Advertisements
Chapter 29 Reading ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ALKALI NE Hukuncin Boye by Marubuciyar Zamani

Author :  Marubuciyar Zamani Category :  Complete Novels

Chapter   29 / 54

84K to 87K   out of 160.3K words

kula da yaran mu wad'an da zamu haifa. Dariya Ra'eez yasa wacce besan da zuwanta ba.


Raheena tace kadena dariya nasan auren mu bazai ja lokaci ba, dan Momy da Dady duk sun san da maganar, kai kawai nake jira ka amince dani kuma nasan zaka amince tunda gashi kana kula ni.



Zeyi magana kiran Rumaisa yashigo wayarsa, dafe kai yayi aranshi yana fad'in ga sarkin kishi nan, amma bari ya gwada ta, sharewa yayi suka cigaba da magana.



Rumaisa kuwa ganin call waiting yasa taji ranta ya b'aci, sake gwadawa tayi amma yana waya, haka tayi ta kiranshi kusan mintuna ashirin begama wayar ba, haushi ne ya isheta tayi wurgi da wayar ta kwanta.



Hankalin Ra'eez gaba d'aya yana wajen Rumaisa, duk da yayi hakan ne dan ya tsokaneta amma sai yaji babu dad'i. Raheena kuwa sai zuba masa surutu takeyi, ganin yanda yake amsawa yasa tace Dear da alamu bacci kakeji.



Ra'eez yace gaskiya kam. Raheena tace shikenan bara na barka bana so na takura maka, ina fatan zakayi bacci mai dad'i. Ra'eez yace sosai kuwa. Raheena tace Dear bazaka ce naci abinci ba? Ya kamata ka lallasheni ko abu marar nauyi ne naci.


Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in to kisha tea da biscuit kafin ki kwanta. Murmushi ta saki tana fad'in yanzu kuwa my one. Sallama yayi mata ya kashe wayar.



Latso lambar Rumaisa yayi, har ta gama k'ara ba'a d'auka ba. Murmushi yayi ya sake kira amma bata d'aga ba. Sai da ya kira so biyar bata d'aga ba. Sako ya tura mata kafin ya aje wayar yana murmushi.


Rumaisa tana kwance ta gama jin wayarta na k'ara amma taki d'agawa wai tayi fushi. Jin alamun sako yasa tayi saurin jawo wayar.



*Tunda baki son jin muryata bara na nemo wadda zata taya ni fira kafin nayi bacci.*


Saurin tashi tayi tana kok'arin kiranshi. Murmushi ya saki a lokacin da yaga kiranta. Kashewa yayi kafin ya kirata.



Tana d'agawa ta fara masa rigima. Dariya yasa yana fad'in ashe dai ana sona? Turo baki tayi tana fad'in Allah Yaya wata rana zakasa zuciyata ta buga.


Ido ya zaro kamar tana ganinsa yace rufa mun asiri, idan zuciyarki ta buga nayi rayuwa da wa kuma? Da wacce kuke waya ka share ni mana.


Dariya yayi yana fad'in nikam naji dad'i domin an nuna ana kishina yau. Rumaisa tace Yaya... Kinga ni bana son wannan Yayan, ga sunaye nan masu dad'i kinemo kisa mun.


Murmushi tayi mai sauti tana fad'in ai bansan su ba. Ra'eez yace shikenan zancigaba da sauraran wacce take kirana da sunaye masu dad'i. Da sauri Rumaisa tace kayi hak'uri *Deel*.


Saurin kallon wayar yayi yana sakin murmushi, zeyi magana ta kashe wayar. Kwanciya tayi ta rufe fuskarta tana murmushi.


Sake kira yayi amma yaji akashe. Murmushi ya saki yana rungume filo, juyi yayi yana jin wani irin sanyi aranshi, tabbas soyayyar Rumaisa tayi nisa aranshi, baya jin zai iya rayuwa ba tare da ita ba, fatanshi a kammala wannan shari'ar ayi maganar aurensu. Haka yayi ta tunani har bacci ya d'aukeshi.


***

A gurguje ya shirya, koda yaje gidansu Rumaisa da kyar yasha tea ya tafi ko had'uwa da Rumaisa basuyi ba dan tunda safe Alhaji Barau yayi masa waya akan maganar jiya hakan yasa yake ta sauri.


***


Zaune yake a ofis d'in Alhaji Barau, mamaki yake ganin yau yashigo da wuri ko dan yau juma'a yasa yazo? Bayan sun gama gaisawa Alhaji Barau yace ai tun jiya naso kazo dan dai kace kana da uzuri.


Dama akan maganar wannan shari'ar ce da aka baka, maganar gaskiya Ra'eez wannan yaron da zaka kare Yaron abokin kasuwancin mu ne, babban aminin Alhaji Marusa ne, kasan yanda talakwa suke idan suna jin haushin mutum, wannan yarinya 'yan unguwarsu ma sun bata shedar bata da hali mai kyau, amma koma menene ina so ka duba shedun da aka baka da kyau, bana so ashiga kotu a samu matsala, domin wannan kotun kowa yasan yanda take da adalci bazan so ace a wannan karon dana zab'eka ace an samu matsala.



Gyara zama Ra'eez yayi yana fad'in insha Allahu Alhaji bazan kasance mai samar da rashin adalci a kotun ka ba, kamar yanda kowa yasan wannan kotu da adalci ina mai tabbatar maka zan tsaya tsayin daka domin a tabbatar da gaskiya a wannan shari'a.


Murmushi Alhaji Barau yayi yana fad'in nasan bazaka bani kunya ba, nagode sosai, zaka iya tafiya. Tashi yayi, har ya kai bakin kofa yaji muryar Alhaji Barau yana fad'in Raheena tace na gaishe ka.



Murmushi kawai Ra'eez yayi ya d'aga kai kafin ya fice. 'Yar dariya ya saki jin wani rashin kai a wajen Alhaji Barau, wai Uba ne yake bada irin wannan sakon. Tsaki kawai yayi yawuce. Kallon mutumin da suka taho tare da Brr. Bajinta yayi, kauda kai yayi yawuce dan ya gane Mr. Kallah tun wancan zuwan da suka had'u.



Bayan sun gaisa da Alhaji Barau Mr. Kallah ya kalli Brr. Bajinta yana fad'in d'an bamu waje zamuyi magana. Gimtse fuska Brr. Bajinta yayi dan beji dad'in abinda yayi masa ba.



Kallonshi Alhaji Barau yayi yana fad'in kaje kawai. Kai ya jinjina kafin ya fice fuska a d'aure.



Gyara zama Mr. Kallah yayi yana fad'in ka ganni da sammako ko? Murmushi Alhaji Barau yayi yana fad'in mamakin da nakeyi kenan, gashi baka kira kace zaka zo ba.


Mr. Kallah yace wani abu ne ya bani haushi siyasa na taso dan nasan baka da masaniyar abun. Alhaji Barau yace menene kuma ya faru? Mr. Kallah yace mutumin ka mana Alhaji Marusa.


Cire glass Alhaji Barau yayi yana fad'in wani abun yayi ko? Tab'e baki Mr. Kallah yayi yana fad'in ai nasha fad'a maka Alhaji Marusa beda gwani, tunda ya iya yakice 'yan uwansa nasan cewar kowama zai iya yakicewa.



Alhaji Barau yace dan Allah ka bani labari duk kasa kaina ya fara caji. Gyara zama Mr. Kllah yayi yana fad'in ajiya cikin dare ina duba Email d'ina sai ga sako yashigo mani daga *Mark* yana fad'a mani maganar da Alhaji Marusa yayi masa akan wannan kasuwancin da mukace zamu bud'e na shigo da manyan kayan zamani da Mark ya gano mana, kasan harkar akwai k'aruwa sosai, dan matuk'ar muka dace mun gama zama masu kud'i a duniya, kai ina tabbatar maka wannan aikin dole ka ajeshi dan zaman garin nan ma began mu ba.


Jinjina kai Alhaji Barau yayi yana fad'in ina jinka.


Mr. Kallah yace ashe Alhaji Marusa ya zagaye ya fad'ama Mark shi kad'ai zai sayi kayan saboda shine ya dad'e a harkar kasuwaci daga baya ya jawo mu, ya kyale mu zai yaga mana wani abu idan komai yayi dai-dai, to ahaka suka tsaya, kasan Mark beda munafurci, shine ya turo mani da sako jiya cikin dare yake fad'a mani yayi mamaki da abinda Alhaji Marusa ya fad'a saboda yasan yanda muka aminta da juna, shi kuma baya iya munafurci dan baya so yaga ta silarshi ya raba abokai, hakan yasa ya fad'a mani domin muje mu sasanta kan mu.


Dariya Alhaji Barau yasa yana buga tebur. Mr. Kallah yace indai Alhaji Marusa ne kuka ma sai ya saka. Tashi Alhaji Barau yayi yana fad'in wallahi k'aryarsa tasha karya, idan yana tak'ama da jinin fulani ajikinsa zan nuna masa irin namu cin duduniyar, ka barni dashi, cikin ruwan sanyi zan nuna masa rashin wayonsa.


Zama yayi yana fad'in kai baka tab'a tunanin dalilin da yasa na rabashi da gidanshi na Surelere ba? Duk da gidan ya kasance da zalunci aka amshe shi amma dai ya biya kud'in gidan, domin nasan da Iyalan Alhaji Maiwada suna nan har abada bazasu manta da wannan gidan ba.


Tun lokacin da wannan gidan ya zama mallakinsa na kudira araina sai na rabashi dashi, hakan yasa cikin ruwan sanyi da muka fara gabatar da kasuwanci atare lokacin da muka samu kaya masu kyau bayan an raba ya nuna yana son wasu daga cikin nawa na barmasa babu ja, da wannan na yaudareshi har ya siyar mani da gidan akan kud'i kalilan gashi yanzu ina rayuwata aciki nida iyalina hankali kwance.


Dariya Mr. Kallah yasa yana fad'in baka da kyau Alhaji Barau, ai tun alokacin na cika da mamakin yanda akayi ya siyar maka da gidan a wannan kud'i, ashe dai ka nuna masa kafishi sanin kan duniya.


Alhaji Barau yace ai karatun lauya ba k'arya bane, cud'anya da mutanen da nayi betashi abanza ba tunda gashi yayi mani amfani. Jinjina kai Mr. Kallah yayi yana fad'in a wannan karon ma baza muyi sanya ba, bana so abotar mu ta tab'u amma kada ka bari yasan munsan komai.



Alhaji Barau yace sa ido kayi kallo kai dai. Dariya sukasa suka cigaba da tattaunawa.


****


Bayan sun fita sallah Ra'eez be jira Jabeer ba ya sulale yaje ya dubo Ummunsa, sosai yaji dad'in ganinta dan jikinta da sauki, sai dai be samu ganin Dr. Saddek ba saboda yana sauri, hakan yasa yawuce.


Lokacin daya koma duk yanda Jabeer yaso yaji inda yaje be fada masa ba yace kawai Mama ce tayi masa kiran gaggawa hakan yasa ya yarda.



Bayan sun tashi daga aiki Ra'eez yace Jabeer ya masa rakiya zuwa gidan su Yaron da zai tsaya mawa. Jabeer yace kamar kasan abinda yake raina kenan, gara muje domin kaji ta bakinsa. Ra'eez yace haka ne, sai dai bana so kowa yasan naje wajenshi.



Jabeer yace muje akwai abinda zan fad'a masa wanda zai hanashi fad'ama kowa. Mota suka shiga suka tafi.


Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:39 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*



2⃣8⃣


Sun dad'e a tsaye jikin mota suna jiran su samu wanda yasan Yaron da suka zo wajenshi. Kallon Jabeer Ra'eez yayi yana fad'in kaga na manta sunan yaron da Baba ya fad'a mana rannan.



Jabeer yace anya ya fad'a mana sunansa kuwa? Gaskiya bana jin ya fad'i sunanshi. Waya Ra'eez ya ciro yana fad'in bara na tambayeshi gara musan sunanshi bana so asan wajenshi muka zo.



Bugu d'aya Baba ya d'auka, bayan sun gaisa Ra'eez ya tambayeshi sunan Yaron? Bab yace sunanshi *Sameer* gidansu shine na biyu akan layinsu yana nan mai bakin gate.


Ra'eez yace shikenan sai munyi waya. Kashewa yayi yana kallon gidan da suke fuskanta. Jabeer yace meye sunansa? Sameer! Ra'eez ya fad'a yana mayar da wayarsa aljihu.


Wani matashi ne yazo wucewa, da sauri Ra'eez yayi masa sallama, bayan sun gaisa yake tambayarsa ko yasan Sameer da yake wancan gidan? Murmushi Matashin yayi yana fad'in *B-Boys* zaka ce.


Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in shi nake nufi. Matashin yace yanzu zaka ganshi ya dawo dan lokacin zuwanshi bitch yayi. Jabeer yace lallai babban yaro ne. Matashin yace idan B-Boys ne ai beda wasa akwai son harka da jin dad'i.


Ra'eez yace mungode. Sallama yayi masu yawuce. Jabeer yace da ka sallameshi taya zamu iya ganeshi bayan bamu tab'a ganinshi ba? Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in sa ido kawai kayi kallo, mu k'arasa k'ofar gidansu zamufi saurin cimmasa.


Basu dad'e a wajen ba sai ga wata rantsatstsiyar mota mai bakin glass ta shigo layin, tun kafin ya iso sauti yake tashi, ganin mutane a bakin gate kuma Matasa ya hana Sameer yin horn, amma a k'aidarsa yana doso gidansu yake horn, kafin ya iso an bud'e gate sai dai kawai ya shige.


Sautin motar ya rage kafin yaja burki ya sauke glass d'in motar. Hannu yasa ya cire bakin glass da yake idonshi yana bin su Ra'eez da kallo, ko ba'a fad'a masa ba yasan wad'an nan matasan masu ji da kansu ne, domin su duka kyawawa ne, shigar jikinsu abun kallo ce domin dogayen kaya sukasa kasancewar yau juma'a.


Saurin matsawa Ra'eez yayi fuskarshi d'auke da murmushi ya mik'a mashi hannu yana fad'in barka da zuwa Sameer. Jiki a sanyaye Sameer ya bashi hannu suka gaisa.



Ra'eez yace idan bazaka damu ba inaso ka juya kan motarka zuwa inda tamu take akwai maganar da nake so muyi. Kallon rashin fahimta Sameer yayi masa.


Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in kada ka damu, sunana Brr. Ra'eez, nine wanda zan kareka a kotu ranar litinin. Jinjina kai Sameer yayi yana fad'in am sorry ban ganeka ba, muje.



Zaune suke a cikin motar Sameer sun zuge glass ta yanda baza'a gansu ba. Kallon Sameer Ra'eez yayi yana fad'in duk da an bani duk wata sheda dazan kareka nafi son nazo wajenka naji da bakin ka hakan zaisa nasan yanda zanyi na kare ka da kyau.


Jiki a sanyaye Sameer ya kalli Ra'eez yana fad'in wallahi Halima sharri take mun fa. Ra'eez yace kasanta kenan? Girgiza kai yayi da sauri yana fad'in haka naji wasu suna kiranta anan nasan sunanta.


Jabeer yace anan unguwar take ne? Sameer yace nifa bansan gidan su ba, kawai tana sona nayi mata wulakanci shine tace sai tasa an d'aure ni, bayan kwana biyu har na manta sai ga mahaifinta yazo wai nayima d'iyarsa fyad'e, ni mema zanyi da wannan k'azamar nida nake harka da.... Saurin had'iye abinda zai fad'a yayi.



Ra'eez yace dama kana harka da wasu matan ne? Saurin girgiza kai yayi yana fad'in nifa ko lafiyar kirki banda ita hakan ne ma yasa banyi aure ba amma har k'anina yayi aure.


Ra'eez yace ashsha, to Allah ya kyauta, shikenan zamu wuce, amma bana so kowa yasan nazo wajen ka idan ba haka ba shirin mu zai rushe.



Jabeer yace kana fad'ama Mahaifinka lauyen ka yazo shikenan hankalinsa zai tashi zaiyi tunanin ka fad'i wata magana. Cike da gamsuwa Sameer yace babu wanda zan fad'amawa dan Allah kada ka bari a rufe ni.


Ra'eez yace kada ka damu kotun mu wajen adalci ne. Jinjina kai Sameer yayi yana fad'in nagode. Sallama sukayi suka fita zuwa motarsu.



Kallon Ra'eez Jabeer yayi yana fad'in meka fahimta agame dashi? Beda gaskiya kawai, Ra'eez ya fad'a. Dariya Jabeer yayi yana fad'in kaifa lauyensa ne ya zaka fad'i haka? Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in su lauya manya, ai kasan Allah baza suyi nasara ba. Jabeer yace sai ka kula fa, bana so su Alhaji Barau su san cewar da gangan ka kadasu. Ra'eez yace kai dai kasa ido zakasha kallo, cikin week end d'in nan zan gama komai.


Jabeer yace Allah ya bada sa'a. Hannu Ra'eez ya bashi yana fad'in sai litinin ko? Jabeer yace haba dai, bazaka shigo ba? Ra'eez yace sai dai wani satin, dan wannan satin bazan fita ba inaso na shiryama wannan shari'ar. Jabeer yace shikenan, nima zan kwanta na huta sai munyi waya.


Sallama sukayi kowa ya nufi motarsa zuwa gida.


****


Wai Raheena har yanzu Ra'eez bece komai ba? Kallon Momy tayi tana fad'in yace mana, uhm! Wallahi Momy D, ya iya soyayya, bakiga yanda yake sona ba, damma suna da shari'a ranar litinin da wannan week end d'in tare zamu yishi anan gidan.



Murmushi Momy tayi tana fad'in amma naji dad'i sosai, shiyasa jiya nayi magana da Dadynki akan shirin bikin ki, waje nake so muje a had'o komai.


Rungume Momy tayi tana fad'in gaskiya naji dad'i, bakiga yanda k'awayena suke santinshi ba, rannan dana d'ora wani hotonshi dana had'a da nawa bakiga yanda mukayi kyau ba kamar atare muka d'auka, wasu sai cewa suke nayi dace.


Momy tace zauna nan su rufe ki da dad'in baki wata ta kwace maki shi. Zaro ido tayi tana fad'in haba dai Momy, ai Ra'eez nawa ne ni kad'ai, idan ban sameshi ba Allah kad'ai yasan halin da.... Saurin rufe mata baki tayi tana fad'in ko da zan rasa komai sai kin aureshi, dan haka ki kwantar da hankalin ki, kisa aranki anyi auren ku, dan yanda na fara fad'ama k'awayena an kusa aurenki bazan bari naji kunya ba.


Murmushi Raheena tayi tana fad'in ina sonki Momy na. Mai aikinsu ce ta shigo da sallama. Bayan sun amsa ta kalli Raheena tana fad'in Aunty lokacin shiga kicin yayi.



Saurin tashi Raheena tayi tana fad'in amma nagode, muje kada mu makara. Dariya Momy tayi tana fad'in Allah nagode maka, gaskiya naji dad'in zuwan Ra'eez rayuwarki Raheena, ta silarsa gashi kin canza, sallah akan lokaci, ga girmama masu aiki sannan abinci ma kin iya, ai dole ma na dage ki auri Ra'eez.


*** ***


Cikin kwana biyu Ra'eez ya kammala abubuwan da yakeyi, ko Ummunsa da kyar yake zuwa ya duba ta saboda beda lokaci, sunyi magana da Dr. Saddek yace sai litinin zasuyi mata awon akwai wani likita da suke jira zaizo.


Gidan su Rumaisa ma so d'aya yake zuwa da rana yaci abinci, yafiso ya kammala komai ta yanda zai shiga kotu da kwarin guiwa, hatta da wayoyinsa baya d'auka sai idan kiran me muhimmanci ne.


***


Safiyar litinin da wuri ya kammala shirinsa, haka ya nufi gidan su Rumaisa, bayan sun gaisa yace zai wuce. Mama tace abinci fa? Ra'eez yace Mama yayi safiya da yawa idan muka kammala zanci.



Girgiza kai tayi tana fad'in zauna kasha ko shayi ne. Haka ya zauna Rumaisa ta kawo masa. Zama tayi tana kallonshi harya kammala. Murmushi yayi yana fad'in kimun addu'a Allah ya bani sa'a kinji.


Kai ta d'aga tana fad'in inayi maka ai, kuma nasan zakayi nasara. Ra'eez yace nagode,

29 / 54