Author : Marubuciyar Zamani Category : Complete Novels
Alhaji Barau yace wallahi nima abinda ya tsaya mani kenan. Alhaji M. Sanda yace ai nasan mahaifin Naseer ko alokcin da abun ya faru da naje gaisuwa yace bazai b'ata lokacinsa wajen shigar da k'ara ba ya barma Allah, dole akwai wanda yake bayan wannan abun kuma zan bincikoshi.
Alhaji Barau yace ka taimaka mana, bani da sauran wata dabara domin na fiku shiga tashin hankali saboda nine Alkalin kotun.
Jinjina kai Alhaji M. Sanda yayi yana fad'in wannan maganar bata waya bace, ka sameni agida, shima lauyen dole mu siyeshi.
Alhaji Barau yace nagode, amma gobe ana buk'atar Fawwaz yazo Alhaji. A tsawace Alhaji M. Sanda yace kasan abinda kake fad'a kuwa Barau? 'Dan nawa ne zaizo kotu ayimasa tambaya, idan ma mafarki kakeyi to ka farka, duk duniya babu wanda ya isa yasa Fawwaz yaje kotu, ka sani ma daga yanzu zan fara nema masa visa ya koma inda ya fito.
Jiki a sanyaye Alhaji Barau yace ayi hak'uri Alhaji sai nazo. Kashe wayar yayi. Hannu Alhaji Barau yasa ya dafe kanshi, wane irin tashin hankali ne haka ya kunno masu kai lokaci guda? Yanzu yazeyi gobe idan akazo babu Fawwaz? Murmushi ya saki yana fad'in nasan Alhaji bazai tab'a bari asirinmu ya tonu ba domin shima yana ciki, bakomai zanje muyi yanda zamuyi, bazan bari ayi saurin gano ni ba, da haka zan shiriritar da shari'ar.
Kayansa ya fara had'awa yana kokarin kiran Mr. Kallah.
**** ****
Fawwaz ina passport d'inka yake? Fawwaz yace wallahi Dady tunda na dawo ban sake bi ta kanshi ba saboda naji kunce bazan sake komawa ba na dawo kenan, Allah yasa ban had'a dashi cikin takardun da nasa akonasu ba.
Alhaji yace kana da hankali kuwa Fawwaz? abu mai muhimmanci zakace baka san inda ka ajeshi ba. Zama Ammi tayi tana fad'in yau kuma meya had'o Alhaji da 'Dansa? Tsaki Dady yayi yana fad'in ki barni dashi kawai.
Matsowa Fawwaz yayi yana fad'in Dady ka fad'a mani abinda yake faruwa dan Allah. Ido Alhaji ya tsura mashi, wani irin tausayinsa ya kamashi, da sauri ya kamoshi ya rungume. Ammi da jikinta yayi sanyi ta matsa tana fad'in Alhaji akwai abinda yake faruwa, tunda har yau ka iya yima Fawwaz fad'a tabbas nasan akwai abinda yake faruwa.
'Dagowa yayi yana fad'in Fawwaz ka shirya zaka bar k'asar nan cikin satin nan, kuma bana so ka sake dawowa, idan muna buk'atar ganin ka zamu kai maka ziyara, ka zab'i wadda kake so ayi maku aure domin can rayuwar ka zata koma.
Farin ciki ne ya cika Fawwaz nan ya hau murna, sai dai ganin damuwa fal a fuskar Dadynsa yasa jikinsa yayi sanyi, hannunshi ya kamo yana fad'in amma Dady wannan canjin na lafiya ne? Kauda kai Dady yayi yana kok'arin cire damuwar da take fuskarshi.
Ammi tace dole akwai wani abu, nifa jikina yana bani akwai matsala, dan Allah kayi mana bayani sai kaga an samu mafita.
Kallon Fawwaz yayi yana fad'in ina abokan ka da kukayi secondary atare? Fawwaz yace Adnan da Sufwan, ai Sufwan na fad'a maka ya rasu lokacin bana k'asar ma, amma Adnan yana nan har yayi aure ko rannan mun had'u har ya bani haushi dan ya tuno mani da abinda ya faru muna makaranta, shiyasa ni yanzu ba ruwana dashi saboda naga ya canza hali tun bayan gama makarantar mu, ya koma wani ustaz.
Da sauri Alhaji yace a ina yake da zama? Fawwaz yace ni bansani ba na fad'a maka ba ruwana dashi fa. Jinjina kai Alhaji yayi yana fad'in wace magana ya tuna maka? Fawwaz yace akan abinda ya faru tsakani na da Farouk ne yake fad'in waishi yana cikin damuwa da abun.
Ammi tace ko Farouk d'in da kayi mafarkinsa rannan? Fawwaz yace shifa. Cije baki Alhaji yayi yana gyad'a kai. Ammi tace towai meya faru? Alhaji yace case d'in Fawwaz ne ake kok'arin maidowa ko kuma ince an maido dan yau aka fara shari'ar a kotun Alhaji Barau, kuma ana buk'atar Fawwaz yaje kotu gobe.
A zabure Fawwaz ya mik'e yana fad'in Dady mene? Dan Allah Dady kada ka bari a kashe ni, wallahi nasan kashe ni zasuyi dan Allah Dady. Kuka yasa mai ban tausayi.
Jikin Ammi ne ya fara rawa jin abinda Fawwaz yace, tashi tayi ta kamoshi tana fad'in babu wanda zai kashe ka Fawwaz, ba dai kace ba kai bane ka kashe shi ba.
Zama yayi jiki a sanyaye dan ya tuna lokacin da abun ya faru Dady ya hanashi ya fad'a mata gaskiya saboda sun san halinta bata goyen bayan zalunci, shiyasa suka fad'a mata daga fad'a aka rabasu shikenan aka tsinci gawarsa a wajen gari.
Alhaji yace matuk'ar ina numfashi babu wanda zai kaika kotu ma bare har ayanke maka hukunci, dan haka ka fara shiri zaka bar k'asar gaba d'aya.
Ammi tace tunda har da gaskiyarshi meye za'a turashi wata k'asa, idan ya tafi kowa zaice beda gaskiya, babu fa wanda zai masa komai tambayarshi kawai za'ayi ya fad'i abinda ya sani.
Alhaji yace amma baki da hankali Ammi, yanzu kina ganin zan bari Fawwaz yaje kotu domin bada sheda ne, to wallahi kisama bakin ki linzami akan wannan maganar matuk'ar kina so mushirya dake, babu ruwanki da inda zaije, idan zaki iya kije ki bada sheda tunda ai kinsan abinda ya faru.
Tashi yayi yaja Fawwaz suka fita waje. Ajiyar zuciya Ammi tayi tana fad'in ikon Allah, lallai duniya babu gaskiya, na dad'e ina tunanin akwai abinda yake faruwa sai yanzu na k'ara tabbatarwa, yau da ace bani na haifi Fawwaz ba sai nayi kuka akan wannan iko, amma bakomai, koma menene bazan fasa mashi addu'a ba, ya Allah ka tabbatar da abinda yafi alkhairi.
A waje Alhaji yace ma Fawwaz ya kake ganin za'ayi da Adnan? Fawwaz yace nasan ko banje ba shi zaije kuma zai bada amsar abinda aka tambayeshi bazai b'oye ba, domin nasan tabbas shine zaisa amaido shari'ar baya domin duk duniya shi kad'ai ne ya rage wanda yasan maganar, ina ganin Dady a hanashi zuwa kotun kawai.
Alhaji yace ba kotu zan hanashi zuwa ba, idan yayi wasa zai bi Naseer inda yaje, ashirye nake na kawar da duk wanda zai kawo mana gargada, domin ban shirya jin kunyar duniya ba, matuk'ar wannan abun ya fasu dole muma zamu shiga ciki, dan haka zansa a saceshi.
Fawwaz yace hakan yayi Dady, ka bari nasa abokaina su sace manishi. Alhaji yace wannan aikin ba naka bane, bana so ma ka saka wasu abokan ka aciki saboda maganar sirri ce, wad'an da suka fara aikin su zasu k'arsashi.
Fawwaz yace nagode Dady, nasan idan kana nan bazan tab'a kuka ba. Murmushi Alhaji yayi yana shafa kanshi.
**** ****
Abbah kamar akwai abinda yake damun ka, tunda muka taho daga kotu nake ganin damuwa a fuskar ka, gashi kuma dama da kyar ka iya tashi a kotu muka taho.
Nabeel nima abinda na fahimta kenan, yau kusan kwana ukku kenan ina ganin canji agurinshi. Nabeel yace wallahi Umma akwai abinda yake damun Abbah kawai bazai fad'a mana ba.
Gyara zama Abbah yayi yana zare glass d'in idonshi, kallonsu yayi yana jin wani nauyi aranshi, taya zai kalli Iyalinsa ya fad'a masu irin abinda yayi, wata zuciyar tace ai gara ka fad'a masu da suna zaune a gano ka.
Wasu zafafan hawaye ne suka zubo mashi, hannu yasa ya goge idonshi, kallonsu yayi yana fad'in kuyafe mani na ciyar daku haram, son zuciya ya hanani na gane illar abinda na aikata ba dai-dai bane, amma na d'aukeshi a matsayin k'addarata, yanzu zan baku labarin abinda na aikata tsahon shekaru shabiyu da suka wuce, amma ina rokon ku da ku yafe mani....
**** ***
*Safiyar Talata a kotu*
Tafe suke a hanya zasu isa kotu, Jabeer yace wai har yanzu likita be kiraka ba? Ra'eez yace na kirashi d'azu yace allurar da akayi mata zata d'auketa kwana biyu saboda suna buk'atar ta huta, kaga kafin lokacin mun kammala wannan shari'ar.
Jabeer yace nakira Adnan wayarsa a kashe sai ta Nabeel na samu yace mun yana hanya yaje wajen aikinsu. Ra'eez yace kila ko rashin caji ne, amma nasan zaizo dan yasan yau ne zamu buk'aci ganinshi.
Lokacin da suka isa kotun sun iske har wasu mutanan sunzo. Jabeer yace dad'ina da mutane akwai sonjin ya akayi. Ra'eez yace har bakin fuska sai ka gani yau, domin duk wanda aka fara shari'ar dashi jiya dole yaso dawowa yau hada k'arin wasu ma.
Bayan da kowa yashiga kotu sai ga Alkali ya iso, duk da k'asan zuciyarsa akwai tsoro amma kasancewarsa tsohon lauya yasa yayi kok'arin b'oye damuwarsa, idan kaganshi tamkar besan komai ba, duk da Alhaji M. Sanda ya k'arfafa masa guiwa amma yana shakkar abinda zai iya biyo baya.
Bayan da yashigo kowa ya nutsu, zama yayi bayan ya kammala abinda yake ya buk'aci Magatakarda daya maimaita shari'ar da sukeyi.
Bayan Magatakarda ya karanto shari'ar Alkali ya kalli mutane yana fad'in ina fatan anzo da Fawwaz M. Sanda gaban kotu? Tashi d'aya daga cikin mutanan da sukaje gidansu Fawwaz yayi yana fad'in ya mai shari'a Fawwaz baya k'asar nan kusan sati biyu.
Jinjina kai Alkali yayi yana fad'in ina lauya mai kare wad'anda suke k'ara? Tashi Ra'eez yayi yana risnawa. Alkali yace zaka iya cigaba da gabatar da shari'ar, sai kaje ga sheda ta gaba saboda wanda ake nema kunji baya k'asar, idan har shari'ar dole tana buk'atar zuwanshi dole sai an maido dashi.
Murmushi Ra'eez yayi a zuciyarsa jin wani sabon rainin hankali, jinjina kai yayi yana fad'in ya mai shari'a abisa binciken da mukayi tabbas Fawwaz yana k'asar nan sai dai idan a jiya ya barta, amma ko daren lahadi mun had'u dashi a wajen siyayya duk da shi bai sanni ba, nayi mamakin da akace wai yafi sati baya k'asar.
Alkali yace ko kana da shedar da zaka tabbatar ma kotu cewar Fawwaz yana k'asar nan? Kai Ra'eez ya girgiza yana fad'in bani da ita ya mai shari'a. Alkali yace wata kila bashi ne ka gani ba, domin nasan mutanan dana aika kiransa bazasu fad'i k'arya ba, shiyasa nace idan har akwai buk'atar zuwansa ko ina yaje kotu tana da ikon da zatasa shi ya dawo, zaka iya cigaba.
Gaba d'aya mutane suka jinjina adalci irin na Alkali.
Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in ya mai shari'a zanso kotu ta bani dama domin nayima Alhaji Sulaiman tsohon shugaban makarantar kings college tambaya.
Dam!!! Gaban Alkali ya bada wani sauti jin abinda Ra'eez yace, tsura mashi ido yayi aranshi yana jinjina tsabar iya aiki na Ra'eez, wato ya shiryama wannan shari'ar, sam sun manta da Alhaji Sulaiman da tun jiya sun sake rufe mashi baki da kud'i, amma yasan bazai yi kok'arin tona masu asiri ba saboda shima yana da laifi.
Ajiyar zuciya ya saki yana fad'in kotu tana buk'atar Alhaji Sulaiman ya fito gabanta.
Ido Alkali ya saki yana jiran yaga tashinsa. Juyawa Ra'eez yayi yana kallon inda Nabeel yake zaune dan yasan jiya akusa dashi ya zauna, sai dai abun mamakin babushi a wajen sai kujerarsa wadda Nabeel ne ya kama masa ita tun bayan da yazo dan ya barshi yana shiryawa shi kuma sai da ya biya wajen aikinsu daga can ya wuto.
Tashi Jabeer yayi ya isa wajen Nabeel, atare suka fita waje. Alkali yace ko dai shima baizo ba? Kai Ra'eez ya jinjina jiki a mace. Alkali yace da alama ba'a shirya wannan shari'ar ba, sai kaje ga sheda ta gaba.
Jiki a sanyaye Ra'eez yace ya mai shari'a sheda ta gabama bai k'araso ba, kuma wayarsa akashe. Murmushin farin ciki Alkali ya saki a zuciyarsa, sai yanzu ya kuma gazgata maganar Alhaji M. Sanda.
Kallon mutane yayi yana fad'in da alama wannan shari'a tazo da wani salo, idan har babu kwararan hujjojin da za'a iya gabatar ma kotu babu amfanin a tara mutane kuma ab'atama kotu lokaci, saboda adalci na wannan kotu yasa ta amshi wannan shari'ar, domin case ne tsoho wanda shekarun da akayishi suke da yawa, sai gashi kuma kun kasa tabbatar da abinda zaisa abima mutane hakkinsu, dan haka tunda har kuka kasa gabatar da wata kwakkwarar hujja agaban kotu, kotu ta....
Dan Allah ya mai shari'a ina buk'atar a k'ara mana lokaci, tabbas akwai abinda yake faruwa, domin shedun nan akwaisu, amma gashi anzo kotu basu k'araso ba, ina rokon wannan kotu mai adalci data d'age wannan shari'ar domin mu samu damar gano abinda yake faruwa.
Alkali yace wannan kotu mai albarka zata maku lazimin d'age shari'ar nan zuwa jibi alhamis, matuk'ar kuka sake dawowa da irin haka tabbas kotu zatayi watsi da wannan shari'ar, kuma zata soketa baza'a sake amsarta a ko ina ba. Kottt!!!!
Cikin hanzari Ra'eez ya had'a kayanshi yayi waje, bayanshi Rafeek yabi shima yana tunanin dalilin da yasa Adnan da Abban Nabeel basu zo ba, bayan kuma ajiya Nabeel ya fad'a masa Abbansa ya amince zai zo ya fad'i gaskiya.
Haka kowa ya fito yana jinjina ma Alkali bisa wannan adalci nashi, yayin da wasu suke ganin kamar shari'ar bazata d'ore ba saboda an kasa gabatar da hujja, haka kowa ya watse wasu suna fad'in bazasu sake dawowa ba tunda abun shirme ne.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:41 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
4⃣2⃣
Wai me yake faruwa Nabeel? Wallahi nima ban sani ba, domin munyi waya da Abbah yace mun ya fito daga gida ya taho, bayan dana iso naga bai zo ba nakira wayarsa bata shiga na d'auka matsalar network ne shiyasa banyi wani abu ba, ga Adnan ma wayarsa gaba d'aya akashe.
Shiru sukayi Ra'eez yace dama nasan da wuya mu kwashe da sauki a wannan shari'ar, domin da manyan mutane abun ya had'o dole sai mun hada' da 'Yan sanda amma amintattu.
Rafeek yace tabbas zargin da nakeyi ya tabbata, Ra'eez kaje ka samu Alkali ni nasan suna buk'atar ka, ina so kayi amfani da wannan damar ka k'ara samun wani abu, nasan dole Alhaji M. Sanda yayi wani abu, kuma k'arya ne ace Fawwaz baya k'asar.
Ra'eez yace wallahi na ganshi. Jabeer yace yanzu ya zamuyi? Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in zanyi magana da abokina inspector Hamza nasan zai taimaka mana, kome ake ciki bazamu bari Fawwaz ya bar k'asar nan ba, dan nasan ayanzu suna gab da fitar dashi, dole muyi wani abu matukar muna son a kammala shari'ar cikin sauki.
Ra'eez yace haka za'ayi, yanzu bara naje wajen Alkali, Jabeer kai da Nabeel kuje abi maku diddikin layin Abbah da Adnan, kafin nan Yaya yaje wajen Inspector Hamza sai kuyi magana dashi dole muna buk'atar 'yan sanda saboda kada a cutar dasu Abbah. Kai suka jinjina gaba d'ayansu.
Wucewa yayi ofis d'in Alkali yayinda Alhaji Mansur suke zaune a mota shida Kawun Jabeer suna tattaunawa.
***
Wallahi Alhaji dole na sara maka, sai yanzu na yarda da maganar ka, tabbas kai d'in kwararre ne, amma abinda ban gane ba, gashi dai kace Adnan kawai za'a sace sai kuma gashi Alhaji Sulaiman bezo kotu ba, kuma alamu sun nuna zai zo d'in saboda sunce ya taho.
Murmushi Alhaji M. Sanda yayi yana fad'in kana wasa dani Alhaji Barau, na fad'a maka duk wani wanda naga zai kawo mana tasgaru a wannan tafiyar zanyi komai dan na kaudashi.
Bayan tafiyarka jiya na zauna ina wani tunani, nasan dole sai an buk'aci ganin shugaban makarantar su Fawwaz, gashi kuma bamuyi wata magana dashi ba hakan yasa zuciyata bata amince abarshi ba, hakan yasa na turama Lucky kwatancen gidanshi nace shima a d'aukemunshi idan ya fito zai taho kotu, yanzu haka suna wajen su Lucky nace sujirani a kammala shari'ar kafin a aiwatar masu, dan yanzu idan aka kashe su wata sabuwar shari'ar ce, kaji yanda nayi dashi.
Jinjina kai Alhaji Barau yayi yana fad'in yanzu kam hankali na ya kwanta, abinda ya rage na kira Ra'eez na siyeshi domin yayi watsi da shari'ar.
A'a kada kayi haka Alhaji Barau, na fad'a maka zuciyata bata kwanta da wannan yaron ba, k'wazonshi yayi yawa, basirarsa baiwace daga Allah, kuma nasan bazai tab'a amincewa da cin hancinka ba, dan haka ka barshi kada kayi abinda zaisa ya gane ko kai waye, dole sai yana da shedu sannan zai gabatar da shari'ar, kuma jibi ne za'a kammala komai, dan haka ka barshi, idan yazo ma ka k'arfafa masa guiwa. Alhaji Barau yace shikenan nagode.
Kwankwasa k'ofar da akayi tasa yayi saurin kashe wayar, izinin shigowa ya bada hakan yasa Ra'eez ya shiga. Bayan ya zauna Alhaji Barau yace sannu da kok'ari Ra'eez, gaskiya kana kokari akan wannan shari'ar, shiyasa ma na kaita zuwa alhamis saboda ka samu damar kammala sauran shedun ka, maganar Fawwaz kuma idan har yana da laifi dole a maidoshi.
Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in nagode Alhaji, nasan ai saboda nine kayi haka kuma naji dad'i. Alhaji Barau yace haba ai bakomai, abinda nakeso da kai ka tsaida hankalin ka ka samo cikakkar hujja dan