Author : Marubuciyar Zamani Category : Complete Novels
azahar.
Komawa yayi ya zauna jiki a sanyaye kamar an zare masa lakka. Kallonsa Mr. Kallah yayi yana fad'in kaga abinda nake fad'a maka ko? Yanzu da ace kaje agaban mutane ka gama wannan bayanin kazo kunna masu sukaga wannan abun ai zasuce kayi wasa da tunanin su ne, babu wanda ya tab'a kawo k'arar Alhaji Marusa, yanzu idan kaje ka kai kuma ka kasa kawo sheda me kake tunanin za'ace? Tun daga ranar za'a dena gazgataka, ko wata rana kazo da wata maganar bazasu d'auketa da muhimmanci ba.
Jinjina kai Alhaji yayi yana fad'in nagode da wannan taimakon da kayi mani, insha Allahu dana koma zan sakar masa kayanshi. Mr. Kallah yace bakomai ka k'ara kiyayewa, aikin kwastam akwai had'i acikinsa. Tashi yayi ya bashi hannu kafin ya fita.
Tunda suke tafiya yayi shiru, gaba d'aya kanshi ya d'aure, tabbas wani ne yashiga ofis d'insa ya goge abinda ya d'auka aka d'aukar masa wannan abun, amma *WAYE NE* (tsohon littafi na) yayi masa wannan abun? Babu wanda yasan ya d'auki wannan abun amma gashi an goge masa, da ace ya fad'ama Mr. Kallah yayi d'auka da sai ya zargeshi.
Hannu yasa ya dafe kanshi. Tabbas maganar Mr. Kallah gaskiya ce, aikin kwastam akwai had'ari acikinsa, kuma ya godema Allah da bai kai wannan shedar ba, dole ya sake sabon taku, domin Lagos tasha ban-ban da sauran wajen da yayi aiki, Lagos shu'umin gari ne, k'aramin yaron daya taso acikinta ma sai yayi maka wayau.
Malan Sani ne yace Alhaji kamar akwai abinda yake damun ka ko? Ajiyar zuciya yayi yana fad'in Malan Sani duniya babu gaskiya, son kud'i ya rufema mutane ido, zasu iya aikata komai akan kud'i, wani babban al'amari ne ya faru ajiya zuwa yau, amma na faad'i, domin ban samu damar aiwatar da aikina ba. Ai kasan Alhaji Marusa ko? Malan sani yace sosai kuwa, a Lagos waye bai sanshi ba........
Labarin abinda ya faru Alhaji ya bashi. Sosai Malan Sani ya tausaya mashi, kallonsa yayi yana fad'in Alhaji haka Lagos take, shiyasa nake tausayin bakon daya zo cikinta, mutane da yawa suna shan wahala idan suka zo Lagos kafin su waye da ita, haka idan aiki ya kawo ka nan matuk'ar baka da masaniya akan komai kana shan wahala, wasu sun sha rasa ransu akan aikin su, a tunani na dad'ewar da kayi kana aiki zaka iya aiki a Lagos, domin nasan ka zagaya garuruwa da yawa.
Murmushi Alhaji yayi yana fad'in nima haka nayi tunani Malan Sani, ashe abun ba haka yake ba, duk yanda na d'auki Lagos ta wuce tunani na, shiyasa tunda nazo nake taka tsan-tsan da mutane, domin nasan yanda cin amana yayi yawa.
Malan Sani yace Alhaji maganar gaskiya kada ka sake yarda da kowa, ni jikina ma be yarda da Mr. Kallah ba, tunda kace mani yace kaje nasan akwai wani abu, dole akwai abinda ya sani shiyasa ya kira ka domin baya so kaji kunya, sai yayi amfani da wannan damar domin yasa ka yarda dashi.
Kallon Malan Sani Alhaji yayi cike da nazari. Kai Malan Sani ya jinjina kafin yacigaba da tuk'i yana fad'in Adebayo shu'umin mutum ne, kasan yaren mutum da kud'i, duk da bansanshi ba, amma labarinsa daka bani yanzu yasa na fahimceshi, bazan ce ga wanda nake zargi ya bada damar shiga ofis d'inka ba, domin nasan idan zakaje sallah dole ka rufe odis d'in ka, amma dole sai ka sake lura Alhaji.
Jinjina kai Alhaji yayi yana fad'in nagose sosai Malan Sani, hakika Allah ya had'a ni da abokin shawara, na yarda da kai, kuma daga yau bani da abokin shawara sai kai, insha Allahu zanyi kamar yanda kace, da sannu sai na gano gaskiya kuma sai na tabbatar da ita, wallahi kaji na rantse maka sai na tabbatar da ainihin fuskar Alhaji Marusa, domin fuska biyu yake da ita, amma zan kwantar da kai domin na samu damar aiwatar da komai cikin sanyi.
Malan Sani yace wannan haka yake, idan mage zata kama b'era kwantar da kai takeyi har sai ta cika burinta, dole sai kayi hak'uri kafin ka tabbatar da gaskiya. Alhaji yace nagode sosai.
Bayan da ya ajeshi ya wuce ofis, sam be nuna komai ba, haka yakira Adebayo yace a saki kayan Alhaji Marusa. Risnawa yayi yana fad'in angama Sir.
Bayan da ya dawo sallar azahar ya iske wasu mutane suna jiranshi. Izinin shiga ya basu. Bayan sun gama gaisawa d'aya daga cikinsu yace sunana Brr. Barau daga babbar kotu, wannan abokin aikina ne Brr. Hamza.
Alhaji yace madalla sannun ku da zuwa, akwai wani abu da kuke buk'ata ne? Brr. Barau yace wani mutumi ne ya shigar da k'ara a kotu saboda wani zalunci da akayi masa, ya kasance yana shigo da taliya dasu makaroni da sabulai daga waje, yau kusan sati d'aya kenan kayansa suka iso, yace ya biya komai amma kuma da aka tashi sakar masa kayan sai aka bashi ba yanda suke ba, wanda hakan ya jawo masa asara sosai, shine yashigar da k'ara, da muka duba sai naga a wajen ku ne, kuma ni ina mutunci da ma'aikatan wajen nan, wanda ya bar wajen ma nine Lauya d'inshi, hakan yasa nace zanzo domin naji yanda gaskiyar abun take, domin mutumin ya d'auko lauya, ni kuma ina giramama ofis d'in ku shiyasa nace zan tsaya maku domin a wanke ku daga zargi, dan idan har akayi shari'ar aka tabbatar daga cikin ku wasu sun danne masa kaya tabbas mutuncin ku zai zube, gashi kai sabon zuwa ne a nan baka gama sanin komai ba, idan akace ma baka da labarin abinda ya faru baza'ayi gardama ba, domin an fad'a mani ajiya ne ka fara sabon tsari.
Cike da mamaki Alhaji yake kallonsu, ak'asan ranshi yana fad'in kaji wata sabuwa kuma. Murmushi Brr. Barau yayi yana fad'in kada ka damu Alhaji, ni da ku babu wani shamaki domin akwai taimakekeniya atsakanin mu, tsofaffin ma'aikatan wajen sun san da haka, domin kowa ya sanni, dan kana sabon zuwa ne, amma shi Adebayo mutumina ne sosai, dan haka kada ka damu a shigar farko zan kada su, domin ni shari'a cin abinci ma yafi mani wahala akanta, domin ni haka nake, wasu ma da *MAI NASARA* suke kirana. (Tsohon littafina,)
Murmushi Alhaji yayi danshi ya ma rasa bakin magana. Tashi Brr. Barau yayi yana fad'in kada ka damu, wannan itace takardar sammaci daga kotu, zuwa ranar litinin za'a shiga, sai kayi kokarin gano wad'an da suka aikata hakan idan baka da masaniya domin kaja masu kunne, zanyi magana da Adebayo sai mu k'arasa komai dan naga baka gama warware wa da wajen ba, gashi lokaci ya k'ure dole muyi sauri domin mu kare mutuncin ku, saboda kai d'in sabon zuwa ne bazamu so ka fara da haka ba.
Kai Alhaji ya jinjina danshi gaba d'aya kanshi ya k'ulle, beda masaniya akan komai, bazai iya shiga abinda bai sani ba, dole ya zuba masu ido yaga abinda zasuyi dan shi yanzu yanda zai b'ullo ma Alhaji Marusa kawai yake damunsa.
Hannu Brr. Barau ya bashi yana fad'in sai ka jini mungode da lokacin daka bamu. Alhaji yace bakomai nagode. Bayan sun fita Alhaji yashiga dogon tunani, tabbas lokacin da aka aikata wannan abun beda masaniya, yanzu shikenan haka za'a danne ma bawan Allah kayansa kuma kotu ta bashi rashin gaskiya? To idan ma yace zai taimaka mashi ta yaya? Dole wannan karon ya aikata laifi kodan kare mutuncin aikin su, amma matukar aka gama da kotu saiya gano wad'an da suka aikata wannan abun kuma sai ya d'auki mataki, dole yajira litinin yaje kotu yaji komai.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:38 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kudi ne, naira 200 kacal, MTN Card ta wannan lambar... 08147669770, kayi screen shoot ka tura ta whatsapp a lambar k'asa, idan kuma bank transfer ne ka tuntube ni a whatsapp ta wannan lambar 08028525263.*
0⃣7⃣
Tafe suke a mota ya kalli Malan Sani yana fad'in wato Malan Sani idan kana da rai zakayi ta ganin abubuwan al'ajabi. Malan Sani yace wani abun akayi maka ko Alhaji? Murmushin gefen baki yayi yana fad'in maganar da mukayi da kai jiya itace ta rushe, an duba kemarar babu komai aciki, an samu wani mai wayon ya goge abinda ta d'auka.
Kallonshi Malan Sani yayi cike da mamaki yana fad'in amma Alhaji ya akayi haka ta faru? Alhaji yace mai son abunka yafika dabara ai, naje sallar azahar lokacin ne aka shiga ofis d'ina.
Malan Sani yace ina Malan Bala to? Alhaji yace atare muka je masallaci dashi kum na rufe ofis d'in. Jinjina kai Malan Sani yayi yana fad'in lallai ko waye ya san takan ofis d'in. Alhaji yace ko waye yayima kansa, kuma insha Allahu matuk'ar ina raye sai na kawo k'arshen zaluncin da akeyi.
Yanzu haka ranar litinin kotu zamuje, d'azu wani Brr. Barau yazo ya kawo mani takardar sammaci wai an zalunci wani ya shigar da k'ara, kayansa ne sukazo sai aka rik'e, bayan daya amsa sai ya samu abubuwa da yawa sun b'ata, yayi asara sosai shine yashigar da k'ara, abinda na lura dashi Brr. Barau ya dad'e yana ma ofis d'in mu aiki, da alama shid'in marar gaskiya ne.
Murmushi Malan Sani yayi yana fad'in Alhaji waye besan Brr. Barau ba, wannan mutumin idan beyi wasa ba sai yaci wutar Allah, duk wata k'ara da aka kaita babbar kotu matuk'ar mutum ya saki kud'i Brr. Barau zai tsaya masa, kafin a kadashi a shari'a da wuya, shi kuma Alkali kwakkwarar sheda yake nema, matuk'ar ya sameta shikenan zai yanke hukunci, wannan adalci da Alkali yakeyi shine yasa mutane suke sonshi, duk da wani lokacin ba akan gaskiya yake yanke hukuncin ba amma babu yanda ya iya, domin abinda ya gani dashi yake aiki, kuma baya yanke hukunci sai kowa ya sheda gaskiyar abinda aka gabatar, shiyasa nake fad'a maka Brr. Barau shine babban azzalumi.
Alhaji yace abinda yake fad'a mani kenan da yazo, wai ni sabon zuwa ne shiyasa yazo da kanshi dan baya so daga zuwana na samu matsala, shiyasa yake so ya wanke mu. Girgiza kai yayi yana fad'in Malan Sani a wannan karon bani da zab'i, domin lokaci ya kure mani, idan nace bazan bi yanda yace ba tabbas nine a k'asa, domin bansan da wannan maganar ba sai zuwanshi.
Tausayi Alhaji ya ba Malan Sani, domin yasan yana son tabbatar da gaskiya amma be gama sanin kan wajen ba. Kallonsa yayi yana fad'in Alhaji kada ka karaya domin Allah yana tare da mai gaskiya, bakomai kaje kotun kaji yanda komai yake Allah yaga zuciyar ka, idan yaso daga baya sai kayi bincike.
Murmushin jin dad'i Alhaji yayi yana fad'in nagode Malan Sani, ina matuk'ar jin dad'in zamanka akusa dani, insha Allahu zanyi kok'arin bincike domin na gano gaskiya, kila ta wannan hanyar ne Allah zai haska mani komai. Malan Sani yace in Allah ya yarda.
***** ****
Ranar litinin haka babbar kotu ta cika, *Alhaji Usman* wanda shine ya shigar da k'ara yana daga gefe shida sauran abokansa tare da lauyen daya d'auko.
Alhaji Maiwada yana isowa Brr. Barau da Adebayo suka tarbeshi. Bayan sun gaisa Brr. Barau yace Alhaji komai ya kammala insha Allahu zamuyi nasara. Murmushin takaici Alhaji yayi yace Brr. Allah ya shige mana gaba. Brr. Barau yace amin.
Cikin lokaci k'ank'ani aka kammala shari'ar wanda Brr. Barau ne yayi nasara, domin ya gabatar da shedun bogi wanda kowa ya d'auka da gaske ne. Alhaji Usman kusan zubewa yayi lokacin da Alkali ya yanke hukunci, zama yayi ana ta yimasa fifitu.
Alhaji Maiwada yana zaune kamar wanda aka dasa, besan lokacin da idonshi ya cika da kwalla ba, lallai duniya babu gaskiya, yanzu shikenan an cuci wannan mutumin? Kallon Brr. Barau yayi yaga suna kashewa da su Umar da Adebayo. Murmushin takaici kawai yayi ya bar kotun ko ta kan Brr. Barau bebi ba suka tafi ranshi a b'ace.
****
Ranar Talata tunda safe Alhaji yaje ofis. Malan Sani shima be tafi ba saboda anyi suna, tunda yazo suke zaune da Malan Bala suna ta fira, a hankali Malan Sani yake tambayar Malan Bala yanda wajen yake. Haka Malan Bala yayi ta bashi labari.
Har zuwa azahar Alhaji yana bincike akan abinda ya faru, wasu daga cikin ma'aikatan da ya yarda dasu yarik'a kira yana masu tambayoyi tun daga ranar da abun ya faru.
Mutum d'aya ya samu mai suna *Abubakar*, shine mataimakin mai kula da kaya, kasancewar shima yana kwatanta gaskiya yasa ake maidashi baya tun lokacin tsohon shugabansu, musamman idan akace kaya masu tsoka sunzo.
Kallon shi Alhaji yayi yana fad'in Abubakar aranar da kayan Alhaji Usman suka zo ya akayi da aka rike masa wasu daga ciki suka b'ace? Gyara zama Abubakar yayi yana fad'in wallahi Alhaji aranar da abun zai faru Adebayo da Umar ne suka karb'i kayan, ina wajen amma sai Adebayo ya bani sako na kaima Alhaji Marusa, ban dawo ba saboda dare yayi sai kawai na wuce gida.
Jinjina kai Alhaji yayi yana fad'in dole sune suka d'auki kayan Alhaji Usman. Abubakar yace kuma sun amshi kud'i da yawa awajenshi kafin suka sakar masa kaya, kuma ina tunanin kayan nan basu raba su ba, dole akwai inda suka aje su, akwai *Moses* abokina ne yasan sirrinsu domin suna yaga masa wani abu saboda sun san halinsa, ina ganin zai iya sanin yanda akayi da kayan.
Alhaji yace Abubakar kira mani shi Allah yasa ya bamu had'in kai. Abubakar yace kada ka damu nasan waye Moses, mutumina ne sosai. Waya ya dauka ya kirashi.
Beyi mintuna biyar ba sai gashi. Risnawa yayi ya gaishe da Alhaji. Wajen zama Alhaji ya nuna masa, bayan ya zauna Abubakar yayi masa bayanin abinda Alhaji yake buk'ata.
Murmushi Moses yayi yana fad'in Sir, wannan abu ai ya dad'e yana faruwa a wajen nan, tun lokacin da nazo Oga John yake abinda yaga dama shida su Oga Adebayo, Omar shima baya da gaskiya, saboda sun san nasan komai yasa suke yaga mani kasona, Sir kasan zuciya da kud'i shiyasa nima nake amsa, amma wancan ranar da suka sace kayan Alaji Osman ni nasan inda suka b'oyesu, sunce sai anyi kamar wata d'aya ko biyu komai ya wuce sai suzo cikin dare su kwashe abunsu su raba, acikinsu akwai wasu ma'aikatan da suke bin bayan su. Sir ina fad'a maka a wajen nan fa akwai b'arayi, ni dai bana sata, amma idan aka bani ina amsa
Alhaji yace yanzu Moses a ina suka aje kayan? Moses yace Sir, zan fad'a maka amma du Allah kada ka beri su gano nine na fad'a maka, ina son kud'i kuma idan suka gano bazasu rik'a bani ba.
Murmushi Alhaji yayi yana fad'in zan rubuta sunanka acikin wad'an da zan dakatar har na tsawon watanni biyu kuwa, domin kana amsar cin hanci wata rana zaka fara d'aukar kayan wasu.
Zubewa Moses yayi yana fad'in du Allah Alaji ka rufa mani asiri, wallayi daga yau zan zama kamar Abubakar, zan rikayin gaskiya. Alhaji yace naji, amma idan na gano kacigaba da karb'ar cin hanci sai na dakatar da kai. Tashi Moses yayi yana murza hannu yace na yarda. Nan ya fad'a masu inda kayan suke.
Jinjina kai Alhaji yayi yace suje. Bayan sun fita yayi shiru yana tunanin yanda zai b'ullo ma al'amarin, baya so ya watsa ma Brr. Barau k'asa a ido, domin idan yace zai bayyanar da gaskiya tamkar yaci masa fuska ne, amma dole ya hukunta duk wanda yake dasa hannu a cikin wannan abun.
Waya ya d'auka yakira Adebayo. Ba'afi mintuna biyar ba sai gashi ya shigo yana ladabin munafurci. Murmushi Alhaji yayi yana fad'in Adebayo na samo inda kayan Alhaji Usman suke, kuma za'a mayar masa da abunsa.
A zabure Adebayo ya mik'e yana fad'in Sir, waye ya fad'a maka inda suke? Alhaji yace kasan b'oyesu akayi kenan? Zama yayi jiki a sanyaye yana fad'in Sir, ba haka bane, naga an gama komai a kotu be kamata amaido maganar baya ba.
Tashi Alhaji yayi yana fad'in na baka nan da anjima ka rubuto mani sunayen wad'an da suke dasa hannu a abinda kukayi, a sunan farko kasa naka dana Umar.
Hannu Adebayo yasa yana goge zufa, hannuwa yahad'e yana fad'in Sir, kayi hak'uri, shikenan zan fito da kayan amma kada a koma kotu domin zamu iya rasa aikin mu kuma za'a iya kaimu gidan yari.
Alhaji yace abu d'aya zakayi, matuk'ar ka rubuta mani sunayen wad'an da suke dasa hannu a abinda kukayi to bazan kai ku kotu ba, amma ina da sharad'i wanda dole ne ku bishi.
Da sauri Adebayo yace yanzu zan fad'a maka, mu biyar ne hada Omar, kuma zamubi sharad'in ka. Jinjina kai Alhaji yayi yana fad'in doka zata fara aiki daga kanku, sai dai zan maku sauki zan dakatar da ku na wata d'aya kawai, sannan zanyi magana da Alhaji Usman, idan ya yafe maku shikenan, idan kuma yace sai an koma kotu bani da zab'i.
Cike da damuwa