ta shirya a falo ta koma d'aki wajen Mama.
Zama tayi tana satar kallon Mamar. Murmushi Mama tayi tacigaba da linke kaya. Kallonta Rumaisa tayi tana fad'in wai Mama naji kinyi shiru sai murmushi kikeyi. Mama tace kuka kike son inyi? Turo baki Rumaisa tayi tana fad'in amma ai ba haka kikeyi ba.
Mama tace ya kike so nayi bayan kina ta shiri da alama bak'o zakiyi ban sani ba. Rufe fuska Rumaisa tayi tana murmushi tace ba wani bakon da zanyi kawai fa abincin Yaya ne na aje masa yace sauri yakeyi kada mu makara.
Mama tace naga alama ai, wannan kwalliyar ta zuwa unguwar ce ko? Tashi Rumaisa tayi tana kwalama Abdallah kira. Dariya Mama tayi tana fad'in kwayi ku gama.
Da gudu Abdallah ya shigo hannunsa d'auke da leda yana fad'in Aunty Yaya ya dawo kinga ya siyo mun kayan dad'i. Amshe ledar tayi tana fad'in kawo insha. Abdallah yace kai Aunty yace fa taki tana mota zai baki.
Rumaisa tace ya akayi ka sani? Abdallah yace daya bani nace masa ina taki shine yace ai taki ta dabance tana mota. Murmushi Rumaisa tayi ta d'auki alewa d'aya.
Muryar Ra'eez taji yana fad'in banda kwad'ai dai. Murmushi tayi tashige falo. Da sallama ya k'arasa shigowa. Mama ce ta fito tana amsawa. Har k'asa ya duk'a yana gaisheta.
Amsawa tayi tana masa sannu da aiki. Ra'eez yace kunjini shiru wallahi wani aiki aka bani ranar litinin ma zamu shiga kotu wata shari'a.
Mama tace aifa shari'a bata k'arewa, to Allah ya tabbatar da alkhairi kuma ya baka sa'a. Ra'eez yace amin. Hannun Abdallah taja tana fad'in kashiga kaci abincin mutafi ko. Sosa kai yayi ya kasa tashi. Murmushi tayi ta wuce d'aki, cike da kunya ya shiga falo. Rumaisa tana jin Mama ta shiga d'aki ta fito da sauri.
Tsayawa tayi a bakin k'ofa tana wasa da hannunta. Ido ya tsura mata yana murmushi, takowa tayi tashigo bakinta d'auke da sallama. Amsawa yayi yana fad'in bazaki dena wannan kunyar ba ko? Saurin zama tayi tana masa sannu da zuwa.
Ra'eez yace yunwa nakeji fa. Saurin bud'e abinci tayi ta fara zuba masa. Kallonta yake yana jin sanyi, sosai tayi masa kyau, tasa bak'ar jallabiya ta yane kanta da pink d'in mayafi fuskarta tasha kwalliya mai sauki.
Mik'a masa abincin tayi tana shirin tashi. Kallonta yayi yana fad'in ina zaki? Kanta ak'asa tace abinci zan barka kaci. Murmushi yayi yana fad'in aiko bazanci ba.
Zama tayi tana murmushi tace to kaci. Cokali ya d'auka yana fad'in damma bance ki bani ba. Saurin cusa kanta tayi a cinyoyinta tana murmushi. Murmushi shima yayi ya fara cin abinci yana mata fira.
Bayan ya gama ta kwashe kayan suka fito. Rufe gidan sukayi Madu na jiransu. Shida Ra'eez ne a gaba su kuma suka shiga baya. Suna tafiya Ra'eez yace wai Mama ina Aunty Hassana kullum ina so na tambayeki ita? Mama tace Allah sarki Sister Hassana sarkin kirki, ai sun dad'e da tashi, tunda aka canzama mijinta wajen aiki itama ta nemi canjin wajen aikinta suka tafi suna Abuja.
Ra'eez yace lallai kunyi nisa sai dai waya. Mama tace tana kirana muna gaisawa kuwa ai tana da kirki har cewa tayi zata zo ta d'auki Rumaisa taje mata hutu can.
A zabure Ra'eez yace ba dai Abuja ba wallahi, waye zai kaita haka kawai mayun garin nan su sa mata ido. Dariyar da Madu yayi ce ta ankarar dashi abinda yayi. Hannu yasa yana sosa kai.
Rumaisa kuwa duk'ewa tayi tana murmushi. Mama tace ni kuwa har na amince mata k'arshen wata zata zo su tafi. Kicin-kicin yayi da fuska yana kallon Rumaisa ta madubin motar, be sake magana ba kawai yayi shiru.
Murmushi Mama tayi tana kallonshi. Madu yace ai Halima baza'ayi haka ba, Ra'eez shine babba kuma shine namiji, dole sai ya amince zata je ko Ra'eez? Fuska a d'aure yace bazan amince ba ma, dan hadda zata fara babu inda zataje hutu.
Dariya Mama tayi, yanda yayi maganar kasan haushi ne yake cinsa. Madu yace angama Alhaji Ra'eez nima ban amince ba. Mama tace ai shikenan tunda kun fini k'arfi. Murmushi Ra'eez yayi yana shafa gefen fuskarshi.
Wajen Kawu suka fara zuwa dan kada magriba tayi. Zaune suke a cikin d'akin da ake ganawa da masu laifi. Bayan sun gama gaisawa da ma'aikacin wajen wanda dama sun saba da Ra'eez, shine ya aika akira Malan Sani.
Kallon Ra'eez yayi yana fad'in ya aiki kuma? Ra'eez yace aiki muntashi sai gobe kuma. Yace to Allah ya taimaka, bara na baku waje ku gaisa. Godiya Ra'eez yayi masa ya fita.
Tunda Malan Sani ya tunkaro wajen idanuwan Mama suka cika da kwallah, da gudu Abdallah yaje ya taroshi, duk ya tsufa saboda wahala, sai dai har yanzu jikinsa akwai jarumta, dan yasa dakiya aranshi hakan yasa zuciyarsa bata raunana ba bare ta shafi lafiyarsa.
Yana zuwa Ra'eez ya tashi yana gyara masa wajen da zai zauna. Zama yayi murmushi d'auke a fuskarshi. Hannu ya mik'ama Madu suka gaisa yana tambayarsa rayuwa.
Har k'asa Ra'eez da Rumaisa suka duk'a suka gaishe da Malan Sani. Kamosu yayi yana murmushi yace lafiya lau ina fatan ana kula da karatu Rumaisa? Kai ta jinjina tana b'oye hawayen da suka taho mata.
Kallon Mama yayi ganin ta kasa magana sai share hawaye.