Advertisements
Chapter 20 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   20 / 54

57K to 60K   out of 160.3K words

jakar da aka gabatar tayi dai-dai da wadda ka gani? Sannan daya shigo kaga yanayin maye atare dashi? Sannan alokacin da kace kaji ihu meyasa bakayi saurin shiga ciki ba amatsayinka na wanda yake kula da mutanan gidan? Kace Malan Sani ya fito da jini a jikinsa, sannan ka ganshi acikin yanayi na maye, amatsayinka na maigadi ya akayi ka barshi har ya fita daga gidan ba tare da ka rik'esa ba?


*Madu*.... E to gaskiya lokacin daya shigo babu yanayin Maye a tare dashi, kawai dai baya cikin natsuwarsa, alamu sun nuna kamar yana cikin tashin hankali domin jan da idanuwansa sukayi sun nuna alamun kamar wanda yayi kuka. A lokacin da naji ihu kuma dalilin da yasa ban shigaba saboda nasan Malan Sani yana ciki, kuma nasan amintaccen gidan ne, alokacin da ya fito kuma nayi kok'arin tareshi amma sai ya ture ni, kuma tabbas da yanayin maye ya fito, sai dai kafin na tashi ya fice, saboda gaskiya jikina ne yayi sanyi saboda ganin abinda ban tab'a zato ba, hakan yasa na kasa yunkurin rikeshi da kyau. Sannan kuma wannan jakar tabbas irin tace na gani a hannunsa, kuma nasan ta Alhaji ce domin koni nasha d'aukarta idan ya fito zai fita domin nasan jakarsa ce da yake saka kamfutarsa.


*Brr. Kamal*.... Kace jakar kamfutarsa ce, kenan lokacin da Malan Sani ya shigo da ita kamfutarce aciki? sannan kace ya fito cikin yanayin maye, shin ya fito da jakar ko kuma be fito da ita ba?


*Brr. Barau*... Ina da ja ya mai shari'a, duk da Madu yace yaga Malan Sani ya shigo da jaka ta kamfutar Alhaji ai be zama dole ace kamfutar bace aciki tunda alokacin be bud'a masa ba, ya kamata abokin aikina yasan irin tambayar da zaiyima mai bada sheda. Nagode.


*Alkali*... Brr. Kamal ka gyara yanayin tambayarka. Risnawa yayi yana fad'in zan kiyaye.


*Brr. Kamal*... Madu kotu tana sauraronka shin kaga Malan Sani ya fito da wannan jakar?


*Madu*.... A gaskiya ban lura da hannunsa ba, saboda yana fitowa naga jini a jikinsa sai hankalina ya tashi hakan yasa bazan iya cewa ya fito da jaka ba. Iya kar abinda na sani kenan.


*Brr. Kamal*.. Jinjina kai yayi yana fad'in mungode zaka iya tafiya. Ina so nayima Malan Sani wasu tambayoyi idan kotu ta bani dama. Kotu ta baka dama.


*Brr. Kamal*... Malan Sani kace alokacin da aka tare ku Alhaji yace ka tafi domin kaje ka tafi da iyalinshi gidan ka, shin ko zaka fad'ama kotu abinda kuka tattauna da yasa yace kaje ka tafi da matarsa.


*Malan Sani*... Tabbas Alhaji shine yace naje na tafi da Hajiya, sannan ya bani jakar kamfutarsa yace na tafi da ita saboda mutanan da suka taremu kada su ansheta dan akwai abubuwa masu muhimmanci aciki.


Hannu Brr. Barau yasa yana gyara zaman gilashinsa jin abinda Malan Sani ya fad'a, kada fa aje allura ta tono galma, kada ace Malan Sani ya b'oye wata shedar da zata tabbatar da abinda sukayi.


*Brr. Kamal*.... Malan Sani kace akwai abubuwa masu muhimmanci acikin kamfutar Alhaji hakan yasa ya baka ka tafi da ita, shin ko zaka fad'a mana wani abu wanda ka sani idan Alhaji ya sanar da kai.


*Malan Sani*... Tabbas akwai masu neman rayuwar Alhaji, kuma hakan ya faru ne saboda sun gano yasan wani sirri nasu akan abubuwan da sukayi mashi, kuma ya shirya komai yana jiran litinin tayi domin ya shigar da k'ara saboda ya samu duk wata sheda da zata tabbatar da abinda sukayi domin shedar bidiyo ce da maganganunsu aciki, wanda suka san duk abinda yayi hakan yasa suka shirya kashe shi. Wannan dalilin ne yasa ya bani kamfutar yace na tafi da ita.


*Brr. Kamal*... Ko zaka iya fad'a mana su waye suke kokarin kashe shi?


*Malan Sani*... E to wad'an da aka turo ban san su ba, amma mutanan da suke cikin kamfutar 'yan tawagar Alhaji Marusa ne kuma shine babban su domin shine abokin takun sak'ar Alhaji.


A zabure Brr. Barau ya tashi yana fad'in ya mai sharia wannan magana da Malan Sani yake fad'a ba gaskiya bane, yariga da yasan komai na Alhaji hakan yasa zeyi amfani da wannan damar ya kare kanshi domin ya ga beda wata hanyar tsira, Malan Sani yasan duk wani sirri na Alhaji, yasan cewar sun samu sab'ani da Alhaji Marusa alokacin baya, hakan yasa zaiyi amfani da wannan damar ya sako Alhaji Marusa a cikin wannan shari'ar, ina so kotu tayi watsi da wannan gurguwar hujjar ta Malan Sani tayi duba da hujjar zahiri da aka gabatar mata domin ta yanke masa hukunci, domin Malan Sani zai b'atama kotu lokaci ne kawai, kuma idan beyi hankali ba Alhaji Marusa yana da damar neman hakkinsa akan b'ata masa suna da yake kok'arin yi. Nagode.


*Brr. Kamal*... Ya mai shari'a maganar Malan Sani tana kan hanya, babu wanda besan alak'ar da take tsakanin Alhaji Marusa da Alhaji Maiwada ba, kuma tabbas hakan zata iya kasancewa domin Alhaji Marusa yana takun sak'a da Alhaji Maiwada. Inaso wannan kotu da tayi duba da maganar Malan Sani, kada tayi saurin yanke hukunci, abashi dama domin ya tabbatar da abinda ya fad'a. Nagode ya mai shari'a.


Hayaniya ce ta cika kotun. Bubbuga tebur Alkali yayi kafin akayi shiru. Kallon Malan Sani yayi yana fad'in Malan Sani ko kana da shedar da zaka tabbatar ma kotu abinda ka fad'a gaskiya ne? Duk'ar da kai Malan Sani yayi hawaye suna zubo masa yace bani da sheda ya mai shari'a domin mutanan da suka shiga gidan Alhaji sune suka amshe kamfutar da shedar take ciki.


Ajiyar zuciya Brr. Barau ya saki jin abinda Malan Sani ya fad'a.


Girgiza kai Alkali yayi yana fad'in kowa ce kotu tana amfani ne da kwakkwarar hujja kafin ta yanke hukunci, dan haka wannan kotu baza tayi amfani da abinda ka fad'a ba amatsayin hujja. Brr. Kamal idan kana da sauran tambaya kotu tana sauraronka.


Jiki a sanyaye Brr. Kamal yace bani da ita ya mai shari'a. Komawa yayi ya zauna yana jin d'aci aranshi, tabbas yasan akwai munakisa acikin wannan shari'ar, amma saboda basu da hujja dole suyi hakuri Allah zai saka masu.


*Alkali*... Brr. Barau kana da sauran abinda zaka fad'ama kotu? Tashi yayi yana fad'in bani da sauran abun fad'a, ina so wannan kotu da tayi gaggawar yanke ma Malan Sani hukunci saboda zaluncin daya aikata. Nagode.


Rubutu Alkali yayi kafin yace kotu zataje hutu na rabin sa'a. Bubbuga tebur yayi kowa ya tashi.


Zamewa k'asa Malan Sani yayi yana sakin kuka mai tsuma zuciya. Da sauri Alhaji Mansur da su Halima sukayo wajensa.



Ur's.
Nabeelert Lady[3/10, 8:38 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shoot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*



1⃣9⃣


Hannu Alhaji Mansur yasa ya kamo Malan Sani yana fad'in kayi hak'uri Malan Sani, Allah yana tare da kai, koda sunyi nasara akan ka yanzu wallahi baza suyi nasara akan ka ba ranar lahira, Allah yasan komai, kuma yana kallon su, shine kad'ai zai saka maka, zuciyata tana mani wani tunani akan wannan Alkalin, sai dai bana so nayi zarginsa kada Allah ya kama ni da laifi, a gaskiya daga farko yanda naga yana yawan goyon bayan Brr. Barau sai nake tunanin ko an bashi cin hanci ne, amma daga baya sai na gano ko wane Alkali hakan zaiyi, domin kotu da sheda take amfani, da yawan Alkalai suna yanke hukunci bisa hujjar da aka gabatar masu, ko da hujjar ta k'aryace matuk'ar aka aminta da ita suna amfani da ita, dan haka kayi hak'uri Allah zai saka maka.


Hannu Malan Sani yasa ya goge ido shi yana fad'in bakomai Alhaji, wallahi tun ba yau ba na sadak'as, nasan dole irin wannan hukuncin ya hau kaina, shiyasa tunda farko ban tsaya b'atama kaina lokaci wajen fad'ama Brr. Barau komai ba daya tambaye ni, ai kunga alokacin banyi maganar dalilin da yasa Alhaji ya bani kamfutarsa ba, ban kawo komai na abinda nasan sunyima Alhaji ba, saboda nasan kona kawo bani da hujjar tabbatar da hakan, saboda Brr. Kamal ne yasa na bud'e baki nayi magana, shima bana so yaga yana mani kok'ari amma naki bashi had'in kai, amma kaga yanzu da yasan babu hujja zai hak'ura, wallahi na d'auki k'addarata, fatana Allah ya bani ikon cinyeta.


Cike da tausayi Alhaji Mansur yace amin Malan Sani. Cikin kuka Halima tace nikam Malan zan tafi gida, bazan iya tsayawa a yanke maka hukunci ba, ina tsoron binda zai faru dani, bana so muyi asarar abinda yake ciki na.


Jinjina kai Malan Sani yayi yana fad'in tunda na ganki naji rashin dad'in zuwanki, kinsan baki da lafiya, kuma nasan matuk'ar aka yanke mani hukunci wani abun zai iya faruwa da ke, dan Allah ki koma gida, kinga an kusa tashin su Rumaisa idan ta koma gida zata iske babu kowa, ki kwantar mata da hankali, bana so tasan abinda yake faruwa har sai ta k'ara hankali.


Alhaji Mansur yace bara mu rakata ta tafi hakan zaifi, dama tace tana son zuwa shiyasa muka taho da ita. Malan Sani yace akwai kud'i a inda nake ajewa kiyi amfani dasu, tunda kina sana'ar cikin gida ki k'ara jari nasan Allah bazai tozarta ki ba. Kai kawai ta d'aga tayi waje da sauri.


***


Bayan kowa ya dawo Alkali yashigo, nan kowa ya natsu. Zama yayi yana gyara takardu. Kotu tayi tsit tana jiran abinda Alkali zai yanke.


*Alkali*... 'Dago kai yayi yana fad'in bayan dogon bincike da kwararan hujjoji da aka gabatar agaban wannan kotu, kotu tayi dogon nazari akansu kuma ta tabbatar da ingancin su, domin duk abinda aka gabatar mata babu wanda yake na bogi, an tabbatar cewar an samu allurar da akayima Alhaji Maiwada agidan Malan Sani, sannan an tabbatar da hoton hannun jikin wuyan Alhaji yayi dai-dai dana Malan Sani, haka zalika an tabbatar da hoton jikin hannun matar Alhaji yayi dai-dai dana Malan Sani, sannan jinin da yake jikin farcenta yayi dai-dai dana Malan Sani, bayan haka Malan Sani ya gaza kawo ma kotu wata hujja da zata tabbatar da abinda ya fad'a gaskiya ne, dan haka kotu zata yanke hukunci.



*A k'arkashin penal code sashe na 302,da 201,da 180, da 340 sashen kisa amfani da makami ko wani abu, bisa la'akari da wannan sashe na kundin tsarin mulki na k'asa penal code, wannan kotu ta yanke ma Malan Sani hukuncin d'aurin rai da rai agidan yari, sannan zai biya tarar naira dubu d'ari biyar ga Iyalan Alhaji amatsayin cin zarafinta da yayi na yunk'urin haike mata, haka zalika zai biya diyya ga Iyalan Alhaji idan suna da buk'atar hakan. Kottttt!!!!.*


Gaba d'aya mutanan kotun suka mike kowa da abinda yake fad'a, wasu suna yabama Alkali da Brr. Barau abisa kok'arin da sukayi, yayin da wasu suke ganin gaskiyar Malan Sani. Haka kowa ya fita 'yan sanda suka taso Malan Sani wanda hawayen idanshi suka k'afe ya koma yin kukan zuci.


Alhaji Mansur kasa motsi yayi daga inda yake, gaba d'aya jiyake kamar amafarki abubuwan suke faruwa. Maman Labiba kuwa kuka kawai takeyi.



Alhaji Musa ne da Alhaji Usman suka k'araso wajen Alhaji Mansur, kamoshi Alhaji Musa yayi suka fito waje. Jingina sukayi da mota Alhaji Musa yana fad'in sai hak'uri Alhaji, Allah kad'ai yasan gaskiyar wannan al'amarin, domin har cikin zuciyata na kasa yarda da abinda ya faru, na jima da sanin Malan Sani haka kawai nake jin bazai iya aikata abinda akace yayi ba.


Alhaji Usman yace wallahi kaji na rantse maka banyarda da abinda aka gabatar ma kotu ba, kawai babu yanda zamuyi ne, koda zamuje kotun da tafi wannan iya hukuncin da za'a zartar kenan, saboda ko waye aka bama wannan shedun dole ya amince dasu, mu da mukasan hakan bazai yuwu ba mu kad'ai zamu iya k'aryatawa, amma an cutar da Malan Sani, domin nasan waye Alhaji Marusa, zai iya komai akan kud'i, tunda naji sun fara takun sak'a da Alhaji Maiwada nasan ba zai barshi haka ba, domin duk wani ma'aikacin kwastam da za'a kawo nan matuk'ar mai gaskiya ne Alhaji Marusa shine yake silar barinsa garin nan, saboda aminin Mr. Kallah ne shugaban Kwastam na k'asa.


Alhaji Musa yace wallahi tunda Malan Sani ya fara bada labarin dalilin da yasa aka kashe Alhaji naji na yarda da abinda ya fad'a, ko Brr. Barau beda gaskiya, domin a lokacin naga yanda yanayinsa ya canza, sai dai kawai mu barma Allah amma sun cutar da Malan Sani.


Alhaji Usman yace kasan abinda yafi bani mamaki? Brr. Barau lauyen Alhaji Marusa ne, sai gashi ana fad'in wannan abu ya fito da wuri amatsayin wanda zai kare Alhaji Maiwada, a tunanina Brr. Kamal shine lauyen daya tsayama Alhaji a wancan karon, amma sai gashi an juya abun, tun daga lokacin nasan akwai wani abu.


Ajiyar zuciya Alhaji Mansur yayi yana fad'in duk abinda zan fad'a maku bazai canza komai ba, amma kusa aranku Brr. Barau, Mr. kallah, 'Yallab'ai da Alhaji Marusa duk a rumfa d'aya suke, nasan mutane ukku d'ayan ne ban sani ba, amma wallahi su dukansu munafukai ne, babu yanda zamuyi ne dole mu barma Allah, zanje na biya tarar da akasa ma Malan Sani, sannan amatsayina na dangin Alhaji da Matarsa mun yafe diyyar da aka fad'a, kuma insha Allahu yau zamu wuce Kano, kome kenan zamuyi waya saboda Bilkisu.


Alhaji Usman yace wannan ba matsala bane, insha Allahu zata samu kulawa kamar tana kusa da ku, su kuma ka barsu, wata rana Allah zai nuna su a lokacin da basuyi zato ba, zasuji kunya tun aduniya, ina rok'on Allah ya k'ara masu tsawon kwana ko dan su girbi abinda suka shuka. Gaba d'aya suka amsa da amin.


K'arasawa sukayi wajen Brr. Kamal, anan sukayi masa godiya. Brr. Kamal kam hak'uri yayi ta basu zuciyarsa cike da damuwa. Alhaji Mansur yace haba wallahi bakomai, mun bar ma Allah.


Kafin a tafi da Malan Sani Alhaji Mansur ya rok'esu alfarmar su bashi mintuna biyar. Matsawa sukayi daga wajen suna fad'in yayi sauri.



Dafa kafad'ar Malan Sani yayi yana fad'in kasa Allah aranka, kuma kacigaba da addu'a Allah maji roko ne, sannan yana saurin amsa addu'ar wanda aka zalunta yayi hak'uri, insha Allahu wata rana zakaga sakamakon hak'urin da kayi, kuma ina tabbatar maka zaka fita daga wajen nan, ta silar Alhaji Maiwada kashigo wajen nan, domin kana aiki a k'asanshi akayi amfani da wannan aka kulla maka wannan abun, insha Allahu jinin Alhaji shine zai kwato maka hakkin ka, da izinin Allah sai Ra'eez ya zama lauya, domin tun yanzu zan fad'a masa irin zaluncin da akayi ma mahaifinsa da kai, zai tashi da burin d'aukar fansa, ta haka ne zai dage ya cimma burinsa.


Kai Malan Sani ya jinjina yana fad'in zan so naga wannan ranar, ka dage Alhaji Ra'eez yayi karatu, kada ka barshi a k'asar nan, domin har yanzu acikin makiyan Alhaji babu wanda yasan yana da 'Dah, insha Allahu sai Ra'eez ya basu mamaki.


Ayanzu da kayi wannan maganar sai naji wani haske ya ziyarci zuciyata, kuncin da nakeji yayi sauki, inajin zan shiga gidan yari hankali kwance, kuma zan zauna ba tare da wata damuwa ba, domin bazan bari damuwa ta kamani ta kassara lafiyata ba, zan roki Allah ya ara mani rana domin naga wannan rana da kake fad'i, nagode sosai Alhaji.


Alhaji Mansur yace haka nake son ji Malan Sani, ayanzu kasa zuciyata tayi dad'i, domin damuwakar zata sa naji babu dad'i, amma ayanzu nasa burin d'aukar fansa, zan tsaya ma Ra'eez har ya kai matsayin da zai tsaya mana, kuma insh Allahu zan kula da matarka da d'iyar ka, Allah ya k'ara maka hak'uri.


Malan Sani yace amin. Haka aka tasa Malan Sani suka shiga mota mutane sai kallonshi akeyi, shi ko gaba d'aya yaji damuwarsa ta ragu sosai, haka suka bar kotu.


***

Hannu Halima tasa ta goge idonta bayan ta gama jin abinda ya faru, sannan Alhaji Mansur ya fad'a mata yanda sukayi da Malan Sani.


Murmushi tayi wanda yafi kuka ciwo tana fad'in daga yau nima zanyi yaki da damuwar da take zuciyata, dole nayi irin ta Malan matuk'ar ina so naga wannan rana, haka idan ina so na raini yaran mu dole na cire komai araina, zan toshe kunnuwana daga jin surutun mutane, zan bama kowa mamaki domin zan kasance jarumar mace wadda tafi wasu mazan, Allah ya shige mana gaba.


Alhaji Mansur yace amin Halimatu, hakika kin k'ara sanyaya mani zuciyata da kalamanki, kamar yanda kika d'auki wannan k'addarar ina tabbatar maki Allah bazai barki haka ba, zan tsaya akan al'amuran ku, duk wata matsala bana so ki b'oye mani, ki d'auke ni amatsayin Yayanki, ga Maman Labiba nan ki d'auketa amatsayin 'Yar uwarki, insha Allahu babu abinda zai gagara.


Jinjina kai Halima tayi tana masu godiya. Alhaji Mansur yace zamuje can gidan domin a kulleshi, zan aiko da duk wasu kayan abinci da suke gidan saboda idan

20 / 54