Advertisements
Chapter 6 Reading Matar Taj Book 2 Complete Hausa Novel Hausa Novels
Advertisements

Matar Taj Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Queenmerh Category :  Complete Novels

Chapter   6 / 107

15K to 18K   out of 320.4K words

ke kwance.
Kallonshi suka dungayi gaba dayansu, fadwa ce tayi saurin cewa “how i wish this will be his ending, i just canto stand him”
Dagowa hidaya tayi ta mata wani irin kallo kafin tace “if you cant stand him zaki iya futa”
“Wai ukty ban gane maki ba? Isn’t that what we all want?…na lura yanxu kina kokarin boye min wasu abubuwa, waye wanda tareeq ke magana akai? Sannan wani file suke magana akai”
“You dont owe me an explation, just get out!”
“Wallahi bazan fita ba saikin fada min ukty, what are you hiding? Meysa kike kokarin outing dina waje? “
Ganin yanda fadwa keyin ihu yasa hidaya taja hannunta suka fuce daga dakin ta jata har wajen motarta.
Suna fita nurse ta shigo dakin daidai nan ya soma bude idanunshi ahankali harya budesu gaba daya tarrr yana kallon ceiling, kanshi wani irin nauyi yake mashi har zuwa lokacin, nurse din na lura da shi tayi saurin futa daga dakin ta wuce wajen doctor lokacin yana tare da sabeeha itama ta farfado,
“Sir the other patient ya farka yanxu”
Sabeeha najin haka ta tashi zaune, sai kawai taji gabanta na faduwa, doctor na ganin haka yace mata “maam you need to rest”
“Dan allah ku barbi naje na ganshi,dan allah, i need to see him please”
Ganin yanda ta damu sosai yasa doctor ya yarda suka fito harda ita suka nufi dakin taj din, har zuwa lokacin gabanta baibar bugu ba sosai, doctor ne ya shiga kafin ta sanya kafarta cikin dakin, a zaune yake ya hade hannayeshi a kirjinsa, budo kofar da akayi yasa shi maida dubansa ga kofar, har idanunsa ya sauka kan doctor, sabeeha data hangoshi zaune cikin sauri ta karaso insa yaoe batayi wata wata ba kawai ta rungumeshi tsam a jikinta, bugun kirjinta na sauyawa “didi, didi are you okay? Meke damunka ? Hope bakaji ciwo ba, im so worried about you,?” Ta karashe tana fitowa daga jiki shi ta kama kafadarshi tana dubawa, kafin ta maida hannayenta kan fuskanshi tace, “talk to me didi? Talk to me please meke maka ciwo”
Yanda yake kallonta haka take kallonshi, gaba daya ya zama so confuse, WHOS THIS? Abunda yake tambayr kanshi kenan, how did i end up here? Yadai tuna suna cikin mota har sukayi accident dalilin yowa kansu da truck dinnan tayi daga nan he can’t remember ya akayi ya shiga motarma, sai yabxu daya bude idanunshi yaganshi anan.
Hannunta data dauka akan fuskanshi ya kama duka da hannenshi ya cire daga kan fuskanshi, fuskanshi a hade kamar bai taba dariya ba babu wasa ya dubeta daga sama har kasa ya bude bakinsa cikin isa da aji yace “Who are you????, what give you the audacity to touch me?”
Dam gaban sabeeha ya bayar, yanda yake magana da yanda yake kallonta gaba daya ya sauya, his tone was very harsh and hard at the same time, sai kawai ta sandare tsabar mamaki, yau didi ne ke tambayar wacece ita? daidai nan aka turo ko hidaya ta shugo,
“I said who the hell are you?” Ya daka mata tsawa wanda yasa jikinta ya soma tsuma, ba sabeeha ba hatta hidaya data shugo gabanta ba karamin faduwa yayi ba jin yanda yayi magana,
Jikin sabeeha na bari gashi ya kama dan hannunta sosai ya rike gam, take taji wani irin tsoronsa ya durar mata,batama san lokacin datace “didi nice fah ni ce bibin ka? Why are you like this”
Yana kallon hawaye na sauka akan idanunta amma bai saki hannunba saima danqewa daya sakeyi yace “can someone explain whats going on here, why I’m i here, who’s this??”
Tuni jikin hidaya ya soma tsuma, dagowar da zaiyi kuwa ya hangota daga bakin kofa, baima san lokacin daya saki hannun sabeeha ba yace “first love…”
Yanda ya fada saida gabanta ya bada wani dammm, muryar shi Nayin amo, at that moment jikin hidaya ne kawai ke dawainiya da ita badai hankalin ta ba don hankalinta ya gama barin jikinta gaba daya, ko ba a fada mata ba she can tell ya dawo hayyacinsa, he has regain his memory…….



✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊

MATAR TAJ (destined with you🩵🤍)
Written by
Queenmarh✍️
Book2
PAID
Chapter 60

Update!!

Yanda ya fada saida gabanta ya bada wani dammm, muryar shi Nayin amo, at that moment jikin hidaya ne kawai ke dawainiya da ita badai hankalin ta ba don hankalinta ya gama barin jikinta gaba daya, ko ba a fada mata ba she can tell ya dawo hayyacinsa, he has regain his memory…
Gaba daya daga sabeehar har doctors din dake tsaye da nurse duk mamaki sukeyi, doctor ne ya karaso inda yake zaune yace, “calm down sir,”
“Why should i calm down? I fucking need an explanation, and who’s this? Wace wannan”
Yayi nuni da sabeeha, tunda ya fara magana jikin sabeeha ya soma tsuma,
first love!” Ya sake kiran hidaya datayi tsaye gaba daya hankalinta ya gushe saida ya sake kiran sunanta kafin ta farfado, ta ma kasa yunkurawa saboda yanda kafafunta suka sage, meke shirin faruwa kenan? Badai abunda take tsoro bane ke shirin faruwa? Hankalinshi ya dawo?”Tambayar da take ma zuciyarta kenan aranta, da yake a bude tabar kofar lokacin data shugo cikin dakin wannan ya bama fadwa data biyo bayanta damar jin duk abubuwan dake faruwa kuma tabbas muryar taj din taji, don haka itama ta shugo tayi sake tana sauraron yanda yake magana.

Dakyar hidaya ta tako zuwa inda yake kafafunta na janta, don ta tabbatar da zargin da take, tana karasowa ta kama hannunshi cikin nata dake ta faman karkarwa yanda yake kallonta haka take kallonshi, gaba daya ya zama confuse ganin yanda suke kallonshi kamar yau suka fara ganinshi, ga sabbin fuskokin da bai taba gani ba a gabanshi, banda hidayar daya gani a tsaye don ko lura da fadwa baiyi ba.
Tana riqe da hannunshi ta soma magana,”big baby!”
“Yes first love,” ya amsa ta
“I can’t believe this, ka tuna komai yanxu? You remember everything?”

Da mamaki yake kallonta ganin yanda take magana surprisingly, “did something happen to me? Meysa kuke kallo na haka? How did i end up here?” Yanda ya karashe zaka gane hankalinshi a tashe yake, yayi wani irin jaa lokaci guda,gaba daya a cikin duhu yake babu abund ayake nema sai karin haske, ganin yanda hankalinshi ya tashi yasa doctor ya soma magana, “sir you had an accident few hours ago, you were rushed to the hospital kaida wann…”
Saurin dakatar da doctor hidaya tayi tace “Alhamdulillah alhamdulillah!!!!! You’re awake finally” tana karashewa ta rungumeshi tsam a jikinta, “oh my god! Big baby, youre back, this is unbelievable”
sabeeha sakqe tayi tana kallon sabon drama da take shinfida tana kallon ikon allah, fadwa kuwa juyawa tayi kafafunta na karkarwa ta fuce daga dakin, she can’t believe abunda kunnuwanta ke juyo mata, hankalinta ba karamin tashi yayi ba, tama rasa wa zata kira a waya a daidai wannan lokacin, afiya ce ta fado mata arai tayi saurin dialing number ta, saida ta kirata kusan sau uku kafin ta dauka, kamar ma daga barci ta tasheta cikin fada tace “why are you calling da safiyar allah nan dan allah, its 6am here in dubai”

“Afiyaaa!! Listen to me, shikenan komai ya lalace”
“Me kike nufi?”
Jikin fadwa har tsuma yake wajen furta,
“ Hankalinshi ya dawo, he has regain his memory”
Zumbur afiya ta miqe zaune, babu wani kayan arziki a jikinta tace
“What do you?,”
“Are you stupid ne? Bakiji me nace bane? Hankalinshi ya dawo he has regain his memory,”

“Na shiga uku” afiya ta fada hankali a tashe kafin ta tari nunfashin fadwa ta cigaba “shikenan… daman ni nasan za ayi haka saida na fada maku lets end him once and for all kuka tsaya, kuna wani kwana kwana, now what if he remembers everything? How we treated him, shikenan…shikenan, we have lost all, wallahi we can’t compete with him,”
Wani irin dogon tsaki fadwa tayi tare da kashe wayarma gaba daya, afiya is not helping d matter kwata kwata
Wayar na tsinkewa afiya ta miqe hankalinta a tashe ta wuce dakin sonata, ta soma banging kofarta,…

Komawa cikin asibitin da fadwa bata sake ba kenan ta shige motarta tabar wajen.
Chan cikin asibiti kuwa, taj na daga zaune yayi saqe yana sauraron hidaya, ganin tana kame kame yasa shi maida dubansa ga calender dake gefen gadon da yake zaune “wait what?? 2023?? Yaushe muka kai 2023? Was i in coma or what?”

Doctor ne ya tari nunfashi sa wajen cewa “sir please you have to calm down first, lets observe you firs, zaka iya tuna last activity da kayi?, i mean inda kaje ko something that you’ve been up to?”
Shuru taj yayi yana kokari tunawa chan kuma ya kama kanshi dake sara mashi yace “i just got into my car, was driving then…then”
Ya dan dakata ya kasa karashewa saboda wani irin Dummm da yaji kunenshi yana mashi, take wani memory din yayi mashi flashing,daya faru lokacin daya masu amnesia,hankalinshi lokaci guda ya sake tashi don kwata kwata he can’t recall sanda hakan ta faru dashi, abu yanda kasan a mafarki haka yake ganin komai, ganin haka yasa hidaya saurin cewa, “hey look at me don’t over think your self, karkayi tunanin komai, ka kwantar da hankalinka i will explain komai idan muka je gida, banason wani abu ya sameka okay?”

Shi Kwata kwata baya jin abunda take fada ma saboda wani hajijiya daya dunga ji, yanda kanshi ke mashi wani dumm, dan dole ya koma ya kwanta kan gadon, yana mai dafe kanshi.

Duban doctor hidaya tayi tace “za a iya sallamarshi yanxu?”
“No ma’am we can’t do that, akwai necessary test da ya kamata ayi mashi,musamman yanxu dana lura kamar he can’t recall yanda akayi yazo nan, and it looks like kamar ya mance da wasu abubuwan it can be a result of shock due to the accident ko yanada wani issue ko lalura kafin ya samu accident?”
“I don’t need any fucking test, Bakaji me tace bane? Dişcharge me right now!”

Ya daka ma doctor tsawa, yanda yake magana daga gani yanada temper, hidaya najin haka ta tabbatar kwarai hankalinshi ya dawo jikinshi he’s back,take taji wani irin sanyi a ranta dukda fargabar da take ciki, agabanshi bata magana daya a musa mata,thats the level of respect he has for her,for now burinta daya kawai ta fiddashi daga asibitin karsu gano wani abun, idan har suka gano to tabbas shima likitoci zasu fayyace mashi komai, wanda hakab zai zame mata babar matsala, don he will suspect her, and he will be disappointed, wanda bazata taba barin hakan ya faru ba, tunda ya dawo yanxu dole tsarin plan dinta ya sauya, she can’t lose to him never…don haka ta tattara duk wani kuzarin daya rage mata ta dubi doctor tace“Can we talk privately about this?”
“Yes” doctor ya amsa ta kafin ya dubi nurse yace “prepare for QR test immediately”
“Yes sir” ta amsa shi kafin su fice gaba dayansu, sabeeha na daga tsaye kamar gunki, tayi saqe kamar wanda aka kwashewa ruwan jikinta, kanta a kasa ta kaasa dagowa ta kalleshi,sai hawaye dake tsiyaya akan fuskanta,har suka fice bata motsa ba daga inda take.

Gaba daya jikinta yayi sanyi kalau,dakyar ta iya dago fuskanta ta kalleshi, ganin ya runtse idanunshi sannan ya dafe kanshi yasa ta sauke kanta kasa, tana tuna yanda yayi mata dazu,babu abunda take sai nazarin komai abunda ya faru ayanxu, yanda yake magana tabbas haka ya tabbatar mata ya dawo hayyacinshi, allahu akbar, yau adduar ta amsu, ya dawo hayyacinshi, kullum fatan allah yasa ya dawo hayyacinshi, abun yazo mata a bazata lokacin da bata taba tsammanin haka ba , ta wani bangaren cikin zuciyarta kuwa fargaba take sosai, sai tsoro daya cika mata zuciya, kamarma bai ganeta ba? Yanda yake kallonta dazu tana hango tsananin furgici akan fuskarci, yana mata kallon wadda bai taba sani ba kamarma ya mantata gaba daya, “innalillahi wa inna ialaihi rajiun” ta soma ta soma furtawa yanayin bugun zuciyarta na sauyawa.

Taj dake kwance ya dafe kanshi babu abunda ke running a mind dinshi sai memories din dake zuwan mashi da bai san yaushe akayi hakan ba.

Hidaya na futowa tare da doctor suka wuce office dinsa, suna zama,ta soma mashi bayanin rashin lpy da taj yayi, sannan ta dora mashi da ya samu amnesia shekara daya da ta wuce around 2022 kuma yanzu tana kyautata tsammanin ya dawo hayyacinshi ne,kuma tana zargin ya warke, saida ta fayyace mashi komai daya danganci health record dinsa kafin ta buqaci a sallameshi da gaggawa, tayi hakan ne don hana doctor yayi wani dogon buncike.
“Inason a sallameshi kawai,akwai consultants dinshi da yake kula da progress dinshi they will take it from here”
“We will do that ma’am amma sai mun tabbatar bai samu wani injury ba daya danganci accident din da sukayi cause he’s our responsibility now”

Ganin doctor na neman jayyaya akan sai yayi bunciken health dinshi yasa tace “he doesn’t need any of that, idan ma yana buqatar hakan
Akwai neurologist specialist din dake managing health dinshi, saboda haka inason a sallameshi”

Dan dole doctor ya amince, aka bashi Referall sannan yayi discharging dinshi.

Sai a lokacin hankalinta ya kwanta ta fito, tana futowa ta nufi dakin da aka kwantar da taj din, har zuwa lokacin yana kwance ya dafe kanshi, bashida natuswa kwata kwata, sabeeha na ganinta kawai taji gabanta ya sake faduwa, tsoronta daya allah yasa ba wata qulalliyar ta qulla ba, karasowa hidayar tayi ta tsaya gabanshu tace “big baby! Muje gida”
Yana jin muryar hidaya ya miqe zaune dukda kanshi na mashi ciwo, cikin izza da sautin muryarshi mai dadin sauraro calmly yace “where’s my car keys?”
Shuru hidaya tayi ta daburce ganin ya kafeta da idanu, “lets go with my car”
Da taimakon hidayar ya miqe tsaye, daidai nan idanunshi ya sauka kan sabeeha itama idanunta ya shige cikin nashi, ganin yana kallon sabeehar har zaiyi magana hidaya ta dakatar dashi “muje”
Sabeeha najin haka ta biyo bayan su suka wuce parking lot inda hidaya tayi parking.
Hidaya ce ta bude mashi seat din gaba ya shige, sabeeha kuma ta shige seat din baya ita kuma hidaya ta zauna mazaunin driver, babu yanda ta iya dan dole ta umarci sabeeha ta biyosu don tasan tabbas saiya tambayi ko wacece ita bayan wannan ma dole yanxu she has to pretend saboda karya fuskanci komai.

Tunda sukabar asibiti Tsit kake ji a cikin motar, hidaya dai har zuwa lokacin ta kasa wrapping mind dinta, fadin irin tashin hankalin da take ciki ma bata lokaci ne, mafita kawai take nema, abun yazo mata a daidai lokacin da bata taba tsammani ba, sai a yanxu take dana sanin qin bin shawarar fadwa, abunda ke bata confidence daya ne ganin kamar bai tuna komai ba, saidai damuwarta daya ayanxu what if ya tuna ranar da accident din daya jawo mashi lossing memory for a year? Inaa bazata taba barin haka ba, dole she has to do koma menene don ganin bai tuna ba, she won’t allow him to remember that, idan ya tuna shikenan komai ya wargaje, bazatayi moulding dinshi yanda ta saba ba bayan wannan ma zatayi lossing yardar dayake mata for over those years, yama za ayi ta bari ya gane she’s behind all of this? No never, she will never allow that, he trusted her all his life, itace komai nashi, baya tsallake maganarta kuma bai taba ba koda sau daya ne kaf rayuwarshi, kuma ayanxu ma for the second time thats what she’s going to use.

Sabeeha dake zaune abubuwa da dama ke yawo a kwakwalwarta, sai ayanxu tunanin mutabb yazo ranta, ayanda taji wajen likitan dayayi attending dinsu ya shaida mata su biyu kawai aka kawo asibitin, fatanta allah yasa ba wani mugun abu ne ya sameshi ba.
Bayan wannan ta soma tunanin meysa ake binsu a baya kuma akeson kashesu? Su waye suke binsu a baya? Ko hidaya ta gano waye mutalib? Ita kadaice kawai tazo ran sabeeha a daidai wannan lokacin, kuma tasan itace ke nemansa, don mutabblib din ya fada mata da kanshi, gaba daya ta dauka mutuwa zasuyi data tuna yanda truck dinnan tayo kansu sai kawai ta runtse idanunta tunawa da yanda taj ya damqo hannunta a lokacin harya furta allahumma ajirninfee musibati, tabbas a daidai wannan lokacin ya soma dawowa hayyacinshi don bata taba jin yayi addua neman tsari ba, ko yayi magana irin ta masu hankali ba.
Tama rasa me zataji aranta, dadin dawowa hayyacinshi ko akasin haka?
Tana cikin wannan tunanin ta dago da kanta ta kalleshi, gashi dai taj din data sani ne amma yanxu sai takejin kamar bashi ba, saiya sauya mata lokaci guda kamar bashi ba, wani irin kwarjini da haiba take gani a tattare dashi, har zuwa lokacin idanunshi a rufe yayi relaxing akan kujerar gaba har suka karaso gida, da kafarshi ya fito daga cikin motar hidayar, yana fitowa yabi gidan da kallo, its feel strange to him sai yake jin kamar ya dade bai shugo gidan ba, zagayowa inda yake hidaya tayi tace “muje”
Gaba yayi hidaya na bunshi a baya,sabeeha ma ta mara masu baya.

Harya daga kafarshi zai shiga sai kawai ya dakata,hidaya fa gaba daya hankalinta a tashe yake yanxu da duk wani motsinsa, ganin yaqi motsawa daga inda yake yasa tace “muje ka huta”
Ta kama hannunshi suka shige daga ciki, suna shiga ya fara bin gidan da kallo, suna karasowa sitting room suka tadda ammu da tareeq da fadwa a zaune, sun sakata gaba suna sauraron labarin warkewar da taj din da yayi lokaci guda.

Ammu na ganin shugowarsu tayi saurin miqewa dukda tana jimamin mutuwar mijinta hakan baisata yi guda ba ta karaso insa yake ta rungumeshi sai hawaye, “allahu akbar allahu akbar, ina godiya ga Allah, oh my sweet boy you’re back? You remember me? Ka tuna ni?ashe dai zuwana yayi albarka, masha Allah yanxu hankalina zai kwanta,” ta karashe tana hawaye, taffin hannayenta na kan fuskanshi tana shafashi kamar yau ta fara ganinshi tsabar murna.

Da mamaki yake kallonta yana kallon su fadwa dake kallonshi harda tareeq, dukkansu ba karamin tashin hankali suke ciki ba, fadwa da hidaya sai kallon juna sukeyi kamar wasu munafukai.

Dakyar ya dake dukda yana jin zafi aranshi gashi ya zama so confuse da alamarin ya Dan rankwafo ya Rungume ammu tsam a jikinshi yana dabbing

6 / 107