Advertisements
Chapter 70 Reading Ajiya A Duhu Book 2 Complete Hausa Novel.doc BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Ajiya A Duhu Book 2 Complete Hausa Novel.doc

Author :  Billyn Abdul Category :  Complete Novels

Chapter   70 / 138

207K to 210K   out of 412.8K words

baki da faWin,.....
'?






*_AJIYA A DUHU na kuWi ne, 500 ne kacal, ?ar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai =??=?O?_*

*09032345899*



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu =?-?=?O?_*
*_Typing=???_*








*_=???AJIYA A DUHU....=???_*




*_Bilyn Abdull ce >??

*_(P3REP 'DDQNGP 'D1QN-RENpFP 'D1QN-PJE_*
_Da sinan Allah, Mai rahama, Mai jin ?ai._

*_My TikTok account =?G?_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram=?G?
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R


_Duk wanda bai fallowing Wina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama=??=??
*_BOOK 2_*


______________


....... Zuwa yanzu ko baki san wanene ni ba kin san daga ina na fito. Kin kuma fahimci zan iya aikata komai idan baki min yanda nake so ba. Sunana Junaid ibn Junaid, kuma Wan Kamila .
? ? ?? Da wani irin razani Mamy ta kallesa yanzu ma har yawu na neman sar?eta ta ce,  Wace Kamilar? .
? ? ? Bayan ke akwai wata Kamila anan ne? Ki maida tunaninki baya, 39years da suka wuce, ranar lahadi ?arfe sha Waya da arba'in na daren litinin, cikin kangon jikin makarantar allon Malam Bello Wan Bichi dake bayan anguwarku. Budurwa ?ar kimanin shekaru goma sha bakwai, ana ruwan sama mai yawan gaske, ita kuma tana dur?ushe tana na?udar haihuwa data fara tun yammaci, fahimtar haihuwa zatai ya sata zuwa wannan kangon ta Suya, bata sha wata wahala ba ta haihu, tsabar taurin zuciya ta yanke cibin jinjirin da kanta sannan ta naWeshi a zani ta koma gefe ta huta batare da ko kallonsa tayi a matsayin sa na wanda ya fito a jikinta ba, kafin ta tashi ta sake Waukar jaririn ta fita a cikin dai wannan ruwan ta tafi can bayan layinsu a ?afa ko tsoro bata ji ta tona bola ta ajiye shi. Babu ko tausayi balle imani a tare da iya ta zuba tarin bolar nan a kansa ta rufe ta juya tabar wajen ranta ko gezau babu na nadama balle jin tausayi ta koma gidansu. A zatonta shike nan shike nan tayi AJIYA A DUHU na har abada, sai dai kuma shi ALLAH babu ruwansa, yayi al?awarin saina more wannan duniyar, harna taka ?asa nazo inda take da ?afafuna a yau a yanzu..
? ? ? ? Tunda Sille ya fara wannan bayanin jikin Mamy ke mazari. Zufa kam ba'a magana tai mata sharkaf. So take tai magana amma ta kasa, dan gaba Waya lissafinta ya birkice... Sille dake kallonta ya wani kwashe da dariyar ?eta yana mi?ewa.  Bara na barki haka, dan na fahimci ?wa?walwarki na bu?atar yin cikakken tunanin daya fi wannan bayanin nawa. KuWina kuma daga yanzu zuwa safiyar gobe ki tabbatar kin haWa min su. Idan ba haka ba zan sake dawowa na amsa da kaina, idan na dawo kuma zan fara ganawa da Alhaji Aliyu Darma ne kafin ke. Dan ya kamata shima fa ya tuna da abokinsa na yarinta Junaid, ya kuma san ala?ar Kamila da Fateema ta asali. Na barki lafiya mahaifiya ....
? ? ??? Iya kwatanta muku Mamy a cikin tashin hankalin da take ciki abu ne mai wahalar gaske, kawai dai kowa ya ?iyarsta a ransa, dan kuwa Sille ya tafi ya barta a wani irin mummunan yanayi ne mara kwatankwacin kintace. Binne sirri mai girma irin haka a kai kaWai batare da kowa ya taSa sani ba, sai bayan tsahon shekaru kwatsam wani yazo yace maka shine wannan sirrin naka, har ya labarta maka exactly abinda ya faru a shuWaWWen yanayin, bayan kayi imanin babu wani mahaluki daya ganka, tunda gashi har tsawon shekaru babu wani daya taSa kwatanta maka ya sani ko'a fuska, shi kuma wannan yaron jariri yake sabuwar haihuwa da baya magana baya gane komai ai ruWanin bashi da kwatankwaci. Yo ko gulma kayi da miji ko Wa ta fita ya kake shiga ruWanin mamaki balle irin wannan na Mamy, ai sai ka rasa ina zaka kama ina zaka ri?e ma gaba Waya. Ga zancen Sille ya tabbatar mana akwai ala?a tsakanin Abah da Junaid ubansa, kenan dai akwai AJIYA A DUHU tsakanin amintakar Kamila da Oum ma tun asali tun fari. Babbar magana. Kumuje zuwa kudai, sannu a hankali komai zai warware kansa dai....

____&
? ??
? ?? Motar AA dake dawowa gida na shigowa gida Sille na ficewa. Da mamaki yake kallonsa, duk da ba fuskarsa ya gani da ?yau ba kamar a gidan Hajiya Turai. Amma gaba Waya zubin mutumin da wata tafiyar rangajin tantirai da take bata mai ba. Kasa ha?uri yay sai da ya tambayi maigadi wanene?.
? ? ? Kai tsaye maigadi yace,  Ranka ya daWe mai gyaran ruwa ne. Pipe ne ya fashe a sashen Hajiya ?arama shine ya gyara.
? ?? Jimmm AA yay yana kallon Sille da yay nesa da gidan kaWan ta cikin mirror Win motar, a ransa yana jinjina kalmar mai gyaran ruwan ?warai da gaske. Dan zubin mutumin sam bai masa kama dana mai aikin arzi?i irin wannan ba. Amma sai bai takura ba yaja motar ya shige ciki. Tarkacen daya sayoma ?ar rigimarsa ya Wiba ya wuce sashensu. Samunta yay tana barci anan falon inda ya barta, ya sauke ajiyar zuciya yana girgiza kai. Kitchen ya wuce da kayan ya ajiye komai a inda ta dace, sannan ya dawo ya kwashe abubuwan data baza na ciye-ciyen da tayi suma yakai kitchen Win ya Wauraye na wankewa ya ajiye na ajiyewa. Koda ya dawo Waukarta yay gaba Waya ya haura sama da ita. Dan yasan wannan kuma barcin in sha ALLAHU ita da farkawa sai kusan sha biyun dare, koda yayi barci shima sai ya tashi saboda wanka kawai take yi da salla tazo ta kanannaWe jikinsa. Tana samun yanda take so zata sake komawa barci. To daga fa sallar asuba kuma bazata sake kwanciya ba sai wata yammar kamar wannan, idan kuma anyi sa'a ta daure yanayin magrib zata kwantan. Oum ma data fahimci yanayin nata ko nemanta batayi idan yamma tayi taji shiru. Wani lokacin kuma acan sashen take barcin sai sun gama hira da cin abincin dare yake Wakkota su dawo nan..

______&

? ? ?? Washe gari tunda wuri ya mata wayo suka bar gidan zuwa MAWAAD. Ta haka ne ?an kai lefe suka tafi lafiya bada saninta ba. Lokacin da suke dawowa gida bayan la'asar kuma sama-sama ta gaida Oum ma ta shige bedroom Winta ta kwanta sai barci.
? ? ? Da daddare sunyi zaman cin abinci Babban Yaya ke tambayar Lilly fa? Dan tun jiya rabonsa da ganinta a gidan, kwana biyun nan kuma ya fahimci Nuwaira da Oum ke girkin dare banda Maanal Win. Oum ta ce masa tana barci a Wakinta tunda suka dawo aiki. Dan ko sashensu ma bataje ba. Mamaki ya kama Babban Yaya, yace,  Bata da lafiya ne? Barcin yamma haka .
? ? ? Kafin Oum tai magana Yaya Fawzan da bakinsa baya iya shiru ya ce,  Anya Babban Yaya Lilly na lafiyar nan kuwa?. Barci dai barci dai maybe akwai malaria tare da ita .
? ? ? ?? RK dake danne dariyarsa da ?yar yay fuska da faWin,  Sai fa malaria Win. Saurayen ne na yanzu Wika-Wika, da sun ciji mutum kuma sai ciwo ba sau?i. ALLAH dai ya ?aremu da lafiya .
? ? ? Harga ALLAH Oum bata gane sha?iyancin RK ba. Kai shi kansa Yaya Fawzan bai hasko komai ba sai da yaga babban Yaya yayi wani miskilin murmushi kawai. AA ma da bai fahimta ba da farko ya ce,  Inaga ya kamata ai feshi a gidan nan gaskiya. Dan Wan zaman da mukai jiya a waje nima sai da naji kamar zanyi zazzaSin alamar nasha cizo .
? ? ?? A wani Wage RK ya Wan dubeshi ya ce,  Ai tunda baka kwanta ba da alama kai naka cizon na musulmin sauro ne. Wanda ya ciji ?ar gidan Oum dai kamar yafi iya cizo .
? ?? Yanzu kam sosai AA ya kallesa, hakama Yaya Fawzan. Ido RK ya kashema Fawzan. Yaya Fawzan ya kwashe da dariya dan ya gano kam yanzu. yace,  Ohhhhh na gane na gane, lallai wanan sauro kam ya iya cizo gallari . Sai suka sake kwashewa da dariya shi da RK. ?asa-?asa suke zancen shiyyasa Oum bata jinsu. Shi kuma AA a tsakkiyarsu yake. Babban Yaya na kusa da Oum. AA da sai yanzu ya fahimci inda iskancin nasu ya dosa ya girgiza kai kawai. Bai sake magana ba saboda Oum da babban Yaya dake wajen, amma yayi al?awarin sai ya rama su duka..

________&

? ? ? ?? Washe gari ?an Kano da suka rabu biyu wasu suka tsaya Zaria gobe idan ALLAH ya kaimu zasu taho da amarya Najma, wasu kuma suka wuto nan abuja dan anan za'a Waura auren Ameerah da Maimoon dan sau?a?ama mutane. Zasuyi tafiyar yamma ne saboda bikin da zasuyi suma can Zariya, anan kuma Abuja gobe za'ai kamu in sha ALLAHU anan gidan Darma. Asabar a Waura aure ai dinner, lahadi walima da safe, da yamma ai buWar kai shike nan amare su shige daga ciki.?
? ? ? ?an Kano na gama hutawa aka kai lefen Ameerah. Lefen ya ?ayatar da kowa dan su Maanal sunyi ?o?arin saka abubuwa na girma. Sosai kuma Hajiya Shuwa da ahalinta da suka iso da ?an Katsina suma da sukace komai ya wuce suka dai-daita da Hajiya Shuwan tun kai kuWi da su Baba Sardauna sukai. Tukuyci mai tsoka su Maanal suka samo. Babu dai dangin Mamy ko Waya a ?an kai lefe hakama Nibras ko ?an Kano bata zo ta gaidar ba. Suna dawowa daga kai lefen Ameerah aka kuma biyosu da lefen Maimoon. Hummm shima dai su Hajiya Shuwa sun rigirgiza kayan arzi?i sai dai ace sambarka kam. Sai kuma abi ma'auratan da addu'ar zaman lafiya da zuri'a masu albarka.
? ? ? A Sangaren Mamy ya?e kawai take da dauriyar dole har ta fito ta gaishe da ?an Kano su Mah-mah, dan su Umma sune a Zaria zasu taho da amarya Najma gobe idan ALLAH ya kaimu........
'?




*_AJIYA A DUHU na kuWi ne, 500 ne kacal, ?ar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai =??=?O?_*

*09032345899*



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu =?-?=?O?_*
*_Typing=???_*








*_=???AJIYA A DUHU....=???_*




*_Bilyn Abdull ce >??

*_(P3REP 'DDQNGP 'D1QN-RENpFP 'D1QN-PJE_*
_Da sinan Allah, Mai rahama, Mai jin ?ai._

*_My TikTok account =?G?_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram=?G?
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R


_Duk wanda bai fallowing Wina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama=??=??
*_BOOK 2_*


______________


.....A yanzu gaba Waya hankalin Mamy ba'a kan auren nan yake ba. Dan Sille ya gama rikita mata al'amari gaba Waya. Amma dai tana ta ?o?arin danne yanayin ta dan bata fatan kowa ya san halin da take ciki a wannan gaSar. Abinda ya bama Abah mamaki yanda ta sake ba kamar bikin Maanal da AA ba. Amma dai baice komai akan hakan ba.
? ? ? A Sangaren Sille kam a yanzu itace mai nemansa a waya ruwa a jallo. Amma abin mamaki kaf layukan da yake kiranta da su bata samunsa. Tun a daren ranar ta bashi 10m daya bu?ata, dan ta fahimci zai yi dukkan abinda ya ambata. Amma ta saka ana mata bincike a kansa dama Junaid, duk da ita tafi kowa sanin abinda ta aikata ma Junaid Win. Amma hankalinta ya?i kwanciya sam. Tana son fita a gidan tana tsoron idon mutane, wani gefe na zuciyarta kuma na tunatar da ita idan ma ta fita Win ina zata samo Sillen. Tunda shi dai ba wani waje da yake zaune ta taSa sani ba. Haka dai ta daure tana sauraren sakamakon binciken data saka anai mata akan Junaid.....

________&

? ? ? A washe garin da za'a iso da Najma da ?yar Oum ta lallaSa Maanal sukaje saloon. Wankin kai kawai ta yarda akai mata, kitso sai ta sakama Oum kuka. ?yaleta tayi suka dawo gida akai zaman mata ?unshi ja da ba?i. A lokacin su AA da zasu Wakko Najma nata shirin wucewa. Ya shigo sashen Oum Win cikin tsokana yace mata saura kitso ta sanya masa kuka. Ita Oum ma sai abin ya bata dariya, ta dai gimtse batai ba. Sai ma ta harari AA da shima yake danne dariyar da ?yar.
? ? ? ?  Yanzu dan ALLAH Auta banda neman faWa ina ruwanka. Munce maka muna son kitso ne.
? ?? AA dai ya sake danne tasa dariyar da ?yar ya ce,  ALLAH ya baku ha?uri Oum nayi shiru. Bani keys Win in dai nine yanzu zan yi gaba . Oum na bashi maimakon ya tafi da arzi?i sai ya faki idonta ya du?o ta bayan kujera saitin kunnen Maanal ya raWa mata magana . Tare da sumbatar wuyanta. Kafin ta juyo ya fice, cikin Waga murya Maanal ta ce,  Sai na rama kuma zaka dawo ai . Mai ?unshi dai abin nasu sai ya bata dariya da birgeta. Dan daka gansu kaga ma'auratan dake matu?ar son juna....

_________&

? ? ? ?
? ? ? A Zaria su Ammie sune amarori ?irjin biki. Amarya Najma tasha gyara Wan gaske ciki da waje sai Waukar idanun mai kallo takeyi. Dan Ammie babu wasa sai da ta fidda ?ar tata Masha ALLAH. ?amshi kuwa ba'a magana, dan bayan nata gana Hajiya Shuwa. A jiya Ammie ta maidata Zaria. Anyi kamu a jiyan da yamma, yau kuma suke ?unshi da safe. Da yamma aka fara yinin bikin Hajiya Majdiya.
? ? ? ? Gaba Waya ran kishiyoyinta su Maman Yaseerah a Sace yake. Suma su Yaseerah dai ?iri-?iri ?an ubancinsu ya kasa Soyuwa akan shagalin bikin Najma Win. Dan sun san dai kam ta kere musu fintin kau kamar yanda uwarta ta kerema iyayensu a komai. Balle kuma ita Yaseerah zuwa yanzu tasan minene family Win Darma. Randa aka kawo lefen Najma habaice-habaice sukaita saki. Kallon inda suke Hajiya Majdiya batai ba balle kuma su Ammie da ke tsaye akan komai. Hajiya Basariyya kam ai ji take ina bashi yiwuwa, koda tsiya-tsiya sai ta kaso auren Huznah ta shiga wannan family na Darma. Sai kuma tura su Madeena ?annen Huznah Win take cikin yaran family Win Darman wai suma ko sa samu mazan aure. Abin ya ba Maman Yaseerah haushi ta hau Hajiya Basariyya da masifa amma saita ?i kulata. Dan ita lissafinta daban dana Maman Yaseerah a yanzu....

? ? ?? Bayan la'asar kaWan tawagar su AA da abokan Yaya Fawzan suka isa Zaria. Zuwa lokacin an gama shirya amarya Najma dake ta shan kuka tsaff cikin lafaya. An kaita gaban iyaye an mata nasiha. Lokacin da aka kaita gaban Hajiya Majdiya suyi sallama sai kawai ta rungumeta tana kuka mai ban tausayi, ita ko Hajiya Majdiya ta dake abinta, acewarta ai Najma gida zataje minene na Waga hankali. Kuma itama dai gobe nan da safe zata wuce Abujan dan ai bikin su babban Yaya da ita. Da ?yar Ammie ta cire Najma a jikin Hajiya Majdiya aka fito da ita. AA da RK ne zasu Wauki amarya, ga Ammie itace ri?e da amarya ita da Aunty Rufaidah.
? ? ? ? Kunya ta kama AA, dan yanzu wani nauyin Ammie yake ji na musamman. Ko a waya ya kirata yata sum-sum da murya kenan. Itama dai Ammien nauyin nasa take ji. Cike da sha?iyanci RK ya ce,  Babbar magana, suruki zai Wauki suruka a mota .
? ? ? ? ?? AA dai bai kula shi ba, dan su Ammie sun riga sun kawo gab da su. Itama kuma sai a lokacin ta farga da shi. A zuciyarta tace (Ya subahannallah ya akai haka) a fili kam ta daure ta saka Najma a motar. Har inda yake AA yazo ya rissina yana gaisheta. Ta amsa masa da kulawa da tambayar yaya hanya. Yace Alhmdllh. Haka dole ta shiga motar, ya rufe mata murfin da kansa sannan ya zagaya ya shiga mazaunin driver dan RK ne ya kawosu, yanzu kuma yace bazai maidasu ba ya gaji sai dai AA Win ya tu?a. Haka dole ya amsa dan Ammie da zata kasance a motar, sai kuma al?awarin da yay ma Yaya Fawzan na shi zai kawo masa Najma har gida. Yana ?o?arin yima motar key kiran Maanal ya shigo masa. Sai da ya saci kallon Ammie da hankalinta ke akan lallashi Najma dake a jikinta sannan ya Waga kiran. ?asa-?asa dan AA ya iya munafuncin magana a ?asan ma?oshi ya ce,  Zuciyar Ajwaad yaya ne? .
? ? ?? Daga can a shagwaSe Maanal dake hammar barci hayaniya ta hanata zama sashen Oum ta gudo sashensu duk da nan ma cike yake da ?ammata ?awayen Maimoon da aka taho da su daga Kano, amma da yake a ?asa suke babu wanda ya hau mata sama sai ta haye saman ita. Tace,  Kun taho? .
? ? ?  Uhm-uhm! A nan zamu kwana .
Ya faWa cikin tsokana. Muryar Maanal harta fara rawa ta ce,  Kwana fa? .
? ? Murmushi yayi jin za'a fara masa kukan shagwaSar. Cike da lallashi ya ce,  Wasa nake, ga amarya nan ma a mota yanzu zamu taho .
? ? ? ? Ajiyar zuciya ta sauke, tare da sakin hamma. ?asa-?asa ya ce,  Barcin ne? .
? ? ? ? ?  Uhmm .
? ?? Ta faWa can ?asan ma?oshi. Murmushi yayi, zai faWa mata tare suke da Ammie yaji ta fara sauke numfashi alamar barcin ya fara Waukarta. Wayar kawai ya katse ya tada motar. Sai suka haWa ido da RK. Kallon da yake masa na sha?iyanci ya sashi hararsa kawai ya Wauke kansa. Haka suka Wakko hanyar Abuja da amarya gwanin sha'awa. RK da Aunty Rufaidah ne kawai ke hira a motar. Ammie nauyin kasancewar AA da shi kansa ma RK Win ya sata yin shiru. Haka shima AA Win tu?insa kawai yake. Duk da dama bamai yawan magana bane ba kowa ya sani.
? ? ? Duk da uban gudun da sukai basu shigo cikin Abuja ba sai gab da sallar isha'i. Dan ma sunyi dabarar bi ta jere ne suka fito ta dutse. Maanal nacan

70 / 138

Chapters