Advertisements
Chapter 22 Reading Matar Taj Book 2 Complete Hausa Novel Hausa Novels
Advertisements

Matar Taj Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Queenmerh Category :  Complete Novels

Chapter   22 / 107

63K to 66K   out of 320.4K words

muryar mutun..”innalillihi wayyo didi..didi…”, haka ta soma kiran sunanshi, duk a tunaninta har cikin zuciyarta aljani ne donta tsorata sosai, bata kawo shine ba don a sitting room table barshi kwance don tama dauka barci ya daukesa.

“ke…ki natsu, its me,…”
Ya daka mata tsawa wanda hakan yasa wata natsuwa tazo mata, “why are you so careless?ina zakije cikin duhun nan?meysa bazaki tsaya wutan ya dawo ba?”

Ya jefo mata tambaya wannan karan muryarshi ta dan sassauto,
Sai a lokacin ta samu damar bashi amsa,”
“daman…wajenka zanje saboda naga kana tsoron duhu..”
Jimm yayi yana nazarin dalilin daukewar wutar dakin, at the same time yana tunanin maganarta, “wayace maki ina tsoron dubu?”
Yanda yayi magana tana jin saukar nunfashinsa akan fuskarta wannan ya tabbatar mata da kusanci daya shiga tsakaninsu a daidai lokacin don bata ankara ba sai yanxu, gashi ya kama kafadunta gaba daya ya rike gam tana facing dinshi.
Faduwar glass bowl din data fara kokarin sakawa a fridge kuma bata rufe fridge dinba ta juya yasa ta furgita batama san lokacin data damko kugunshi ba, dake ya fita tsayi sosai wannan yasa ta tsaya daidai kirjinshi, fuskanta na kan kirjinshi nashi tana shakar kamshin sa.
Take yanayin bugun kirjinta ya sauya,kamshinsu ya hade lokaci guda, har nashi yaso rinjayar nata, hannunta kuwa data damke kugunshi dashi har zufa yake.
Sun dade sosai a haka baice bata qala
Ba haka zalika itama batace mashi komai ba har suka dauki wajen 15mins a haka kafin wutar gidan ta dawo gaba daya.
Tunda wutan ya dawo ya bude idanunshi yana kallon gashinta dake kwance an mata kitso guda hudu ta daureshi daga baya tayi kamar dough, mayafin data daure kan dashi ma ya zame,har zuwa kafadarta.
Bangaren sabeeha batama san an kawo wutar ba saboda idanunta data rintse gam goshin har zuwa lokacin yana kan kafarshi, hannunta na kugunshi ta kankame shi, tana ji ya sauke hannunshi daga kan kafadarta, “zaki kwana ne a haka?” Take tambayar nan tashi ta shiga kwakwalwarta, tayi saurin bude idanunta, take taga hasken ya bade kitchen din, cikin hanzari ta zame hannunta daga kugunshi tayi ba, yanda take tafiyar nan ganin tana kokarin zuwa wajen glass din bowl din daya tarwatse a kasa yasa shi saurin takowa, taku daya ya damko hannunta ya janyota gaba ta fado jikinshi, hazel idanunta ta zaro tana mai kallon cikin idanunshi, wani irin yanayi mara misaltuwa ta tainci kanta a wannan lokacin, shika kallon cikin idanun nata yakeyi ya kasa daukewa, fuskan nan nashi tana nan yanda take, “kinada taurin kai ko? Didn’t i warn you earlier?“
Bata gane me yake nufi ba saida ya sake magana, “don’t make me repeat my self again, the next time na sake maki magana…..”
Ya tabe baki tare da jefanta wani irin kallo mai wuyar fassara kafin yace “watch your steps”
Yana fadin haka ya juya har zai bar kitcehn din ya dakata, “bring me coffee”
Yana fadin haka ya fuce daga dakin yana tuna maganarta, daman tun futowarta daga bathroom harta dauki tray din ta futa dashi yana ankare da ita, bayan futar tata kuwa ana dauke wutan nan kawai yaji wani abu zqi iya faruwa fa ita wannan yasa ya futo cikin duhun nan har zuwa kirchen din, lafiyarta matters to him yanxu sosai.

Ta dade sosai a tsaye tana calculating maganganunshi kafin ta daidaita natsuwarta ta dauka standing broom ta tattare kwalbar sannan ta sake reboiling coffee din ta zuba a wani mug din kafin ta futo.
Saida ta daga kafarta ta soma jin zafi sosai saboda buguwar datayi haka dai ta daure ta shigo dakin bakinta dauke da sallama.
Tunda ta shigo ya mata kallo daya kafin ya duake idanunshi harta karaso inda yake, taqi yarda su hada idanu saboda wata iriyar kunya dataji ta lulubeta lokaci guda.
“Bismillah” ta furat ahankali,karba yayi kafin yace “thanks” chan kasan maqoshi.

Tana bashi ta zagaya gefen gadonta zauna kamar me neman gafara, harya gama shan coffee din ya miqe zai futa dashi ta dakatar dashi, “kawo nakai kitchen din”
Bai tanka ta ba fuce daga dakin, yana futa ta shingida jiki a mace ta kwanta abunta.
Harya shugo dakin ya zagayo tana jinshi saidai bata yarda ta bude idanunta ba, shima yayi kwanciyarshi, itadai cikin mintuna qalilan barci ya kwasheta shiko ya dade kafin barcin ya fuzgeshi..

Abuja nigeria….
Abubuwa da dama sun sauya cikin ahalin gidan Anne, masu dadi da marasa dadi, rayuwar maya ta sauya gaba daya sai ya zamana kamar yanxu ne ta bude sabon babin rayuwarta yanda taga dama babu idanun daddy akanta, har zuwa yanxu suna zuwa makaranta ita da laila saidai ko’ba a fada ba da an gansu za a gane banbancin halayyansu,musamman wajen maida hankalin wajen karatun,ayanxu suna matakin 300 level.
Duk abubuwan da maya keyi babu wanda ya sani sai laila dake tare da ita koda yaushe, bata maida hankali wajen karatun kwata kwata, itace bin yayan manya, da yake makarantar ta yayan wane da wane ne kowa yana ji da kanshi, a hakan ma taso a ce a hostel take don ta fantama yanda take so saidai hakan bai yuwu ba, yanxu idanunta ya gama budewa saima tafi jin dadin rayuwa anan fiye da lokacin da take acahn california.
Kullum zasuyi waya da mummynta da daddy, ada idan sukayi waya babu abunda take yawan tambaya sai lokacin da zasu dawo naija suma, yanxu tama daina complaining dawowar tasu saboda hakan yama fi mata dadi saboda tasan halin dadin nata.
Bata da matsalar komai daidai daga kan kudin kashewa, daddy na tura mata haka zalika anan gida ma anne tana basu allowance.



✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊

MATAR TAJ (destined with you🩵🤍)
Written by
Queenmarh✍️
Book2
PAID
Chapter 71
Washe gari da safe tun wajen karfe biyar ya farka kmar kullum juyowan da zaiyi ya ganta gaba daya ta gangaro inda yake kwance ta hade jikinta waje guda don yana hango yar fuskarta sleeping peacefully hankalinta kwance, ya dauka wajen minti biyu yana kallonta, memories dinsu shida ita na flashing a fuskanshi,lashes dinta dake kwance yabi da kallo har zuwa dogon hancinta dake miqe,she looks so young and innocent, saurin kauda idanunshi yayi akanta ya tashi zaune kafin ya ambaci sunan allah ya sauko daga gadon yana miqa ahankali.
Bathrroom ya wuce ya dauro alwala kafin ya fito ya sauya zuwa jallabiya fara qal sannan ya dawo dakin wajen inda yake sallah.

Bude kofar dayayi yayi daidai da farkawarta, saida ya tasa kabbarar sallah kafin ta miqe itama, tana taku daya taji kafarta ta rike kyamm… sai a lokacin ta tuna da bugewar datayi jiya da daddare, “washh” ta furta ahanklai saboda wani irin radadi dataji saboda kafar tayi tsami, tunawa da warning din daya shumfida mata jiya yasa ta daure ta wuce bathroom cikin natsuwa ta dauro alwala tana jan kafar, sannan ta wuce wajen closet ta dauko hijab dinta ta saka kafij ta fito daga dakin, daga nesa ta hango yana sujjada a natse.
Nufar wajen da yake tayi daga gefenshi wajen carpet din itama ta tsaye daga bayanshi kadan har tana jin kamshin turaren dake jikinsa,sai ha zamana kamar tare zasuyi sallahr don tana daga gefenshi gwanin sha ‘awa,
Raka’atainul fajir ta fara tana idarwa ta ganshi tsaye,harya tada kabbarar sallar subh, a gaggauce tabi bayanshi ya jasu sallah.
Tunda suka idar da sallah ya ankare da ita saidai ya nuna kamarma baisan tana wajen ba, ya dade sosai yana addua’oin mafi yawa cikinsu shine na neman tsari, wasu adduao da yake ma kwata kwata bata iyasu ba sai a bakinsa ta taba ji, kuma tayi mamaki sosai yanda yake da addini, da farko data zo gidan lokacin da bashi lafiya batayi tsammanin yanada ilimi ba.
Shafawa yayi itama ta shafa, daman tasan miqewa zaiyi wannan ya bata damar cewa “sabahal khair didi”
Shuru ya danyi na yan saqanni bai tashi ba haka zalika baice mata uppan ba saima jingina da yayi da bango, kamar bazai ce komai ba chan kuma ya amsa ta a natse “sabahal noor”

Yana fadin haka kowannen su yayi shuru, daman batayi expecting jin komai daga gareshi ba don haka tayi shuru abunta kuma batayi kokarin tashi ba, “akwai abunda kike buqata?Akwai abunda ke damunki? Do you need anything?”
A jere ya jefo mata tambayoyin kamar wani lawyer,in so much concern for her.
Saurin sauke kanta tayi qasa sai taji wani irin farin ciki ya lulubeta,yanda yake mata magana gaba daya ya sauya daga yanda yake a baya, wani sa’in har mamakin abun take, yanxu maturedly yake komai.
“Alhamdulillah bana buqatar komai, and babu abunda ke damuna”
Ta amsa shi a tsanake, tunda ta fara magana ya juyo yana kallonta, zai iya rantsewa baima san sanda ya juyo ba,akwai wani abu da muryarta dake tasiri a cikin zuciyarshi,baisan yanda zai fassara abunba kwata kwata.
Jin shuru yasa ta dawo karaf idanunta ya sarke da nashi kamar anyi magneting dinsu waje guda, sun dade a haka harta soma jin idanunshi sun mata nauyi sosai wannan yasa tayi hanzari kauda nata.
Tana son tambayarshi abu amma saitaji kamar an kulle mata bakin nata, dakyar ta iya bude bakinta tace “a kawo maka coffee?”
Tana fadin haka ya kauda idanunshi daga nata sannan ya miqe tsaye ya wuce closet ya cire jallabiyan ya rage dagashi sai mini short dinshi, har zai futo haka ya tuna bashi kadai ke zaune a dakin ba, baya son matsi kwata kwata shiyasa bayason kowa ya shigo dakinshi, idan yana daki zamanshi yake confortably babu takura babu matsi.
Cikin set of bathrobe dinshi ya jawo daya fara khaal ya saka akan short din kafin ya fito ya nufi gado ya kwanta, sabod ayanxu ya daina futa da safe daman futar bata wuce zuwa gym yanxu kuma ya sauya timing din zuwanshi zuwa evening.
Akan idanunta ya futo yayi kwanciyarshi, tayi mamaki sosai don tasan a wannan lokacin wanka yakeyi sannan ya fara shiri.
Mikewa tayi ta zare hijab din jikinta, shaf tama manta babu mayafi akanta haka ta nade mayafin ta ajiye sannan ta shiga bathroom ta soma wanke.
Wani irin barci ne mai dadi ya fuzgesa, baima san lokacin da barcin ya kwashesa ba.
Ta dade a bathroom kafin don harda feww kayayyayakinsa dake cikin laudry ta wanke kafin ta fito, wace walk in ta gyara kayanta tsaf, tana gamawa ta futo, tundaga chan nesa ta hangoshi ya kwanta yayi irin rub da ciki dinnan, kaffaunshi na hanging a bakin gado, kallo daya ta mashi ta gane he’s fast a sleep wannan ya bata damar takowa bakin gadon wajen inda yake ta tsugunna a kasa wajen gefenshi tana mai kallon kyakyawar fuskarshi da gashi ya zagayeta, ga sumar kanshi a kwance tasha gyara kamar gashin jariri, samun kanta tayi da murmusawa kallonshi kawai da takeyi, hannunta ta daga kamar mai jin tsoro ta fara tattare gashi daya dan zubo mashi akan fuskanshi, wannan ya bata damar ganinshi da kyau.
“Masha Allah” vakinta ya furta…tana fadin haka ta sauke murmushi, shuru tayi tana tuna rayuwarsu a baya da yanda yasha wahala wajen yan uwansa, saitaji wani irin aranta take emotions da wasu feelings ya darsu a zuciyarta, she really want to protect him, bata son ya cutu ko wani abu ya cutar dashi ko kadan, itace zata bada labari irin wahalar rayuwa daya hannun makusantansa dayake masu kallan ahalinshi.
“Allah ga wannan bawa naka, karka bari yasha wahalar dayasha achan baya lokacin da baya cikin tunaninshi, ya allah ka tsareshi daga duk wani sharri, allah kaine sheda, kuma kaine ka jarabceshi da wannan, allah ka fayyace mashi gaskiyar lamarin rayuwar dayake ciki da wanda yayi a baya, ya allah karka barshi yasha wahalr dayasha a baya, ya all..” sai kawai ta fashe da kuka mai tsuma zuciya a hankali, saurin toshe bakinta tayi gudun karya farka, saida tayi mai isarta kafin ta bude idanunta a hankali, ta saukesu akanshi sai hannunta mai dumi dake kan fuskar shi.
Gabanta ne ya bada dam ganin idanunshi da sukayi jaa a bude, lumshesu yayi ya sake budewa a hankali kamar wani maiyin maye haka yake kallonta, dumin hannunta datake caressing fuskanshi ne ya farkar dashi daga barci sai dan sheshekar kukanta daya soma ji kadan kadan, tunda ta fara maganganunnan yake sauraronta tundaga farko har karshe, a daidai lokacin itakuma ya rufe idanunta bata ma ya farka ba, dukda ya farka da matsanancin ciwon kai wannan bai hanashi jin duk abubuwan data fada ba.
Gaba daya ta gama confusing dinshi da kalamnta,tunda ya kafa mata idanu ya kasa daukewa harta bude idanunta, hannunta dake kan fuskanshi kuwa allah kadai yasan yanda yakejinsu akan fuskarshi, she was caresing him with so much affection, ya rasa ta yanda zaiyi describing abun.
Saurin dauke hannunta tayi daga fuskarshi jikinta na tsuma sosai kamar mazari, duk saita tsorata lokaci guda, tunda ta dauke hannunta yake binta da da ido, cikin hanzari tayi baya tare da saurin miqe jikinta na rawa a daidai lokacin idanunshi ya sauka kan boucing boobs dinta da bai taba yi masu kyakyawan kallo ba sai yau, dukda cikin kaya take abun saiya zo mashi a bazata lokaci guda yayi noticing gashi jikinta na rawa.
“Daman…daman zan tambayeka ne ko zaka sha coffee”
Tana fadin haka tayi saurin juya mashi baya,jin shuru babu response yasa ta dan juyo kadan da mamakinta taga ya koma barcinsa hankali kwance.
Take taji wani irin sanyi a ranta, cikin sauri tabar dakin ma gaba daya.
Tana futa ya bude idanunshi, daman yayi hakan ne don kartayi tunanin koya ji duk abunda ta fada wannan yasa yayi pretending ya koma barci.

Maganganunta ne suka fara mashi yawo a kwakwalwar shi, daga yanda take magana he can see and feel how sincere she is, saita barshi da zulunmi daw rudani a cikin zuciyarshi ya gama na’am da ita don yanajin akwai wani abu a ciki Maganganunta, shi karan kanshi ne yaqi yarda da ita completely.
Ya dade sosai a kwance yana dogon nazari abund ayafi tsaya mashi arai shine “what is she talking about? Meysa take neman mashi tsari daga wajen allah? Wake kokarin cutar dashi? Meya faru dashi a lokacin da baya cikin hayyacinsa?wacce irin wahala yasha datake rokon allah karya bari yasha wahalar yanxu? Wace gaskiyar lamari take rokon allah ya fayyace mashi?”
Hes so curious about everything, ada yabar komai kawai tunda first love tace yabar komai daya wuce a baya, dukda hea so eager yo know everything amma yanxu baya jin zai iya hakura, wannan maganganun nata is like a call up for him, he wants to know everything, amma where wilm he start from? What if wani plot ne yarinyar nan keyi? What if??” Shuru yayi duk yanda yaso yayi doubting ko ya karyarta magnganun yarinyar nan ko masu wata fassara daban ya kasa zuciyarshi ta gama aminta da maganganunta kamar an dasa su a wajen sai ayanxu yakeji there has to be something saboda bai taba jin irin haka ga kowa ba sai ita, hidaya kawai yakema irin wannan yardar datayi magana shikenan zuciyarhsi ta aminta da ita completly.


Istanbul…
Bude mata kofa tayi ta sanyo kafarta ahankali, hidaya ce sanye da classy doguwar riga ta alfarma, daga kan daham dake jikinta kadai is speaking luxury, tafiyar sassafiya tayi yau dinnan zuwa istanbul saboda wani muhimmin meeting da zatayi da sabbin investors din data samu, dakyar ta samu sukayi scheduling meeting dinnan inda suka buqaci ita da kanta tazo da proposal din abunda kamfaninsu ke buqata.
Gefenta secretary dinta ne yana biye da ita da takardu da laptop dinta,
ta kwama wani irin tsadaddan shade a fuskarta sai handbag data rike a hannunta mai tsadan gaske.
Kallon tafkeken hotel din da suka tsaya a wajen tayi kafin ta maida dubanta ga secretary dinta daya zagayo inda take, “are you sure nan sukayi scheduling meeting din”
“Yes ma’am”
“Wannan wani irin organization ne dasu? This is so unprofessional”
Shidai sacretary shuru yayi yana hiye da ita tana gaba, ciki suka shiga har wajen conference address din da aka basu suna zuwa daidai wajen daya daga cikin receptionist din ya jagorance su zuwa conference meeting lounge din.
Suna zuwa wajen ya dan dakatar da ita sannan ya danna wani button kafin kofar ta bude, babban lounge ne kamar hall yasha haduwar tables da kujeru hadaddu masu shegen kyau sosai.
Ahankali ta soma takowa babu abunda ke tashi sai saurin takalminta kwas kwasa harta karaso ciki, tana shugowa ta fuskanci inda taga mutun zaune sai wani a tsaye a gefen mutumin shi,

A hankali na zaune ya soma juyo da kujerarsa harya juyo inda take fuskantar kujerar,cikin hanzari ta sauke shade din dake gabanta don tabbatar da wanda ke gaban nata, “wait what the heck is going on here?”
Ta furta ahankali tana mai abdul basit, owner of BB companies, kuma baban family enemie dinsu kuka competitor din taheel company.. rai a bace take kallon secretary dinshi don tabbatar da yasan da wannan banzan hadin dayayi? Saurin girgiza mata kai yayi don shima duk ya rude, kwafa tayi ta maida dubanta ga abdul basit dake kallonta yana murmusawa sosai, “welcome to my empire mrs hidaya”
“Whats the meaning of this?”
“It is what is it my dear…please have a seat, wanna. Meeting din zai amfanemu gaba dayanmu.”
Badan taso ba taja kujera ta zauna, tana zama yaronahi ya zagayo inda take ya ajiye mata proposal paper dinsu, kafin ya koma wajen oganshi, yana komawa abdul basit ya bashi damar futa, yana gab da futa ya kallo nata secretary din, wannan yasa ya buqaci ta bashi damar futa shima, batace komai ba ta girgiza mashi kai ya bi bayan dayan suka fuce suka barsu su biyu a zaune.
Tunda ta zauna yake kallon fuskarta yana murmushi, wani irin dadi yake ji sosai ganinta da yayi kawai, saita tuno mashi da fuskar da bazai taba manta da ita ba kaf duniya, fsukar datayi sanadiyar arzikinsa, mace mai babban matsayi a zuciyarshi.

Tunda ta zauna akan kujera take bin proposal din dake gabanta da kallo,
“Zan baki power, zan baki duk Abunda kikeso, kudi..arziki..power..”
“Hahahaha.. ta kece da dariya vatama san lokacin da dariyar ta kubce mata ba..” what a joke?”

“You have all the time for your self, everything is clear and simply, I’m giving you power, ki zauna kiyi tunani akai, i have no bad intentions on this, i want you to join hand with us, zakiyi duk abunda kikeso da kamfanin,this is only chance for you to save your company...bayan wata biyar zaki iya tarminating proposal

22 / 107