Advertisements
Chapter 61 Reading Matar Taj Book 2 Complete Hausa Novel BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Matar Taj Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Queenmerh Category :  Complete Novels

Chapter   61 / 107

180K to 183K   out of 320.4K words

there? Hello sir” maganar da akayi daga wayar ne yasashi maida hankali a wayar yace “yes yes go ahead”
Jiki a mace maya ta wuce wajen motar, daidai nan hamad ya karaso tare laila, sabeeha dake tsaye jikin motar wajen budewar baya tana jiran isowar su batayi auni ba kawai taji an wani tureta gefe an bude motar, har littafanta na watsewa a kasa.
“Excuse me!!!” Maya tayi magana tare da banko kofar, hamad bai lura dasu ba don sauri yakeyi don ya samu ya saukesu.

Tunda ya aje wayar da yayi da merk ya koma ciki nanna tace ya je ya shirya zasu fita tare da ita.
It was a pleasant day for him, nanna tayi driving motar suka wuce har office dinta, inda take gudanar da business dinta, tanada cute iffice da facilities sosai daman tana harkar interior,kuma da manyan companies take dealing idan an bata kwangila irinsu nnpc da hotels.
Sun dade sosai kafin yamma su dawo.

4 nayi hamad yazo daukansu tare da abal daya damu saiya biyosa.
Laila ce ta fara fitowa tana hango abal a tsaye bakin mota tace “ya hamad da wannan futsararran kukazo?”
“Ke ban girmeki ba kike cemin futsararre?”
“Waka girma din? Age dinmu daya”
“Kamata yayi ki dunga gaisheni kina kirana da yaya tunda na fuki da 5months”
“Wallahi karya ne mami tace shekarunmu daya ao don’t feel like your head is big”
Daidai nan maya ta karaso, abal ya kalleta kafin yace “hey!!! Ashe kin dawo nigeria da zama? Lol how do you cope?”
Wani irin kallo ta mashi kafin tace “what sort of a question is that? Do i look depressed to you?”
Abal najin haka yasan daman mai hali ay baya chanza halinsa, tun tuni daman yar masufa ce tun suna yara, shiyasa baya ma shiga har karta.
“Nawa for you…” ta fada yana galla mata harara.

Tsaki tayi ta bude kofar baya ta shiga, sabeeha daketa faman sauri sauri har tana haki ta iso itama, “salam! Ina wuni ya hamad”
Ganin yanda take panting yasa hamad cewa “wa alaiki salam, why are you panting”
“Inata sauri ne karna bata maka lokaci” ta bashi amsa a natse babu hayaniya, abal ya zuba mata idanu sosai yace “ya hamad who’s that?”
Ko kallonshi baiba yace “get in”
Bude gaba abal yayi wannan yasa sabeeha tsayawa sarere ta rasa ya zatayi, saida taji horning yasa ta saurin bude baya batama san maya ce a ta wajen ba tana bude wa ta bita da wani makirin kallo kamar a kusa take da ita tace “are you mad??? Badai tunanin zama tare damu kike ba?”
“Fatima get inn!!!” Hamad ya bata umarnin haka
“Ya hamad wallahi wannan qazamiyar yar aikin bazata zauna kusa dani ba saidai ta nemi abun hawa”
“Saidai ke ki sauka ki nemi abun hawan, don’t waste my time”
“Wallahi bazata zauna a bayan nan ba, munafuka kawai kina wani sunne kai kamar wata ta Allah”
A fusace ya juyo kamar zai maketa yace “don’t you ever insult her again, in kika sake sai ranki yayi mugun baci”
Dake bata da kunya kuma ba sanin darajar babba take ba wannan yasa ta cewa “wallahil azeem bazqta zauja a baya ba,who is she not be insulted? Ba yar aikin bace? Yar wanke wanke”
Ay baisan sanda ya futo ba rau a bace ya bude seat din baya da take zaune yace “get outttttt, fita min a mota”
Jikin maya har tsuma yake tsabar masifa, ya dizgata gaban yar aiki, “bazan futa ba, wallahil azeem bazan futa ba akan wannan abar zaka sani na sauka a mota? Motar ta ubanta ce?“
Hannu ya daga zai kwasheta da mari laila tayi aaurin interfeing tace “yaya dan allah kayi hakuri, hannunshi gar karkarwa yake tsabar bacin rai,
“Ay wallahi idan ka mareni saina rama” kiri kiri fa take magana a gabanshi kamar wani sa’anta kai yarinyar nan batada kunya sam sam, very disrespectful,
“Yaya bari na futo na zauna a bayan tare dasu”
“No karka sake ka futo,” hakad ya fada yana kallonshi, kafin ya maida dubanshi ga maya yace “ke motan na ubanki ne?”
“Ni ka zaga saboda wannan?”
“In ya making zafi zaki iya futa, find your way home”
Ay ko yana rufe baki ta bude kkfar ta futo rai a bace ya kalli sabeeha babu wasa yace “shiga”
Jiki na bari ta shiga fa zauna inda maya ta tashi, suka wuce, akan idanun maya ta shiga motar ta zauna a seat dinta.
Suna barin wajen maya ta zaro wayarta tayi dialing number mummynta.
Bahijja dake tare da fadila suna hira tana ganin call din mayar ta dauka taka dauka ko sun dawo ne bata ganta ba,“ yes babu…”
“Mummy……..”
Miqewa bahijja tayi tana sauraron wayar nata tace “calm down ki fada min menene kukan me kikeyi?”
“Mummy na fada maki basa sona, kowa baya sona ni bansan mey nayi masu ba, ya hamad,sun tafi sun barni anan saboda yar aikin nan, har marina saida yayi, wai na fita a mota na nemi mai kawoni”
“Shi hamad dinne ya mareki?”
“Eh, sun barni a school babu kowa, mummy tsun tsaneni kowa na gidan nan, marina yayi wai na fita a mota tund aba motar ubana bane”
ta karashe tana fashe wa da kuka ta katse wayar.
Kiran duniya bahijja tayi mata wayar a kashe tuni hankalinta ya tashi.
Fadila data lura tace menene “wai hamad ne ya barta a schoo ita dayal”
“ hamad din?”
Ay bata tsaya saurarobta ba ta miqe tace “bari naje school din”

Futowa tayi tasa cikin drivers ya dauketa suka wuce school dinsu gaba daya hankalinta a tashe.
After few minutes da futarta saiga su hamad sun dawo, gaba daya daga laila har sabeeha da abal jikinsu duk yayi la’asar gaba dayansu.
Hanad ko hes fed up with her drama da rainin ta wannan yasa yayi maganinta, gaba daya futoqa sukayi ya rage hamad dinne kawai sai sabeeha data kasa tafiya ta tsaya ya futo.
“Ya hamad dan allah kayi hkuri mu koma a daukota”
Yanda take magana jikinta na bari yasashi gane cewa a tsorace take
“Go inside i will get her back”
Wani irin ajiyar zuciya ta sauke badon san rabta ba ta shiga ciki.

Wayarshi dake ringing ya dauka ganin sunan mamin shi, yana dagawa ta sima fada “kai kana ina? Me kayi ma maya? Meysa ka barta a school eh?
Haka fadila ta soma balbaleshi da fada sosai batama tsaya sauraronsa ba, karshe ma dayaqi kulata kashe wayar tayi.
Kalamanta na karshe yasashi shiga motar ya futa daga gidan, wallahi badan mami ba bazai dauko ba yau dinnan saidai tasan yanda zatayi.

Bahijja na zuwa school ta samu mayar zaune a gefen school entrance kai kace wata abar tausayi ce, tayi jabe jabe da hawaye.
Jikin bahijja har rawa yake, tana kaunar yarta kamar me shiyasa ko kukanta batason jin ko kadan ita kadaice allah ya basu, kaunar da take mata babu measures.
Tsakanin da uwa sai Allah, harga allah bahijja taji zafin abunda hamad yayi na barin mayar, saita fara tunanin toh kodai bason zaman mayar ake a gidan ba, tun ba yanxu ba tasan anne bason mahaifin mayar take ba, har lokacin tana tsoron kar avun ya shafi yar tata, sai yanxu take ganin abun kamar haka ne, ba sau daya ba ba sau biyu ba maya ke kira ta tana complain ba a sonta a gidan an takura mata.

Koda suka shugo gida gaba daya kowa na zazzaune a sitting room, fadilana gefe babu abunda take sai harara hamad din don anne tasashi ya dawo gida tunda bayijja ta tafi daukota, kuma kiri kiri anne ta hana fadial ta mashi fada har suka iso.
Maya na ganin kowa a zazzaune harda anne take tasha jinin jikinta.
Da ta wani maqale bahijja gwanin ban tausayi kai kace yankata akayi aka watsar.
Zama sukayi anne ta dubi hamad tace “babana meysa ka barta a school?, nasan haka kawai bazaka barta ba tunda kaina bama jagorancin kula dasu da harkar makarantarsu.”
Sunkuyar da kanshi yayi ya kasa dagowa yana jin kunyar anty bahijja sosai, sai yaji dama bai barta ba wallahi.
“I’m sorry raina ne ya baci hakan bazata sake faruwa ba”
Anne tace “tayi maka rashin kunya ne?”
Bai bada amsa ba yayi shuru kawai anne ta kalli mayar babu wasa tace “kinyi mashi rashin kunya ne?”
Kukan munafurci ta fara “ni ban mashi rashin kunya ba, kawai sabd nace fatima bazata zauna inda nake zaune ba shine yace na sauka tunda ba moton ubana bane” ta karashe harda share kwalla.

Laila datayi tsuru anne ta kalla tace “ke me tayi mashi?”
Yanda anne ke tambayr me maya ta mashi ba tare da sauraron abubuwan da ya fada ma mayan ba yasa bahijja jin babu dadi.
“Mun shiga mota ne sai yaya yace fatima ta koma baya saboda abal na zaune a gaba shine maya tace bazata zauna damu ba,”
Dan dakatawa tayi ganin irin kallon da maya ke mata kafin ta cigaba, “maya was insulting towards sabeeha tace wai ita dake yar aiki bazata zauna damu ba tunda ba ubanta ya saya motan ba, shine yaya yace karta sake zaginta..shine shine…”
Ta kasa karasawa anne ta sauke ajiyar zuciya tace “a gidan nan ba’a goranta ma na kasa damu, bama wulaqanta wanda ke hidima damu, idan yar wanke wanke ce itama iyaye ne suka haifeta,ni nasan haka kawai hamad bazaice ta sauka motar nan ba, ga abunda tayi nan,ninasa yarinyar nan tana binku makaranta don itama yace kamar kowa anan, don bata da gata bashine ya baki liberty din yi mata gori ba, karna sake jin haka, karna sake.. this should be the last time da zan sake jin haka”
Maya ta fashe ta kuka sosai ta shiga jikin mamanta bahijja ta rukota zuciyanta na mata daci, judgement din bai mata dadi ba ganin yanda mayar ke kuka.
“Amma anne ba laifi bane dan tace bazata zauna da yarinyar ba, tunda su yan gi…”
Wani irin kallo anne ta mata dayasa ta rufe bakinta kawai, anne ta miqe rai a bace ta wuce sama.
Fadial ta kalli hamad tace “kai kuma wani iri babba ne? Are not supposed to protect them? Ka bani kunya”
Tana cikin yi mashi fada bahijja ta miqe da maya suka wuce sama, fadila saitaji babu dadi kwata kwata, bahijja akwai son yaya kamar me, bataga laifinta ba tunda maya kawai allah ya basu.
Suna hawa sama bahijja ta danna ma majid waya, ta insa take hawa ba tanan take sauka ba, daman tund amayar ta dawo shi take blaming don shine ya turo ta don yayi punishing dinta.
Tun daga ranar maya ta kullaci sabeeha sosai aranta tsanarta ta tsananta sosai ba kadan ba.

Bayan kwana biyu.
Yau yayi daidai da saura kwana biyu komawan bahijja saboda hutun data dauka daman just is just a week ne, babu abunda take sai tunanin komawa da maya kawai chan don hankalinta yafi kwanciya saidai batasan ta inda zata bulla anne ba.

Hadiza na zaune a daki, yau kusan kwana nawa rabonta da futowa duk a sunan wai batada lafiya, wanda ba hakan bane futowa ne kawai batason yi don karsu hadu da bahijja.

Tana zaune misalin wajen karfe biyar daidai maya ta kira ta a waya, kamar kullum jiki na bari ta dauka, tana dagawa takai kunne, “meysa baki zo kin gyara min part dina ba yau kusan kwana nawa”
Da tsawa tayi maganar wanda hakan yasa hadiza saurin miqewa zaune tace “yi hkuri hajiya ta takaina, banajin dadi ne kwana biyu shiyasa amma bari nazo”
“Ah ah ki zauna ki tura yarki tajw ta gyara kin part din sannan kisa ta kwaso kayana dake part din mummy a wankesu”
“Toh yanxu ma kuwa yi hkuri kinji”
Kit ta kashe wayar, sabeeha na shugowa da plate din abunci hadiza tace “aje ki wuce sama ki gyara part din maya sannan kije bangaren ….”
Shuru tayi tama rasa me zata ce tace “ki tambayi rabi ta nuna maki bangaren mamanta ki kwaso kayan wanki kizo ki wanke su yanxu yanxun nan”
Aje abuncin data debo tayi a kasa, jiki a mace yau ko lunch batayi ba sbd haya batazo ba daman ita ke saya masu, gashi ta kwaso gajiya sosai.
Saman ta wuce allah yaso daidai lokacin dayar kai aikinsu dake gyaran sama ta futo nan ta tambayeta ta nuna mata.
Kamar yanda hadiza tace tayi hakan tayi ta gyara ko’ina kafin ta futo ta shiga na mummyn maya ta kwaso kayan laudry din sannan ta futo ta sauka kasa ta fara wanki.
Saida ta wanke tas gaba daya har ana kiran sallah kafin ta samu tayi sallah taci abunci ta fito backyard da littafinta tana karatu.
Motar da suka fita ne da isa ta tsaya a harabar gidan maya ta futo da kayanne shopping da yawa da mummynta tayi mata, murna take soaai ka kadan ba,bahijja ko dadi takeji ganin yar tata na cikin farin ciki.
Shugowa sukayi daga ciki babu kowa a kasan bahijja ta dubeta tace “ jeki sama bari na leka part din mami ko”
“Okay” maya ta bata amsa, saman ta wuce ita kuma ta futa.
Bata dade ba ta sauko kasan tana dube dube kafin ta wuce hanyar kitcwhn har zuwa bangaren su sabeeha,koda ta shugo cikin dakin babu kowa wannan yasa taji wani sanyi aranta.

Tana gab da futa daga dakin hadiza ta fito daga toilet.
“Subhanallahi nema kike baki ganni ba ko? Kinga wanka na shiga ne, ay da baki wahalar da kanki kin zo ba!!!”
Yaqi mayar tayi ta kalleta tace “inason fresh pineapple juice yanxu”
“Toh bari nazo nayo maki, shikenan ko akwai wani abun?”
“Ah ah babu shikenan” tana fadin haka ta futa da sauri.
Tana futa ta sauke ajiyar zuciya tare da smirking allah kadai yasan abunda ke ranta.

The next day!!!!
Tun daga ranar da abunnan ya faru sabeeha ke dari dari da al’amarin maya, wallahi badan dole ba bata son ma zama inuwa daya da mayar.
Bangaren taj ko yanxu babu abunda ke addabarsa kamar tunanin sabeeha, daga yaci ya koshi ya kwanta shikenan sai tunaninta saima tunanin ya zamana kamar yafi na da, yanajinta kamar tana kusa dashi jikinsa na bashi hakan.

Gashi ya kasa kiran khaal ya tambayeta akanta, inama zai iya, gaba daya neman ta ya rasa ta ina zai fara.
Wata dabara ce tazo mashi, mutun daya yazo ranshi wato salim, ya buqaci ya nemo mashi agencies din dake nan abuja dake kai domestic workers kasashen wajen, koda ya sashi nema mashi bai tsaya wani bata lokaci ba ya nemo masa few daga cikin waenda ya buncika.
Har gida salim yazo suka fita tare, daga ranar ya fara stepping forward wajen neman sabeeha, har zuwa lokacin kuwa hes guilty if abubuwan dayayi mata.


Anty bahijja nata faman shirye shiryen komawa gobe, duk yanda taso tafiya da maya kasawa tayi saboda karatunta da kuma fadan da sukayi da majeed dayace bai amince ta dawo da ita ba, kuma idan tayi haka batayi kara ba sam sam anne bazata ji dadi ba.
Dole ta hkura ganin kamar mayan ma bata nuna tanason binta ba don tasan washe gari zata tafi, dubaga yanda take ta son komawa chan abaya.

Shugowa maya tayi da wayanta a hannu ganin mummynta na shirya kaya yasa ta marairaice “mummy please karki tafi,ki bari bayi hutu aaimu tafi tare”
“Baby i can’t, inada aiki sosai i cant abandon mu duties kinji”
Shuru maya tayi batace komai ba har bahijja ta gama prepping kayan nata ta bude handbag dinta don kwaso jewlries dinta tasa a box dinsu.
Da mamaki take zazzage jakar surprisingly ganin bataga bangle din da dadyn maya ya saya mata ba,bangle din na diamond ne yawanci yana hannunta koda yaushe bata cika cireshi ba.
“Mummy are you looking for something”
“Yea baby bangle din dake hnnuna koda yaushe i cant find it”
“Wannan diamond bangle din? Diamond Bulgari?”
“Yes…bade saceshi akayi ba?” Maya tayi magana tana tayara duba kayan.
“I kept it here jiya kafin mu fita shopping”
“Hold on..jiya nasa yarinyar nan ta dauka min kayana anan badai ita ta dauka ba?”
“Wa kenan? Who would do such a thing a thing”
“Hmm daman ta taba sata a school wallahi mummy, definitely itace”
“Wacece ita din?”
“Wanna yar aikin mana fatima, ai wallahi saita futo dashi.
A fusace maya ta sauko kasa jiki na bari bahijja tabi bayanta tana kwalla mata kira.
Bata tsaya ko’ina ba sai bangaren su hadiza tana zuwa ta banka kofa kamar zata balla,
“Wallahil azeem saikin fito da diamond din da kika dauka barauniya”
Hadiza dataga shugowa tana tsaka da figar kaza tana ganinta ta miqe,”meya faru karamar hajiya?”
Sabeeha na daga zaune tana kokarin yin shimfidar kwanciya.
“Dallah yi mana shuru, idan ta sato ke zata kawoma ay wallahi bata isa ta dauka abun mummy na ba karyanku keda ita”
Ta soma buncike dakin nasu tana watso da kayansu, daidai nan bahijja ta karaso dakin tana maya, tana kicibus da hadiza ta tsaya, hadiza tayi saurin sakin kazar dake hannunta, bahijja ta hade rai sosai ba kadan ba kamar bata taba dariya ba.
“Mummy i told you…gashi nan gashi nan..”
Ta fada tana fidda bangle din, “a cikin nan na ganshi mummy”
Hadiza da abun kunya ya mata yawa bataso bahijja ta tsince ta a wannan yanayin ba na qasqanci.
“Daman na fada maki mummy yarinyar nan barauniya ce itace ta dauka ta kawoma mamanta, because she is jealous of me, tana jin haushi allah bai basu daukaka ba”
The fact that bangle din daga majeed ne kuma abune datake treasuring sosai yasa ran bahijja baci ta kalli sabeeha tace “ya akayi wannan yazo nan dakin?”
Jikin sabeeha ya soma tsuma tsoro ya bayyana a fuskarta abunka da someone that is innocent.
Hadiza ta cin mutun ya mata yawa ta rasa ina zata saka kanta ta dubi sabeeha tama kasa ce mata komai saida maya tace ,
“Mummy why would you ask, jiya nace taje ta kwashi laudry na a wanke propably ta haka ta samu damar dauka”

Sai a lokacin hadiza ta fuskanshi abunda ke faruwa ta dubi sabeeha “dan abu kaza kazan ki ya akayi abunnan yazo dakin nan eh????, banace karki sake ki jawo min abun magana ba”
Sabeeha data fara hawaye ta kalli maman nata tace “na rantse da allah mummy ban dauka komai ba, ban dauka ba”
Rufeta da duka hadiza ta soma yi kamar zata illata, “yau saikin fada min yanda akayi kika dauko wannan abu”
“Kibar dukanta” bahijja tayi magana tace “ay ba lallai laifinta bane qila tarbiyar da kika mata kenan”
Kai wannan abu yayi ma hadiza zafi sosai ba kadan ba, “maya lets go”
Suka fita gaba dayansu,hadiza ta dubi sabeeha tace “na rantse da allah gobe goben nan zan maidaki lafiya babu makawa, shegiyar yarinya haihuwar ki bata amfane ni da komai ba, fita ki bani

61 / 107