Author : Marubuciyar Zamani Category : Complete Novels
suna da amana, kuma nima naji dad'in zamanshi anan domin kariya ce, a jiya har Dadyn 'yan biyu yana mani magana ko a samo maki maigadi saboda tsaro, to sai kuma daya dawo da dare yake fad'a mani yaga wani mutum a shagon gidan idan nashigo na tambayeki ashe ma na gida ne.
Halima tace wallahi kuwa. Sister Hassana tace to Allah ya k'ara tsarewa, ita kuma Allah ya bata lafiya. Halima tace amin. Sallama tayi mata ta fita.
Madu ne yayi sallama ya tsaya a zaure. Hijabi Halima ta d'auka ta lek'a. Bayan sun gaisa ya k'ara jajanta mana kafin yace dama kasuwa zaije yayo sarin kaya shine ya leko ko tana da sako.
Halima tace ina da sako kuwa, bari na rubuto maka abubuwan da za'a siyo mani, tunda zaka bud'e shago sai na canza wasu abubuwan da nake saidawa a gida.
Madu yace baza'ayi haka ba, ki rubuto mani abubuwan da kike saidawa sai asiyo maki a zubasu ashago sai na rik'a saida maki, sauran abinda baza'a aje a shago ba kuma sai ki ajeshi a cikin gida.
Murmushi Halima tayi tana fad'in nagode sosai Madu. Yace haba ai bakomai, zan samo littafi sai arik'a rubuta komai. Halima tace haba meye na wani rubutu. Madu yace ko musulunci ya yarda da rubutu ai, dan haka babu komai. Halima tace nagode sosai.
**** ****
A washe garin ranar da suka dawo Alhaji Mansur ya nufi makarantar su Ra'eez, bayan sun gama gaisawa da shugaban makarantar ya fad'a masa abinda yake faruwa. Shugaban makarantar yace Allah sarki, ashe Alhaji Maiwada yana da yaro a makarantar nan? Alhaji Mansur yace wallahi kuwa, da yake nine na ke zuwa wajensa shiyasa.
Jajanta masa yayi kafin yace yanzu jarabawa sukeyi saura sati d'aya suyi hutu, ranar juma'ar nan suke gamawa kaga yau saura kwana biyu kenan tunda yau muna laraba, me zai hana kayi hak'uri zuwa ranar juma'a sai kazo ka tafi dashi.
Alhaji Mnsur yace haka ne kuma, idan yasan Mahaifinsa ya rasu zai shiga damuwa wata kilama ya kasa rubuta jarabawar, shikenan, dama ina jin tsoron kada yasan labarin daga sama ne, amma tunda sun kusa gamawa ranar juma'ar zan dawo. Shugaban makarantar yace bakomai Allah yajikansa. Alhaji yace amin. Sallama yayi masa ya tafi.
***
A ranar juma'a yazo ya d'auki Ra'eez, duk hankalin Ra'eez ya tashi ganin anzo d'aukarsa ba'ayi butu ba, duk da Alhaji Mansur yace masa bakomai amma hankalinsa yaki kwanciya, saboda sunsha ganin ana zuwa d'aukar wasu idan iyayensu suka rasu.
Tun amota Ra'eez ya fara kuka, Alhaji Mansur sai lallashinsa yakeyi shima hawayen suna shirin zubo masa, ganin Ra'eez sai ya sake dawo masa da mutuwar sabuwa.
Haka suka isa gida ba tare daya fad'a masa komai ba. Maman Labiba ma tana ganin Ra'eez ta fashe da kuka, saurin juyawa Alhaji Mansur yayi saboda hawayen da suka zubo mashi.
Zama Ra'eez yayi yana sakin wani kukan. Ya jima ahaka kafin Alhaji Mansur yafito. Abinci yasa Maman Labiba ta kawo masa, sai dai duk yanda sukayi yaci kinci yayi.
Gyara zama Alhaji Mansur yayi ya jawo Ra'eez, cikin kwantar da hankali ya fara bashi labarin abinda ya faru......
Ra'eez yasha kuka bana wasa ba, wanda kukan da yakeyi ya sakar masa zazzafan zazzab'i lokaci guda. Gaba d'ayansu suma kukan sukeyi, jin jikinshi yayi zafi sosai yasa Alhaji Mansur ya kaishi d'akinsa, rigarsa ya cire ya kawo ruwa ya fara goge masa jikinsa.
Ya dad'e yana masa haka har sai da jikin yayi sauki, magani yasa Maman Labiba ta kawo masa, tadashi yayi yasha sannan ya kwanta, cikin lokaci kad'an bacci yayi gaba dashi.
Fitowa sukayi Maman Labiba tana fad'in irin wannan ranar nake tsoro, dole Ra'eez yashiga damuwa, domin yasan komai akan Iyayensa, Allah ne kawai zai saka masa, bawan Allah gashi dai yaro amma yana da halin manya.
Alhaji Mansur yace bazan bari sai nan da shekara biyu kafin ya gama makaranta ba, tunda yana da kok'arinsa idan sun koma makaranta aji biyar zai shiga, zanyi magana da shugaban mkarantar asa sunanshi cikin 'yan aji shidda domin ya zana jarabawa acikinsu, kinga zuwa shekara mai zuwa sune zasu gama sai kawai yaje ya fara karatunshi.
Maman Labiba tace hakan yayi dai-dai, Allah ya saka masa kok'ari da hazak'a ya kuma bashi ikon cimma wannan burin da muka d'auka. Alhaji Mansur yace amin.
**** ****
Tun daga wannan lokacin Ra'eez ya koma shiru-shiru, hatta wasan da sukeyi da Labiba tamkar abokan wasa yanzu sai dai yayi murmushi, gaba d'aya baya dariya sai ta kama dole, a islamiyarsu kuwa sosai yake maida hankali, yanda kasan an bud'e masa kwakwalwa yanzu haka yake karatu, duk abinda ya d'auka sai ya iyashi.
Kasancewar dogon hutu ne na canjin aji yasa suka dad'e agida, ana saura sati biyu su koma ya roki Alhaji Mansur akan suje Lagos yaga Ummunsa. Babu b'ata lokaci Alhaji Mansur ya amince, dama saboda kada ya tada masa hankali yasa bece suje ba. Haka suka shirya suka tafi su biyu dan ta jirgi suka bi.
**** ***
Halima tana zaune tsakar gida ita da Rumaisa suna gyara alaiyahun da zata zuba amiya, sai sauri sukeyi dan Alhaji Mansur yayi mata waya tun jiya yace zasu zo. Rumaisa sai murna take Yayanta zai zo.
Bayan ta gama komai suna zaman jiransu sai sallama sukaji, hakan yasa Rumaisa tayi saurin tashi tana murna. Amsa sallamar Halima tayi ta sako hijabi tana fad'in bismilla sannun ku da zuwa.
Shigowa sukayi Ra'eez yana goge idonshi, dan tunda suka sauka a Lagos yake kuka. Idanuwan Halima ne suka cika da kwalla ganin Ra'eez. Bayan Rumaisa tayi masu shimfid'a suka zauna.
Bayan sun gama gaisawa Halima ta kamo Ra'eez tana shafa kanshi sai hak'uri take bashi. Zama Rumaisa tayi tana fad'in Yayana kadena kuka mana, ai Mama tace da Baba da Abbu sunje unguwa sai na girma zasu dawo kaima kadena kuka kaji.
Murmushi Ra'eez ya saki hawaye suna zubo masa jin shirmen Rumaisa. Dad'i Alhaji Mansur yaji ganin Rumaisa tasa Ra'eez murmushi.
Tashi Halima tayi zata kawo masu abinci Alhaji yace Halima bar abincin nan sai anjima, yanzu ina so muje wajen Bilkisu ne, ina Madu ko baya nan ne? Halima tace yanzu ya leko yace mun zaije can gidansu Alhaji ya dawo.
Alhaji Mansur yace Allah sarki, ya zaman naku yake babu wata matsala ko? Halima tace babu komai wallahi, ai Madu ya zame mani tamkar d'an uwana, dole Alhaji yake rik'eshi, domin mutum ne mai gaskiya da amana, babu abinda bayayi mana, cefane duk bayan kwana biyu sai yayo mana, haka Rumaisa shine yake bata kud'in tara, sannan ya amshi kayan da nake sayarwa anan yasa ashago yana tara mani ribar, gaskiya babu abinda zance sai Allah yasa albarka, amma Alhaji ya tafi ya barmu da masu kula damu, Allah yajik'ansa.
Alhaji Mansur yace amin, ai gaskiya Madu mutumin kirki ne, Allah ya saka masa da alkhairi, ina Ladi fa? Halima tace jiya ma tazo nan mun wuni sai yamma ta tafi, gaskiya ta rike alkawari tana zuwa wallahi, gaskiya bana cikin damuwa sai ta rashin Malan, amma Allah ya had'ani da mutanan arziki, ga Sister Hassana da mijinta babu abinda basa mani, wancan satin ma naje naga M.....
Shiru tayi ganin Rumaisa tana wajen. Alhaji yace na gane, yana lafiya ko? Halima tace lafiya lau, dan naji dad'in ganinsa a haka, shine ma yasa hankalina ya k'ara kwanciya dan shima ya kwantar da nashi hankalin.
Alhaji Mansur yace idan kin gama muje asibitin sai muwuce wajensa, Rumaisa kije gidan Sister ki zauna zamuje mudawo kinji. Kai ta d'aga tana fad'in Yayana taho muje.
Alhaji Mansur yace asibiti za'a kaishi yanzu zamu dawo. Rumaisa tace wayyo sannu kaji, idan anyi maka allura da zafi ka fad'a mani zan rama maka.
Dariya Ra'eez yasa yana kallonta. Da mamaki Alhaji Mansur yake kallonshi ganin yayi dariya. Gyara wajen Halima tayi suka fita.
***
Kasancewar an mayar da Ummu asibitin Mahaukata yasa suka nufi can. Suna zuwa shima Dr. Saddik ya isa dan sunyi waya dashi. Bayan sun biya mai mota kud'insa suka k'arasa ciki.
Da fara'a Dr. Saddik ya tarbe su, bayan sun gama gaisawa suka shiga ciki. Ofis d'in *Dr. Najib* suka nufa. Bayan sun gama gaisawa Alhaji yayi masa godiya akan kok'arin da yakeyi. Dr. Najib yace haba bakomai wallahi, ai jikinta da sauki sai dai acigaba da addu'a.
Alhaji yace mungode fa. Dr. Saddik yace muje su gaisa ga yaronta nan. Dr. Najib yace ikon Allah, sannu kaji sai hak'uri. Kai kawai Ra'eez ya d'aga yana maida kwallar data taho masa.
Suna tura k'ofar d'akin da take Ra'eez yayi saurin shigewa, jikinsa har rawa yakeyi yana so yaga Ummunsa. Kwance take idanuwanta a rufe kamar me bacci.
K'arasawa Ra'eez yayi ya kamo hannunta hawaye suna zubo masa, a hankali ya furta Ummunah! Da sauri ta mik'e tsaye, ganin Ra'eez agabanta yasa ta kwala k'ara tana fad'in Ra'eez sun kashe shi, wallahi sun kashe shi, ka samo mani wuk'ar Makka sai na kashe su dukansu.
Tashi Ra'eez yayi yana kuka ganin yanda Ummunsa ta koma, su kansu sai da jikinsu yayi sanyi ganin yanda tsigar jikinta ta tashi sai rawa jikinta yakeyi. Hannu tasa ta rik'e kanta tana wani k'ara.
Da sauri Dr. Najib yayo kanta, kafin ya k'araso ta tafi zata faad'i, aguje ya tareta ta fad'a jikinsa a sume.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:39 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
2⃣1⃣
Sai da aka yi mata allurar bacci kafin suka samu kanta, gaba d'aya yau jikinta ya rikice zuwan Ra'eez. Bayan ta samu bacci Dr. Najib yace suje ofis.
Kallon su yayi yana fad'in ayau naga wani canji atare da ita ganin d'anta da tayi, alamu sun nuna bata mance dashi ba, kuma ina ganin idan tana ganinshi zata iya tunawa da wani abun, tunda kace karatu yakeyi mai zai hana duk hutu yarik'a zuwa yana ganinta kila ta haka zamu samu shawo kanta.
Gyara zama Alhaji Mansur yayi yana fad'in likita zuwan Ra'eez bazai yuwu ba, domin zai shiga aji shidda, kuma kaga zasu fara karatu mai zurfi ga islamiyya yanayi hakan nema yasa koda Mahaifansa suna nan baya zuwa wajensu, bayan nan kuma gaskiya waje nakeso yayi karatu, akwai wata makaranta *Queen Mary*, law school ce a Landon, tunda nasa ma raina inaso ya karanci fannin shari'a na fara duba makarantu masu kyau, hakan yasa na zab'a masa wannan makarantar, kuma bana so idan ya tafi ya rik'a dawowa, amma tunda akwai wannan lalurar zanyi kok'ari yarik'a zuwa ko so d'aya a shekara ne.
Jinjina kai Dr. Najib yayi yana fad'in kaima da naka uzurin, bakomai, tunda zai rik'a zuwa hakan ma yayi, dama bana so ace kwata-kwata bazai rik'a zuwa ba domin yin hakan zai maida mu baya.
Alhaji yace insha Allahu zai zo, Allah ya bata lafiya. Gaba d'aya suka amsa da amin. Tashi sukayi suka masa godiya. Ra'eez yace abarsa a wajenta. Alhaji Mansur yace Ra'eez kaga ciwonta yana tashi kana so tarik'a shan wahala? Kai ya grigiza yana goge hawayen idonshi.
Alhaji Mansur yace kayi hak'uri zan barka a gidan Maman ku kayi sati d'aya kaga idan zata zo ganin Ummunka sai kuzo tare kaji. Kai ya jinjina.
Murmushi Dr. Najib yayi yana fad'in gara kasa juriya azuciyarka hakan zaisa kayi karatu sosai, idan kasa damuwa aranka bazaka gama karatu da wuri kazo ka kwato maku hakkin ku ba.
Godiya sukayi masa suka tafi. Dr. Saddik yaso ya kaisu amma Alhaji Mansur yace ya barshi, baya son arik'a ganinsu tare. Haka suka wuce gidan yari wajen Malan Sani.
***
Malan Sani yasha kuka, ganin Ra'eez sai ya dawo masa da mutuwar sabuwa, shima Ra'eez d'in kuka yakeyi, duk dauriyar da Halima takeyi sai da tayi kuka, da kyar Alhaji Mansur ya basu hak'uri.
Kamo Ra'eez Malan Sani yayi yana fad'in wallahi sharri sukayi mani Ra'eez, ban kashe Alhaji ba, haka kuma ban.... Rufe masa baki Ra'eez yayi yana girgiza kai.
Zame hannunsa yayi yana fad'in Kawu kadena fad'ar haka, duk da k'arancin shekaruna nasan abinda zakayi da wanda baza kayi ba, tunda Abbah ya bani labarin abinda ya faru nasan cewar ba gaskiya bane sharri akayi maka, zanje nayi karatu insha Allahu wata rana sai ka fita daga nan, kuma sai gaskiya ta tabbata.
Gaba d'ayansu tsayawa sukayi suna kallon Ra'eez jin yanda yake sako magana mai cike da hankali da nutsuwa sai kace wani babba, alokacin gaba d'aya shekarunsa bazasu wuce 17 ba amma yana maganar masu shekaru da yawa.
Murmushi Alhaji Mansur yayi aranshi yana fad'in Allah mai iko, Allah mai shirya yanda yaso, gashi dai ya hukunta wannan abun sai kuma ya kawo Ra'eez, yasa masa natsuwa da zurfin tunani. Ya Allah ka tabbatar da ikon ka akan wannan bawan naka.
Sun dad'e a wajen Malan Sani suna fira, lokacin da zasu tafi Alhaji Mansur ya samu shugaban ma'aikatan suka gaisa, alheri yayi masa yana rok'onsa akan ya kula da Malan Sani. Murmushi yayi yana fad'in bakomai Alhaji, babu abinda zamuce da wannan k'asa tamu sai addu'a, amma wata shari'ar sai a lahira. Godiya Alhaji Mansur yayi masa suka tafi.
***
Bayan sun gama cin abinci sukayi sallah. Zama sukayi da Madu suna ta fira. Madu yake fad'a masa komai lafiya na gidan Alhaji, dan Maigadin yana kula da komai, motar Alhaji ma an rufeta da tampol, sai dai yana ganin gara a cire tayoyin a d'ageta zaifi.
Kallon Ra'eez Alhaji Mansur yayi yana fad'in Ra'eez ko dai asiyar da motar asaka maka kud'in a banki tunda nan gaba yayinta zai wuce? Kallonsa Ra'eez yayi yana fad'in Abbah idan aka barta har na girma akwai abinda zai sameta? Kai ya girgiza masa.
Ra'eez yace dan Allah Abbah abarta, ina so idan na girma na tuk'ata domin narik'a tunawa da Abbu kaji. Murmushi Alhaji Mansur yayi yana fad'in angama Ra'eez, insha Allahu baza'a sai da ta ba, kuma sai ka tuk'ata da izinin Allah, sai dai ina ganin zamu tafi da ita can kano kaga akwai gareji sai sata ciki kawai.
Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in yauwa Abbah. Madu yace shikenan ma, nima hankalina zaifi kwanciya idan aka tafi da ita, domin za'a iya d'auketa, amma idan aka tafi da ita ya rage sai gida kawai shiko babu wanda zai d'aukeshi, shima dan kace abarshi amma da an sayar dashi hankalin kowa ya kwanta.
Alhaji Mansur yace akwai dalilin da yasa nace baza'a siyar dashi ba, wata rana Ra'eez zai zo yayi aiki agarin nan, kuma bana so ya zauna a wani waje, dan haka ka barshi babu abinda zai sameshi da izinin Allah, idan ma Maigadin ya gaji sai asamo wani. Madu yace begaji ba, shikenan ayi yanda kace.
Rumaisa ce ta shigo tana fad'in Yaya kazo muje kaga takarduna to. Murmushi yayi yana fad'in kilama duk ziro kikaci. Rumaisa tace wallahi duk na cinye, kok'ari fa gareni, kusan kullum sai an bani kyauta a aji. Ra'eez yace to muje na gani.
Dariya sukayi Alhaji yana fad'in ina ruwan Ra'eez, tunda yasan mutuwar mahaifinsa ban sake ganinsa cikin annashuwa ba sai da mukazo yaga Rumaisa, shiyasa na yanke shawarar barinsa yayi sati d'aya idan yaso sai ya taho ta jirgi, ni kuma sai na tafi da motar dan bana son na tafi dashi amota kasan hanyar Lagos. Madu yace haka ne, Allah ya tsare mana kai. Alhaji yace amin.
**** ****
Wshe gari tunda asuba Alhaji Mansur ya tafi bayan ya cika Halima da kud'i ita da Madu. Ra'eez da Rumaisa sai dad'i sukeji zai zauna yayi sati.
Sosai Halima take jin dad'in zaman Ra'eez domin koda yaushe yana koyama Rumaisa karatu, haka idan tayi ba dai-dai ba yana tsawatar mata, sai take ji ina ma abar matashi kodan Rumaisa.
Tunda sukaje asibiti basu sake komawa ba sai ana saura kwana biyu Ra'eez ya tafi, a wannan rana jikin Ummu bai tashi ba, haka Ra'eez ya wuni a wajenta dan Halima acan ta barosa, duk da ita kad'ai take shirmenta amma shi d'auka yake fira sukeyi, dan ita labarin Abbu kawai take bashi, hakan yasa shima yayita bata labarin Abbun.
Idan ka gansu sai ka d'auka mai hankali ce, gaba d'aya masu kula da ita aranar sunyi farin ciki domin kowa yasan Ra'eez yazo, duk wanda yaje sai ta fad'a masa ga Ra'eez shine zaije makka yasiyo mata wuk'ar da zata kashe wad'an da suk kashe mata Abbun Ra'eez, gaba d'aya aranar kowa sai da ya gaji da jin sunan Abbun Ra'eez.
Sai da yamma sosai Madu yazo tafiya da Ra'eez, anan fa Ummu tace bata san maganar ba, kuka da ihu tashiga yi za'a sace mata Ra'eez, haka ta rik'eshi tana kuka duk ta yakushe shi, sosai Ra'eez ya tsorata da yanayinta, duk yanda aka so akwace Ra'eez abun ya faskara domin wani irin k'arfi ne yazo mata, ta jima mutane da yawa ciwo hakan yasa dole suka kira Dr. Najib.
Koda yazo shima yasha fama,