Advertisements
Chapter 21 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   21 / 54

60K to 63K   out of 160.3K words

an barsu zasu lalace, nasan hakkin Ra'eez ne da Bilkisu, kuma zan masa bayani nasan bazai hana a baku ba, ita kuma Bilkisu ga halin da take ciki, saboda haka babu wata matsala dan an baku abinci, sauran kayanta zan aikama Likita dasu saboda arika kula da tsaftar ta, idan akwai wad'an da ya kamata abayar zan fad'a masa ya aika dasu gidan marayu, haka kayan Alhaji duk zan tafi dasu, idan Ra'eez ya d'auki wanda yake so sauran za'a bada sadakarsu dan banga amfanin ajesu ba, sauran abinda yake da amfani duk zamu tafi dasu, kaya masu nauyi ne kawai zamu bari nasan babu abinda zai samesu, domin munyi magana da Alhaji Musa yace zai kawo maigadin da zai zauna agidan sai na rik'a biyanshi saboda Madu yace bazai iya zama ba.


Halima tace mungode sosai, Allah ya biyaka da alkhairinsa, kuma insha Allahu zan rik'a zuwa duba Ummun Ra'eez sai ka fad'a mani sunan asibitin.


Alhaji Mansur yace sai dai muje tare domin likitan ya ganki, dan na fad'a masa kada ya yarda da kowa, tunda gaki ke kad'aice wadda zata rik'a zuwa wajenta dan ina jin tsoron a illata ta. Maman Labiba tace wannan haka yake.


Tashi yayi yana fad'in bara muje mu fara da wuri dole ma sai gobe zamu tafi saboda mu gama komai, tunda ga mota Alhaji Musa ya bani nayi zirga-zirga da ita gara na gama, idan zamu kawo kayan abincin sai ki shirya muje can asibitin. Halima tace shikenan sai kunzo.


**

Duk wani abu mai muhimmanci na takardun Alhaji sai da suka had'asu a cikin akwati, kayansa kaf sun had'a, dama shi Alhaji Maiwada baya tara sutura, da yayi d'inki yake bayar da wasu dan baya son tara kaya.


Haka kayan Ummu duk sun had'a mata, sai kayan abinci suka had'a komai sukasa amota. Madu sai kuka yakeyi. Suna cikin had'a kaya sai sukaji sallamar Ladi.



Bayan tashigo sai tayi turus, kada dai abinda takeji gaskiya ne? Tunda ta shigo Lagos a mota take jin ana wani labari, sai dai bata gazgata ba. Ganin Madu yana kuka yasa tayi saurin matsowa tana tambayarsa.


**

Kuka kawai Ladi takeyi bayan da ta gama jin komai. Maman Labiba tace sai hak'uri Ladi, haka Allah ya tsara bamu da hanyar kaucewa. Ladi tace ikon Allah, wannan abu da me yayi kama? Da zan tafi dubu ashirin Alhaji ya bani kud'in gudummuwa Hajiya ta k'ara mani goma ashe shikenan rabuwar kenan, ya Allah kajik'an Alhaji, itama kuma Hajiya Allah ya bata lafiya, Malan Sani kuma Allah ya saka mashi.


Gaba d'aya suka amsa da amin. Ladi tace dan Allah kuje dani na gano Hajiya, shikenan yanzu dole na koma gidana amma insha Allahu bazan manta da alkhairinsu ba. Alhaji Mansur yace shikenan bara mu k'arasa sai mu tafi.


Ladi tana kuka haka ta tayasu had'a kaya, sun bata wasu kayan abincin hada wasu kayan Ummu Maman Labiba ta bata. Alhaji Mansur yace zaije ya ciri kud'i sai ya basu na sallamarsu. Haka suka rufe ko ina bayan sun zare mahad'ar wutar gidan, dama kuma wutar kati ce.


Bayan sun fito suka rufe gate d'in gidan suka tafi hada Madu, Alhaji Mansur yace idan ya dawo anjima sai ya bama Alhaji Musa mukullin gate d'in da motarsa tunda a hotel zasu kwana saboda da wuri zasu tafi.



Sai da suka aje kayan sannan suka d'auki Halima suka nufi asibiti. A mota sai jajanta ma Halima Ladi takeyi tana fad'in tunda unguwarsu babu nisa bazata yarda zumunci ba.


***

Kallon su kawai Ummu takeyi, domin tunda ta farka bata magana sai kallon mutane. Ganin su Halima da Ladi suna kuka yasa itama ta fashe da kuka. Girgiza kai Dr. Saddik yayi yana fad'in abinda takeyi kenan tunda ta farka, idan ta gama kallon mutum sai kawai ta fashe da kuka.


Alhaji Mansur yace yaushe ne za'a maidata can? Dr. Saddik yace nan da kwana biyu idan ta k'arasa warwarewa.


Alhaji Mansur yace ga Halima nan itace Matar Malan Sani, idan ba ita ba kada abar kowa yazo wajenta. Dr. Saddik yace wannan ba damuwa, zan amshi lambarta kome kenan zan rik'a mata bayani. Alhaji Mansur yace mungode likita.



Haka suka gama ganinta ba tare da tace masu komai ba suka tashi zasu tafi bayan sun aje akwatin kayanta. Har sun kai k'ofa sukaji muryarta tana fad'in Abbun Ra'eez sun kashe shi, akira mani Ra'eez kada su kashe mani shi. Saurin juyowa sukayi gaba d'aya.


Shiru tayi sai kuma ta fashe da kuka tana fad'in duk saina kashe su da wuk'ar makka. Hatta da Alhaji Mansur sai da kwalla ta cika masa ido, jiki a sanyaye suka bar d'akin. Dr. Saddik yace kada ku damu, dama fatana ta fara magana, tunda ta fara sai mugodema Allah, insha Allahu zata samu lafiya. Alhaji Mansur yace mungode sosai. Haka sukayi mashi sallama suka tafi.


**

Bayan Alhaji Mansur ya ciro kud'i yayi masu sallama mai tsok'a, godiya sukayi mashi Madu yace zai tafi. Alhaji Mansur yace wai Madu yanzu ina zakaje? Madu yace zanje na nemi wajen da zan zauna kuma.


Da sauri Halima tace idan zaka yarda ka zauna a shagon waje na gidan mu hakan zai zamar mana tsaro musamman yanzu da babu namiji agidan dan Allah.


Jinjina kai Alhaji Mansur yayi yana fad'in maganar ki gaskiyace, abinda zuciyata take tunani kenan. Dan Allah Madu ka zauna hakan zai zame masu kariya, kaga akwai Rumaisa, kuma kana da amana ka zama tamkar d'an uwa agaremu, duk da wanda ya had'amu baya raye be kamata mubar abinda ya had'a ya lalace haka ba.


Jinjina kai Madu yayi yana fad'in shikenan zan zauna sai na rik'a biyan kud'in haya. Halima tace wallahi bazamu amsa ba, kayi zamanka har mutuwa ta raba babu wani abu, dama mutanan unguwar sun saba ganinka agidan, dan ka dawo ba wani abu bane, tunda shagunan biyu ne sai ka bud'e shagon saida abubuwa a d'ayan dama Malan Sani yana so ya bada hayarsa, tunda ga yanda komai ya kasance sai kawai kayi amfani dashi saboda kada ka zauna haka, akwai band'aki a cikin d'ayan shagon sai ka d'aukeshi a d'akin ka.


Alhaji Mansur yace wannan haka yake, kuma bana so kace a'a. Madu yace shikenan nagode da wannan abu da kukayi mani, wallahi da zan iya zama agidan Alhaji da bazan bari wani ya zauna ba, kawai idan na zauna hankalina bazai kwanta ba, amma nine yafi cancanta na zauna na rik'e amanar gidan, amma duk da haka zan rik'a kula da gidan bazan bari wani abu ya sameshi ba, saboda wanda za'a ba gadin gidan abokina ne agidan Alhaji Musa yake gadi su biyu ne.



Alhaji Mansur yace bakomai Madu na fahimceka, kunyi sabo sosai da Alhaii, dama nasan bazaka iya zama agidan ba, hakan ma da zakayi yayi, dan haka zan fad'ama Alhaji Musa kaine zaka rik'a kula da gidan. Madu yace nagode.



Bayan sun aje su aka bud'ema Madu shagunan domin ya gyara, katifarsa daya d'auko da kayansa ya shigar dasu ciki kafin ya gama gyara. Ladi kuwa sallama tayi masu tana godiya kafin ta sake zagayowa saboda basu da nisa.


Kud'i Alhaji Mansur ya bama Halima masu yawa yana fad'in idan zaiyi aike zai turoma Dr. Saddik sai yarik'a bata tunda bata da account. Godiya tayi masa kafin suka fita.


A mota yake fad'ama Maman Labiba zasuje ya kama d'aki sai ya barta ta huta yana so yaje yaga Mr. Kallah yasan gobe zai koma abuja, duk da sune suka kashe Alhaji amma shine shugabansu ta hanyarsa za'a samu kud'in Alhaji su fito cikin sauki, kuma idan yaga yaje wajensa da maganar zaifi maida hankali kodan su fita daga zargi.


**

Bayan ya kama d'aki suka shiga, wanka ya farayi kafin yayi sallah yasa aka kawo masu abinci sukaci. Tashi yayi yana fad'in ta kulle zaije ya dawo. Addu'a tayi masa kafin ya nufi wajen Mr. Kallah.


Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:38 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shoot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*



2⃣0⃣


Gaba d'aya kunya ce ta rufe Mr. Kallah, ji yake kamar Alhaji Mansur zai gano su, da kyar yasa jarumta aranshi. Canza fuska yayi zuwa kalar tausayi yace yanzu shikenan fa, har yanzu na kasa mantawa da mutuwar Alhaji Maiwada, shiyasa muka tsaya sai da aka yanke ma direbansa hukunci domin munyi zaman amana da Alhaji.


Alhaji Mansur yace an dai yanke hukunci, amma wad'an da suke da laifi ai sun san kansu dan wata shari'ar sai alahira.


K'warewa Mr. Kallah yayi da sauri ya d'auki ruwa yasha. Murmushi Alhaji Mansur yayi yana fad'in sannu. Kai Mr. Kallah ya d'aga yana fad'in yanzu meke tafe da kai? Alhaji Mansur yace akan maganar kud'in Alhaji Maiwada ne.


Jawo takarda Mr. Kallah yayi yana fad'in wannan baka da damuwa, Alhaji Maiwada na mu ne, dole mu tsaya komai nashi ya fito. Yanzu ka bani lambarka kome kenan zamuyi magana, amma ina tabbatar maka kud'inshi bazasu dad'e ba nayi maka alk'awari.


Jinjina kai Alhaji Mansur yayi yana fad'in nagode sosai, kawo wayar taka nasa maka lambartawa. Bayan ya gama saka masa yayi masa sallama, har bakin mota Mr. Kallah ya rakoshi.


Yana tafiya ya saki ajiyar zuciya. Ciki ya koma yana lalaubar lambar Alhaji Marusa. Yana d'agawa Mr. Kallah ya fad'a masa yanda sukayi da Alhaji Mansur.


Alhaji Marusa yace abokina kasan yanda zakayi komai ya fito cikin lokaci, bana son asake tada maganar Alhaji Maiwada, gara a sallamesu nasan bazai sake zuwa garin nan ba.


Mr. Kallah yace amma ina tsoron matarsa ta warke ta tona mana asiri. Alhaji Marusa yace ai babu abinda ta sani, iyaka tace Malan Sani beyi mata abinda aka fad'a ba, amma bazata k'aryata kisan da muka d'ora masa ba, idan kuma kana ganin akwai matsala itama tabi bayan mijinta kawai.


Da sauri Mr. Kallah yace haba Alhaji, wai wace irin zuciya kake da ita ne haka? Kai kisa baya maka wahala, kada kamanta rayuwaka biyu muka kashe fa, dan Allah kabar wannan maganar, shikenan bani da wata damuwa akan matarsa abarshi ahaka gobe ma zan koma abuja daga can zanje waje nayo sati biyu dan na samu natsuwa.


Dariya Alhaji Marusa yasa yana fd'in abokina kacika tsoro, nifa akan dukiyata babu abinda bazan iya ba, dan haka kadena sako mani maganar wata matsala. Mr. Kallah yace shikenan na dena. Sallama sukayi Alhaji Marusa yana ta tsokanarsa.


****

Wai Maman Naseer baza kici abincin ba, haba dan Allah, ya kike so nayi ne, ga rashin Naseer ke kuma kina so ki jefa kanki cikin damuwa.


Hannu tasa ta goge idonta tana fad'in yanzu shikenan haka zamu bar wad'an da suka kashe Naseer susha banza kenan Baffan Naseer, kana gani wanda aka kashe su a rana d'aya har an yankema makashin hukunci amma mun kasa tab'uka komai sai kace an kashe mana karan gida.


Hannunta ya kamo yana fad'in Hajiya Zainabu Abu kenan, wani lokacin mata k'aramin tunani gare ku, shi wanda aka yanke ma hukuncin kinsan irin hujjojin da aka gabatar ma kotu kuwa? To bari kiji, duk da banje kotu ba a labarai naji yanda shari'ar ta kasance, hatta da lauyen da ya tsayama Alhaji Maiwada sai da aka bashi lambar yabo domin ya gabatar da shedu kwarara wanda a kowace kotu akaje dole ta amshe su, kinga kuwa bazamu had'a kanmu da su ba.


Ni na barma Allah akan mutuwar Naseer, domin nasan zamusha wahala ne kawai idan mukace zamu nemo wad'an da suka kashe shi, domin babu wata alama da aka bari a mutuwar Naseer, ko Waye ya kashe Naseer ba k'aramin makashi ba ne, abinda nake so da ke kema ki barma Allah sai ya saka mana.


Jinjina kai tayi tana fad'in shikenan Baffan Naseer tunda ka fad'i haka, insha Allahu bazan sake d'aga maganar ba, dama su biyu Allah ya bamu koma waye ya aikata hakan zan cigaba da addu'a Allah ya tona asirinsa.


Baffa yace amin Zainabu. Murmushi tayi tana goge fuskarta. Sallamar Yayan Naseer ce tasa suka kalli k'ofar tare da amsawa. Zama yayi yana fad'in sannun ku da gida. Baffa yace yauwa sannu *RAFIK*.


Maman Naseer tace ga abincinka a kicin ka d'auko kaci ina kaje haka ne? Kallonta yayi yana fad'in Mama kinci naki ko? Baffa yace ina fa taci, yanzu nake mata magana kasan yanda tasa damuwa akan rashin gano wanda ya kashe Naseer aranta.


Maman Naseer tace baka bani amsata ba. Rafik yace naje wajen Junaidu ne nayi masa gaisuwa kinsan makarantar mu d'aya shima k'aninsa ne aka tsinci gawarsa an kashe shi da wuk'a kuma d'an makarantar su Naseer ne, shine naje nayi masa gaisuwa kinsa abokina ne abu iri d'aya muke karantawa ma.


Baffa yace ikon Allah, dama fa naji ana sanarwa a masallaci an kashe d'an makarantar su Naseer har nake cewa nazo gida naji ko Naseer yasan shi ashe nima bazan iske nawa d'an ba, ya Allah ka tona asirin ko suwa suke aikata wannan mugun abun, ace duk lokaci guda akashe mutum ukku.



Maman Naseer tace shiyasa nake damuwa da mutuwar Naseer, ina ma akwai wata sheda da mun shiga kotu. Rafik yace haba Mama mu barshi da Allah kawai, wahala zamusha idan mukace zamu shigar da k'ara domin babu sheda, Allah yajik'an Naseer ya bamu ikon jure rashinsa kawai, gashi yau har anyi sadakar ukku ma.


Baffa yace amin dai. Yaushe zaka koma makaranta? Rafik yace sai anyi kwana bakwai sannan, shima saboda mun kusa fara jarabawa ne. Baffa yace wannan karatu naku akwai wahala ko? Rafik yace da sauki Baffa, idan muka dawo sai munyi (IT) kafin mu koma.


Baffa yace lallai kace zaka fara karanto labarai. Rafik yace da saura dai, ai yanzu muka fara baza'a bamu karanta labarai ba, zamu dai je muga yanda akeyi.


Mama tace ina ruwan Rafik d'an jarida. Dariya sukayi Baffa yace zamusha tambaya dai. Rafik yace Baffa ai sai a wajen aiki ake surutu amma agida wazan ma tambaya. Baffa yace Allah dai ya taimaka ya cika maka burinka ka zama cikekken d'an jarida. Gaba d'aya suka amsa da amin.


**** ****

Washe gari tunda wuri suka bar kano cike da kewar su Alhaji Maiwada. Alhaji Mansur sai da yayi kwalla lokacin da jirginsu ya tashi saboda tunowa da amininsa kuma d'an uwansa.


***

Koda Halima ta gama abincin safe sai ta zuba ma Madu ta bama Rumaisa ta kai masa. Da fara'a Madu ya amsa gaisuwarta yana fad'in hada abinci haka, to kice mata nagode sosai.


Bayan ta koma taci abincinta Halima tace Rumaisa ki maida hankali akarantun ki kinji, kinga Babanki yace idan baki karatu zaku b'ata. Rumaisa tace Mama yaushe Baba zai dawo to? Halima tace Babanki yayi tafiya shida Abbun Ra'eez zuwa wata k'asa bazasu dawo ba sai kunyi girma.


Dariya Rumaisa tasa tana fad'in zasu kawo mana tsara ko? Halima tace sosai kuwa, ke dai ki maida hankali kiyi karatu, babu ruwanki da k'awa kiyi rayuwarki ke kad'ai domin k'awaye gori garesu, ko tashi akayi kada ki tsaya kowa kiyi tahowarki kinji.


Kai ta d'aga tana fad'in ai babu ruwana da kowa idan akayi break ma ni kad'ai nake zama naci abincina, kuma kinga Auntyn mu tace saura sati biyu muyi hutu da mun dawo zamu shiga aji biyar ai kinga mun kusa gamawa.


Halima tace sosai ma kuwa, shikenan sai atafi wata makarantar. Rumaisa tace to Mama zan tafi kada amun duka. Halima tace Allah ya ba da sa'a kiyi addu'ar fita daga gida kinji, kuma duk wanda ya tare ki yana maki tambaya akan Babanki ko kallonsa kada kiyi, kome zaice kitafi kada kitsaya duk karya sukeyi kinji. Rumaisa tace to bazan tsaya ba.



Bayan Halima ta gama karyawa sai ga Sister Hassana tashigo dan su gaisa. Zama tayi suka gaisa, bayan sun gama gaisawa tace Maman Rumaisa ashe haka abu ya kasance kuma? Duk'ar da kai Halima tayi tana kok'arin maida kwallar data taho mata.


Sister Hassana tace Allah ya kyauta gaba, dan Allah Maman Rumaisa kada kisa damuwa aranki, wallahi har cikin raina ban yarda da abinda akace Malan ya aikata ba, kinsan dama haka aikin Kwastam yake, matuk'ar zakayishi da gaskiya dole ka samu makiya musamnan masu kud'i, dan haka kicigaba dayi masa addu'a wata rana gaskiya zata fito, Allah ya baki ikon jurewa.


Halima tace amin nagode Sister Allah ya bar zumunci. Sister Hassana tace amin. Ina so duk abinda kike da buk'ata kiyi mani magana matuk'ar befi k'arfina ba zanyi maki, ina fatan kina shan maganin ki? Halima tace ina sha, sister tace yauwa, idan yashiga watan fara zuwa awo sai ki fara insha Allahu babu abinda zai gagara.


Halima tace nagode sosai. Dubu biyu Sister Hassana ta aje mata tana fad'in zan wuce sai na dawo. Halima tace nagode sister Allah ya saka da alkhairi tace amin.


Har ta juya ta dawo tana fad'in yauwa wannan mutumin da nagani a shagon k'ofar gida kamar ina ganinsa yana zuwa wajen Malan ko? Kai Halima ta d'aga mata kafin ta bata labarin yanda akayi.


Murmushi Sister Hassana tayi tana fad'in amma gaskiya ya kyauta, irin wad'annan mutanan ba'a barinsu domin

21 / 54