Advertisements
Chapter 53 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   53 / 54

156K to 159K   out of 160.3K words

burina ya cika, takardar aje aikina tana nan na dad'e da rubuta ta kwanan wata kawai zan saka na basu abunsu, nifa na kosa mu bar garin nan ma.


Dariya suka sa gaba d'aya. Ummu tace maganar ka gaskiya ce Ra'eez, koni bazan barka kacigaba da wannan aikin ba, haka kuma jina nake kamar ina zaune asaman k'aya domin garin nan ya fitar mun arai.


Jinjina kai Abbah yayi yana fad'in tsarin mu yana kan hanya d'aya, dama na tambayeshi ne dan ban sani ba ko ya canza ra'ayi, amma tunda kana kan ra'ayin ka shikenan Allah ya albarkaci aikin da kayi, sai mu koma Kano a sama maka wani aikin, amma wane aiki kafi so?


Murmushi Ra'eez yayi
yana fad'in nafi son naganni ina koyawa a jami'a, domin buri na ne, shiyasa ma dana samu aikin nake son na k'aro karatu, dan arayuwata ina son aikin da yake da lokaci, wanda mutum zai iya tsara lokacinsa da kanshi, kuma kowa yasan koyarwa ce kad'ai take da wannan tsarin.


Kai Yaya makarantar 'yan mata kuma zakayi aiki? Rumaisa ta fad'a kamar an tsikareta, hannu tasa ta rufe bakinta ganin a inda tayi maganar. Da sauri ta mik'e tayi waje hakan yasa suka kwashe da dariya.


Umma tace kina da gaskiya 'Diyata, nima na fara tayaki kishi haka kawai zaije cikin 'yan mata yarik'a bud'e murya yana koya masu. Mama tace ai Yarona beda kalle-kalle kusha kurimin ku babu abinda zai faru.


Dariya sukasa Ummu ta duk'ar da kai tana murmushi. Abbah yace tunda dai shine ra'ayinsa zan sama maka, kai ina tabbatar maka wannan shari'ar da kayi zata d'aukaka ka, duk inda ka nemi aiki a fad'in k'asar nan sai ka samu, dan haka mu fara shirin tafiya, Malan Sani gara mu tafi daga baya sai mu dawo asa duk gidajen kasuwa domin mun bar Lagos kenan sai dai muzo da yawo saboda mutanan arziki.


Malan Sani yace duk yanda kace Alhaji haka za'ayi, domin banki kada na kwana alagos ba yau dan wallahi ta fitar mun arai. Abbah yace shikenan zuwa nan da kwana biyu sai mu tafi kafin nan an kammala komai.


Madu ne ya kalli Malan Sani yana fad'in dan Allah Malan Sani ka yafe mani, har yanzu ina jin kunyar shedar dana bayar akan ka wancan lokacin.


Murmushi Malan Sani yayi yana fad'in wai Madu bazaka dena wannan maganar ba, tun yaushe nace na yafe maka, ko nine fa amatsayin ka wallahi shedar da zan bayar kenan, dan haka komai yawuce.


Abbah yace ai wannan maganar ma abar tada ta, wad'an da suka assasa fitinar ma suna can nasan mutanan gidan Yarin kad'ai sun ishesu, dan haka kowa yayi nagari kansa, ubangiji Allah ya k'ara tsare mana Imanin mu da zuk'atan mu.


Sai magana ta gaba, muna komawa Kano zanyi bikin Yarana dan bazan jira komai ba, ko kuma hada Raheenar zaka had'a? Waro ido Ra'eez yayi yana kallon Abbah da yake kunshe dariya.


Umma tace Allah ya kyauta wallahi Yarona bazai had'a zuri'a da wad'annan mutanan ba. Dariya sukasa Abbah yace dama tsokana ce, babu wata amarya agidan Ra'eez sai Rumaisa ta. Malan Sani yace ai duk yaranka ne duk yanda kayi yayi, Allah yasa alkhairi. Gaba d'aya suka amsa da amin.


*** ***


Maganar ka gaskiya ce Nabeel, dama ka fad'a, zuwa kwana biyu za'a dena labarina, gashi kuma ya tabbata, sai fatan Allah ya yafe mani, dad'in da nakeji yanda Iyayen Farouk suka yafe mani.


Nabeel yace ai Abbah dama na fad'a maka, duk abinda mutum ya aikata akwai wanda ya aikata abinda yafi nashi, Allah dai ya k'ara tsare mu baki d'aya.



Ummansa tace amin Nabeel, ya jikin Raheenar kuma? Kallonsu Abbah yayi yana fad'in wacece kuma Raheena? Duk'ar da kai Nabeel yayi yana murmushi.


Murmushi Abbah yayi yana fad'in to nagane, na samu surika kenan, amma a ina take haka? Sosa kai Nabeel yayi yana fad'in Abbah anan garin take, sai dai zuciyata tana cikin damuwa saboda nasan na d'auko abinda bazaku amince dashi ba, nima wallahi bansan yanda akayi zuciyata ta kamu da sonta ba, domin komai ya faru ne ayau, yanzu hakama daga wajen ta nake tana asibiti bata da lafiya.



Hannunsa Abbah ya kamo yana fad'in bana so kasa aranka ni zan iya tauye maka hakkin ka, fad'a mani wacece ita? Kallon Umma yayi yana fad'in 'Yar gidan Alhaji Barau ce Alkali.


Ajiyar zuciya Umma ta sauke tayi shiru tana kallonsu. Shiru shima Abbah yayi har Nabeel ya fara tsorata da shirunsu, can Abbah ya saki murmushi yana fad'in Allah mai juya al'amura, nine nake tsoron ranar da zaka kawo mani surika arik'a goranta maka abinda Mahaifinka yayi, sai gashi Allah ya k'ulla alak'a tsakanin ka da wacce laifin Mahaifinta ya take na Mahaifin ka so dubu, matuk'ar ita yarinyar tana da hali mai kyau bazan hana ka aurenta ba, domin laifin wani baya shafar wani, Allah ya tabbatar da alkhairi.


Kallon Umma Nabeel yayi yana matse idanu. Hannu tasa ta ja kunnansa tana fad'in amsata kake jira? Kai ya d'aga yana kallonta. Murmushi tayi tace Allah yasa abokiyar rayuwarka kace.


Rungume Umma yayi yana fad'in amin Ummana, nagode sosai, yanzu na samu kwarin guiwar tunkararta da maganar dama amincewar ku nake jira sai dai kutayani da addu'a akwai soyayyar wani a zuciyarta, sanin bazata sameshi ba yasa tashiga cikin wannan halin.


Abbah yace *WAYE NE*? Nabeel yace Brr. Ra'eez ne. Jinjina kai Umma tayi tana fad'in itama ta d'ebo da zafi, koda yake kowama sai yanzu yasan d'an gidan marigayi ne, babu komai, matuk'ar kana sonta kaje ka gwada sa'ar ka. Abbah yace Allah ya baka sa'a. Yace amin.


*** ***

Kwance take ajikin Momy tana kuka, hakuri Momy take ta bata. Raheena tace Momy Dady ya cuceni, ba dan wannan abun daya aikata ba nasan dole na samu Ra'eez, amma kina gani sai dai na hakura dashi, gashima har yana da matar aure, shikenan nasan bazanyi aure ba har na mutu domin Dady ya goga mani bakin fenti.



Shafa kanta Momy tayi tana fad'in zakiyi aure Raheena, domin a yau da kika rasa Ra'eez Allah ya kawo maki wani, abinda nakeso da ke ki daure ki amshe shi, domin idan kika rasashi zaiyi wuya ki sake samun wani, domin shine yazo maki alokacin daya kamata kowa ya gujeki, dan haka ina mai baki shawara daki amshe shi, tunda kika suma yake tare da ke be jima da tafiya ba yace zai dawo, shima abokin Ra'eez ne, sunanshi Nabeel, d'an gidan tsohon shugaban makarantar kings college ne wanda aka yanke ma Mahaifinsa hukunci wan can satin shida Alhaji M. Sanda, yaron kirki ne ina maki sha'awarsa.


Shiru Raheena tayi ta d'ago kai tana kallon Momy, zatayi magana aka turo k'ofa. Nabeel ne dasu Ra'eez suka shigo bakinsu d'auke da sallama.


Saurin duk'ar da kai Raheena tayi dan yanzu kunyar Ra'eez takeji. Momy ce ta amsa masu tana masu sannu da zuwa. Zama sukayi suka gaisheta tare da tambayar mai jiki.


Momy tace gatanan taji sauki likita ma ya sallame mu dama zaman jiranku nakeyi tunda Nabeel yace mujirashi. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in K'anwata babu magana.


'Boye fuskarta tayi tana murmushi. Jabeer yace ko saboda Nabeel ai sai a kallemu. Murmushi Nabeel yayi yana fad'in dan Allah kubarta ta huta. Tashi Ra'eez yayi yana fad'in anbarta mai Raheena, Momy kutashi mu wuce.


'Dago kai Raheena tayi zata kalli Nabeel caraf suka had'a ido, da sauri ta kauda kai tana jin fad'uwar gaba. Haka suka tattara suka wuce gida.


Bayan sun ajesu Ra'eez ya fad'a masu nan da kwana biyu zasu koma Kano da zama. Momy tace muma ai bazamu zauna ba Kanon zamu koma gobe ma.


Ra'eez yace ashe muna kusa, to Allah ya taimaka, na manta Alhaji yace na fad'a maki ya datse igiyar auren ku. Tsaki Momy taja tana fad'in shi ya sani dai, nagode maku, kome kenan zamuyi waya.



Ra'eez yace shikenan. Sallama sukayi masu Nabeel yace nima ina nan. Jabeer yace dama kaji munce kaTaho? Ai gara ka zauna kuyi sallama.


Fita sujayi suna dariya. Suna shiga mota Jabeer yace wai da gaske garin nan zaku bari? Ra'eez yace wallahi kuwa. Jabeer yace aikuwa wallahi tare zamu tafi nima na rubuta takardar aje aiki na. Waro ido Ra'eez yayi yana fad'in yaushe? Jabeer yace tun lokacin da nasan zaka aje naka.


Ra'eez yace su Abbah bazasu barka ba ai. Jabeer yace tuni ma suka amince, da ace mace ce ni ai dole na rabu dasu saboda aure, dan haka sun amince zan koma Kano da zama kuma nima rin aikika zanyi.


Rungumeshi Ra'eez yayi hawayen farin ciki suna sakko masa, bayansa ya dafa yana fad'in nagode d'an uwana, hakika tarayyar mu daga Allah take, na dad'e cikin damuwar rabuwar mu, ashe zamu kasance tare, muje dole nayima su Abbah godiya.


Dariya Jabeer yasa yana fad'in sai dai zuwa anjima yanzu muje ka rakani na shigar da kaina wajen Husnah kaga muna komawa sai asha bikin mu tare. Dariya Ra'eez yasa yana fad'in yanzu kuwa.


*** ***

Kafin dare an gama kammala duk wasu labarai, tun daga gidan tv, gidan radio, yanar gizo, kai duk wata kafa ta yad'a labarai sai da aka yad'a maganar shari'ar su Alhaji Barau.


Ba iya Lagos ko Nijeriya ba, gaba d'aya duniya labarin wannan shari'a ya watsu, duk inda kasan akwai yanar gizo to dole su samu wanann labari.


Mutanan da suka kalli wannan shari'a basa kirguwa domin abune daya tab'a zuk'atan mutane, yayin da wasu suke Allah wadai da halin su Alhaji Barau.


Haka Rafeek sai da ya bada firar da suka tab'ayi da Kwamishna a gidan Tv aka kunna, wanda hakan ya jawo karin surutu awajen mutane, kowa yana fad'in ta bakinsa, yanda Kwamishna yake lailaya zance ta kamar mutumin kirki ashe azzalumi ne.


*** ***


Washe gari wajen k'arfe sha d'aya aka aiko kiran Alhaji Marusa. Koda yazo yayi mamakin wanda ya iske a wajen. Zama yayi jikinsa a sanyaye. Jin shiru anki magana yasa Alhaji Marusa yace Khalil!.


Idanuwa kawai Khalil ya tsura mashi ya kasa magana. Matsowa Alhaji Marusa yayi hawaye suna sauko masa, hannu ya kai zai kamo Khalil yayi saurin kwace hannun sa yana fad'in kada ka tab'ani. Alhaji Marusa yace kayi hakuri Khalil, nasan bani da bakin da zan maka magana amma inaso ka d'auka kaddarace ta sameni.


Tashi Khalil yayi yana fad'in babu wata K'addara Dady, kai ne ka zab'ama kan ka wannan rayuwar, ko haihuwar mu da kayi Allah ne yasa zamu fito duniya, kud'in ka sune Mahaifanmu domin sune suke kula damu ba kai ba, bakasan komai namu ba, baka san tarbiyar mu ba, kawai ka turamu cikin turawa dan kada muzauna akusa da kai mutakura maka, Alhamdulillahi ina k'ara godiya ga Allah daya shirya ni, haka ina bakin ciki da Yaya ya tsinci kasan a irin halin da kake ciki, dama kuma barewa bazatayi gudu d'anta yayi rarrafe ba, bansan abinda kayima Momy kenan ba sai jiya Yaya yake fad'a mani da mukayi waya bayan daya samu aron waya dan yaga abinda ya faru da kai.


Tunda aka kamashi so d'aya bakaje ba, shiyasa ya aiko ni na fad'a maka yana tayaka murnar zaman gidan yari, dalilin zuwana saboda ka fad'a mani inda Momy take naje na nemota domin bazan iya barinta ba, saboda itama bata barmu ba alokacin da baka kula damu.


Cikin kuka Alhaji Marusa yace kayi hakuri Khalil, nasan ban kyauta maku ba, kuma naji dad'i dana ganka cikin kamala, dama kuma Allah yana fitar da rayayye a jikin matacce, bakasan abinda Momynku tayi bane amma zan fad'a maka......


Hawayen bakin ciki ne suka zuboma Khalil daya gama jin abinda ya faru. Alhaji Marusa yace bayan tafiyarta da kwana biyu na samu labarin mutuwarta, ashe barin ta nan abinda saurayinta yayi mata ya jawo mata ciwon zuciya, ciwon kwana biyu zuciyarta ta kumbura ta mutu, kayi hakuri da ban fa....


Saurin tashi Khalil yayi yana fad'in ya isa, ba sai ka k'arasa ba, Allah yajik'anta, nima zan koma inda ka koya mani rayuwa, Alhamdulillahi na had'u da Ubangida nagari mai ilimin addini, duk da kasancewarsa farar fata amma musulmi ne, kuma ya samar mani shedar zama d'an k'asa, yanzu haka bikin mu za'ayi da d'iyarsa, dan haka daga yau ni ba d'an najeriya bane na manta da ita zan rik'e surukaina amatsayin iyayena.


Rikoshi Alhaji Marusa yayi yana fad'in na amince da haka, kuma naji dad'i, amma inaso kaje gidana cikin d'akina zakaga takardun kadarorina ka d'auka gadonka ne duk... Hannu ya d'aga masa yana fad'in kai da kotu ta bayar da dukiyar ka ina kake da wasu kud'i? Ko kana dasu wallahi bazan sake cin sisin ka ba domin dukansu haram ne, nizan wuce, ina rokon ka da ka yafe mani idan na maka badede ba.



Kuka Alhaji Marusa yasa yana kiran Khalil amma ko juyowa beyi ba. Zubewa yayi a wajen yana wani irin kuka. Masu gadi ne sukazo suka korashi ciki.


Haka ya koma wajen da suke fasa duwatsu, yana kuka yana cigaba da aiki, su Alhaji Barau ne suke bashi hakuri suma kukan suke, tausayin kansu ne ya kamasu, acikin kwana daya komai ya canza masu, lallai duniya abun tsoro ce.


*** ***


Duk wata dukiya ta masu laifi sai da jami'an tsaro suka had'a kanta, gidaje da sauran kadarori duk sun had'a takardunsu za'a sasu kasuwa dan sai an fitar da abinda kotu ta yanke idan anyi saura a basu kayansu.


Su Momy tuni suka kama hanyar Kano wanda Nabeel ne ya d'auki nauyin kaisu dan yakasa ya tsare dole sai da Raheena ta saurareshi, hakan yasa yace zai kaisu domin ya gano waje. Itama Raheena tana jinsa aranta dan tana kokarin cire Ra'eez dan tasan ta rasashi, gara ta amshi Nabeel koba komai yanzu ta fara sanin dad'in so saboda ta samu mai sonta ba wanda take so ba, domin za'a kirata aji lafiyarta, sab'anin da itace take kira.



Lokacin da shugaban kula da hakkin wad'an da kotu ta nema da a damk'ama tarar da ta yanke ya buk'aci ganin Malan Sani da Iyayen Naseer, bayan da yayi masu jawabi sai Malan Sani yace gaba d'aya abinda aka bashi a mik'asu gidan marayu dan bazai iya amfani da kayan haram ba, haka ma Baffa yace.


Wannan abu da sukayi bak'aramun burge mutane yayi ba, anan ya fito yasheda ma 'yan jarida komai, su kuma suka shiga rattabawa a labaransu, hakan ya jawo masu d'aukaka da addu'oi a wajen mutane, domin ba kowa bane zai iya tsallake irin wannan dukiya ayanzu.


*** ***


Aje aikin Ra'eez da Jabeer ya tab'a zuk'atan manyansu da sauran mutane, domin sun san sunyi asarar hazikai, tun daga can sama aka aiko da sakon ban hakuri da neman alfarma akan Ra'eez ya koma bakin aikinsa amma yace ayi hak'uri ya gama aikin lauya, duk yanda Alhaji Kamal yaso amma hakan be samu ba dole sai dai sukayi hakuri.



'Yan jarida kowa so yake yayi fira da Ra'eez amma yaki basu had'in kai, da sun tambayesa dalilin aje aikinsa amsar d'aya ce, dama cikar burinsa yake jira kuma ya cika shiyasa ya aje.



Tarin masoyan Ra'eez na garuruwa dama k'asashe basu fad'uwa domin har dena kunna data yayi saboda yawan sako.



*** ***


A ranar da zasu tafi kasancewar jirgin yamma zasubi hakan yasa Alhaji Mansur ya shirya masu taro a harabar gidansu Ra'eez, duk wasu abokan arziki sai da suka zo wannan taron domin su k'ara tayasu murna.


Iyayen Nabeel, Iyayen Sameer, Iyayen Rafeek, Iyayen Jabeer duk sunzo dan sunce zumunci yanzu aka fara.


Anci ansha kuma anyi raha, anan Alhaji Mansur ya tashi yana mik'a godiyarsa abisa goyon baya da kuma had'in kan da suka basu wajen ganin an kammala wannans shari'a, haka yayi ma Iyayen Jabeer godiya da suka amince mashi ya bisu, kuma yayi masu alk'awarin kula dashi kamar yanda zai kula da Ra'eez.


Anan ya kalli Iyayen Sameer yana fad'in ina nema ma 'Dana Jabeer auren Husnah domin inaso da an koma a had'a bikinsu dana Ra'eez. Dariya akasa nan Dadyn Sameer yace ai duk 'ya'yanka ne, dan haka na bama Jabeer Husnah.


Cusa fuska Husnah tayi cikin mayafinta tana sakin murmushi. Dadyn Sameer yace biki biyu zanyi, domin tare za'a had'a dana Sameer.


Abban Nabeel yace ashe kuwa za'ayi babban taro, domin shima Nabeel zan had'a nashi da Raheena, kunga kuwa ya kamata ace an tsaida bikin a waje d'aya.


Alhaji Kamal yace idan haka ne nine zan bada wannan shawarar, tunda mutanan Kano sunfi yawa kuma a cikin mu babu d'an asalin garin nan duk munfi kusa da can wajajen ina gani zamu maida bikin mu a kano, domin kuwa nasan zata d'auke mu.


Tafi akasa gaba d'aya kowa yana fad'in hakan yayi dai-dai. Baffa yace gaskiya naji dad'in wannan zumunci da yaran mu suka had'a, ubangiji Allah ya k'ara k'arfafashi har zuwa jikokin mu da masu zuwa bayansu.


Gaba d'aya aka amsa da amin. Alhaji Mansur yace insha Allahu zamu tsara yanda komai zai kasance, sai dai zamu aro al'ada, inaso bikin ya kasance tamkar na Yarbawa, ma'ana ayi komai arana d'aya atashi, a d'aura aure

53 / 54